Da Me Ake Ado Part 1 Complete Hausa Novel
By Sajida Niger
Book Page

Da Me Ake Ado Part 1 Complete Hausa Novel

Author: Sajida Niger
Paragraphs: 119
Starting position: 1
Reading position: 1 / 119
Listen Mode
Login and upgrade to premium to unlock listening.
Reader Top
Ad slot ready: reader_top

 DAME AKE ADO part (1) 1⃣Mahaukaciya yarmacukule mahaukaciya tasaci zare dandazon yaran da suka zagaye mahaukaciyar ke ihu suna fada yaukam adurkushe take tana kuka tarike cikinta sabanin canbaya da idan suna wannan wakar take rawa eyehuuh eyehuuh kuka takeyi yau babu rawa suka kakama fada suna ihu malam sulaiman dayake dosowa tundaga nesa yacika yacika dataikaicin yanda yaran unguwar suka takurawa matar dababu wanda yasan daga indatake kawai an wayi garine anganta a unguwar yadauko tsumagiya yayi kansu yafara dukansu sai suka watse sunaci gaba da ihu dawakarsu filin yazama sai ita kadai harlokacin tana durkushe tana kuka 2⃣ya isa gurinta yana fadin baiwar Allah tashi kitafi abinki kinjiko wayyo Allah cikina mutuwa zanyi maganar datafito daga bakin mahaukaciyar kenan wacce tasanyashi kara kallonta da mamaki dan tsawon wata tara dayasan matar baitabajin tayi maganaba saiyau kuma abin dayabashi mamaki baiwuce jin maganar tata yau irin tamutumin dayasan ciwonkasa baceba kafin yakai gacewa wani abu yakuma jin tace wayyo Allah zanmutu saiyaga jini yanazubowa ta karkashinta dasauri yace subhanallahi haihuwa ce zakiyi dandama tanada ciki wanda akezargin wanine yayimata akan bolar datake kwana tabayan gidan malam sulaiman din baiyi wata wataba yakamota dasaurinsa danjin kamar tana nishi ga yaran basu bar gurinba sai ihu suke tayi yaciccibeta yakaita soron gidansa dake jikin bolar ya tura kyaure 3⃣soron yanufi cikin gida dasauri yana kwalawa matarsa kira Deeje Deeje sukaci karo tana tahowa dasauri takalleshi lfy malam zomuje mahaukaciyar nan dake kwana akan bolar nan tajikin gidan nance babu lfy ina tunanin nakuda cetakeyi subhanallah muje mlm tafada atsorace sanda suka karasa soron tabbas nakudace takeyi bari nadauko zannuwa kirawo Lami acikin gidansu mama yanufi gidansu Lami wacce yakasance soro guda akeshiga cikin gidan matar kanin malam dince yafara sallama daga bakinkofar da zata sadaka da gida nasu

3⃣soron yanufi cikin gida dasauri yana kwalawa matarsa kira Deeje Deeje sukaci karo tana tahowa dasauri takalleshi lfy malam zomuje mahaukaciyar nan dake kwana akan bolar nan tajikin gidan nance babu lfy ina tunanin nakuda cetakeyi subhanallah muje mlm tafada atsorace sanda suka karasa soron tabbas nakudace takeyi bari nadauko zannuwa kirawo Lami acikin gidansu mama yanufi gidansu Lami wacce yakasance soro guda akeshiga cikin gidan matar kanin malam dince yafara sallama daga bakinkofar da zata sadaka da gida nasu

5⃣Allah zaitaimakeshi mlm din yafada cike da matsananciyar damuwa ko ajikinta wai antsikari kakkausa sai ma cewa tayi gaskiya saidai kayi hkr amman bazan iyatabataba abinda akace wurinda akahaifi shege ka taka kaida arziki har abada nidazakuji ta tawa ma aidakunfita daga soron gidanmu kada tashafamana talauci karabuda ita malam kaje kasamo mota akai matar nan asibiti zubar jini tayi yawa tafi don Allah kada ta mutu malam din yayi duru duru sannan yafice dasauri yajanyo kofar lami tayi tsaki takoma cikin gidanta tana cigaba da fadin Allah daiyakawo mlm wlh waje za.ayi da ita bazata goga mana talauci ba daman kulum anata fama sai anfita asamu dakyar ita dai Deeje kamo mahaukaciyar tayi dake tafadin wayyo cikina mutuwa zanyi 6⃣deeje tace kinga daina cewa wayyo kama salati ringa kiran sunan Allah Aikuwa cikin ikon Allah mahaukaciyar takama kiran sunan Allah dakarfi deeje tana rike da ita tadinga wani irin wani irin nishi saiga katon da deeje tace insha Allah sauraki mahaifa daure kiyi nishi kozata fado takama yin nishi da karfinta deeje tafara fadin subhanallahi ahankali zakiyi Amman ina yitakeyi da iyakar karfinta sai deeje takula ba ita takeyin numfashinba daga Allah ne kawai saigigice ta rude ganin mahaifar tafado jinin kuma yana bulbula kamar fanfo dakyar ta iya janyo yaron tayanke masa cibiya jin yana ihu daidai lokacin mlm sulaiman yaturo kofar yana fadin deeje gamai motar nan kota haihu ne cikin kuka take fadin shigo mlm shigo kaga halinda take ciki yaturo kofar yashigo kallo daya yayimata

7⃣hankalinsa ya dugunzuma yakama cewa da deejan kamota muje Asibiti deejan nakokarin kamata sai dai mahaukaciyar tariko hannunta tana fadin mutuwa zanyi kada kukaini asibiti kuwahala sunana Asma.u haki yakamata deeje takuma rudewa tana fadin innalillahi kifadi gidanku wacece ke maimakon ta iya cewa wani abu sai kalmar farko da deeje ta ambata ta innalillahi wainna ilaihi rajuun raiyayi halinsa talangabe anan hankalinsa deeje da mlm yayi matukar tashi deeje tafashe dakuka tanafadin mlm munshiga ukku hankalin mlm sulaiman yatashi jikinsa yaduki rawa duk yarudema yarasa abinyi deeje ce tace mlm kasanar da jama.ar unguwa sukawo mana 8⃣ dauki Allah yasani niyyar taimako mukayi mlm yanafadin dole saimun sanar da hukuma kulada yaron da gawar bari na je nadawo kafin takara cewa wani abu yabazama yafice tatsugunna tana kallon yaron daketa wutsil wutsil cikin zani kyakkyawa gwanin bansha.awa son yaron yafara shigarta Lami taleko tana fadin yaya tahaihu ne tayi turus cike da tsoro tana kallon mahaukaciyar saita dafe kirji tanaci gaba da fadin badai tamutuba deeje wane bala.i kuke shirin kawomuna wlh babu ruwanmu takoma dabaya deeje tadaga kai tana harararta ranta abace amman tagaza cewa komai don takaici 9⃣tana nan zaune tsawon minti arba.in tajiyo karar jiniya tamike jikinta yana bari jin datake bata taba shiga police station ba amma yau ga motar police harkofar gidansu tana nansaiga mlm sunshigo dayan sanda ukku kowanne dauke da bindiga daya dagacikin su yakalli mlm sulaiman yana fadi mlm katabbata abinda kafada shine gaskiyar magana wlh babu kari ko ragi Allah yana kallona mlm yafadi dasauri har lokacin hankalinsa tashe dansanda yagirgiza kai yana fadin duk dahaka zamu tafi dakai da matarka danzamuyimaku wasu tambayoyi deeje tawaro ido tana fadin nashiga ukku don Allah yallabai kayimini rai wlh bantaba shiga irin wannan 1⃣0⃣motarba yakatseta kada kidamu hjy bawani abu zamuyikiba tambayoyi kawai zaku amsa jiyo karar zuwan motar yankwana kwana suka kuma rudewa haka nan akasanya mahaukaciya deeje rungume dayaron suka fice daga gidan cikin rakiyar yansanda Lami tana labe tana lekensu ta kofa tana dariya tana ganin sun fice tafara fadin Allah yakara maganinku masu neman suna kenan banda haka daga ganin mahaukaciya tana nakuda har wani kinkimota kukawo kamar kukukafi ubankowa imani koda yake ai neman sunane kuma kunsamu tamurguda hannu ta tafa acinya tana juya idanuwa sanda suka fice jama.ar unguwar sun fito cirko cirko ana kallonsu kowa da abinda yake fada mlm jibrin yashigo gida fakan fakan cike da tashin hankali yana kwalama matarshi kira Lami Lami 1⃣1⃣DAME AKE ADO ......Tafito daga daki dasaurinta tanafadin mlm lfy wannan irin kiran kamar zaka tsagan dodon kunne yakalleta cike datashin hankali yace jinayi ance yansanda sunzo gidanmu sunyasheku gabadaya Anyi police station daku wai antsinci gawa agidan tarike kugu tana kada kafa A.a bakarya bane gaskiyane saidai ba.abaka lbr dai dai ba andaitafi dayaya da deeja dansu suka debo ruwan dafakansu kamar yaya kinanufin yanzu shi yayan da deeje suna can wurin yansanda? Dagaske kenan Ansami gawar kaibakacin ribar zance wlh katsaya nagayamaka yanda Abin yafaru mana 1⃣2⃣DAME AKE ADO Baikoma tankawaba hartasanar dashi duk Abinda yafaru tadora dacewar danhaka nibaganin laifin yansanda wlh sunyi daidai kokai yayakagani? Yadansaki rai yana fadin nasha gayawa yaya wannan halin nasa watarana saiyaja masa masifa gashinan kuwa mutum yace kofada yaga anayi saiya raba can yaje yakarata idan naga abin yayi tsananani naje nasarwa da Abokinsa mlm Habu bani ruwa nasha nakoma kasuwa yakarasa magana yana haki 1⃣3⃣DAME AKE ADO Malam sulaimai da deeje suna zaune agaban tebur din DPO kusan awannisu shidda kenan apolice station din DPO yadaga kai yakallesu shikenan malam tamutu kada kadaina taimako domin ladanka yana gun Allah yanzu zaku wuce dayaron gobe zamu turo wasu jami.an namu zasu amsheshi amikashi gidan marayu Allah yasaka da Alkhairi Ran mlm yayi fari yamike daidai lokacin damatar tasa ta mike itama tana fadin babu damuwa ranka yadade dahaka sukabar ofis din deeje tana rungume da yaron suna isa gida deeje tadora amurhu tawanke yaron tas wanda yayi kuka haryagaji malam yasamo zam zam da 1⃣4⃣ DAME AKE ADO ...Dadabino akabashi yasha sannan ya kuma yasiyo madara irin tagari akajika masa da ruwan zafi yasha saigashi yakama bacci Auwalu da sani diyoyin deeje sai murna suke wai ansiyo musu yaro akasuwa sun sami kani mahaifiyar tasu dariya kawai take musu tana rungume dayaron dayake kuma shiga ranta duk bugun dakika mlm yadawo daga masallaci yataddata rungume dashi yayi dariya yana fadin Deeje uwa kenan ki ajiye dannan koyafijin dadin yin bacci tayi dariya tana kwantarda shi agado tace wlh mlm jinyaron nake kamar nice nahaifeshi yayi dariya yana zama sallamar malam jibrila daga bakin kofa takatse musu hirar tasu mlm sulaman yatashi dasauri ya leka yana fadin jibrilu yaya akayi ne? Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part2. Jibrila yagyara tsayuwar sannan yace wani lbr nakeji yanzu gurin Lami danadawo wai ankaiku police station amman yaya ka kasa aikawa agayamani ai da na biku naji abinda yafaru yayi dan yake yana fadi gani nayi ba wata babbar bace ba shiyasanya ban Aiki maka ba amman yanzu komai yawuce da izinin Allah to Aishikenan Allah yakiyaye gaba amman dai yaya karage halin nan naka watarana zai iya janyo maka adaureka mlm sulaiman yayi murmushi yana fadin kayya duk Abinda da Allah yakaddarowa bawa babu makawa saiya sameshi Amman kuma dai yaya ance gidan da aka haifi shege masifu suna sauka acikinsa yanzu baka gudun abinda zaije yazo madaukakin mamaki yaziyarci mlm sulaiman yadinga kallonsa baki bude da ................. Dakyar yadaure yace A wanne hadisin ko ayar kaci karo da wannan batu Ya kama sosa keya na rashin madafa yasan halin yaya nasa sarai zai iya yimasa wankin babban bargo dan haka ya wuce dasauri yana fadin aishikenan Allah dai yasa ruwan sama yawanke mana daudar yabishi dakallo har yakule sannan yaja tsaki cike da taikici yakoma ...Dasafe tun Asuba Deeje tadora ruwan wanka ta wanke yaron tas tasanya masa kayan jarirai mlm yashigo tana rungume dashi tana bashi madara a filinboti ya kama kuwa yata zuka yakalleta tana dariya yace tomasu amsar yaron sun iso kishirya muwuce akaishi tadaga kai takalleshi nandanan hankalinta yatashi yakula dahakan danhaka yayi sauri yadauke kansa yafice GIDAN RAINON YARA Ankammala duk rubuce rubuce da dakaura hotuna harda na gawar Asma.u mahaukaciya mlm da deeje zaune gaban shugabar gidan tana tana musu godiya takirawo wata cikin ma.aikata data amshi yaron wanda harlokaci deeje take kankame dashi dan angama bincike ta goyeshi abaya ma.aikaciyar jinyar tayi tsaye kikam tana jiran deeje takwanto yaron amman taki mlm sulaiman yadan zungureta yana fadin kwantoshi mana deeje sai tamanne kafada suka zubamata ido da mamaki sai kawai tafashe muru dakuka mamaki yacika kowa agurin shugabar gidan takasa magana tana kallon ikon Allah koda yake takula dayanayin deeje tunda suka shigo bakuma yaune tafara ganin irin hakaba saidai amatsayinsu na.ama aikata bazusuturawa mutum da baisanya kansa ba dangudun azabtarda yaron nidai dan Allah Abarmini yaron nan tunda kunada su dayawa mlm sulaiman yadibeta damamaki Allah yasani abinda keransa kenan amman kuma baisaniba ko anayin hakan ba shugabar Hjy Amina tayi dan murmurshi gami da komawa takwanta jikin kujerarta tana fadin daina kuka malama deeje zamu iya barmiki yaron nan saidai akwai wasu sharudda da zamu gidayamiki 1⃣9⃣ wlh nayadda da duk sharadin da zaku gindayamani takatse shugabar cikin hanzari Atake anan shugabar tagindaya musu sharadin amsar yaron suka amince harda sanya hannu a rubuce sunrabu da shugabar akan duk wata guda zasu dinga kawo yaron anaganinshi da haka sukayi sallama cike da jin dadi suna tafe ahanya deeje takara kankame yaron tna dariya kai mlm da.ankwace yaron nan dasainayi jinya yaron dashi rai yake wlh yayi dariya yana fadin ke kam da baki taba haihuwa ba da anshiga ukku kin kankame yaro kamar zaki maidashi ciki to barka da mlm wane suna zakasanya masa kuwa Ta tambaya Aubakiji sunandana fadi gurin cike takaddunba koda yake lokacin kin rude aitinjiya da daddare nayi masa huduba da AHMAD 2⃣0⃣ idan Allah yakaimu ranar sunansa ta zagayo sai ayanka hakika ayi radin sunan A masallaci gurin shayawar ne dai nake tunani yanda za.ayi tunda kina dauke da cikin wata ukku bamu sani ba ko zaiyiwu kishayar da shi amman dai matambayi malaman Asibiti tayi ajiyar zuciya kuma kaga na shekara ukku rabona da haihuwa sai dai mu shayarda shi madara siyo madarar shanu yakama ka kenan kullum tana dariya to yaya na iya tunda Allah yabani da haka suka isa gida cike da nishadi lami tana jiyo sallamarsu takwasa da gudu tana lekowa sam basu kula da itaba tarike haba cike da mamaki ganin sun dawo dayaron abayan Deeje dan haka takuma tabbatarwa har cikin gidan taleka taga sunata shigowa dakayan arziki wanda hjy Amina tahado su da shi tayi musu Alkawarin zata dinga zuwa tana dubashi 2⃣1⃣ don Ta amshi Adireshinsu duk da sunce zasu dinga kaishi din sanda jibril yadawo yatadda Lami a cunkushe ya tambayeta abinda ya faru saita fitittike tana fadin sai dai azabi daya azaman gidan nan ko ni ko shegen yaron can sunfa dawo dashi dayaya zamu yadda murayu da shegen a gida yagyara tsayuwa yana kankance ido don Allah kada ki gaya mini zancen banza inace da safe suka tafi da shi kina nufin sun kuma dawowa dashi tagalla masa harara to zanmaka karyane ka shiga gidan nasu kagani mana kuma da alama da shirin zama ya dawo don nagansu da siyayyar kayan jarirai kala kala ya shuri takalmi cikin bacin rai yayi gidan yayan nasa ko sallama babu suna tsakar gida azaune deeje tanayiwa Ahmad gashin cibiya 2⃣2⃣ Malam sulaiman yadaga kai ya kalleshi da mamaki yana fadin lfy dai jibrilu kashigo babu ko sallama yasamu guri yazauna yana muzurai ramsa abace yace kayi hkr yaya rainane abace nashafa.a jinayi ance wai kadawo dashegen yaron nan me kuma yadawo yi? Ransa yabaci amman yadanne yace ba shege yakeba sunanshi Ahmad kuma yawuce wai tunda hargashi nan kana gani ana masa gashin cibiya haba yaya wanne irin tonon siline saikace baka taba haihuwaba idan karin ya'ya kakeso basaikaje kadauki nawaba ko kuma kaje kauye kadauko wasu ba Amman saika bige da dauko shege nagayamaka kada kakuma kiransa da shege kajiko kuma naki daukar naka dan ko kuma nakauye shidin dainakeso idan kuma kaine sama dani sainaji marar kunyar banza ..........2⃣3⃣ irin naka duk wani abu dazaka aikata na Alkhairi saiyazamana kaidashi kake gaba wannan yaron kasan iyakacin baiwar da Allah yayimasa to tsaya nagayamaka daga yau yashiga cikin 'ya'yana zan kuma rubuta wasiyya ko bayan na mutu araba dukiyata kashi shidda Abashi kaso daya don Allah baihalasta Wani yagaji wani bane ba danace yagajeni jibrilu yayi shiru cike da takaici don yasan halin yayan nasa akwai fada idan kataboshi danhaka yamike sumi sumi yang fadin Aishike nan nidaman inaguje maka illar da akace zama da shege yana kawowa ne inji ubanwa aihar yau kakasa kawo mini hadisi ko ayar datace hakan nakuma gayamaka kadaina Ambaton dana Ahmad dashege kajiko yakarasa ficewa yana gunguni babu yanda zaiyi 2⃣4⃣ malam sulaiman yacigaba dafada sokon yaro sai mace ta huroka kazo kana yiwa mutane fiffika daga ganinka wannan bara.ayinka bane ba matarce taroshi shakiyiya kawai deeje takwantar da murya tana fadin karabudashi Lami kam saidai Ayimata Addu.a matar da yaran gidan bata bariba balle wannan mudai Allah yarayamana shi cikin Albarka yakoma gida cikin borin kunya yatadda lami tsaye tana jiransa yana shiga tatareshi yaya kukayi dashi? Yasamu guri yazauna yana dafe kunci yayi tsaki yana fadin bakiji yanda yabalbaleni dafadaba kamar wani ubana harfa cewa yayi bazairike dana kona wani dangi sai wannan shegen ke har doka yakafa min waina kiransa dashege ma tayamutsa fuska tana fadin maganinka kenan mara zuciya saunawa nake gayamaka kadaure kayi gidan kanka muhuta da mulkin mallaka dan wannan dakin biyun dayabamu ke rudinsa dayasanan kana da iko agidan aida baiyimaka haba saikayitayi kada ka mallaki nakanka kayita zaman karoro 2⃣5⃣ Ahmad yataso yaro maicike dakwarjini da hikima da basira wanda kowa ke kauna. Duk inda yazauna zakaga ana sonsa iyayensa suna nuna masa gata kullum yana cikin yan uwansa suje islamiyya da dare kuma suzauna kofar gida saida rake ko mangwaro saidai tunda yatashi ya kula da tsangwama da kyarar da Lami da mijinta ke masa ga wani suna dasuke yawaita kiransa dashi shege amman yakula har sauran yayyansa da kanne Lami bata kauna saidai sanda yayi shekaru ukku yagano azabarta ko ahanya suka hadu saita rankwasheshi musane abokinsa a gidan kuma sa.ansa tasu tazo daya sauda yakanbishi gidansu wasa kamar yanda shima yake biyoshi amman duk sanda yabishi saita azabtar da shi har wuta ta tabawatsomasa wata rana kuwa ta kulle abandaki wai wuni guda mamanshi na nema har kuka tafarayi tadinga zagaye unguwa sai gab da magriba ta hankodoshi yasha kuka majina damiyau lokacin yanada shekaru biyar sanda mamansa tagansa tarungumeshi tanafadin 2⃣6⃣ Ahmad dina inakashiga kaida nasanka bakada yawo cikin muryan kuka yake fadamta innarsu musa ce takulle ni abandaki wai saina shaki kashi namutu narasa abinda nayimata ta tsaneni Ummata kigayawa baba yasake mana gida mana tausayin yaron yakamata tasha bala.i da Lami akan yaron tun yana da wata ukku da Auwalu yashiga dashi tashaka masa ruwan kumfa ahanci har kusan dambe sukayi tundaga tadaina baiwa kowa danta ga tirtsetsen cikin haka zata goya abinta haryayi shekara ukku saita ajiye kaninsa Rabi.u tasungumeshi abaya don haka rigimar tayi sauki yanzu kuwa yawuce goyo duk irin tsakanin mlm dayimusu takiji hakanan dai rayuwa taci gaba da gudana cikin wahala da azabar Lami shidai jibiril baya dukansa Amman baya ko kallonsa don yace masa baffa saiya dokamasa harara yau ummansa tadawo awo abakin Asibiti saita siyowa kowa kayan sanyi da mlm yabata sallahu duk tashi tafi kyau don hoton dan bal din nanne maradona daman shi yana da son bal don haka yasuri tashi yayi waje da gudu kai tsaye gidan jibril yashiga yana kwalawa abokinsa musa kira musa yafito daga daki aguje mahaifiyarsa na kwalamasa kira Amman baitsayaba saida yadangana datsakar gida inda Abokinsa Ahmad ketsaye cikin farin ciki da dariya Ahmad ke daga masa rigar yana fadin kalli yaro babanmu ne yabaiwa umma kudi tasiyowomuna kalli harda maradona ajiki shugaban yan kwallo duk randa zamuje filin bal da ita zani kaikuwa bakada ita musa yatsaya turus cike da takaici saiya saki kuka mahaifiyarsa tafito daga daki dasaurinta tana fadin tsinanne shege dukanka yayi ko? Yagirgiza kai yana fadi a.a badukana yayiba riga babansu yasiyo masa maihoton maradona zai dinga yin ado yanafina kyau nadaina zuwa filin kwalloma adaki zandinga zamana jikin Ahmad yayi sanyi yakalli abokinsa yamika masa rigar yana fadin kada kadaina zuwa don Allah garigar tawa kadinga Ado da ita yamika masa saidai tuni mahaifiyarsa ta warce tana fadin Banza soko aibada riga ake ado ba kaga wannan tanuna rigar ana saidata akasuwa da uba ake ado wanda shikuma ba.asaidashi akasuwa kasha kuriminka wata rana ko rigar gwal da zinare yasanya yafita saiya tsani kanshi don baida rigar Ainihi ta mutunci tawurgawa Ahmad rigar tanacigaba da fadin dauki tsiyarka kawuce shegen banza watarana zakagane Abinda nake nufi hankalin yaran gabadaya yatashi duk basu fahimci komai azance ba yakwasa da gudu ganin tayi kansa da ice gadan gadan saida ta kaishi har babban soro sannan takoma yanufi gidansu jikinsa sanyi kalau yana hawaye Ummansa tafito daga daki dazummar dora girkh taci karo dashi zaune shiru gabanta yafadi don tasan yarone mai kazar kazar da wasa tabbas bashida lfy takara dasauri tana kiran sunansa manya yaya na ganka anan zaune shiru meke damunka yadaga kai yana kallonta idonsa yakada yayi jajir saita kuma rudewa tace gayamini meyake damunka cikin shashshekar kuka yace innarsu musa ce takoroni don naje nunama musa rigar da babanmu yace kisiyomana tayi ajiyar zuciya wato dai bazaka daina shiga gidan nan ba kadaina kajiko yadagamata kai Alamar to sannan yace Amman idan musa yakwalamini kira indan leka amman kada nashi dakinta ko? Abin yaso bata dariya wata irin shakuwa ce tsakaninsa da musa wacce bazata iya rabasuba dan Allah ne yahadasu da daddare suna barbaje atsakar gida suna cin abinci cikin tsakiyar hasken farin wata tuwone da danyar kubewa wacce tasha kifi Ahmad yakai katuwar loma bakinsa yahidiye tadakyar yakalli Ummansu tasu yana fadin Umman wai meye shege ne? Gabanta ya yanke yafadi matuka tawaro idanu waje ........... Cike datashin hankali can kuma saitayi saurin dakewa takwantar da murya tace banace kadaina tambaya irin wannanba Ahmad meye Amfanin wannan tambayar inace a makaranta malaminku yace kudaina tambaya akan duk wani abu dabayada Amfani gabadaya duk tarude jikinta har rawa yake ganin haka yasanya shima hankalinsa yatashi don baya son yabatawa ummansa rai yace kiyi hkr umma nadaina daman innarsu musa ce naji kullum saitace mini shege canake ma suna ne Ashe magana ce mara kyau ma takuma Rudewa tace kadaina damuwa idan tace haka idan akace da mutum shege aiyayi wata gwaninta ne yayi dari.a yana fadin natuna har kika hanasu cewa hakan ko? Tace yauwa yarona ashe kagane ka daina damuwa idanta kuma cemaka kuma kada na kuma jin kalmar abankinka kada kuma ka tambaxi wani ko malaminmu tunda kaga nagaya kako yace to umma bazan kuma tambayaba sannan yacigaba dacin Abincinsa tayi wawiyar Ajiyar zuciya cike dafargaba saitaji duk Abinci yafita daga kanta magabadaya tabbas dole mijinta yadauki mataki akan wannan abin idan bahakaba saidai tabar gidan da yaranta dantayi Alkawarin har abada bazata gayawa Ahmad wayeshiba saboda hakama tunyana dansheka ukku tadaina kaishi gidan rainon yara shugabar makarantar ce kezuwa taganshi har gida har sanda tabar aikin agidan rainon yaran takanzo ganinsa saboda tana masifar sonsa itama hartadinga danasanin barinsa agurinsu din gashi babu damar ta amsheshi a lokacin dadaddare duk yaran sunyi bacci ta tashi maigidan nata wanda shima haryafayin bacci yatashi cike da mamaki da fargaba don tun dayamma yaga ranta abace nakula tunda maraice akwai wani Abu dakike boyemin to kinshiya fada kenan yanzu tafashe da kuka tana fadin aidazun mabakin gaya maka haka kawai ba sai don gudun kada yaransu ji Abinda zamu tattaunawa to wallah nagaji dazaman gidan nan na.amince kakamini haya da masifar da ake shirin kunno mini saita kara fashewa da kuka batunyau ba nake sanarda kai irin azabar da matar nan takeyiwa yaron nan Ahmad ba har Abin yakai nadaina sanarda kai toyau takai har Lami kenunuwa Ahmad shi shege ne bazan yadda ba Allah wannan neman masifa ne dason tozartani Hankalin mlm sulaiman yatashi yadinga fadin subhanallahi garin yaya hakan tafaru tasan kuma doka ce nasanya agidan nan tunba yauba ko mijinta nace yafadi wannan maganar zamuraba gari dashi 2⃣9⃣ DAME AKE ADO ....... ........... Dasassafe yatura yaran makanrata safe kamar yanda suka saba duk Ranar Assabar da lahadi da babu boko saisu tafi daukar darasi amasallacin Unguwar kaitsaye suka shiga gidan jibiril sunyi sa.a kuwa yaran gidan suma sunfice sai matar gidan zaune akan tabarma suna ta hira suna jin sallamar su mlm suka daga kaida mamaki dominsunsan baya shiga gidansu saita baci jibril yamike yana fadin A.a yayane sannu dazuwa zauna mana yadaga hannu yana fadin ba wannan takawoni ba gargadi nashigo yiwa matarka duk da nasan kasan duk abinda take aikatawa to wlh ahir dinta hawainiyarta takiyayi ramata Lami ta dafe kirji tana fadin nikam nashiga ukku nazama shara komai aka kwaso sai ayaba mini yanzu kuma nayi..... Rufemin baki marar kunya banza aikinfi kowa sani Abinda kikayi waike danbakida mutunci harkike tsare yaron nan Ahmadu kina masa habaici dole duk saiyasan shiba mune iyayensaba ko? Lailaha ilallahu nidin wlh sharri akemin yaushe nataba tareshi nagayamasa wannan maganar kuma? Yakalli deeje yana cigaba dafadin gayamata duk abinda tafadi tasan ya dawo kunnenmu deeje tamaimaita duk Abinda Ahmad yasanar da ita har shegen datake cemasa sai lami tayi wuki wuki babu kuma bakin magana dontasan tafada yanda kuma suka tsara sai take tunanin ko deejen taji nema

ABDULLAHI YUSUF MAITAMA 09034598552

9 April 2015 at 07:24 · Public Save · More Like React Comment Share Like55 Write a comment...

· Saihanatu Umar Umar mungode sosai Like · React · Reply · More · 28 Feb 2019 Fatima Bintu Mohammed thanks allah yasaka Like · React · Reply · More · 21 Mar 2018 Sadam Yusuf Ana wata gawata Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Muhammad Layya Misau Ina gai suwa yusuf maitama Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 El-aliyu Hudu Mairafi Tnkx Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Usman Mustapha Muna Godiya Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Dauda Yahaya Masanawa MADALLAH Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Ayshee Mohammed 8 Like · React · Reply · More · 14 Apr 2015 Abubakar Ibrahim Godiya ba adadi Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 Ukashat A Abbakar thnks alot 1 · Like · React · Reply · More · 9 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books -------> DAME AKE ADO part 3.

3⃣0⃣ Malam sulaiman yace to yaya koharyanzu sharri ake miki eye? Mijinta ya amshe don Allah yaya kayi hakuri kuskurene akasamu kuskuren gidanku nace kuskuren gidanku tun yaro nan yana wata guda matarka ke cutar dashi yanzu kuma abin yanzu kuma abinda zata koma yi kenan idan kinkwantar da hankalinki watarana zan sanarwa Ahmad wacece mahaifiyarsa kodon yadinga yimata Addu.a ma amma sai sanda ya mallaki hankalin kanshi yatara iyali yasami wadanda zasu debemasa kewar danginsa amman ayanzu banshirya sanardashiba don banason hargitsa masa rayuwa yakasa karatu da.anfanar rayuwarsa idan kuma bazaki daina ba zan saida gidan mukoma haya kowa ma yahuta don daki salwantarda rayuwa Ahmad gwara na kare rayuwata ahaya har Abada kana jina yanuna jibirilu kaine mijinta banason jin makamanciyar wannan magana a gidan don Allah yaya kayi hakuri wallahi tadaina insha Allah baisaurareshiba yakalli deeje yace maza wuce mutafi duk sanda yakuma sanardake irin wannan maganar datafito daga bakin Lami kisanar dani nikuma za.aga hukunci dazanyi wlh suka wuce suka fice Lami tabisuda harara tanafadin aikin banza ko kunya bayaji mace tasakoshi agaba yazo yana jaraba kaikuma takalli mijinta awulakance saiwani rawar jiki kake kana bashi hkr yana kara kumbura to idan ancemasa shege shin karya akayi? Yanada uban tsinanne dan mahaukaciya insha Allahu sainayi Ajalinsu aitsintacciyar mage bata mage yau tundasafe gidan babu dadi gurin samarin gidan dasuka fara mallakar hankalinsu domin tunsafe Ummansu batada lfy A Iyakacin shekarun Ahmad sha ukku da sani shabiyar da Auwalu shabakwai rabi.u shabiyu sunfahimci nakuda ce takeyi tunsafe yan uwan maman nasu mata keshige da fice anyi su tafi makarntar boko sunkasa zuwa alokacin Auwalu yanada shekar karshe sani yana aji hudu Ahmad yana aji daya hakama Rabi.u dayake kusan tard akemusu komai donsun tashi kamar yanbiyu cankamar daga sama suka farajin kukan jariri suka mimmike a rude suna lekawa amman sun kasa fita sunajiran Abasu izini saida aka kammala gyara uwar dajaririyata sannan akwala musu kira har rige rigen fita sukeyi ganin Umman tasu tana zaune akan filo afalo kamar ba ita ce tahaihu ba tayi kyau sai kamshin turaren wuta ketashi suna shiga ta washe baki cike da farinciki tana dariya inna balkisu kanwar tace tace Albishirinku samarin umma Atare sukace goro inna tayi dariya tanafadin yara saikunbani tunda nayi muku albishir yar budurwa da.aka haifa muku wacce kuke marmari amakota sasuka saka ihu atare saida umma ta kwabesu sannan suka natsu suka dinga amsar yarinyar suna kallo duk wanda ya.amsheta baison baiwa dan uwansa saboda kyan yarinyar Ahmad kam kamar jira yake su fito yakwasa dagudu yayi gurin Abokinsa musa yama manta shaf yana makaranta domin yanaimasa gorin kanne mata shi guda biyu yake dasu Raliya yarsheka shidda da Amina yar shekara ukku kofada suke saiyayi masa gori don haka yaga yashiga da ihunsa ko sallama babu yana fadin musa musa zokaga kanwata nima yau Ummanmu tahaifa mana mace mekyau datafi yan gidanku..... Yatsaya turus cike da tsoro sanda lami tafito daga daki tana muzurai kamar zata cinyeshi danye cikin tace shege meyakawoka gidanmu tsinanne yatsaya jikinsa yana kyarma bakinsa yana rawa yace daman..... Daman um Ummarmu ce tahaifi diya mace shine nazo nagayamasa takara dokamasa tsawa kaitafican banza shege ummanku ko ko ummansu kana murna anhaifi mace agidan wasu ko shashasha da baisan ko shi waye ba shege 3⃣2⃣ fice kabani guri kuma kaje kasanar da uwar rikon naka inci ubanka shege yajuya yafice dasauri jikinsa yana rawa yana jujjuya maganganunta aransa yakasa fahimtar abinda take nufi sukaci karo da musa azaure yakalleshh yana fadin Ashe ummanku tahaifi mace yanzu rabi.u yake gayamin Awaje yadaure yayi yar dariya ainashiga nagayama banganka ba dokin yarbudurwa yamantardashi Abinda innar musa tayi masa Ranar da hjy Amina tazo barka ranar kwana biyar da haihuwa sanda zata tafi mlm sulaiman yashigo dakayan lambu masu yawan gaske dayake sana.arshi kenan suyake saidawa kasuwar yankaba shagone dashi babba yasamya akadibarmata mai yawa tace yabarshi yace saita tafi dashi saidai motar haya tazo gidan domin motarta tana wurin gyara Ahmad yadaukar mata kayan yakaimata bakin titi suna tafe suna hirar makarantarsu dasauran Abubuwa saiyace mata Anti daman inason Intambayeki wani abu tatattara hankalinta agurinsa tace masa Uhum inajinka yagyara kayan dake kansa yace wai meye shege da Uwar riko kuma? Hjy Amina taja wani wawan birki tatsaya cike datashin hankali tace kai waye yake gayama wannan maganar badai ummar kaba ko ganin tarude yanda ummansa tayi idan yasanar mata yasanya gabanshi faduwa dan Allah kada kigayawa ummana zatamini fada daman Innarsu musa ce take gayamini kuma canake wani abune mai Amfani shine nake tambaya tayi ajiyar zuciya don zatonta deeje kefada masa haka tace lallai ta cika munafuka tunda take nuna batason kowa yanuna masa ba itace tahaifeshi ba amman duk da haka har lokacin ranta abace yake ta daure tace Agaban ummarka take gayamaka haka kuma yagirgiza kai yana fadin a.a saidai idan nashiga gidanta kuma ummana ma tahanani shiga ranar suna yarinya taci suna Asma.u sunan da deeje kenacin idantahaifi mace asanya mata saboda kaunarta ga mahaukaciya babar Ahmad tun washe garin suna tafara kiranta da ma'u kwanakinsu goma da haihuwa Hjy Amina tayomusu Asubanci sundan tsorata daganinta dasassafe amman ganin tanata wasa da dariya dayara yasanya suka fahimci ba wani abu ne yafaruba saida yaran suka wuce makaranta sannan suka kule adaki aka kara gaisawa suka nutsu sunajiran abinda ketafe da ita tagyara zama tace tabbas kunzama iyaye nagari masu rikon Amana kuma kuncancanci kuyi rainon kowane irin da banzo amatsayin shugabar gidan rainon yara ba domin nayi ritaya saidai nazo amatsayin inakaunarku dason danku Ahmad inafatar idan nafadamuku dalilin dayasa nakeson amsarsa bazaku bata rankuba tunda tafara magana suke kallonta jintazo wannan gaba yasanya deeje mikewa tana fadin tafdi jam ai wlh bazai yiwu ba koshugaban kasa bai isa ya.amshi Ahmad ahannunaba clkin matukar tashin hankali da kuka take maganar shikanshi malam din yakadu dayake namijine yasanya yadanyi karfin hali Yakwantar da kai yanafadin Adokar daukar yara agidan daman tanuna akwai wani lokaci da ake karbar yaro daga iyayen rainonsa ba.asanar damuba ko kuma rainonmu kikaraina kinaganin kinfimu iya raino hajiya takula dayanda suka shiga Rudu daman kuma tayi tunani haka zata faru dantasan yanda suke matukar son yaron takwantarda murya tana fadin kufahimci kamar yadda nasar da ku banzo da sunanan ma.aikaciya ba saidai yar uwa agurinku Ahmad bashida iyayen dasuka fiku saidai inason na rikeshi nawani lokacine har zuwa sanda zai iya daukar kowacce irin magana akwakwalwasa nasan kun san halin matar can Lami kumasha jin irin rigimar da kuke yi da ita akan yaron to abinnata yakiyin sauki donhaka mezaihana kubani aronsa haryagama Karatunsa na University insha Allah sannan nadawomuku dashi gabadaya suka sauka daga kan fushin nasu dansunsan inda maganarta tasanya gaba donhaka sungano magana tafimtar juna takawota mlm yace shin wani abune yafaru takwashe duk yanda sukayi da Ahmad tasanar dasu sanda zai rakata tahau mota sai deeje tasanya kuka tana fadin Ahaf ainasha gayawa mlm maganar nan matarnan batada mutunci wlh bazan yadda ba Hajiya kiyi hakuri wlh bazan iya rabuwa da Ahmad ba sai inmutuwa ce tarabamu kifahimci Abinda nake nufi Deeje bawai zankwacemiki Ahmad bane dawata manufa hjy Amina tafada da lallashi ganin yanda duk Deejan tabirkice mata mlm ne ya raba gardamar dafadin ke hajiya kiyi hakuri dan wlh rabamu da Ahmad babbar matsalane sannan hakan ma zai iya tona Asirin dakike son Rufewa indai lami ce matsala to zanyi maganinta ayau ba sai gobe ba dakyar suka shawo kanta ta amince zata barshi amman dole tace taza yiwa Lami kashedi da barazana don haka tare suka shiga gidan Lami da ita lami tamike jiki yana rawa tashimfida musu tabarma dan Allah yayita datsoron Hukuma tasan tsaf za.a iya daureta hajiya ce tafara magana cikin bacin rai kinfi kowa sanin laifinki bawai rarrashinki nazo yi ko rokon kiba a.a umurni ne nake baki abinda kikayiwa yaron nan yasarnar damu cikin rawar murya tace wai menayi mlm sulaiman ya yunkura da bacin rai zaiyi magana hajiya Amina datakatar dashi takalli lami tana fadin Kinmance sanda yashigo gayawa abonkinsa musa haihuwa abinda kikace to zakiyi bayani agaban hukuma tunda tunaninki rashin mutunci saita mike tsaye Hankali jibirilu yatashi yamike dasauri yana fadin a.ah hajiya baza.ayi hakaba tabbas tayi kuskure ayimata afuwa dan Allah yaya kasanya baki Lami kuwa tuni tafashe dakuka tagigice mlm sulaiman yayi dariya aransa yana fadin fitsarar riyar banza saida suka wanasu sannan tayadda tajanye sanarda hukumar yansanda wannan tasanya tadaina kiran Ahmad da shege koda sunhadu ahanya bata kyarar sa saidan harara kawai gabaki daya yaran sundauki soyayyar su sundora kan ma.u shekarunta biyar akasanxata aprimary saidai kullum sai dai kullum sai anyi dambe da ita kamar dage yawanfadan dasukeyi da raliya yasanya ummansu tayimasa kashedi akanta don kullum Dan kullum Lami ahanyar kawo kara take tayita zage zage da gore gore kalala dole tasanya yadaina kulasu Rayuwa yin Allah ayanzu haka Ahmad yana BUK takano inda yake karatunsa akan computar science Sani kam diploma yayi anan FCE sai yayi sa.a yasamu yasamu aiki awani kamfani maizaman kansa shikuwa Auwalu makarantar aiki tsafta yayi HND yabude chemist anan jikin gidansu yakuma samu aiki a temprary rabi u kam yanbokone nahakika ma.u kam ana aji daya a secondary school saikara firirita ake da iyayi da gwalli tafi kowa kokari a ajinsu gaba daya kai harma acikin tsaran ajinta itace kedaukar na daya wannan yake karamata soyuwa awurin yayyanta kafin ummansu ko babanta yayimata abu daya sunmata goma dominshi idan yatashi saiya hada dasu Raliya danhaka tafisu komai Raliya datake ganin itace budurwa dayadace tayi kwalliya sai taga ma.u tafita dawani yammaci lokacin ma.u tadawo hutu domin makarantar kwana take tataso daga islamiyya tana rike da kur.ani tahango lariya taci kwalliya tanufi shagon sisko wani dangayene a Unguwartasu da inmace kekulasu ake ganinta mara kamunkai dan haka tanaganin Raliya tashiga shagon sisko jikinta yadauki rawa hankalinta baikara tashiba saida taga saida ta hango sisko yadan leko yakalli gabas da yamma sannan yaja kofar shagon nasa dasauri ya kulle tayi dum dum cike da tsoro da fargaba tayi hanyar gidansu dasauri tasanarwa da yayyanta tayi sa.a ta tadda Ahmad da musa akofar gida zaune suna hira jikinta yana rawa idonta nazubda hawaye tanufesu Ahmad ne ya farga da ita yakalleta da mamaki yana fadin yadai ma.un baba lfy cikin rawar murya tace Raliya Raliya ce tashiga dakin sisko suka mike atare arude suna fadin Raliya zomuje saidai wani Abin bakinciki sanda suka isa kofar shagon suka hango cincirindon mutane ashe wani saurayi yaga sanda tashiga darufe kofar da akayi ya gayyato wasu matasa aka balle kofar dakyar suka barta tadaura zani suna mata ihu suka fito da ita tanufi hanyar gida tana kuka shikuwa sisko rufeshi sukayi da duka Ahmad da musa suka isowurin cike da bacinrai tundaga nan suka zare belt dinsu suka fara narkarta tana ihu tanufi gida da gudu Ahmad yarufamata baya shiko musa takaici ya isheshi yaga garayaje yakoyawa sisko hankali tashiga gidansu dagudu tana ihu daga itasai daurin kirji yankayanta data dauko duk tawatsar dan zafi duka yabita hargidan nasu yana dukanta tana ihu lami tafito daga daki arude tana fadin meyene yake faruwa tatsaya turus ganin Ahmad nadukan Raliya har cikin gida wata zuciya ta ciyota ta isa dasauri 3⃣5⃣ ta angajeshi tana fadin shege dan iska mediyata tayimaka dazaka biyota kana dukanta tamike cike damamakin ganin diyar tata daga ita sai daurin kirjg Ahmad yamike yataso daga cikin kwanikan wanke wanke data hankadashi yana karkade jikinsa ya isa kusa da ita yana fadin inna wannan yarinyar yau ta tona asirin gidannan ta tozartamu ashagon sisko aka kamata yara suka rakota suna mata ihu meyafi wannan takaici da tozarta sunan gidannan yakarasa maganar da kunan rai Lami takalleshi cike da wani irin bakin ciki data kasa rikewa tace Ahayye yaufa karin maganar hausawa tafito SHEGE YANA YI DAMAI ZINA don ankama Raliya ashagon sisko zaka biyota kana mata wannan dukan kaine kafi cancanta da adaka ba Raliya ba Shege irinka ne zaitonawa maiyin zina asiri cikin tada jijiyar wuya take magana musa dayashigo bakomai ahannunsa ya isa cike da bacin rai dadamuwa ganin yanda Ahmad ya tsaya sororo yana kallonta cike da madaukakin mamaki donshi sam baifahimci tana daurewa diyarta gindi ne akan abin da ta.aikata musa ne yace haba inna baidace kidaurewa yarinyar nan gindiba har kidinga ciwa Ahmad mutunci ba kai rufemin baki da.ace kai ko Auwalu ko sani suka kamo yarimyar nan dawani banzan damuba tunda ku kowa yasan "ya"yan halak ne ba shegu ba amman wannan yaron shege ne zai aibata diyar da akahaifa tahanyar Auren sunna ta Nuna Ahmad gaba daya suka tsaya suna kallonta cike da fargaba tashin Hankali musa yafara magana cikin kaduwa da gigita inna kazafi baida kyau kada tunanin nemawa Raliya kariya yasanya kifita daga haiyyacinki harkije ki fadi abinda baidaceba ninasan Ahmad dan gidan baffa sulaiman ne kuma...... Kai tafi can toyau zanfasa kwan da.akajima ana kiwonsa yau zansanarda kai abinda bakusaniba saunawa nake gayamuku kudaina damuwa dan Ahmad yafiku wani abu kasha damuwa danyafika kokari kasha damuwa danyafika kaya nasha gayamaka duk dayafika aikin banza ne tunda ku kunada abin ado wato uba shikuwa shege ne dan mahaukaciya wacce ba.asan daga inda ta fitoba ........ Innalillahiwainna ilaihi rajuun lahaula walakuwati illah billah muryan Ummansu Deeje ta ankardasu wacce ta shigon gidan gigice jiyo hayaniyar da akeyi taleko taga abinda ke faruwa Ahmad kam mutuwar tsaye yayi yakasa motsawa daga inda yake tabbas yasha tunanin maganganu Lami dake fada akansa Ummansa da Hjy Amina suna tauye masa tunaninsa wannan ne yasanya hankalinsa ketashi aduk sanda sukaji ance masa shege faduwar da Ummansa tayi jib dafasa ihun ma.u ne yadawo dashi cikin hayyacinsa Yanufeta da gudu kamar yanda yaga musa yayi idonta yabirkice yajuye da alama banumfashi a tattare da ita cikin karaji ma.u kefadin umma kada kimutu kibarmu dan Allah Umma kitashi shikam gaba daya tunaninsa da basirar sa suntushe yakasa cewa komai sai hawaye da idonsa keyi musa ne yamike dagudu yadebo ruwa abuta ya yayyafa mata amman abanza bata ko motsi sai asannan ya iya bude baki yana fadin Umma kada kimutu kece Uwata maisona idan kika mutu zankasance banida kowa kitashi Umma kici gaba darikeni a matsayanin danki na cikinki kada ki mutu Umma na yana kuka da majina yake wannan magana musa ne yayi dabara fita dagudu yanufi gurin Auwalu dake chemist wanda bai san wainar da ake toyawaba Lami kam tayi tsuru tsuru tsaye da fargabar da tashin hankalin abinda zaije yazo Raliya kam sai sharbar kuka take yi cike da takaici da dana sani Auwalu yashigo aguje hannunsa rike da fanfon auna jini ya isa gurin mahaifiyar tasa yahada bakinsa danata yafara bata taimakon gaggawa da ake kira da mouth to mouth yatallafo kanta cikin ikon Allah saiga numfashin nata yadawo tabude idonta dasauri saita mike zaune kamar ba itace tasuma ba yanzu takamo Ahmad tana fadin karya take nice nahaifeka ba mahaukaciya ba ranar dana haifeka ne tazo nan gidan katambayi malam kaji ainasha gayamaka Lami makaryaciyace tana kuka take maganar shima Ahmad kuka yakeyi Auwalu da baisan abinda ke faruwa ba yamike cike da mamaki yana fadin wai meye yafaru me yasameki Umma? Arude yake maganar saita mike cikin karfin hali tana fadin babu komai kuzo muje gida banason kara kallon fuskar Azzalumar matarnan tanuna Lami da hannunta Ahmad yarirriketa dakafarsa suka nufi gidansu harlokacin musa Ahmad da ma.u kuka suke Lami ji take yi kamar maganar tadawo tamaidata cikin ta donbatasan abinda zaibiyo baya ba amman saboda tsabar taurin rai saida taga sunfice eh gaskiya ce nafada sai dai Akasheni wallahi haka kawai shege zaitonawa diyata Asiri yanda yatona m ini asiri nima natona masa 3⃣7⃣ koda suka iso gidan abin datake maimaitawa kenan Auwalu yace Umma mema tacene? Meyafaru ne? Cikin kuka tace Azzalumace Lami waicewa tayi Ahmad shege ne bayan nice nahaifeshi da cikina cewa tayi dan mahaukaciyane bayan gashi dana ne ranar dana haifeshi ranar mahaukaciya tazo nan gidan bari kuganima na dauko muku takaddar dazaku san danane saita mike jiki yana rawa takama lalube saidai abinda batasaniba shaidar datake son kare ta itace zata kara sanyawa abin yafito fili tunda duk mutumin dayakasance danka dakahaifa aibabu bukatar wata shaidar takarda arubuce gashi ita batasan abinda akarubuta na yarjejeniya bace baiwar Allah saida tafito dakayan wata tsohuwar adaka sannan takwakulo wata takarda acan kasan jikinta yana rawa tamikama Ahmad tana fadin karanta kagani karya takeyi nice babarka ya.amsa yafara karantawa bawani abu Acikiba illah yarjejeni sun amsheshi zasu rikeshi kuma duma duplicate ce aka basu da.alamu original din tana can inda suka basu shi kukansa yakuma karuwa hankalinsa yakuma tashi tabbas ba sune iyayensa ba Auwalu ya warce takardar yafara karantowa yakalli mahaifiyar tasu datausayi datashin hankali rashin ilimi datayine yasanya batasan Abinda takardar takunsa ba data sani data kara boye takardar cikin sheshshekar kuka yake fadin Umma wannan takardar tana nuna yarjejeniya dakukayi ne asanda zaku amshi wani yaro nasan ba Ahmad bane mantawa kikayi kika fito da ita sai asannan tagano wautar datayi amman taji dadin yanda Auwalu din yakawo mata mafita dasauri tace ahaf namanta wannan ajiya ce akabani bari nazakulo wancan bani na adana wannan din kafin masu ita suzo nema ta.amsa dasauri tanufi akwatin tana cigaba dalalube tsanananin tausayin dasoyaryar Ummansu tashigeshi yakula da idan baiyi wani abuba zata iya rasa hankalinta ko wani yashigeta yanufeta inda take tazakulo kaya daga cikin tsohuwar adakar yadafa bayanta yana kokarin kwantar mata da hankali yace Umma kidaina lalube nifa nasan kece mahaifiyata bakece kikasha gayamin innarsu musa karya ne da ita ba tayaya zanyadda damaganarta dake ba uwataba ce ba saikin nunamini watarana dakuma saiwani yayi mini gori acikin layin nan kishare maganarta ki kwanta ki huta tana son bata miki raine don ankamo diyarta dakin sisko suna iskanci tadago cike da matsananci farinciki tana fadin haba ainasan saboda mugunta take son rabani dakai tahadda samaka wani ciwon dazan rasaka bakayadda da abinda taceba kenan? Yadaga mata kai yana kokarin kakalo murmushi wannan yasanya tadan sami sassauci aranta daga wannan karon anyita takare ko ita ko lami dole dayan yabar gidan dakyar ta iya kyalesu suka tafi masallaci bada farali gani take yi kamar daga can bazata koma ganin Ahmad dinta ba saidai shi yana sallah yana kuka ransa yayi baki ashe shi yanata barankadama da homa ashe shi shege ne bashida kowa aduniya shin wacece mahaifiyarsa datayi shegensa koda yake ance mahaukaciya ce to waye mara imani dayayi mata ciki har kawo shi duniya 3⃣8⃣ tana ina ita mahaukaciyar ta warkene kohar yanzu tana cikin haukan? Yakasa natsuwa daga masallaci yalallaba yafice yayi gabas yana ta tafiya baisan inda zaidosaba Anshirya cin abinci yanda aka saba amman babu Ahmad tun Ummansu nasanya rai zaishigo har tafara karaya bacin rai datake kokarin boyewa yafara yabaiyana tadinga sanyawa ana nemansa sam tahana kowa cin Abinci nan malam yashigo cike da taikaci yana fadin wai Ahmad yaro ne dazaki sanya ayi ta wani nemansa saika ce wanda zaibata kinsa dai bazai wuce yana gidan yaron Abokinsa Abdullahi ba cikin sheshshekar kuka basan abinda nasaniba tabbas idan Ahmad bai bata ba to zaigudu kuwa saita fashe dakuka cikin mamaki yakd kallonta hasken wutar lantarki da.aka kawo yanafadin wace irin magana kike yi khadijatu kamar wacce tayi gamo memukayi masa da zai gujemu cikin kuka tace yau Lami tasanar da Ahmad shi shege ne tasanar da shi banice nahaifeshi ba tagayamasa shidan mahaukaciyane baniba... Kuka take yi sosai kamar wata karamar yarinya malam yamike cikin tashin hankali yana fadin mekikeson sanar dani khadija inanilillahi wainna ilaihi rajuun yanzu ina Ahmadu bari nanemoshi... Baijira yi jin abinda zatace ba ya fice sani da salisu da rabi.u ne agurin sunkuma riga sun fahimci abinda ake anufi saidai harkarfen dayan dare babu Ahmad babu labarinsa hankalin kowa yatashi sanda malam sulaiman yashigo gidan Umma Deeje tamike tana fadin yaya dai malam kungan shi yagirgiza kai cike da damuwa mai tsanani takuma wurga masa tambaya hargidansu Abdullahi mlm kunje munje taredashi muke ta nemansa ma yanzu haka nabarsu shida Auwalu suna ta bin gidajen Abokanansu Akanme zaku wahalarda kanku wanda yabata ake nema bawanda yagudu ba Ahmad bazaije inda zaku ganshi ba abinda najima ina nusar da kai kenan wlh Lami bamasoyiyar mu bace ko Ahmadu yadawo ko baidawoba nagama zama a gidannan yanda Ahmad yatafi haka nima zatasalwantar min yarana tana magana tana kuka ya hasala matuka gaya yama rasa hukunci dazaiyanke sai kawai yamike cikin fushi yanufi gidansu Lami Yanashiga yakama kwada sallama kamar zaitsaga gidan dafarko sunyi shuru adaki don lami tagayamasa tabargazar dayayi duk da lika abin asharri yayiwa diyarta ammam duk da haka mijin nata yabata rashin gaskiya don yana tsoron abin da zaije yazo can dai sai ga mlm jibiril yabayyana cike da tsoro mlm sulaiman yagalla masu harara yana fadin Barkanku Ahmad yagudu yabace mana yarabu da mu saidai kusani jibril yanda Ahmad yarabu damu tokaima karabu da komai nawa kashirya kayanka agobe zansanya gidan kasuwa tunda dai zamanmu tare baida Amfani sai haddasa masifa nima nahakura dazaman gidan gabadaya hankalin jibril yatashi idan yarabu dan uwansa inazaisoma rayuwarsa waye zai iyaciga dabashi taimakon dayake bashi tabbas shikansa yanzu lami ta isheshi yabi dan uwansa yana bashi hakuri amman ina tuni yafice yadawo tsakar gidan yayi duru duru cike da tashim hankali saiyafada dakin dasauri yatadda lami zaune tayi wuki wuki tana zare ido yana shiga tafara magana ka kwantar da hankalinka malam indai akan gidane muje mukama haya tunda ai....... Rufemin baki munafuka sau nawa nake cemiki kicire hannunki daga kan maganar yaran nan yaji koshi waye aduniya amman saida kika fadamasa to tsaya kiji banida wani gata dayawuce na Allah da dan uwana daya daukoni daga cikin wahala yanemo mini aurenki yaci gaba da dawainiya dani kisani idan na bar nan banida wurin zuwa don haka kedai da kika janyowa kanki kece zakibar gidan dolenki kuwa takalleshi damamaki matuka tana fadin malam akanfadin gaskiya kake wannan furucin kinga banja dagon zance dakeba kiwuce kawai nasakeki yana kaiwa nan ya fice daga dakin .......4⃣0⃣ Lami tafashe da kuka tana fadin na shiga ukku yanzu akan dan shege har akasane natsani wannan yaro daman nasan zuwanshi gidannan Annoba ce kuma harzuwa yanzu banyi nadamar fadin cewar shi shege neba dawannan tadinga sambatu tana kuka Sunwayi gari cikin tashin hankali kam tun Asuba tabar gidan saboda yanda jibril ketayimata kwakwazo hankalin yayanta yatashi matuka musamman Raliya da Amina musa kam yanajin ciwo sakin mahaifiyar tasa Amman yanajin takaicin Abinda ta.aikata gaba daya gidan angaza karyawa kowa yanacikin damuwa ma'u kam kuka takeyi tana fadin danasani dabangayawa yaya Ahmad abinda raliya keyiba duk da deeje tana cikin tashin hankali hakan baihanata rarrashin diyar tata ba tunda suka dawo daga masallaci jibril yatare malam yana kara bashi hkr dasanar dashi hukunci daya yanke tun dare jiya malam sulaiman yakalli dan uwansa cike da tashin hankali yace subhanallahi meya sanya ka.aikata haka nima bacin raine yasanya fadin abinda nafada kayi hakuri da abinda nayimaka dankai dan uwa nane jinina daban isa nasakakaba Dejee kam bataji ko dar da mutuwar auren lamiba tunda tarasa danta komaima yafaru wajen misalin karfe goma sai Hajiya Amina ta iso akidime don yan dubo Ahmad sun iso hargidanta duk yanda deeje kekorin taddanne zuciyarta saida ta fashe dakuka ganin hjy Amina tana fadin yagudu hjy bamusa inda yashigaba danasani munbakishi ina zankai hakkin yaron nan tadafa kafadarta cikin kwantar da murya take fadin kidaina wannan maganar deeje ko ina yake aibazaiwuce kaddararshi ba Nakuma tabbata duk inda Ahmad yake zaidawo inda kuke muyi Addu.a kalaman hjy ne suka dan kwantar mata da hankali tace kuma adaina zuwa nemansa zaidawo dakanshi tasoyin maganin lami saidai tasamu lbr sakin da.akayimata kwanaki ukku suka cika cikin tashin hankali abincin kirki babu maici agidan Ranar kwana na hudu datafiyar tasa ma.u tadawo daga kai markaden gero na kokon da yamma sakaliya tana tafe tarera wakokinta tahangoshi tafe da kayansa tunna ranar dayatafi yarame yayi duhu dakyar yake tafiya kamar me ciwon kafa batasan sanda ta watsar da robar markadan ta falla gida dagudu tana fadin Umma gayaya Ahmad umman dake tukin tuwo tafito da.azama jikinta sai kyarma yake harzaninta yana neman faduwa darawar baki tace A ina kikanshi gashinan zaishigo gidannan yashigo gidan dasallama 4⃣1⃣ yatsaya turus cikeda farin ciki ganin ummansa itama tsayawa tayi turus tana kallonshi kuma kome tatuna saita nufeshi da sauri ta wanka masa mari sai kuma tafashe dakuka tajuya gida da sauri ma.u dake tsaye ta zuba masa ido wanda ya ciko da kwalla shima idon ya zubamata yana hawaye shida kansa yasan abin da yayi bai kyauta ba cikin kuka tace yaya Ahmad mai yasanya ka gudu ka barmu Umma ta daina bacci tadaina cin Abinci baba yadaina fita kasuwa yaya Auwalu yadaina zama a chemist sani yadaina zuwa kasuwa ni idan akaturani makaranta bana zuwa sai intafi nemanka ranar har gwammaja naje dakafuna nemanka memukayimaka kagudu kabarmu yakamo yarinyar maicike dawayo ya rungume yana kuka yafadin ba gudowa nayiba tafiya nayi nasamu natsuwar zuciya ta saidai bansamuba zama daku shine nutsuwar zuciyata yamike hannunta suka nufi cikin gida saidai duk yanda yaso yayi wa Umma magana taki sauraronsa tayi fishi dashi maitsanani wanda yakara tada masa hankali Malam sulaiman yagyara zama yana fadin tabbas hjy Amina tayi gaskiya tace mini Ahmad bazai iyabarinmuba munyi masa rikon dako mahaifiyarsa ce tadawo duniya bazatayimasa irinsa ba saidai nayi mamaki dakabarmu Ahmad shinkanaganin kayimana adalci yadukar dakai cikin kuka yake fadin kuyafemin baba tabbas nasan na.aikata muku laifi mai girma wani irin tausayi yakama malam mai tsanani shikadai yasan Abinda yakeji Azuciyar sa game da yaron 4⃣2⃣ kwanaki sunja ga Lami tun tana ganin abin kamar wasa har karamar magana tazama babba domin sam mlm jibril yaki zuwa biko sai abin yazamomasa kamar gaba takaishi domin daga gidan yayansa yayansa akefitomasa da girki maidadi wanda yafi namatar sa Su raliya kam kullum saita saci jiki ta tafi gurin uwarta suyita ta kitsa mugunta dadai lami ta kula abin bana wasa baneba hankalinta yafara tashi ga wahalar gidan tafara damunta da yunwa don haka tafara bin kan mahaifinta ABDULLAHI YUSUF MAITAMA 09034598552 @whatsapp

11 April 2015 at 06:49 · Public Save · More Like React Comment Share Like61 Write a comment...

· Dauda Yahaya Masanawa MADALLAH Like · React · Reply · More · 11 Apr 2015 Mukhtar Umar Daura Muna gdy Like · React · Reply · More · 12 Apr 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 11 Apr 2015 Halima Ibrahim Tanks Like · React · Reply · More · 11 Apr 2015 Halima Abdullahi tnx Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Zainab Muh'd Zakariyya Wldn Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Ahmad Sabo Sannu da kokari Like · React · Reply · More · 12 Apr 2015 Yusuf Mamman Nadaji Godiya muke, babu admin kamar ka a cikin wannan zauren! Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Sardaunan Telolin BG Wannan lbrn har sai da ya sanya ni hawayee Like · React · Reply · More · 12 Apr 2015 Yahuxa Kabir tnx Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO PART 4

Saidai mlm jibril yace bashi za.aba hankuriba yayansa za.aje abaiwa idan yahakura shikenan dan bawan Allah baiyi kasa agwiwaba yanufi gurin mlm sulaiman din darajar tsohon tasanya yace shikenan komai yawuce amman sujawa Lami kunne matuka domin bazasu kuma yadda da irin wannan rashin tarbiya ba haka tsohon yatafi yana godiya haka aka tarkato Lami aka dawo da ita su Raliya tamkar sallah shi kuwa mlm jibril sai cika yake domin wahala takuma dawo masa sabuwa dal yanayin Rayuwar Ahmad tasanya gaba daya yadukufa kan karatunsa bashida lokacin komai sai karatu idan kaga yana dariya yana cikin gidan donka da Ummansa ta damu ahaka har suka shiga aji hudu Ummi sada itace yariyar data dafe masa tun farkon shigowar su take bibbiyarsa dafarko dasigar koyon karatu tashige shi har shakuwa tashiga tsakaninsu ahankali tajuya soyayya kusan kowa yasan halin da ake ciki cikin dakinsa ma katon hoton tane kyakykyawa ce fara da ita duk da bata cika tsayiba Ummi ce kadai kesanyashi farinciki idan yana cikin damuwa yana son Ummi matuka musamman yanda iyayanta suka daukeshi kamar su suka haifeshi yana tsaye adaki yana kallon hotonshi na ranar dasuka kammala karatu yana sanye da kaya wadanda digiri yan uwansa sun baibayeshi cike da farin ciki ga hajiya Amina agefe dakuma babansa ga ma'u nan anyimata kwalliya yana matukar son hoton arayuwarsa domin yasanshi dangata ne lokuta dadama kalmar shege tafado masa yatuna wannan matsayin dayake kai yakuma tuno yanda yan uwansa da iyayensa kesonshi sai yaji zuciyarsa tayi wasai baitaba kukan rashin dangiba sakamakonsa yayi kyau matuka har an turashi jahar taraba bautar kasa hankalin Ummi gabadaya yatashi domin batason yayi nisa da ita aganinta shekara tayi yawa saida yadinga tausarta dasu ishak sannan tahakura itakam tayi sa.a batayi nisa ba jigawa akaturata amman bakincikin rabuwa damasoyinta yaraunana farincikinta kwanci tashi kamar yaune shekara guda sai gashi haryadawo umma tayi murna matuka hajiya Amina kamar itace tayo sabon digiri sai murna take yi da Alfari ta amshi takardunsa daniyar tanemasa aiki saidai abin yaci tura domin samun aiki agarin saika shirya daga karshe dai tasamomishi aiki n gidan wani mai dasuke mutunci da maigidanta da maigidan man kwarai dagaske Alhaji nura kwangila yayi murna kwarai da samu don babu abinda yake buri illah yafara cin gashin kansa yataimakawa iyayensa kamar yanda suka yimasa duk sanda yatuno iri dawainiyar dasukayi dashi saiyaji son su yakuma cika ranshi Lami tayi tagama tsakaninta dashi saikallo sai harara domin tunbayan dawowarta gidan tashiga taitayinta saidai samun aikin nasa yatsaya aranta matuka domin cikin kankani lokaci komai nasa yasauya yakuma yama dan gayu cikin lokaci kankani yasayi babur dinsa irin wanda samarin zamani ke yayi tsutsun soyayya ... 4⃣4⃣ ba umma ba hatta mlm yadaina kukan babu domin Auwalu da sani da Ahmad sun isheshi kowa akwai abinda yaware yake siya awata don ma dai Auwalu yatattago Aure amman duk da haka yana iyakacin kokarinsa ko kishin yanda rayuwar gidan ke gudana Lami batayi nata sanya yayanta suzama mutane nagari idan kafidda musa saishegen kishin tsiya da kyashi Raliya kam likkafa taci gaba tazama gogaggiyar yarduniya domin duk tayi billicin tayi fari tas kamar gauta ga tara samari kala kala akofar gidan tun yayyen suna fada har sun gaji sun watsar domin lami ke dauremata gindi tace anayiwa hassada dakyashi cikin wannan sati aka kai kayan Auren Ahmad gidansu ummi saidai mahaifinta yatsaida lokacin biki gabadaya wata hudu wannan abin yafi yiwa Ahmad da ummi dadi domin sunkagu sumallaki junansu Abba da umma kuwa sunyi farinciki da hakan Ahmad kam yadage hada kayan Aure sai Alokacin yagano kokarin da Auwalu yayi dominshi har gini mayayi koda yake tuni yazama cikakken ma.aikaci yana da albashi me kyau shi kam haya zaikama dole amman gaskiya ba zai kama hayar karamin gida ba domin yasan Umminsa yar gayuce gwara ya kama gidan da zaiburgeta saura wata daya biki yagama hada kayan lefensa yayi kokari matuka domin saida yayi akwatuna hudu sanda yakawowa su umma kaya sun cika mamakin kokarinsa daganan yafara kokarin nemo gida da kudin haya dama babansa ya sauke masa sadaki domin tun sanda za.akai kayan lefe yabada dubu ashirin na sadaki biki yarage sauran sati biyu yasami gidan sa makyau acan Unguwar gaida mai dakuna madaidata guda ukku da kichen da bandaki dangin Ummi harsunzo sun gani sunyaba komai gabadaya gidan ansanya masa wuta yaimasa fenti maikyau saidai abinda yafi damunsa da za.ayi bikinsa ma.u bataman domin suna gab dafara jarabawa tunsauran kwana goma biki yafara rabao iv nabiki yabaiwa Ummi nata anshirya shagali daidai na takala ma'u kam harkuka tayi amakaranta domin tana lissafin bikin yayanta yazo saura sati guda biki da magriba Umma tana tsakar gida tana ta aikace aikace mata suka fara shigowa gidan da sallama dauke da akwatuna riki riki mamaki yacikata ta mike tsaye tana tambayar lafiya daga inakuma? Domin tasan basuda wata budurwa daza.akawo kayan aure saida suka gama ajiye kayan babu ko gaisuwa daya daga cikinsu ta kalli umma tace daga gidansu Ummi aka aiko mu mudawomuku dakayan aurenku domin ajiya mukasamu labarin ashe yaron dake neman diyarmu ba danku bane ba shege ne daba.asan asalinsa ba Umma tadafe kirji cike da fargaba daidai lokacin Ahmad yashigo gida inyajikomai akunnensa don haka yatsaya turus a bakin kofa cike da tsananin damuwa datashin hankali MUHADU AKASHI NA BIYU

BOOK 2

1⃣ DAME AKE ADO 2 Uban waye yagaya muku wane munafuki ne yasanar daku wannan magana Umma tafadi ahasale batabar sunce komai ba tadora da masifa to duk wanda yagayamuku karya yake yi hassada ce kawai nice nahaifi Ahmad nice uwarsa Afusace take maganar Daya daga cikinsu takuma amshewa haba baiwar Allah kiyi hakuri munriga munji komai zance duniya fa baya buya Idan har danki ne mai yasanya aka cireshi daga lissafin sunan yayan gidan kinada Auwalu da sani da rabi'u yaya akayi shi yafita daban? Mu kinga yansako ne kiyi hakuri sai anjima tadire kudin sadaki akan kayan suka juya suka nufi kofar fita Umma tabisu dasauri tana fadin don Allah kudawo nayi muku cikakken bayani don Allah kudawo Basu saurareta ba suka nifi kofa suna ficewa suna ganin Ahmad suka kalleshi suka wuce kawai Umma data biyosu da sauri arude taci karo da Ahmad tsaye ta yi turus cike da tsanani tashin hankali tana kallonsa Ahmad yana tsaye idonsa yana zubda hawaye cikin muryan kuka yake fadin kirabudasu Umma ki kyalesu gaskiya suka fada munyi laifi dabamu gayamusu gaskiya tun farkoba wannan wace irin masifa ce wane irin cin mutunci ne wannan don cuta sai da muka gama komai harmun raba katin biki zasuzo mana dawannan maganar wane irin Abin kunyane wannan shikam tsananin tausayin Umma yafi komai yawa aransa wane irin so ne wannan baiwar Allah take yimasa ina ma itace tazo a matsayin mahaifiyarsa inama ana komawa baya asauya Uwa daya koma yafita daga cikin mahaukaciya yakoma cikin Ummansa mlm sulaiman dake sallama yashigo da hanzari jin kuka matarsa a rude yake yakalli deeje dake kuka yakalli Ahmad cikin tsananin damuwa yace lfy deeje meke faruwa haka kike kuka subhanallahi Dahannu ta nuna masa tulin kayan lefe dake jibge yakallesu yadawo da kallon kanta yakuma shiga rudu kansa ya kulle yace banfahimta ba deeje ? Cikin kuka tace daga gidnsu Ummi wacce Ahmad zai aura waisun fasa auren ...... Takuma fashewa dakuka yawaro ido waje da wata irin kidima mara fasaltuwa gabadaya jijiyoyin jikinsa sun janye saiji tamkar yadaskare dakyar ya iya karfin halin kakalo wani zancen bangane sunfasa Auren ba wani abu akayimusu tadansausata kukan tana goge hawaye 2⃣ tace ba.ayimusu kome ba mlm saidai munafukai sun shiga ciki lamarin anje angayamusu Ahmad wai shege ne ba shida uba banda wulakacin mai yasanya tunfarko basu ce haka ba saida aka kammala komai malam yayi shiru yama rasa abinda zaice domin iliminsa da tunaninsa suntsaya gabadaya na wucin gadin Lami dake labe tana jinsu tadaka tsalle cike da tsananin murna har da daga hannu sama ta fadi Alhamdulillahi da.anayimin wata fuffuka kullum yaro yana shiga manyan riguna shiga masu gida daman nafadamasa ba da riga ake ado ba da uba ake ado ehe! Takuma zuro kanta tana jiran jin abin da mlm din zaice tasami nadorawa sai jiyo shi yana fadin kunga kuwuce ciki muyi maganar kantabarma suka zauzzauna mlm yadubesu da damuwa yace duk Abinda Allah yakaddara babu makawa sai ya sami bawa daman can Allah baikaddaro ummi matarka bace Ahmad don haka babu yanda za.ayi ka aureta Umma tace Amman mlm baka ganin anbata masa suna kana ganin ko wata diyar yaje aure zata yadda ta aureshi malam ? Ahmad yadafe kai yana kallon umma tausayinta yana kuma karuwa aransa da kyar ya iya bude baki saboda nauyinda yayi masa yace Umma kiyi hakuri kiyi hakuri .......kuka yaci karfinsa malam yadube shi da tausayawa wato Umman yake baiwa hakuri Umma tace Ahmadu kai ya dace mu baiwa hakuri tunda mun kasa kareka daga wannan suna mummuna mun kasa cire kalmar shege daga jikinka Balaifinku bane ba Umma bakuda laifi kunyi duk wani yunkuri na boye wannan mummunan suna daga gareni Amman Allah yakaddara sai najishi Umma idan wanka ba.aboye cibifa malam yakalleshi da hanzari yace kaga tashi kawuce dakinka zansan yanda za.ayi idan takama aje a sulhunta nema zanyi zannemeka yamike dasauri yana tangadi iska naneman kayardashi saboda juwa akarshen kwanar gidan yaci karo da Lami tana lekensu takalle shi da hanzari saita juya tayi cikin gidanta yabita ka llo cike da mamaki mai tsanani bai san abinda yayima matar nan ba tasanyashi agaba yanufi gidansu Ummi yayi shiru yana tunanin idan yacemata shine zata iyakin fitowa kokuma iyayenta suhanata don haka yace da yaro kace Abdul ne bayan tafiyar yaron da kamar sakan talatin saigasu tare da Ummi fuskarta dauke da tsananin mamaki waye kuma Abdul yake sallama da ita mamakin ta yadada karuwa sanda takula bakowa bane sai Ahmad tsaye ya hade hannuwa akirji gabanta ya yanke yafadi tayi dan dum dum kamar zata koma sai kuma ta dake ta bata rai tace gani yaya akayine ? Tana magana babu ko fara.a 3⃣ tsananin mamaki yacika Ahmad yau Ummi ke masa haka yadaure da kyar yace Ummi babu gaisuwa kenanko? Takara hade rai tana fadin baikamata nagaida mayaudari ba kacuceni matuka Ahmad kasanya nabata lokacina daduk wani tunanina akanka Ashe kai shege ne bakada Asali maganar tadakin kirjin kwarai dagaske idonshi yakuma cikowa da kwalla kamar zaifashe da kuka yakwantar da murya cikin lallashi yana fadin Ummi yanda muka gina soyayyarmu cikin aminci banyi zantan dan Abu kalilan irin haka zai iya mana itaba...... Takalleshe afusace tana fadin Au kai agurinka wannan yar karamar matsalace kenan amman ka bani mamaki matuka to idan kai ta zama karamar matsala a gurinka kana ganin doka kasance shege bawani abu bane to nikam Allah yasani babbar matsala ce bazanso nahaifi ya ya adinga cewar Ubansu shege ne mara asali ba maganar mungina soyayyarmu kuwa daman can akan tubalin toka da karya muka ginata don laillai dana san kai shege ne da banta lokacina akanka ba na soka Ahmad ashe kai mara asali ne ka boyemini kacuceni wlh kayaudaran .... Saita fashe dakuka 4⃣ DAME AKE ADO ....... Ahmad yaji duk yatsani kansa da rayuwarsa tabbas Ummi tayi gaskiya waye zaiso hada zuri.a da shege mara.asali hawaye dayake ta hadiyewa suka ci gaba da biyo kuncinsa yakasa cewa komai domin bashida sauran abinda fada din Ummi ta kalleshi afusace tace idan abinda ya kawoka kenan nizan koma domin inada abinyi a gida yayi dum yana kallonta da tsananin mamaki da damuwa jiyake kamar ya bita yakamota shikenan Ummi tayimasa nisa haka yajuya yanufi gida baisan yanda akayi yajeba yasandai Allah ne yakaishi Acikin gidama duk wanda akasanar da shi abinda yafaru cikin yan uwansa sai hankalinsa yatashi abinda suke tambaya shin Uban waye yaje yafada duk yanda sukaso ganin Ahmad sulallasheshi abin yatura don ya kargame kansa acikin daki Malam sulaiman kam yajima yayi shiru akan dakali yana tunanin mafita har zuwa lokacin da ya cimma burin tunanin nasa yasanya yaro yakira masa dan uwansa mlm jibril bada jimawa ba ya fito ya zauna kusa da yayansa yace malam gani naji ance kana kira na yakalle shi tsahon lokaci sannan yace kaji abinda yafaru da Ahmad kuwa? Dasauri yace naji wlh dazu na shiga gida Lami take sanar dani Abin kam baiyi dadi ba mlm sulaiman yanisa yace tunda abin nan yafaru nake tunanin mafita har Allah yasanya tunanina yafado kan diyarka Raliya da hanzari yadubeshi yace Raliya kuma mlm yagyada kai yana fadin ita kuwa kamar yanda kasani nima nasani Raliya tazama gagararriya wacce duk wani kokari namu dana yan uwanta yagagara gyara ta saidai addu.a gashi tayi girman daya dace ace tafidda miji amman anrasa wanda zaifito dagaske yace yana sonta saboda sanya shashanci datayi agabanta hakan nakeganin abune mawuyaci Raliya tasamu miji nutsattse don haka tunani yasanarda ni mezai hana tunda anyi haka amaida ranar auren Ahmad kanta kada acanza komai ayinan da wata gudan amman kai yakagani domin ka fini hakki akanta yayi shiru tsawoh lokaci yana nazari can yadaga kai yakalli yayanasa yace yaya duk abinda kayanke yayi saidai kana gana ganin Ahmadu bashida wata illah da zata iyayiwa rayuwar Raliya illah ? 5⃣ mlm sulaiman yaduberhe da sauri yace kada kace mini kacikin mutane masu jahilci dakama wani da laifin wasu wlh bagori zanyiwa kaina ba Ahmadu yafi duk yayanda muka haifa nagarta balle Raliya da kai kanka kasan irin abubuwan kunyar da ta daukowa gidan nan auren nasu shi zai zama rufin Asirinsu baki daya jibril ya girgiza kai yana fadin wannan haka yake to Allah yasanya Alkhairi mlm sulaiman yayi murmushi cike dajin dadi yace Amincewarka tafi komai agareni kuma koda hakan batafaruba kayan dakin raliya daman akaina suke tunda dai nine waliyinta dahaka suka rabu ran malam yahaskake yasan yana da damar kara kyautatawa Ahmad da mai dakinsa Adaki yatta Umma tana lazimi da alama addu.a take yiwa danta yasami guri yazauna yana murmurshi yace Allah dai ya.amsa Addu.arki saiki kwanta ki soma bacci Umma tadubeshi damamaki Fuskarta babu yabo ba fallasa tace malam kenan kana zaton hankulanmu zasu kwanta cikin sauki kuma wannan kankanin lokaci ? Yakuramata ido yana karantar yanayinta yace Amman ai tunda abin nan yafaru Allah muke gayawa ba kyazato zai kawo mana mafita cikin gaggawa tayi saurin yadda da batunsa har daga fuskarta yafimci hakan ta hanyar yin murmushinta tana fadin duk abinda da akace Allah magana takare Amman taimakeni sanar dani wannan Abin dadin yayi dariya yana kokarin tattaro farin cikinsa suyi rabonshi tare yace danki dai yasami matar aure kuma awannan rana za.ayi bada fashi takalleshi datsananin murna da mamaki wacce tagaza boyuwa akan fuskarta tace najima banji labari mai dadin wannan ba dan Allah mlm wacece dan Uwanane ya.amince da baiwa Ahmad auren diyarsa Raliya kinga Asiri yarufu ko ? 7⃣ DAME AKE ADO Anacigaba dagudanarda sha anin biki Abba duk yaraba iv ga dangi da abokansa abin mamaki har sanarwa yasa agidan radio itama Umma tadauki dukanin burinta tasanya akan bikinnan hakanne yasanya yadanne zuciyarsa da damuwarshi ake gudanarda komai cikin farinciki duk da bahakanne akasan ranshiba Abinda yabashi mamaki da tsoro ya kuma sanya Raliya tafita daga ranshi baiwuce rashin mutunci datayi mashi cikin soron gidanba malam yayi matukar kokarinsa domin shine yayi duk wasu kayan daki na Raliya akaje akayi jere hatta kayan daya dace ace uwa tayi shine yayi domin lami cewa tayi Auren da akayiwa diyarta na dole ne donhaka ko tsinke bazatayi ba wadanda suka haka suzasuyi komai saidai mutane dayawa sungane borin kunyane domin babu tsiyar dataaje domin Auren diyarta tuncan baya kudinta wurin bin malamai yake karewa balle yanzu datake iyakacin kokarinta na wannan Auren baitabbataba domin acewarta diyarta kalar masu kudice da Asali ba kamar Ahmad fakiri ba Ranar kamu amarya ba yabo ba fallasa tayi kwalliya kamar gaske koda yake yayyanta sunyi mata fada harda mahaifinta da Abban duk da Ahmad duk da Ahmad bahalarta wurin kamun ba yayi farinciki kwarai dagaske da lbr dayaji gurin yara na yadda Amarya ta cashe rawa

13 April 2015 at 09:38 · Public Save · More Like React Comment Share LikeSadAngry78 Write a comment...

· Halima Ibrahim Allah yabiya Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Zuhra Maigari TANX,amma dan Allah adinga mana posting kullm. 1 · Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Bernges Kanu duk maisan group din hausa novel na whatsap to yamin magana ta account dina dan samun shiga group din Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Ya'aqub M Sabo Hm daman can ummey bason ahmad din take b . Da tanasonsh jin cewa shi shege ne bazai sauya ra'ayinta ko taji cewa za ta iya wulakantashi b. Kawai tanunamasa halinsu na mata wato yaudara hakan na nuni da cewa koda ya aureta taji shi shege ne cewa zatai yasaketa. Kugyara halinku mata. Daga SULEIMAN MUSA SABO COPING. Like · React · Reply · More · 14 Apr 2015 Musa Yusuf Shariff Thanks Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Khadija Haruna Thnks Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Jabeeru Inuwa thanks alot Like · React · Reply · More · 14 Apr 2015 Adama Adam Maidala kash na so ace an hadashi aure da Asma'u Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 Nabanje Samaila Saidu Allah abin godiya Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Bala Sani Hafsat Tnxxx 1 · Like · React · Reply · More · 13 Apr 2015 View more comments…

Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books ------>DAME AKE ADO part 5. 8⣠DAME AKE ADO Karfe biyar daidai motonci daukar Amarya suka iso Raliya tayi wanka duk da batayi wata kwalliyaba amman tayi fes domin wata yayar Lami takama fada tanafadin tunda akadaura ya kamata su watsarda makaman yakinsu surungumi kaddara yaushe za ace akai amarya haka wannan yasanya tadan kimtsa idonta kemadagas babu alamun kunya itakadai tasan tanadin datayiwa Angon nata narashin mutunci buhu buhu haka akawuce gidan mijinta da ita saiwajen karfe 9 nadare Ahmad yagama kammala shirya kayansa tsaf cikin jakarsa don haka rataya kawai yayi yanufi gurin Ummansa tana zaune arumfa dasauran yan biki basu watseba yadurkusa yanagadin Umma zanwuce inabukatar Adduarku idan nayimuku wani abu kuyafemin don Allah yasunkuyarda kansa jin muryansa tana rawa tamkar zaifashe dakuka idanuwan Ummansa sunciko da kwallah tanajin kamar zata rabu da dantane har Abada Allah yajarabeta da tsananin son Ahmad bata son Abinda zainisantasu saigashi yau Aure zairabasu tayi shiru tsawon lokaci sannan tadaga kai ta kalleshi yana tsugunne kan kafafuwansa Kansa yana kasa Tunda nake dakai banta ganin wani abu na ashsha kona kaico agarekaba nasan Raliya zata iyayin komai domin ta tunziraka ta kuma hasalaka banason jin komai daga gareka sai alkhairi kada kayadda wani abu nabacin rai yafito daga wurinka kayi komai domin kafarantawa" babanka rai kiyayyar mace takaitacciya ce wata rana zata daina ranar daza awayi gari kunfara tara zuria shikenan komai yazama tarihi Allah yayimaka Albarka idanuwansa suka dinga zubdaí ½í¸­ inama yanda yake da iyaye nagari sukai masa fada yaji Raliya ma tanada su da Aurensu yazauna lfy daga can saman kansa yaji umma nafadin tashi kaje kada dare yayi Allah yayi maka Albarka yamike sumu sumi yana fadin Amin yawuce shikenan kyau zai bar gidansu zai bar cin abinci Ummansa ya isa kofar gidan nashi da babur dinsa yasauka yatura kofar ga mamakinsa sai yaga kofar abude take donhaka yatura babur dinsa yashiga tundaga tsakar gida yafara jiyo kugin radio ankure wakokin turawan zamani mamaki yacika shi domin dai daga dakin dake kulle wakokin suke fitowa yasan wannan dakin baccin Raliya ne yakada kai yanufi dakinda aka jera kujeru aciki domin yasan dakin da raliya take bazaisamu damar kwana acikiba ko bata rufo kofarba balle dakin abame yake ma har ya kwanta akan kujera yaga dacewar yakoma shagon gidansa kawai da kayansa ya zauna nanne dakinsa da asuba yatashi ya nufi masallaci tayi sallah yadawo yafara lazimi kamar yanda yasaba daman baisanya ran raliya zata tashi tayi sallah ba domin yasan batada wannan tarbiyar sai wajen 10 nasafe take tashi ai kuwa yau dinma hakane saida rana tatake sannan tatashi lokacin tuni yadade da karyawa domin flask yadauka yaje yasiyo musu shayi dayasha yabar mata nata aflask duk da yanacan daki yana hangota ta windo yaga tafito amman abinda yabashi mamaki har karfe goma raliya bata fitoba kuma gidan ba irin na yangun nan bane mai bandaki aciki balle yace tayi Alwala aciki can saiyajiyo sautin radio ansa kidan jiya naturawan zamani yaso yashareta amman sai yatuna yanzu hakkin raliya da tarbiyar ta duk suna kanshi dole yatunatar da ita gaskiya don haka yamike yanufi dakin nata yatura kofa dasallama tadaga kai cike da tsananin mamaki tana dubansa shikam yanayin daya taddata ne yasanyashi tsananin firgita da rudewa domin wata yar figigiyar rigar bacci ce ajikinta dukkan surarta tana waje jikinnan nata yayi jajur tasha man kanti gashi tana kan kurciyarta saiwani sheki da sulbi fatarta keyi 9⣠DAME AKE ADO Wani abu yadinga jin yanaimasa yawo cikin kanshi saboda baitaba baitaba ganin wata mace cikin irin wannan yanayiba yayi masa wani kallon banza sama dakasa tana yatsina fuska tace inazaton kayi batan kaine ko malam yanayin yanda tayimasa maganar yayi gaggawar dawo dashi cikin haiyacinsa yayi kokarin tattaro jarumtakarsa da nutsuwarsa yasanya akan fuskarsa duk da zuciyarsa tayi kokarin bijirema hakan sannan yayi kokarin zakulo abinda yakawoshi inatasau raren ganin kinfito kinyi sallah asuba saikuna naji kin kunna radio ma alamar bakida niyyar gaida ubangijinki Tayi dariya tayi shewa tayi masa irin kallon da akeyiwa yantasha Au ashe fa Ustazu aka kakaba mini ko? Wai kayi zaton zuwa nayi zama agidanka dan Allah dubeni kadubi fatata aikasan banyi kalar dazan iya zama acikin wannan gidan kirar talakawaba talauci yahaifeni nakuma yadda nazauna natayu acikinsa amman bazan yadda na dauwama har nakare rayuwata acikin saba batun sallah kuwa kada ka matsamini domin ba kabarinmu dayaba bakuma bazo zama bane jira nake kashigo kabani red card dina Ransa yabaci ainun banda kaddara me ye hadinsa da Raliya komai jahila bata iya komaiba sai wauta amman ace itace matarsa takuma zage tana zaginsa haka yayi kamar yakara magana saiyaga rashin dacewar hakan danhaka yajuya da zummar ficewa saiya jiyota daga bayansa tana fadin malam fitafa bata kama kaba gwara kasallameni tunban yagama rigar mutuncinkaba baikulataba yafice domin tunaninta irin na dabbobine idan yaci gaba dajinta komai na iya faruwa kawai sai yafice daga gidan yaukam abin yafi najiya domin tundaga kofar gida akejin sautin kida yashiga da sallama badon yasan zatajiba sai domin mutanen boye abin mamaki saiya hango takalmi barkatai na mata dakuma hayaniyarsu anata shewa ga tukwane da kwanuka Nan anyi girki anbata gidan yayi faca faca harda garar abban

See translation 18 April 2015 at 11:18 · Public Save · More Like React Comment Share Like50 Write a comment...

· Yahuxa Kabir hmm raliya abi duniya a sannu Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Babangida Lawan Miko Da kyau Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Hassan S Saddiq ttnx Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Maman Ihsan mungode Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Rukayya Abba nice Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Kabiru D Shagari Tnks. Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Jameeylarh Dalhart sannu da kokari Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Muazz Alawo Weldone Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 Abubakar Ibrahim Pls my friend be patient, everything will be normal soon Like · React · Reply · More · 18 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 7. duniya tayi mata yanda takeso kenan tsawon sati guda kenan anazaman yan marina agidan babu wani da Raliya dakeyi na zaman Aure hatta shara shiyakeyinta wanke wanke kawai take yi shima dan ita take bata kwanikan da kawayenta dake wuni kullum agidan dayafita aiki sukuma zasu dira basu barin gidan sai dare zuwan Lami nafarko kuma nakarshe shiyakara dagula komai suna daki ita da diyarta sunata kulle kullensu ya iso gidan agajiye yake tubus domin yau bai tsaya hutawa ba kamar yanda yasaba yana rashi daga aiki yayo gida kawai kai tsaye yashigo da babur dinsa gidan Dai dai lokacin da yaji Lami tafito daga dakin Raliya nabiye da ita furucinta nakarshe ne ya doki dodon kunnensa 1⃣2⃣ DAME AKE ADO 2 Yayi tsai yana jiyo ta tana ta habaici da zage zage dukkan kalamanta bakomai bane illa tunin kalaman da mahaifiyarta kegaya masa sanda yana yaro har ya girma bashida abinyi bayan neman tsari daga shaidan dan kada yatunzurashi ya aikata abinda zaisanyashi dana sani agaba yana jin kiran sallah magriba yayi sauri yafice dan bada farali acan masallaci ya zauna yana lazimi har akayi sallar isha I yayi sannan yanufi wani gidan Abinci namasu karamin karfi yaci yakoshi ya jima agurin yana tunane tunane domin yarage dare fatanshi sanda zai isa gidan Raliya matar jaraba tayi bacci don haka sai wajen karfe shadaya yanufi gidansa ya tura kofar a hankali ya shiga yamaida kofar yarufe cikin gida yawuce yadauro Alwala domin dai yau daren jumua ne waton ranar Alhamis daren da Allah kanyi saurin amsar Addua bayinsa don haka yayi Alkawarin kaima Allah kukansa shima yau yazabamasa Abinda yafi Alkhairi yana sallah yajiyo bugun kofar raliya kamar zata balle masa kofar abinda yabashi mamaki biyu ne na farko kofar abude take amman taketa dukanta nabiyu kuma me yakawota dakinsa saidai yakula bazata barshi yayi sallah nan idan har baikulataba dan da karfi take bugun kofar tayi kokarin yin sallam yanufo kofar yadubeta sanda take kallon sa tadaina dukan kofar cikin tsananin mamaki yace lfy takalleshi araine tayi wani tsaki zuwa nayi Amsar sallamata domin nagaji dazama wannan akurkin naka nakula bakada zuciya domin kare yacinye dazai iya dayanzu zaiyiwa Raliya saki dubu sai dai bazai iya baiwa iyayensa kunya ba amman yau yakamata ya nunawa raliya shima fa baya kaunarta ko sau daya cikin kallon isgilanci yace waikina zaton ina zaune dakene dan kyawon fuskarki ko kyawon jikinki kiwata dabia maikyau dana gani agareki kiyi sani kamar yanda kika tsaneni kika kuma tsani aure na kodon inasonki a a kodaya nima haka nakeji harnawa ya linka naki tayi shewa da dariya tana kallonsa cikin tsakiyar idonsa da tsananin raini da wulakanci Ahayye wannan shi akecewa shege yi da maizina kaiko rayiwarka kayace nikam zan iya duk abinda naga dama nadawo natuba nakuma Auru sabanin kai da anriga anrubuto kai shege ne babu kankara shut up stupid yadakamata wata irin gigitacciyar tsawa data sanyaya firgita yaci gaba damagana cikin bacin rai koda nakasance shege wlh nafiki Albarka damutunci a idanuwan kowa dabba shashasha kiyita gorin naki dafadar abinda kikaga dama domin halinki irin na wawaye ne jahilai amman kisani idan har ga hannuna saki yake bazan taba sakinki ba sokuwa kawai yajuya dazummar komawa cikin shagon saidai riko wuyan rigarsa datayi tabaya ne yasanya yakasa cigaba datafiyar tarikeshi katamau tana fadin wlh ba indazaka saika sakeni meye kawai banda naci banason aurenka dolene wlh yawon karuwanci yafimin wannan kalgaggen auren naka zuciyarsa yadinga zillo datafasa afusace ya banbare hannuta cikin zafinrai ya hanbareta tayi taga taga tafadi warwas akasa tayi karo dabango tafasa wata kara domin hannunta yabugu da alama tayi targadema tafashe dakukan azaba ya kalleta dajan ido yana fadin sokuwa kinyadda duka guda zai iya maganinki kisani bawannan rayuwa ce agabanaba tadabbobi inada hankali da tunani idan har kinason rabuwa dani kije can kisami can wadanda suka daura kisanar dasu yamaida kofar yarufe raliya kam dakyar tatshi daga faduwar datayi tanakuka sakale da hannuta saidai bakinta bai mutuba taci gaba datijara ta Allah ya isa shege tsinanne dan mahaukaciyar kan bola daba asan aslinsaba duk abinda yazo bakinta fadi takeyi afatanta nata tunzirashi yafadi kalmar saki agareta kamar yanda Lami tabata umurni tagayamasa kalaman dazasu tunzirashi amman baice uffanba saidai hawaye

See translation 20 April 2015 at 07:54 · Public Save · More Like React Comment Share Like52 Write a comment...

· Murtala Ibrahim Dan halak kayi Like · React · Reply · More · 13 Sep 2018 Mukhtar Moh'd Mopol good Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Hussaina Umar tnx Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Abdullahi Mai Nasara Abdullahi Mdk Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Abdulrahaman Shuaibu Tnx Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Azinatu Umar MUNGODE Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Ahmad Sabo Kwana 2 ko saceku akai ne? Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Khadijat Ahmad Mashi Ammafa yayi hakuri sosai Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Ayshee Mohammed 5 Like · React · Reply · More · 20 Apr 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 4 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 8. baice uffanba saidai hawayeí ½í¸­í ½í¸­ dayake zubdawa yana tasbihi ga Allah afili dazuci harzuwa lokcin datagaji datijarar takama hanya tawuce dakinta tana kukan bakinciki kukan nata kashi biyu ne nafarko narashin cikar burinta nasakinta dayakiyi nabiyu kuma nabugewar datayi hartayi targade dayadaina jinmuryarta saiyamike yaci gaba da sallarsa yana kuka yana sanarda Allah halin dayake ciki ..........DAME AKE ADO 2 .................Saiwajen karfe 3 dawani abu nadare yaji gwiwoinsa sunyi sanyi idanuwansa sunyi nauyi babu abinda yake bukata illah yakwanta yahuta don haka yayi addua yakwanta bisa tabarmarsa cikin kankani lokaci kuwa bacci yadauke shi saboda rashin bacci daibaiyi da wuriba yasashi yamakara baitashi da asuba yayi sallah ba saida hasken rana yashigo dakin ta wundo ya haskemasa ido sannan yafarka afirgice ya duba agogon dake jikin wayarsa saiyaga yanuna karfe 7 nasafe yamike dasauri yana istigfari yanufi kofa yabude kaitsaye cikin gidan yanufa don daura Alwala abinda yabashi mamaki yau baiwuce rashin jiyo sautin kidan raliya ba wanda kullaum dashi take farkawa kamar shedaniya yashiga yakama ruwa yadawo yatsuguna gundi rariya yana daura Alwala yana satar kallon dakin nata yana adduar Allah yasanya harya gama Raliya batafitoba domin bayason ko kallon fuskarta cikin ikon Allah kuwa har yakammala din bata fitoba yanufi shagonsa yayi tusur cike datsananin tsoro domin ganin kofar gidan abude abinda yabashi tsoro kuwa tunda suke agidan raliya bata taba bude kofar gidaba yawaiga cikin gida saiyaga babu takalman Raliya akofar dakinta dasauri yadaga labule gamamakinsa saiyaga duk anwatsar da kaya acikin sif dakin yayi kaca kaca da alamar andibi wasu kayan gabansa ya kuma faduwa badai gudowa raliya tayiba dagacan kan gado yahango wata takarda ayashe ya isa dasauri yadauka yabude cikin wani cukurkudadden Rubutu yaga sakon nata yafara karantawa BAKA BUKATAR SALLAMA DOMIN BATA DACE DA SHEGE IRINKABA DUK WASU HANYOYI DA NASAN ZAN IYABI DON GANIN KASAUWAKEMIN WANNAN KALGAGGEN AUREN NAKA NABI AMMAN KAKI SAUWAKEMIN DON HAKA NABI HANYAR DATAFI DACEWA WATON NAGUDU NABARKA DA AURENKA IDAN KAGA DAMA YANZU KA IYA AIKAMA IYAYENA DATAKARDAR SAKINA DOMIN SANDA ZAKACI KARO DAWANNAN TAKARDA TUNI NAYIMAKA NISA KAIDA RAYUWARKA SAIKUMA ACIGABA DAZAMAN GAURANTAKA DONNASAN HARKA KOMA GA ALLAH BABU MACEN DAZATA YARDA TA AURI SHEGE BA .SAIWATA RANA RALIYA yaruntse idanuwansa sanda yakai karshen takardar sako mafi muni dazafi da idanuwansa suka tabacin karo dashi yajima tsaye yana tunanin meyadace yayi farincikin rabuwa da Raliya ko kuma bakin cikin gudunshi datayi 1â£5⣠DAME AKE ADO2 Mlm jibrilu ne yafara tambayar yaya akayi yaya Allah dai yasanya lfy domin naganku cikin damuwa malam sulaiman yamika masa takarda yana fadin karanra kagani malam jibril yakalli takarda batare da ya amsaba yace yaya aikasan ban iya karatun boko sosai ba danhaka bana gane kowane rubutu balle wannan danake ganinsa kamar zane tsutsotsi mlm sulaiman ya gyara tsayuwa yanuna masa takardar yace kaga wannan takardace da raliya ta rubuta kafin tatafi yawon karuwanci mlm jibrilu yadafe girji dadamuwa yaya wane irin yawon karuwanci kuma A iya sanina Raliya tana gidan mijinta naji dadi dakace a iya saninka alama bakasan gaibuba kenan to kabuda kunnuwanka dakyau kaji Raliya tabar gidan amadu yau da asuba bayan duk tayi wani cinmutunci dazagi baikulataba tabar wasika takuma ce dazaman auren Ahmadu gara taje tayi karuwanci yafiyemata kaga abunda nake nusar dakai tun abaya ko? Mlm jibril yayishiru cike da tsananin damuwa yamarasa mezaice dan idanuwansa sunkada suyi jajir gwanin bantausayi itakuwa Lami babu wata damuwa ko kyas atare da ita saiwani fici fici take da idanu irin namarasa gaskiya tana kara tsare gida mlm jibril yace yanzu to yaza ayi kenan kobin sahunta za ayine? Abita ina Raliya bayarinya bace tunda har taiya hada kayanta tagudu takuma furta kalmar tafiya karuwanci abin yakai intaha saidai Abinda tace Ayau zankaryatashi da tace sai dai Ahmadu yamutu babu Aure to tayi karya itace zata mutu babu Aure ba Ahmadu yaron kirki ba taje duniya fadine da ita wanda baizobama jiransa take yakada kai yashige dakinsa yana huci Umma kam saicika take tana batsewa tamkar tashako lami domin tariga tagane dasanya hannun lami takuta tace idan anguji dan wata illah abanza domin shi baida laifin kimai wanda kuma yake aikata irin laifin kumafa ? Karuwanci sana ace babba mai lasisi saidai tanada darussanta muna zuba ido muga karshen butulci darashin tarbiya lami takulu da kalaman umma tayamutsa fuska tana fadin oho kome za afada taba tarago tunda aibamu mukace raliya tatafiba duk kuma inda take Allah ne zaikareta Allah bazaikare Raliyaba lami yarinyar data tafi da hakkin mijinta da Aurenta kike zaton zatasamu kariyar Allah wlh ta barranta daga rahamar Allah bakuma zanyafemata wannan tozarci da cinmutunci dajamini ba Ahmadu dayake namiji yayi hakuri amman ita takasa taje duniyace mlm jibril yakarasa maganar tamkar zairushe dakuka domin yana ganin iyakacin tozarci raliya tayimasa Lami takuma cika afili tace Allah dai shike raba rahama ba mutumba mlm jibril yabita da kallo kamar yashakota amman saiya dake yakyaleta ya gyada kanshi yana kallon kofar dakin yayansa yace malam kafito mukarasa maganar nan kayi hakuri Ahmad dai yana durkushe yana kallonsu. Abdullahi maitama. 09034598552 @whatsapp

See translation 21 April 2015 at 08:47 · Public Save · More Like React Comment Share Like68 Write a comment...

· Maryam Muhammad Abashi ma'u kawai kowa ya huta tunda iyayen bazasui mishi goriba itama ma'un da wuya taimai gori 1 · Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Maryam Muhammad replied · 2 replies Aminu Ibrahim thanks Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 4 May 2015 Marvin Jonnhy Dakyau Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Abdull Muh'd Thankx oga kahuta Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Isa Sileman Thank Like · React · Reply · More · 22 Apr 2015 زينب عبد القادر Zai aure ta ai ba shiri gashi bata iya ko girki ba shi yake yi Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Aminu M Sirajo Tnx Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 حفصة أبو بكر tnx Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 Umar Bala Muhammad THANKS Like · React · Reply · More · 21 Apr 2015 View more comments…

Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 9. 1⃣6⃣ DAME AKE ADO 2 Daga masallaci makarantar su Asma u yanufa yadaukota daga can bakin kofa yaji wata sinio tana kwala mata kira Asma'u sulaiman tana ina tamike dasauri jikinta yana rawa tayi zaton wani laifi tayi kokuma dealing dinne yamotsa na sinio hajara domin shegiyar kazamace kayanta har tsami suke dahaka takwace kanta da maryam kemata kalbar da maryam keyimata tanufi wurin sinio hajara tana fadin tanafadin senio hajara gani senio hajara takalleta sama da kasa da alama yarinya uwarki ko ubanki sun mutu domin sir Abdul yace kije kitafi da dukkanin kayanki domin gidanku zaki wuce ma'u tadafe kai cike da fargaba sai tafashe da kuka tana fadin wayyo nashiga ukku Allah yasanya ba umma ko abba bane suka mutu ba wayyo Allah ni ma'u nazama marainiya ihu takeyi iyakacin karfinta gabadaya hostel akayi shuru anakallonta kawayenta tuni sun iso inda take dasauri suna tambayar abinda yafaru senio hajara takama masifa ke sakarya nibance miki wani naki yarasuba cewa nayi kawai inajin kihado kayanki muwuce kusai kutayata debo kayan nata ta kalli sauran kawayen nata dasauri ma'u tanufi gurin kayanta taci gaba da hadawa tana kuka sosai kawayenta suna bata hakuri da rarrashunta sanda suka isa wurin sir Abdul yakalleta damamaki yana fadin ma'u meyasanyaki kuka? Cikin sheshshekar kuka tace senio hajarace tace wai babana ko ummana sunmutu yabata rai matuka yace inji ubanwa? Hajara tanada matsala kawai nace kihado kayanki babanki zaitafi dake shike nan zatace haka barta kawai karya takeyi hankalin ma'u yadan kwanta saidai tana cike da tsananin mamakin abinda zaisanya babanta yazo daukarta bayan anfara jarabawa bukin yayanta kuma ankammala tuni domin alissafinta yau sati biyu kenan da bikin yayanta kokuma dagawa akayine dawanna tunanin tayi sallama dakawayenta sir Abdul yadaukar mata wasu kayan su maryam da jamila suna bata sakon abinda zatasawomusu idan zatadawo tana cewa to batasan wannan ce rana takarashe dazata kara komawa wannan makaranta ba dasunan karatu ba yaune dazata rabu dakawayenta rabuwa tahar abada kuwa ta isa ta tadda abbanta zaune a ofis din principal suna wasu magunguna dabata fahimci komaiba hankalinta yadan kwanta saboda ganin abbanta bakuma cikin wata da muwaba ta durkusa tagaisheda abbanta tagaida principal Abban nata yamike yana fadin to hajiya nagode Allah yataimaka yakuma kara daukaka principal tamike tana fadin Ameen amman munyi missing daliba maikwazo da hazaka Ubangiji yatsareta aduk inda take malam yace Amin dasauri principal tadaga kan ma'u tana fadin Allah kaddara saduwarmu kidage bisa kyawawan halin danasanki kinjiko? Itadai ma'u to kawai take cewa batasan me ake nufiba abbanta yadaukar mata wasu daga cikin kayanta tadauki sauran suka nufi titi sanda suka isa gida anata kiraye kirayen sallah magriba Umma tana kicin tana kokarin hura wuta da alama tayi daren tuwo ne tajiyo sallamarsu ta mike da mamaki tanafadin malam kamar muryan ma'u nakeji mamaki yakoma karuwa ma'u cedai biye da Abbanta yakalli Asma u yace bakama bace deeje itace yanzu na daukota daga makarantarsu mamaki yakoma cikata tace malam amman banji lbr anyi hutuba naji kamar jarabawa suke ma lfy yanufi kofar bandaki ya dauki wata buta da aka ajiye daruwa yana magana lfy kalau kidai kiramin dukkan yaran gidannan awaya kice inason ganinsu idan nadawo daga masallaci zakiji karin bayani yashige cikin bandaki don yakama ruwa Umma tamaida kallonta ga ma'u kamar zata koma tambayarta sai kuma tafasa tace shiga dakayan cikin daki kizo kidaura Alwala ma'u tayi abinda mahaifiyar tata ta umurceta bayan tacire uniform din dake jikinta tasake kaya tafito ta daura Alwala itakuma Umma kokarin fara kiran wayoyin yaran gidan ta isar da sakon da mahaifinsu tasanardasu sannan tadaura Alwala tashiga sallah 1⃣7⃣ DAME AKE ADO 2 Har suka kammala taruwa malam din baishigo ba domin saida ya tsaya yasiyo goro da alawa yataho dasu suna tsakar gida bisa babbar tabarma anata tattaunawa akan maganar gudun Raliya Rabiu yace wlh dani tahadu dashi datuni lbr yasha bamban shegiya kodaddiyar banza kawai taje indai duniya ce wanda baizobama jiransa take shidai Ahmad jinsu yake yana jin tamkar Anrabashi da wata babbar masifa ne arayuwarsa domin kallon raliya bayason yakoma yi yasan Allah ne ya.amshi adduar sa yayi gaggawar rabashi da ita saidai kamar yanda tace din yasan shida aure har abada domin bazai iya kara tunkarar wata mace da sunan yana sonta ba balle haryajawa kansa wulakanci ba zaici gaba dazama ahaka idan yaji zai takura sai yayi azumi Sallamar malam dince ta katse musu hirar su Ahmad yamike da sauri ya amso kayan da malam din yashigo dasu yana fadin sannu abba yakarasa yazauna akan tabarma da yaran ke kai daya bayan daya suka dinga gaisheshi ya .amsa sannan ya kalli Umma yace ina ma'un take kuma? Umma takalli kofa tana cikin daki kasan indai yayanta suna hira bata fitowa cikinsu tazauna wata kilama tayi bacci kotayi bacci atasota yakalli kofar dakin ma'u Asma'u kina inane tafito dasauri tana goge idonta inaciki Abba kadawo sannu dazuwa ya.amsa yauwa samu wuri zauna sannan yaturawa Umma buhun Alewa da goro dake gabansa yana fadin bude kigani deeje Umma taja buhun tafara budawa tadaga kai takalle shi da mamaki goro da alewane kowakilcin Aure zakayi kodaya goron daurin Asma'u da Ahmad ne an daura tundazu a masallacin jumu'a na gidan maimartaba mamaki yakama kowa har akarasa mai iya karfin halin.

See translation 23 April 2015 at 10:45 · Public Save · More Like React Comment Share Like50 Write a comment...

· Atika A Umar NICE one Like · React · Reply · More · 24 Apr 2018 Hureira Suleiman Tnks Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Abubakar Ibrahim Tnx Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Muazz Alawo gud Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Musa Abdullahi 9ce Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Abashiyyah Umar waww nyc wlh dame ake ado nake so......bcox akwai nishadi.... Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Surayyah Abdallah thanks Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Bala Sani Hafsat Tnxxx Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 Dauda Gimba Tnx Like · React · Reply · More · 23 Apr 2015 View more comments…

Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 10. Umma ce tafara karfin halin yin magana tace malam kaji abinda kace kuwa ? Malam ya gyara zama kwarai da gaske saidai idan kece bakiji ba nasake maimaitamiki goron auren diyata Asma'u da Ahmad ne wanda aka daura dazu a masallacin gidan sarki Ahmad yaji wani abu dim akirjinsa tamkar ancaka masa mashi gabadaya kuzari da tunaninsa ya kwace yama rasa meyada ce yayi Auwalu yayi kokarin yin magana cikin yaran Allah yasanya Alkhari yakuma zaman lfy da zuri'a dayyaba gabadaya suka amsa da Ameen sani yace baba yabatun karatunta kuma wannan yana hannun mijinta dukkan hukunci da yazartar shine daidai daman karatun badole bane ba 1⃣8⃣ DAME AKE ADO 2 Umma ta girgiza kai tace hakane to yanzu yaya za ayi kenan malam Gyalenta zata dauka tayafa suwuce gidan mijinta wannan goron kuma da alawar kirabashi gidan makota domin suma sushaida Ahmad yakalli abbansa Afirgice daidai lokacin da Asmau takalleshi itama saitake ganin abin kamar amafarki anya kuwa dagaskene haka daman ake aure Umma takwantar da kai tace malam da anbari har ashirya ahankali sai akaita yadaga mata hannu babu wani shiri dazaayi kidauko mata hijab dinta suwuce da mijinta duk wanda kika aikawa da goron kice har tatare gidan mijinta fakat akayi shiru babu mai abincewa malam yadubi Ahmad wanda yakasa motsi tamkar anzare masa dukkan lakkar jikinsa yace tashi Ahmad kama matarka kuwuce gidanku Ahmad yayi firgigit yamike har alokacin yana tsammanin zolayace amman yasan Abbansu bayamasa irin wannan wasar Umma tamike tashiga cikin daki tadauko hijab tamikawa Asma'u tana fadin Allah yayimaki Albarka yabaku zuria dayyiba yasa Anyi kenan sauran suka amsa da Amin ma'u ta amshi gyalenta tasanya takasa yin komai don tsabar fargaba kamata kuwuce mana malam yakara basu umurni Ahmad saiyake ganin da kunya yakama hannun ma'u musaman da malam ya ambaci matarsa ce wai ayau don haka yawuce dasauri yanufi soro agobe yake kokarin yatattara kayansa yadawo rayuwa da ummansa ashe bashida rabon sake zama tare da ita wato yabarta kenan har abada Umma takama hannun ma'u domin takula duk tarude tarikice gabadaya abinda kedamun umma dayane yanda bata taba koyarda ma'u komai na rayuwar gidan mijiba atsammaninta saitakara girma takara wayo da hankali ashe bazatakai wannan lokacin ba ayimata aure ba bata tsammanin kofar shinkafa ma'u ta iya dafawa wannan kadai shine abinda zaidameta har abada har saida takaita bakin zaure sannan tatsaya tana fadin maza wuce kutafi Allah yayi muku Albarka Malam dasauran yaran suka taso suka rakosu hargaban babur din sannan yakarkatamata takama ta hau yatuka suka tafi suna daga musu hannu malam yadubi sauran yace to masu iyali suwuce gidansu kukuma marasa iyali kushiga kutaya mahaifiyarku kullin kayan daurin aure nizan wuce gidan malam habu nasanar dashi dahaka yawuce suma yaran kowa yakama gabanshi sai samari dakanana ne suka shiga cikin gida suka fara din Salisu yace Umma waidaman kunshirya hakanne da Abba bakusanar damuba Umma tagallamasa harara tace bansaniba tambai sarkin tambaya sainaji matsa zanbaka Amsa yanda ta amsa maganar afusace yadan bashi tsoro yace Allah yahuci yahuci zuciyarki Umma kiyi hkr hakan datayiwa salisu yasa kowa yakunshe tashi acikinsa saiwani lokaci Ahanya suna tafe bisa babur kowa da abinda yake sakawa cikin ransa itakam ma'u har lokacin bata yadda ba mafarki takeba domin ko alittafin hikaya bata tabajin irin wannan lbr maiban mamaki ba shi kam Ahmad jinjina kyautayin da karamcin bayin Allah nan ne aransa dama zai iya sakamusu da karamcin dasuke yimasa waye zai iya aikata irin wannan abin dasuka aikata awannan zamani daya lalace darayuwa irinta jari hujja tabbas sai antona harsuka isa kofar gidan kowa yana sakawa da kwancewa yatsaida babur din yasauka yarike yana fadin sakko 1⃣9⃣ DAME AKE ADO 2 Yakalleta da kulawa saiyaji duk kunya dafargaba sun kamashi wai ma'unsa kanwarsa yau itace tazama matarshi Allah sarkin iko dabuwaya yadaure yacemata muje mana Tashige yanabinta abaya har suka isa kofar yasanya makulli yabude suka shiga tatsaya atsakar gidan tana karemasa kallo bata kawo komai arantaba sai daman anshirya komai itace kawai ba asanarwa ba tunda gashi har gidan antanada ansanya komai yakalleta amman baibari sunhada idoba yace kije dakin can kiyi sallah ki kwanta dasauri tace to tanufi dakin kamar wacce ke kan kaya daman yabita dakallo har tashige sannan yanufi dan dakinsa shago yasamu wuri yazauna yadafe kumatu Raliya ta tafi Asma'u tashigo shin ita wanne irin zama zasuyi kenan ko amafarki baitaba hango wannan ranana balle idan yafarka yayimata wani nazari hakan yasanya yakasa tabuka tunanin komai sai gyada kai kamar dan kadangariya tana shiga daki tazauna gefen gado tana karewa dakin kallo daga gani natane sabuwar amarya amman yaya akayi ba asanarda ita komaiba duk wani shirin da akeyi meyasanya sanda yaje baisanarda ita cewar za ahada auren su ba sai yabata lbr Aurensa da Raliya amman da alama shima baida masaniya akan komai tuno raliya datayi yasanya zuciyarta yin kunci waton daman ita kishiyar raliya ce a iyakacin tunaninta bata taba tunano zasa hada miji da Raliya ba meyasanya su Abbanta sukayimata haka tadafe kirjinta yana bugu kamar zaibullo yayo waje idanuwanta suka ciko da kakwalla jikinta yadauki rawa saitakejin kamar ana likamata kiyayyar raliya aranta kishi maigirma yarufeta saita fashe dakuka meya sanya rayuwarta tazomata da wannan akasin itama matar yayanta Ahmad ce tadade tana kukanta kamin tayunkura tafito tsakar gida tadauro alwala takoma daki domin yin sallah ta idar da sallah tana kallon dakin tana lazimi tana sakawa da kwancewa harzuwa sanda tagaji tamike da hijab din jikinta dakomai tahaye gado takwanta saidai me haushin karnuka datake jiyowa akan titi dakukan gyare sun sunhadu sunbirkitama ta tunani sun assasamata tsananin tsoro bata taba kwana ita kadai adakiba idan tana gida tana makale bayan ummanta har bacci yadauketa sai cikin dare umma ke zamewa tagudu dakin maigidanta da anyi kiran sallar farko tadawo takwanta amakaranta kuwa dakinsu su goma shatara ne don haka bata taba kwana itadaya ba ta mike dasauri tana waigen dakin tome yakamata tayine shin yayanta yakamata takira kokuma rufe kofa zatayi harta kama kofa zata tura saitaji kamar anmata kuwwa cikin kunnen ta danhaka tafito daga cikin dakin dasauri danma dahasken wutar nefa tajima tsaye atsakar gidan tana sakawa da kwancewa tarasa madafa saitaga kamar gidan yana yimata gizo dan haka tayi soro dasauri yayi sa a kofar dakin nasa abude take dan haka tasamu guri ta tsuguna tanannade jikinta cikin hijab tamkar maijin sanyi ahaka har bacci yafara daukara 2⃣0⃣ DAME AKE ADO 2 Ahmad yanaciki baisan abinda kefaruwa asoronba tunda yazauna yakasa motsawa yarasa abinda yadace yayai tsawon lokaci yana awannan halin hardare yafara ja saiyaga dacewar yatashi yadaura Alwala yayi sallar isha'i sannan yanemi yardar Allah da amincinsa bisa wannan auren dayazomasa bagatatan yamike yanufi kofar dakinsa yayi baya tsorace yana ambatan sunan Allah domin karo dayaci da ma'u wacce keta shirgan baccinta haikan babu wata fargaba saida yanutsu sannan yasan itace mamaki yakoma kamashi yamatsa kusa da ita yanakallonta meyakawota nan meyasanyata bacci ahaka cikin daga murya yafara ambaton sunanta domin yaga alamar batasan dashi agurinba tafarka afirgice cike da tsananin tsoro dafirgita tana waige waige yadurkusa agabanta nine nana kwantar da hankalinki meyakawo ki nan kina bacciya yafada cikin rarrashi domin yakula duk akidime take tayi narai narai da idonta domin tana tsoron kar yadaketa Allah yaya tsoron dakin nakeji sai naji kamar anamotsi abayan kyauren yayi murmushi yace nana haryazu ke sokuwace ko? Tomeyasanya baki sanar da niba tasunkuyarda kai tanasosa keyarta cike da tsananin kunya yakula tunda suka iso gidan ma 'u kejin kunyar hada ido dashi shima nauyinta yakeji kwarai dagaske jinbata niyar cewa komai yasanya yamike yakama hannunta yanafadin taso muje ki kwanta kada kikara kwanciya anan bamusu tabishi amman hankalinta amman hankalinta yatashi saboda rikemata hannu dayayi saiya sanya tsikar jikinta tashi ahaka harsuka isa dakin yazaunarda ita gefen gado yanafadin to kwanta bari nakwanta akasan yadauko filo daya daga kan gado yajefar kan tayal yakwanta yajuyamata baya Umma tana kwance datsananin damuwa idonta nazubda hawaye batasan sheshshekar kukanta yabaiyanaba malam yamike zaune yakunna fitilar dakin yakalleta duk da tajuya masa baya yasan ba bacci takeyiba cikin raunanniyar murya yakira sunanta khadija kitashi nasan ba bacci kikeba tashi kisanarda ni dalilin kukanki tsoro dafargaba suka kamata ashe kukanta yabayyana har malam yajiyota tashiga ukku meyadace tayi yanzu nace kitashi muyi magana khadijah tsawarshi tasanyata mikewa dasauri jikinta yana rawa domin takula ran malam yabaci yatsareta da idonshi wanda yakada tayi jajir kisanardani abinda keranki khadija kigayamini komai da bakinki cikin rawar murya tace wlh malam bakomai araina karya kikeyi akwai abinda keranki deeje mutum bayayin kuka kawai saida damuwa nalura dake tunda nasanar dake auren ma'u da Ahmad yanayinki yasauya furkarki tanuna bakiji dadin hakaba shinkina kyamar Ahmad dan bayada ubane kece kike nuna jin haushin abinda wasu kemasa kamin wannan lokaci deeje baibarta tabada amsaba taci gaba dafadansa idan harkikayi haka kinbani kunya kinkuma ci Amanar ahmad Ahmad zaitabbatar da lallai bashida uwa bashida galihu kowa yana kyamarsa yakarasa maganar da kunci dazafin zuciya tadaga kai tanafadin kodaya malam wlh abinda kake zato nahaka bane bantaba kin Ahmad ba 2⃣1⃣ DAME AKE ADO 2 Bantaba danasanin kasancewarsa tare daniba bantaba danasanin zamanshi danaba haka banajin komai game da aurensa da ma'u kukan dakaga inayi banakin aurensu bane illah tausayinsu gabadaya Asma'u yarinyace karama bata iya komaiba saiwauta da tsiwa bankoyamata komaiba na rayuwar aureba nayi sakaci bantaba bata lbr meye aureba shikuma Ahmad yarone dabaisan komai gameda rayuwar aureba shin yaya zai kalli ma'u da halayenta inatsananin jin tausayin ma u dakewarta wlh wannan shine kadai abinda ke damuna amma har abada bazantaba dana sanin hada auren nan da akayiba nayi mamakinma da wannan zargin yazo ranka malam takarasa maganar datsananin damuwa yayi ajiyar zuciyar cike dagarinciki acikin ransa yana godiya ga Allah dayasanya ba abinda yake zargibane aran deejen ba yakalleta yayi murmushi Amman shirmenki yayi yawa waton har abada mace bata girma danwannan abinne kawai yasanyaki damuwa kodayake nasani harda soyayyar ma u dakukan rabuwa da itako yakarasa maganar da zolaya tasunkuyar dakai tana murmushi kasa kasa malam yaci gaba dajawabi kikwantar da hankalinki daga Ahmad har ma'u duk rainonkine watakima ahmad yafiki sanin halayen ma 'u dan haka babu wani abu dazaibiyo baya insha Allah sai Alkhairi nayi imani zaikoyarda ita komai tunda kinkoyamasa kokin manta da dannaki ya iya girki kala kala ne? Yakarasa yana dariya abinda yasanyata darawa itama ya dinga zolayarta haryasamu ta sakko Suka fahimci juna sannan suka kwanta baccinsu sunawa yayansu addua tunda asuba yatasheta tayi sallah shikuma yawuce massalaci bayan yadawo yazarto dakin yazauna yacigaba da lazimi itakam baccinta takara komawa aranta tanaganin babu abinda yafi gadonta dadi kamar wacce akatasa karfe bakwai tafarka ta tadda yayan nata har lokacin yana lazimi tamike tsam tanufi kofa ya bita da kallo kamar zaiyi magana saikuma yafasa don yayi zaton bandaki zatashiga itakam kicin tawuce tayi zaune tanasakawa da warwarewa akan abinda yakamata tayi domin sanda yatafi masallaci umma takira wayarshi tadauka umma tace waye tace nice tace yauwa daman kedin nakeson kidauka domin nasan yanzu Ahmad yana masallaci kinaji idan gari yawaye kishiga kicin ki girkamuku abinda zaku karya sannan kishare gidan kigoge ko ina nasan kin iya shara daguga dan kinayi amakaranta ko dasauri tace eh inayi tace to kitabbatar kinyi kinjiko? 2⃣2⃣ DAME AKE ADO 2 Takoma amsawa da to shine yanzu tana tsaka da bacci maganar Umma tatasheta tadauko doya tafara ferewa bayan takammala tayankata gutsi gutsi kamar zatayi faten doya sannan tadauki kwai ukku tafasa akan doya ta kunna risho tadora mai kozafi baiyiba takama kwan da doyar ta zuba tana jiran su soyu daga can acikin daki yafara jiyo kauri dasauri yamike domin zuciyarsa tabashi ma'u ce yanufi kicin din dasuri saiyaga doya da kwai da mai sunata zabalbala yarike baki damamaki yana fadin Nana mezakiyi? Mekike dafawa? Tayi firgigit ganin kallon dayake mata tace doya da kwai zanyi sai akacemiki kuma haka akeyi waye yasanyaki girki kuma baki iyaba cikin zafin rai yake maganar tayi kwal kwal da ido tana jada baya domin tana gudun kada yadoketa tace Umma ce tace nayi abincin Kari kuma............kuma..........yadoka mata tsawa get out mekika iya bayan shirme yadauko kaskon suyar daga kan wuta yayi waje dashi sukaci karo abakin kofa tana tsaye tana gunguni yayi baya dasauri dan sauran kiris yakifamata yakoma kuluwa yace Amman bakyajin magana nana bance kibar gurinnanba dasauri tawuce tabar wurin takoma gefe tatsaya yanufi gindin rariya da abinci yasamu kwano yazuba yasanya ruwa yawanke kaskon sannan yanufi kicin din tana tsaye tana kallonsa yadauki wata tukunya yazuba ruwa yadaura shayi duk tana tsaye tana hangensa yanata kaiwa da komowa acikin gida harya kammala dafa shayin yajuye aflask yanufi kofar gida tana ganin yafice tanufi kicin Don ganin abinda yayi bata hango komaiba tafara bubbude kwanika cikin tsautsayi bataga flask din yazuba shayinba tabangaje yafado jikake tush flask din yafashe shayin yazube atsakar kicin din tarike baki cike da tsoro dafargaba saita kasa gaba takasayin baya kamar ancilloshi yashigo gidan tundaga nesa ya hangota akicin yakarasa da sauri yana fadin nana meyakawoko kicin dinnan bance kada kisake kishigaba tayi tsuru tsuru daidai lokacin daya karasa yadauki dogon salati sanda yaga flask din shayi duk kwance akasa yana ambaliya ya kalleta yama rasa abinda zaice cikin rawar murya tace Allah yaya bangani bansan da flask agurinba yayi ajiyar zuciya yayi kokarin hadiye fushin shi domin ma'u yargaban goshin shice duk da banzan rawar kanta yanunamat kofa zokiwuce daki maza tataho tana rakube rakube tana goge ido tana gudun kada yadoketa har ta isa bakin kofa data samu tafice ta falla da gudu saida tadire acikin daki sannan tazaya tana haki da dariya wai Allah nagodema da yaya Ahmad ya mini irin ko rankwashinsa ne aida naga takaina tarike haba tana haki shi kam kada kai yayi da takaici sannan ya shiga yashare kicin din yakara dora wani shayin yazuzzuba akofi yakaimata nata hardaki ta amsa tana fadin nagode yaya 2⃣3⃣ DAME AKE ADO 2 yadaga kai kawai sannan ya zauna yafara shan nasa ma'u tadubeshi yana shan shayin tace yaya don Allah zankoma makaranta kaga ranar monday za afara jarrabawa kuma Abba yace saikayadda zankoma yadaga kayi yakalleta saiyaga ikacin gaskiyarta take maganar babu wani bayani dazaiyi uagamsada ita saiyace aibazakiyi wannan jarabawarba kihakura kawai tawaro ido cike da fargaba yaya kanufin nadaina karatu kenan kainefa kace zanzama likita yajijjiga kaida damuwa ma'u tayi kankanta da Aure tayi kadan dafuskantar irin wannan matsalolin donhaka gara yasanar da ita gaskiyar komai yadubeta da nutsuwa yace nana kinsan yanzu ke matar aure ce ko? Tadaga kai alamar eh yagyara zama yauwa kinga ai makarantarku ta yanmatace babu matan aure ko? Towannan dalilin yasanya bazaki kara komawaba kinkammala makarantar kenan yanzu zakizauna zaman aurenki kinemi Aljannarki tamike atsorace cike dafaduwar gaba yaya zakace haka yaya Ahmad shikenan niyanzu bazankoma zuwa ko inaba sainan gidan kuma bazan zama likitaba......yaya bakayin karya amman yanzu kayi meyasanya tambayar tacazamasa kwakwalwa harya rasa amsar dazaibata saiyasake hade ransa yace kincikani dasurutu nana tashi maza kiyi wanka kishare gidan kiwanke kwanika tayi narai narai da ido domin tana matukar son karatunta tace amman yaya...............yadaka mata tsawa isaid get out ma'u jikinta yadauki yadauki rawa hawaye yamakale ido yafara tafice dasauri ta nagoge idonta tana aiki tana kuka yanajiyo sautin kukan nata bashida zabi babu yanda zaiyi abba yagama yanke hukunci daga karshe ma saiyayi wanka yafice yabar gidan wannan shune yakara dagamata hankali saitaji gidan yakara mata girma tazauna tsuru babu abinyi sai tsoro yafara shigarta tamike tanufi soro takama leken waje tana hango mutane dake kaiwa da komowa saitaji sanyi aranta donhaka saita zauna akofar gidan tana kalle kalle dakaramin hijab akanta idan taga abin dariya tayi idan taga abin mamaki tayi mutane suna wucewa suna kallonta babu wanda yayi zaton matar gidance domin komakota basusan ankawo amaryaba sunyi zaton Raliya ce itakuwa daga yanayin kawayenta da gantalin datake fita kullum yasanya suka gano bamatar arzikiceba donhaka babu wani wanda yarabeta tsawon lokaci tananan zaune tana cike da nishadi shikam Ahmad gidansu yanufa kaitsaye yatadda yan uwansa sunzo dayake ranar assabar din karshe sati ce anata cafta saiyazauna anatayi dashi Umma saishige dafice takeyi wurin ganin takammala kirkin rana kunya da nauyi sunhana ta tambayi ma'u takula shima Ahmad kunyar yimata maganar ma'u yake amman daga yanayinsa talura babu wata matsala anan sukaci abinci lokacin da inna tazuba abincinne ma yatuna da ma'u da abinda zataci saidai Allah yataimakeshi umma tacika flask din da dambu datayi tadire tace gana yar gidanka Ahmadu yaji dadin hakan danyana kammala cin abincin yadauki flask yahaye babur dinsa yanufi gidanshi abinda ybashi mamaki da tsoro baiwuce hangon ma'un shi zaune akofar gida daramba tana hirarta da wasu yara da alama yayan makota tasamu tabiye musu yanacigaba da karatowa mamakinsa nakara linkuwa harzuwa sanda ya iso indatake da babur dinsa tadaga kai takalleshi saitadan firgita masamman yanda yanayinsa yacanza lokaci guda takalli yaran dake gabanta tayi duru duru sai tamike ta shige cikin gida dagudu batayi birki ko inaba saibayan gado tana huci talabe cankurya tana maida numfashi yashigo gidan ransa yana suya ya iso harbayan gadon yajawo kunnenta tafasa ihu jikinta naci gaba da bari dan Allah yaya Ahmad kayi hakuri Uban wa yace kifita waje kizauna komunkoya miji wannan tarbiyar agidane? Cikin sheshshekar kuka tace A ah gidan ne shiru ga tsoro shine naleka waje don Allah kayi hakuri tafashe dakuka yadunkule hannu ya rankwasheta yana fadin koda zanhakura saikinji ajikinki kifita kofar gida kizauna kamar wata sokuwa inakikakai aurenki yakoma rankwashemata kai kwas akanta takuma sanya ihu saida yajeramata guda hudu sannan yasakarmata kunne takuma fashewa dai kuka lokacin yafice daga cikin dakin yanufi shago domin yasanya uniform dinshi yatafi wurin aiki saidai yanashirin kukan ma'u yana dukan zuciyarshi tuncan baya bayason bacin ranta yakanyi komai dankar abatamata rai balle dayaji sunan mahaifiyarsa ne akasanya mata hakan yakara soyayyarta acikin zuciyarsa yanzu kuma gashi tazama matarsa wato yanzu soyayyarta agareshi hawa ukku ce don haka dole intana kuka yarikaji harcikin bargonsa da kyar yakammala shirinsa yanufi soro da zummar yafice saikuma yaga rashin dacewar hakan dan haka yajuya cikin gidan yanufi dakinta tana rakube a inda yabarta abayan gado tana kuka ya isa inda take tahada kai da gwiwa tana sharbe yakira sunana tadago takalleshi dafaduwar gaba don batasan yadawo dakinba tayi zaton kara dukanta zaiyi donhaka tafara ja dabaya tana sharbe majinarta tana kuka

24 April 2015 at 08:03 · Public Save · More Like React Comment Share Like51 Write a comment...

· Aminu M Sirajo Tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Omar Uba Abbaskk tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Bilkisu Mukhtar Tnx.. Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Zainab Yahaya Bappah mungode muna jira Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Hassan S Saddiq tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Usman Mustapha Yayi Kyau Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Faisal Sa'ad Isma'il Mungode Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Afra Ahmad Please ayi posting kallon kitse Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 Fatima Yaquub tnx Like · React · Reply · More · 24 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Sirrin zuciya DAME AKE ADO part 11. 2⃣4⃣ DAME AKE ADO 2 Dan Allah kayi hakuri wlh bazan kara fitaba nadaina..........yakada kai yana karemata kallo wlh da Abba yayi shawara dashi dazaice abar ma'u takammala karatunta tazama cikakkiyar mace kafin ayimata wannan auren yarinya ce tsaba yanzu tafara kirgen dangi irin namata baikallonta da komai haryanzu sai kanwarsa ihunta yadawoda shi hayyacinsa yace kinga badukanki zanyiba cewa zanyi kidaina fita waje idan nafita zanturo miki yaran sudinga tayaki hira kinjiko? Tadaga kai dagamsuwa tanacew to tuni kukun nata yakoma ciki tafara dariya gawannan idan kinason cin wani Abu kisaya gakuma abinci can aflask Umma tace akawomiki ta amsa hannu biyu tana godiya yakada kai yafice tabishi dasaikadawo yaya kamar yadda tasaba yimasa agida ya amsa da Allah yasa yafice takalli dari nan tadaka tsalle cike da murna waiyau itace keda dari duk tatace lallai Allah yasanya yara sushigo su siyomata agwalima yayi sa akuwa yan yaran dayatadda azaune dasu har lokacin sunanan zaune suna wasansu don haka yace maza suje sutayata hira dahanzari suka shige gidan suna murna sallamarsu tatsinkayo acikin gidan tayi waje dagudu cike da murna sai alokacin tahango flask din abinci tashiga kicin tadauko faranti tadebi nata suma tazuba masu nasu suka zauna sunaci suna hira itakuma tana kwasar dariya tundaga wannan rana gidan nata yazama gidan yara domin ance laifi yaro kiwa laifin babba rowa Asma'u kam hannunta asake yake akwaita da kyauta Ahmad hankalinsa yakwanta shike hadamusu abinci dazasuci dasafe darana da dare saidai idan yasan yanada aikin safe tun asuba zaidora kirkin rana yazuba aflask ya ajiyemata da daddare kuwa yazomata da ( take away ) domin yace batayi wayon dazatayi girkiba harta kunna risho ba aikinta kawai wanke wanke da shara ko wanki shine kemusu sanda yakeda lokaci saidai yanashan fama da kurciyar ma'u da shirmenta yautunda safe yakammala girkin yazubamata aflask yarufe harya kammala shirinsa tana gindin Tv tana kallon NTA muhawarace akeyi da daliban makarantarsu dana wata makaranta cikin harshen turanci tanajin kamar tatsallake tafada cikin tv idan anyi tambayar dayan makarantar suka kasa amsawa tasani saitayi karaf tace dan Allah kazane kuce kaza ahaka ya isketa tsahon zamani yana kallonta batasan yazoba tausayinta yakamashi ma'u tanason karatu kwarai shima yanason tayi karatun saidai yanada tsananin kishi bazaitaba yadda ace matarsa tanazuwa makaranta kullumba dama dai ace takammala karatunta akayi aurensu dayaga batada niyyar dawowa hankalinta yakira sunanta tawaiga dasauri tace la yaya harka gama shiri zo dan Allah kaga wadannan sokayen sunkasa amsa tambayoyo nafi sauki kumafa sinio dinmune a school yayi murmushi yace nana nidake sauri zantafi aiki inanakeda lokacin kallo amshi Nan yamikamata kudin tasanya hannu ta amsa yaci gaba da magana zanwuce sainadawo akwai abinci aflask banason barna dawarkai kada kilalata komai kinjiko idankuma andauke wuta kikashe kayan kallo duka dan kada akawo wuta sulalace ta amsa dato tana cigaba da kallonta haryakai bakin kofa baiji tace saikadawo ba yawaiga yakalleta yace yauba babu adawo lfy kanwata dasauri tace lah yaya namanta adawo lfy tana fadin haka tamaida kanta wurin kallonta yayi dariya yafice baijima dafitaba kuma nepa suka dauke wuta bakinciki kamar yakasheta domin taso taga karshen wasan takoma kan kujera takwanta tafara tunane tunanen duniya kwatsam yayarta kuma kishiyarta tafadomata saitaji gaba daya ranta yabaci saidai abinda kedauremata kai baiwuce rashin zuwa gurinta da yaya Ahmad keyiba ko maganarta ma bayayi sam tanason tatambayeshi amman kishi da haushi raliya yahanata don haka tabar abin cikin ranta tana kwance tana sakawa da kwancewa har kawayenta suka fara shigowa tamike tafita suka fara lido A'ilo daya daga cikin yaran ta kalleta tace waike ma'u bakyayin sabon girkine kullum saidai naga kindebo acikin flask ma'u tatabe baki da damuwa ban iya girkinba yayana ne yakeyi yazuba acikin flask A'ilo tace cabdijan to idan bakya gwalgwalawa yaza ayi ki iya kinganni bankai girmankiba har wake dashinkafa nake dafawa babanmu arisho bama da murhuba mamaki yakama ma'u tace ke A'ilo koni danagirmeki ummana bata bani girkina saitace kazantane saidai kawai na izamata wuta amman kice harwani girki akebaki A'ilo ta tafa hannu tadoki cinya shekarata shabiyu amman wlh ina girki tambayi kanena ma sale idan yashigo saiga sale yashigo da gudu tamkar yasan nemansa ake A'ilo tace yauwa sale zo dan Allah banayiwa ummanmu girki sale yatsaya yana haki kinayi mana ranar har danwake kikayimana ma'u tafe kirji danwake lallai kin iya girki daman inason na iya don allah ya akeyi A'ilo tayi murmushi dadai akwai fulawa ne dasai nanuna miki yanda akeyi ma'u tace bari naduba inada yake ajiye kayan abincin nasa Allah yasanya da fulawar daman nagaji dacin shinkafa da miya ko dafaduka shikenan fa abinda ya iya tanufi dakin taduba ga rashin sa arta bata tadda fulawaba amman saitace ga kudi asiyo gwangwani ukku nafulawa su kwaba dadi ya cika yaran suna murna yauzasuci girkin amarya ihu suke yi tamkar ranar sallah nandai sale yafalle dagudu yasiyo fulawa aka kwada aka kunna risho aka fara kokarin saka danwake gabadaya akaduru akicin din sugoma A'ilo ce agan risho tun ruwan bai tafasaba akafara saka danwake duk sanya daya sai anyi ihu tafi ahaka akammala sakawa aka koma gefe anajiran yatafasa gabadaya danwake ruwa yahadu ya cakude ahaka akafara kokarin saukewa anduba babu tsumman da za asauke ma'u tace bari tasauke bakin zanenta takama tana kokarin saukewa ashe zanin yalaso wuta zafin wutar dayatabota yasanya tafasa ihu tasaki tukunya da zaninta dayakama da wuta nanfa akayi waje ana ihu domin ruwan danwake yafadi akasa yafallasawa kowa zanen ma'u yacigaba daci dawuta sukuma suna ihu gobara! Gobara!gobara haryafara laso kayan kicin kamar Anjefo shi Ahmad yashigo agigice jin ihunsu yahango abinda kefaruwa yakalli ma'u dake ihu daga ita sai siket duk saiya dimauce yama rasa mezaiyi candabara tafadomasa yadauki wani omo da ruwa yanufi kicin dagudu yafara watsawa dakyar yasamu tamutu yadawo dabaya yatsaya yana haki saikuma suka kama ihu wai wutar tamutu takaici ya isheshi yanufesu afusace yafara dukan yaran suka sukayi waje aguje afirgice domin abin yabasu mamaki domin sunsan duk ihun dasuke baya ce musu kala amman yau saigashi harda duka yakoma kan ma'u yazabgamata mari yakoma zabgamata tafasa ihu tarike kunce maimakon tabashi tausayi saima kuluwa yayi yahauta da bala I sai da yayi iyakacin son ransa sannan yanufi kicin din yafara gyarawa ranar dai har dare yana bala'i da masifar dabatasanshi da itaba tayi kum adaki saikuka washe gari baije ko inaba yakuma hana kowashigowa gidan duk yaron dayazo saiya fatattakeshi yafita dagudu dan haka adaki tawuni tawuni tanakuka saidai tagama saka abinda zatayi lokacin daya fita sallar isha'i tadauko kayanta data kulle adankwali tanufi hanyar soro tanatafe afirgice cike da tsoro domin batason kowa yasan inda zata gudu tagaji dazaman gidan tunda aiba birsina baceba tafito tajanyo kofar gidan ahankali tabi gefen duhuwar dake kofar gidan tafara sauri tana waige don batason wani yaganta HMMM MUHADU AKASHI NA UKK U DAME AKE ADO BOOK 3 1⃣ DAME AKE ADO 3 Ma'u tanatafe cikin duhuwa tanata sauri burinta tayi nisa dagidan cikin ranta tana saka bazataje gidan yayyentaba kogidan umma bazata ba domin zasu iyadawo da ita gidan yaya Ahmad shikuma yacigaba da dukanta yana kulleta cikin gidan kamar mayya bata Ankaraba tayi karo Dawani mutum kayanta suka zube yayi taga taga kamar zata fadi Allah daiyasanya bata fadinba mutumin yazabga salati yana kokarin bata hakuri saigabanta yahau bugabawa domin muryan yayan natane hakan yasanya tagintse bakinta batace komaiba tasuri kullin kayanta tawuceshi dasauri cikin ikon Allah aka kawo wuta daidai lokacin da Ahmad kebata hakuri yadan bita da kallo da mamakin jin wacce yabuge din batace komaiba har ya ayyana cikin ranshi ko kurma ce sai kuma ya hango kamar ma'un sace mamakinsa yakara karuwa ganin tanata sauri tayi gaba yafara kwalla mata kira ma'u ma'u jikinta yadauki rawa saboda yagama shigarta tatsaya cak takasa matsawa daga inda take takuma kasa cigaba da tafiya har ya isa inda take tsaye yaleka fuskarta don kara tabbatarwa itace hankalinsa yatashi da yatabbatar itace cikin fargaba yace ma'u inazaki har lokacin taka magana sai idonta dake zubda hawayen tsoro kamar yakara yin magana saikuma yafasa ya kama hannuta kawai yafara tafiya Asma'u tafara binsa tana hawaye SHIKENAN TASHIGA UKKU TASAN YAU MAIRABATA DA YAYA AHMAD SAI ALLAH GASHI GIDAN BABU KOWA BABU MAIKWATAR TA Hakatayita binsa zaro zaro tanarungume dakayanta harsuka shiga gidan suna shiga yamaida gidan dasakta yadatse hakan yakuma yakadamata ciki tafashe dakuka sosai yakalleta harlokacin hannunta yana rike cikin nasa baice komaiba saida suka dangana cikin dakinsu yazaunarda ita gefen kujera yana fadin inazuwa bari nazo yafice yanufi dayan dakin dasauri tamike tafara zagaya dakin tana kuka hannunta bisa kanta tafara magiya don Allah kayi hakuri yaya nadaina wlh bazankara daidai lokacin yazo da zabgegiyar belt saita kuma zabura tafara ihu dakarfi yasanya hannu bisa lebensa yana fadin shishshi kidaina kuka ma'u badukanki zanyiba nadauko ne domin kidakeni kirama dukan danayimiki yanzu nagano illar abinda na aikata Amshi kirama ma'u yamike mata belt din mamaki yacikata tafara ja dabaya domin bata yarda domin batayarda harzuciyarshi abinda yake nufiba kenan tafi yarda yanayin hakan ne domin yasami damar kamata kawai ganin tanaja dabaya yasanya yacabko hannunta gam cikin nasa saitafasa kara jikinta narawa yadamkata belt din yana fadin dagaske nake ma'u badukanki zanyiba kirama dukanda nayimaki indai har zakidaina yunkuri gudowa kibarni ma'u kalamansa suka sata yin sororo tana kallonsa rike da belt ahannunta duk da karamcin shekarunta maganar yayan nata tagirgizata yasakarmata hannu da belt yajuya yazauna akan kujera yana maicigaba da kallonta ki dakeni ma'u kirama don Allah gani nazauna yanda zaki iya dukan nawa bana fatan kikara yunkurin gudowa idan kika gudu nashiga ukku bansan indazan sanya rayuwataba kobakisan Raliya ma guduwa tayi tabarni da aure naba? Tadan zare ido tana mamakin jin abinda yace tadaure tace dagaske Raliya tagudu? Itama dukanta kayi tagudu yaya?yanda tayi tambayar abin yaso yabashi dariya amman yadake yace bandaketaba kinsan halin Raliya ban isama natabataba balle duka banso kema kigudu idan kika gudu kowa bazai yafeminba harda INNATA MAISONA Kirama don natabbatar kinhuce kinji ma'u Tayi murmushi zuwa yanzu hankalinta yadan kwanta ta isa gabansa tadurkusa tamikamasa belt din tanafadin yaya bazan iya dukankaba nasan nice nayi laifin ma kayi hakuri bazan karaba ranshi yayi haske yace shikenan nahakura amman kimin alkawarin bazaki kara yunkuri guduwa kibarniba Allah bazan karaba nadaina bazanyimaka irin abinda raliya tayimakaba Alkawari abune maigirma ma'u kiyi kokarin rikeshi tadaga kai alamar to tana murmushi ya mike tsaye shikenan kinhuce yanzu mikikeson nadafamiki kici ki kwanta ta turo baki gaba da shagwaba yaya kaine kace nadinga yin abu irin na matan aure amman kakibari nakoyi girki daman umma ma batakoya miniba saitace jagwalgwalo nakeyi kuma ai matan aure sune sukeyin girkinsu dakansu nagani yayi murmushi ma'u ko buhun shiririta yakamo hannuta....

25 April 2015 at 08:47 · Public Like Page · Save · More Like React Comment Share Like7 Write a comment...

· Maryam Balarabe nyc stry wlh Like · React · Reply · More · 25 Apr 2015 Jamilubello Bello Nxt pls Like · React · Reply · More · 25 Apr 2015 Tajudeen Aminullah Abubakar Tnx 1 · Like · React · Reply · More · 25 Apr 2015 Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 12. 2⃣ DAME AKE ADO 3 Zanfara koya miki girki dagayau amman bazaki fatara yin girkiba harsai kin iya sosai eh nayarda saranda na iya zanyi bazan kara sabamakaba tafada cikin hanzari shikenan muje kicin din mezamu dafa yanzu tanabiye dashi saida suka nufi kicin din tace danmalele da wainar fulawa Mai manja wannan duk abinci bane kayan kwadayine kuma ni ban iyasuba yanzu dare yayi indomie zamudafa da Albasa muci yabata Amsa Ai itama tanadadi yaya amma ni na iya itabafa sai ansanya awutaba idan akasanyata aruwa tadade saikaga tayi laushi sai aci yakalleta dasauri da mamaki yace waye yace miki haka akedafa indomie ma'u tasami kujera tazauna tana dariya ganin yanda yasaki baki yana kallonta tace amakaranta bording haka mukeyi tunda ba abarinmu mukunna risho kuma akicin ma ba abarinmu sai siniyoyi kawai suke bari tobahaka akeyi bari yanzu nakoyamiki yanda akeyi yafara kokarin bude indomie din yana zubawa acikin tukunya yadauko albasa ya yanka yazuba akai haka rayuwarsu taci gabada gudana kullum ma'u saikara girma take halittun jikinta nakara bayyana shikuma Ahmad sonta da sha'awarta nakara karuwa acikin ransa saidai tsananin tausayinta yahanashi aikata komai akanta hasalima kogado daya baibari sunkwanta da itaba itatana gado shiyana kasa akan leda dafilo yawurgar haka ake baccin kullum tasaki jikinta da gidan domin yabar yaran suna shigomata sutayata hira suyita wasansu irin na yara sannan yana koyarda ita girki hartasoma iyawa saidai abinda yake damunta baiwuce rashin zuwan Ummanta gidan ba gashi tayi kusan wattanni goma sha ukku kuma shi yayan nata yakibarinta taje bayanshi kullum saiyaje yanata lallabata dai akan tayi hakuri yau tunsafe yafice aiki yabata damar tadafa shikafa da miya domin ta iya yanzu amman kadatabari kowane yaro yafara shigarmata kichin zuwa yanzu ma natsuwa tafara shigarta duk wannan shiriritar ta YAR AUTA tafara dainawa ta iya gyara gidanta tsaf kamar bashiba tashare tagoge ko ina girki ma indai bamai wahala bane tana kokarin yinsa iyakacinta dayaran aike kawai kosuyimata wanke wanke dashara wajen karfe bakwai yashigo gidan abunda yabashi mamaki baiwuce yin horn dayayi sama da sau ukku amman ma'u batazo tazo tabudemasa gidanba domin dayayi horn daya biyu ana ukkun zata fallo koyajiyo muryanta tana fadin yaya inazuwa amman yau yayi yafi sau shidda amman baijiyo matsinta ba saiya matsa jikin kofar gidan sosai yatura da hannunsa saiyaji kofar tabude yashigar da mashin dinsa yasami guri ya ajiyeshi ga mamakinsa saiyaga gidan kaca kaca babu gyara kamar yanda yasaba gani Ransa yabaci dayajiyo karar talabijin da alama kallone yadauke mata hankali tamanta da gyara harda budemasa kofarma yayi nufin shiga dakin yajiyo kauri daga kicin danhaka yanufi kicin din dasauri shinkaface akan risho takama harta kusa konewa gaba daya miyar kuma gatacan gefe marfi yabude hangam takaici yakara kamashi me ma'u keyine nashiririta yau agidan? Yasauke shinkafar yakashe risho dasauri sannan yanufi dan falon nasu kobai daki ma'u ba zatasha fada yadaga labulen yana kwalla mata kira ga mamakinsa saiyaga babu kawa dakin sai TV dakefaman babatu itadaya daga sannan hankalinsa yafara tashi da wutar nepa babu ma'u gaban Tv tana kallo lallai akwai matsala MEKEFARUWANE? saiya saki labule dasauri yanufi dakin gado yanacigaba dakiran sunanta ma'u ma'u yadaga labule yanaware ido kozaihangota amman babu ita acikin dakin babu alamunta hantar cikinsa takada afili yace na shiga ukku ina ma'u tashigane ma'u yasake kwalamata kira dakarfi saiyaji kamar sheshshekar kukan mutum abayan gado yashiga cikin dakin dasauri yana cigaba da kiranta gamamakinsa saiya hangota rakube bayan gado ta tattare jikinta kamar wacce akasanya zama ahaka dole mamaki yabaiyana akan fuskarsa ganin yanda take ta hada gumi idonta yayi jajir alamar tayi kuka takoshi sai ajiyar zuciya take ya isa gabanta yana tanbamyarta ma'u lfy meyafaru meyasameki? Saikawai takara fashewa da kuka tanaja dabaya tanafadin don Allah yaya Ahmad kada kadakeni kaine kace bazaka kara dukanaba kome nayi maka narantse da Allah banyi iskanci dakowaba banyi abinda Raliya tayi da sisco ba kakawo kur'ani nadafa mamaki yakara kamashi datsoro ganin yanakara nufarta tana karaja baya jikin lungu yadan dakata da kwantarda hankali yace tsaya ma'u gayamin meya faru bazan dakekina nako rantse da Allah kome kikayi bazan dakekiba kobakisan kingirmaba yanzu ko umma bazata dakekiba balleni gayamin meyafaru? Cikin sheshshekar kuka tana kara tsatstsare jikinta tana kudundunewa tace Amman dai kasan niba yar iskabace ko yaya yadaga kai cikin rawar jiki nasani ma'una salihace ba yar iska bace ba meyafaru wanine yashigo gidan yayi miki fyade ne ma'u kigayamini zan iya zandaukan dukan abinda yafaru akanki nasan kaddara ce kaji harkafara fada tun bangayamaka ba wlh banyi iskanci dakowaba yaya banyi komaiba yafara fusata haba ma'u kisanarda ni meyafaru kigayamini meye menene cikin karaji da ihu yayi maganar maimakon tadawo natsuwarta saima takara gigicewa kamar zatashiga cikin gadon tafashe da kuka maikarfi jikinsa yayi sanyi yagamo yatafka wauta yadubeta yace ok calm down ma'u yi hakuri gayamin tell me menene ? Ganin batada niyyar magana yasanya yafaki numfashinta ya cafke hannunata yadaga cak saita kara fashewa da kuka da ihu takankame jikinta kamar zata suma fadi take wlh banyi iskanci dakowaba yaya narantse da Allah gabansa yadinga faduwa ganin jini guda guda ajikin zaninta da gurin gabadaya hankalinsa yatashi kwarai da gaske takasa cigaba dakuka cikin karaji yace ma'u meye wannan mezangani haka 3⃣ DAME AKE ADO 3 Bajinin al.ada bane irin naku namata ba....... Cikin kuka tace nima dafarko nayi zaton irin abinnan dawasu kawayena keyine mistration idan sanya Auduga da.ake goge hanci shikenan saiya tsaya nikuma dana sanya saiya jike nakoma sanyawa yajike saikuma jinin yadinga zubuwo bayan banyi komai wlh banyi komaiba Abin sai ma yabashi dariya duk da jinin yazuba dayawa yasaki hannunta domin tadansamu natsuwa sannan yafara magana bakomaiba ne ma'u kowace mace dayanda take fara Al.adarta amman zo cire kayanki kiyi wanka saimuje chemist muji ko wata matsalace tayi doguwar ajiyar zuciya da jindadi tama manta da yayanta yana gabanta tafara kokarin cire rigarta da sauri baiyi zaton ganin abinda yaganiba YAUSHE MA'U TAZAMA HAKA ? ASHE TAZAMA MACE CIKAKKIYA BAISANIBA ? Bugun kirjinsa yafara sauyawa sai yakauda kansa dasauri yana kokarin nemo nutsuwa yasanya cikin nutsuwarta cire kayan takeson yi gaba daya yau babu yar kunyar da take nunawa agabansa saboda bata cikin nutsuwarta tadauko wani zaninta tadaura kafin yazubamata ruwa cikin bokiti yasanya mata abandaki tana fatowa yace maza shiga bandaki kiyi wanka batare da yakalleta ba itama bata kula da komaiba tanufi bandakin tanashiga ya shige dakin da bokiti ahannunsa ya fara kwashe kayan nata dasuka baci yayo waje dasu sannan yafice domin siyo mata Audugar mata Har yadawo tana cikin bandakin bata gama wanka ba hakan ya bashi damar gyara dakin yana tsaka da gyara da gyaran tashigo da sallama yadaga kai da sauri yakalleta yana amsawa cikin shagwaba tace yaya nagama amman haryanzu yana zubowa kadan kadan dariya takwace masa yadaga kai yana kallonta waike wacce irin sakaryata ce ne ma'u ? Amshi nan kisanya da pant dinki Aikinsan yanda akeyi ko ? Tadaga masa kai alamar eh tasani yauwa shirya kafin nima nawatso ruwa nima yanzu nadawo nadan gaji ta amsa yafice shima yajuya domin shiga wanka amman zuciyarsa naci gaba da sakawa da kwancewa Ahaka sukaje chemist din wata ma.aikaciyar jinya datake dan taimakawa acikin Unguwa idan dare yayi duk karadin Ma'u kasayimata bayani tayi sai rufe fuska da dariya kawai ta iya Aunty deeja ma'aikaciyar jinyar tadinga dariya tana zolayar ma'u daga karshe tayiwa Ahmad bayanin babu wata matsala daman wasu matan sukanyi haka farkon fara Al'adarsu amma da sunyi saudaya shikenan idan zasu karayi jinin baya zuba kamar na farko tabasu magunguna da shawarwari sannan suka bar gurinta Ahanya ma'u tayi shiru taga inda yayan nata zaikaisu domin taga ba hanyar gidansu sukayiba gamamakinta sai taga kamar hanyar gidansu Ummanta ake nufa tayi shiru dai tashanye murnarta saidai sanda taga sun shiga layin dadi ya cikata harta gaza boyewa sai data rukunkumeshi tana zabga ihun dadi dafari yadan tsorata da yanda yaji ta makalkaleshi har suka faduwa amma da yagano murnar jindadi ce sai ya saki ranshi amman rikon datayi masa yakara tsinka jijiyoyin jikinsa cikin ranshi yafara korafin abin da yarinyar ke masa cikin lokacin yagaza jurewa yana ganin zai iya karya Alkawarin da ya daukarwa zuciyarshi na barin ma'u tazama CIKAKKIYAR MACE Tasan kanta kafin ya tunkareta da wasu Al'amura na aur e 4⃣ DAME AKE ADO 3 Haka yadaure yakarasa kofar gidan yatsaida babur din yana tsayawa tana dira tun bai karasa tsayuwar ba caraf yacafko hannuta ganin tana shirin zubawa da gudu tayi cikin gida ma'u bakida hankali gudu zaki sanya atsakaiyar titi? Kobakisan ke matar aurebace yanzu saiki sanya mukoma wlh kifasa shiga gidan takwantar da kai cike da fargaba domin tasan kadan ne abinda yayan nata zai iya aikatawa tace yi hakuri yaya nadaina bazan komaba yasaki hannun nata yana girgiza kai to kitsaya mushiga tare banason zumudi nagaya miki takada kai kawai takasa cewa komai amman murna da zumudi suncikata tadan daure tatsaya yagyara tsayuwar babur dinsa yakulleshi sannan suka nufi cikin gida yaya Auwalu yana cikin chemist dinsa azaune ya hangosu tundaga nesa yafara wangale baki da fara'a don ganin yanda ma'unsa tazama butikekiya sunagab da shagon ma'u takufce tafalla dagudu tayi cikin gida domin bazata iya jure wannan jan ran da Ahmad kemataba Ahmad yabita dakallo da tsananin mamaki kafin yafashe dadariya yaya Auwalu ma yafito daga cikin chemist din yana babbaka dariya yace Hoo! Autar Umma wai haka take daman haryanzu batayi hankaliba Ahmad? Ahmad yayi dariya dasauki dai haryanzu yaya yamikawa yayansa nasa hannu suka gaisa suna cigaba da dariya subiyun yaya Auwalu yacigaba da magana Rufe chemist yakamani domin yazama dole naje naga AUTAR UMMA don kada umma tayi fushi dani suka sakeyin dariya sannan suka rantaya sukayi cikin gida gaba dayansu bayan yaya Auwalu yarufe chemist din nasa Acan cikin gida Umma da malam suna zaune suna kallo kasancewa akwai nepa labaran karfe tara suke kallo ma'u tashigo aguje ta manta babu ko sallama ta fada dakin tana kwallawa umma kira dasauri suka jiyo suna dubanta don fargaba Umma kam kasa magana tayi sai malam ne yayi karfin halin daka mata tsawa lokacin data iso tafada cinyar ummanta tana dariya Ke asm'u lafiyarki ke halan kinayin haukane ko? Cikin dariyar farinciki tace yi hakuri baba wlh dadine yacikani nadade bangankuba ina yini ..... Umma dai kallon Autar tata takeyi bakinta yaki rufuwa domin takoma wata babbar budurwa malam yadaure yahadiye fadan domin yayi murna daganin autar tasa yace har kullum dai bazaki daina sakarciba ina mijin naki yake kuma tarike baki tana dariya Umma kinji abinda baba yace wai inamijina maimakon yace yayana? Abin yabasu dariya gaba dayansu suka bushe da dariya Umma nashafa kan ma'un dafadin Ho! Autata naga randa zakidaina shiririta wlh dai dai lokacin Auwalu da Ahmad suka shigo ma'u takalli yaya Ahmad tana yar dariya tace yaya bazankara guduba Allah yanzu ma nakagune naga Ummatane yakada kai yana murmushi baice komaiba Auwalu yayi hararar wasa yanafadin nikuwa meye laifina da aki tsayawa agaidani tarufe fuska tana dariya yaya inawuni banacin kwantai yabata amsa umma tana dariya tace duk kin cikamu dasurutu kinhanani gaisawa da dana Manya yaya akayine saigaku da daddare kuma lfy Ahmad yasami guri yazauna yana dan yake yana satar kallon ma'u da tafara raba ido yace lafiya lau munzo kawai gaishekune baba inawuni malam sulaiman ya amsa dasakin fuska sannan ya gaida Umma tashi daga nan akaballe da hira anata dariya Ma'u dadi yacikata tanaji kamar kada takoma gidan mijinta shikansa Ahmad hirar tayimasa dadi jiyake kamar kada yabar gidan iyayen nasa domin hira cikin danginsa da iyayensa tafi komai yimasa dadi malam ne yafara ankara yace kai saiyaushe ne zaku tafi ne naga kuntsaresu sai hira kuke sharba deeje Umma tayi dariya tana fadin nibabu ruwana sutafi mana aiban hanasuba ma'u taturo baki gaba kamar zata fashe dakuka nidai mukwana anan don Allah baba kwana kuma? Malam yatambaya Ahmad yace eh gobe saimuwuce dasafe Auwalu yafashe dadar5⃣ DAME AKE ADO 3 kardai Ace rayinyar nan yakoyama shiriritar ta Ahmad banda hakan kawai saiku kwana gidan bawani dalili yamike tsaye gwara nawuce ni domin naga bakuda niyyar tafiya Aitafiya yazama dole kuwa kutashi kuwuce inji malam itadai Umma murmushi takeyi idan zasu kwana anan haka takeso tasamu damar ganawa da diyarta ta domin tagayamata dukkan abinda takeson gayamata saboda takasa zuwa gidansu duk da tanason zuwa malam ne yahanata yanacewa wai me zatayi gidan yara tunda suna zaune lfy aishikenan haka ma'u tatashi tana kumbura saiga hawaye yazubomata malam ne yahau salati yace Asma'u kuka kuma todayau kindaina zuwa gidannan tunda hakane karka kara barinta tazo Ahmad saita fashe da kuka tana fadin baba kayi hakuri shiyake hanani zuwa ko ina idan natafiyau bansan randa zankara zuwaba Hakan yadace yayi kumuje dan Allah idan muka biyewa shiriritar Asma'u saikukai dare gabadayansu suka nufi kofa banda umma data kamo hannun Asma'u dasauri taja baya dadi yacika ma'u dantayi tsammani cewa zatayi tazauna saitaga tahauta dafada amman cikin nasiha kinajina ma'u yanzu kinga kinzama matar Aure ba iridaya kike darayuwarki tabayaba don haka saikin nutsu kinyi komai yanda yakamata kidaina gudu da tsalle koba ayimiki aureba yakamata kinutsu haka kobakisan kinfara zama budurwaba Tarufe ido tana dariya kunya takamata waidan ma umma batasan Abinda yafaru da itaba yau kenan Umma takatsemata kunyar kinga bude idonki muyi magana kinga babu lokaci tabude idonta tana kallon umman nata Umma taci gaba da magana cikin hanzari yaya batun girki kin iya yanzu kullum idan yayanki yazo natambayeshi sai yace wai kin iya tayi dariya na iya umma na iya dafa indomie da shikafa da taliya rannan har miya nayi Umma tayi ajiyar zuciya haryanzu dai dasauranki zansiyamiki littafin koyon girki zanbaiwa yayanki yakawomiki muje kada sugaji da jiranki sukayi hanyar fita dasauri Umma tanaci gaba dayimata fada saida suka fita waje sannan takalli umman nata tace Umma shikuma yaya bakiyimasa fada kice yadinga barina inazuwa gida sannan yabarni bakoma makaranta dan Allah Umma umman nata tayi shiru damuwa tadan bayyana akan fukarta tace A ah babu maganar zuwanki gida kullum yanzu baikamata kifara yawoba kibari sai nangaba to Umma makarantar kumafa kinsan yayane yakecewa zanzama likita daidai lokacin dasuka iso wurin su Ahmad dake tsaye asoron gidan maganar ta karshe tadoki kunnawansu gabadaya ma'u tayi shiru ganin duk sunzubamata ido sai takama ina ina gaban Ahmad yayanke fadi domin indai ma'u tahadashi da mahaifiyarta akan maganar makaranta tagama dashi domin bazai iyaja da maganar mahaifiyarsaba sam maganar malam takatse musa fargabar dayake ciki kashiga kugaida jibril mana Ahmad yakalli malam dasauri ma'u taturo baki gaba kamar zatayi magana maganar umma takatseta malam ai inaganin yanzu sunyi bacci kosunyi bacci aizasu iya zuwa sutashesu sugaisa dai kushiga kugaidasu malam yabata amsa Ahmad yashga gaba ma'u tarufamasa baya Abin mamaki saisukaga lami tafito daga bayan kyaure soro sumi sumi babu kunya balle tsoron Allah Ashe labe takeyimusu daman tasan kuma idan suka shigo gidan mijinta zaifara nemanta Umma da malam sukabita da kallo lokacin dasu Ahmad suka shiga gidan tanajin hirarsu sanda taji sungama zasu tafi tafito dagudu talabe abayan kyauren bata taba zaton zasu shigo gidanba Lami tawuce sum sum tanufi cikin gidan kaitsaye malam yabita da kallo baki bude Umma kuwa salati tasanya tana fadin oh ni deeje Allah mai iko baka damu da mutumba ammanshi yamaida lamarin rayuwarasa gabadaya akanka malam yadagamata hannu ganin tafara masifa yana fadin kinga ya isa wuce muje ciki mukwanta deeje tayi kwafa tawuce ciki tana huci ta gyada kai malam yabita duk ransa yabaci amman yana kokarin boyAbdullahi yusuf maitama 09034598552ewaiya

26 April 2015 at 07:57 · Public Save · More Like React Comment Share LikeHaha58 Write a comment...

· Bintu Zahra Ammafa Kayi Mana Tsallake... 2 · Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Hajara Umar Jibril Tenx 1 · Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Ahmad Sabo To ina labarin raliya? 1 · Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Haba dan allah acigaba Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Ummin Mustafa Muhd amma kana kokari Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Salees Naja'at angaida maitama Like · React · Reply · More · 27 Apr 2015 Bintu Zahra Mungode Sannu Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Mukhtar Umar Daura Kayi kokari Like · React · Reply · More · 27 Apr 2015 Princess Hauwa Gaskiya wannan labarin yana dadi Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 Hussaina Abdulkadir THANKS Like · React · Reply · More · 26 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Sirrin zuciya DAME AKE ADO part 13. Asma'u da Ahmad suka shiga gidan suna kwallah sallama jibrilu yafito daga cikin daki yanagoge idonsa dakokarin gano masu sallamar domin akwai haske wutar nepa mamaki yadan bayyana akan fuskarsa yabude baki yana fadin wai wanake gani kamar Asma'u tadan kalli yayan nata tana murmushi nice baba ina yini lafiya kalau Asma'u Ahmad yadan durkusa dasauri yana fadin baba inayini jibrilu yakalleshi dasauri koshi yasauya amman sauyawar ma'u dagirmanta yafi bashi mamaki kwarai dagaske danshi yana dan ganinsa jifa jifa yana Amsa gaisuwar Ahmad yana kallon ma'un kafin yafara kwallawa lami kira saigata ta bullo simi simi cikeda borin kunya yakalleta cikin yanayin tuhuma daga inakike haka kuma lami? Gabadaya suka kalleta suma saitakama susar keya nadan leka wurin dijene nasamo ashana yakada kai yanafadin oho! Malam jibrilu yacigaba da magana ga Asma'u sunshigo gaishemu yamaida subansa ga Asma'u waiyaushe kuka iso gidan nema? Ahmad yace bamujima dazuwaba yamike tsaya bari muwuce dare yayi Allah yatashemu lfy cikin hanzari mlm jibrilu yace Ameen wani irin dadi yacika ransa ganin yanda ma'u tazama sukayi musu sallama suka kuya sukanufi kofar fita daga gidan shikuma yabisu da kallo yana kada kai Lami kuma tabisu dawata uwar harara kamar idonta zaifadi tasaki uban tsaki wanda harsaida yaran suka jiyo ma'un ce tawaiga dasauri amman yayan nata yajata suka wuce malam yamaida kallonsa akan lami kekuwa lafiyarki kike wannan tsaki saikace wata tsaka A a macijiya ba tsakaba tabashi amsa tana murguda baki yakada kai yashige daki yanafadin saikuma kiyi Lami nibacci nakeji Duk wani taimako da dabara Ahmad yakoyama ma'u yanda zata tsabtace kanta tun tanajin kunya hardai tasaki jikinta dashi bata iya boye masa komai domin randa jininma yadauke saida ta taddashi yana kallo tace yaya kasan wani abin dadi kuwa yakada kai yana murmushi yau jinin yadauke gaba daya yayi murmushi ho ma'u waton andaina jinkuyata ma kenan yanzu ko? Shikenan saiyin wankan haila kin iya ko ta isa kusadashi tazauna tana murmushi na iya yaya tun amakarantar islamiyya nakoya mana saidai wanka yanadayawa Akwai wankan janaba Akwai na hailah dana wankan biki dasauransu Toni wanne zanyi kodayake aiduk iri dayane saidai niyace tabambata ko? 7⃣ DAME AKE ADO 3 Yadaga kai hakane kezaki yi wankan haila ne don haka saikice nawaitul guslul haila farillah sannan saiki fara yin wankan tunda kince kin iyako tadaga kai na iya mana itakuma janabar mece ita ta tsareshi da ido tanason jin amsar da zainata shikuma duk yarikice yama rasa mezaicemata ma'u datambayar tsiya take amman bari yayi mata baro baro yahuta kinsanme akeyi idan anyi aure tsakanin miji da mata kamin yakai karshe tace nasani mana wanke wanke da shara ko? Baisan sanda yagashe da dariyaba yace bawannan bane raya sunnar ma aiki ne aure takuma katseshi raya sunnar ma aiki kuma yin sallar dare ko Azimin litinin da Alhamis duk basu bane bari nanumiki raya sunnar ma aiki saiya kamo hannunta yajata jikinsa ya kankameta domin hakan zuciyarsa ta aiyanomasa yayi tuntuni yaturo bakinsa cikin nata jikinta yadauki rawa tsoro yakamata firgici yashigeta takama kokarin kwace kanta dason fasa ihu amman tagaza shida kanshi yaji wani yadarsu azuciyarsa yasaketa dasauri jikinsa amma yana rawa tafara daja dabaya kamin tafasa kuka tanaganin anyin irin wannan amman cikin fina finai wanda aganinta sai yan iska ne sukeyi meyasanya yayanta zaimata haka kunya dafar gaba duk suka baibayeshi waiwane irin rashin hankaline yajagoranci zuciyarshi ya aikata hakan ga ma'u yarinyar dabatasan komaiba yamike ya isa inda ta takure tana sheshshekar kuka ma'u meye abin kuka kuma wai bakisan meye aure bane wannan abin danaimiki shine soyayyar aure bashi bane wannan iskanci ne turawane keyinsa acikin film yadafe kai dadamuwa wai wace irin yarinyace ma'u gata haihuwar birni kuma yar makaranta wadda yakamata ace tasan komai amman ba abinda tasani yagyara murya yana shirin lallabata amman tini tafice daga dakin tanacigaba da kuka yabita da kallo yama rasa mezaiyi washe gari dasassafe yashirya yafice gurin aikinsa yabarmata rubutu atakadda ganin bata tashi daga bacci ba yau basu kwana daki daya ba ma shi falo yakwana don ganin duk tafirgice dashi zuciyarshi fal tunani kamar yanda suka saba kullum saisunyi meeting kafin sufara aiki da manajojin gidan man sannan ayi lisafin abinda ke cikin litar kowa yau mai gidan manne baki daya da kansh yazo wato ALHAJI NURA KWANGILA YAN LEMAN duk ma aikacin dayaganshi sai gabanshi yafadi domin yariga kowa isowa Ahmad kusan nakarashe a shigowa gabansa yayanke yafadi amman daya dubi wayar hannunsa yaga haryanzu bakwai bata karasaba yadanji dadi aransa domin yasan baiyi latti ba bayan duk sun taru babban manaja yasanardasu yabude sabbin gidan mai a legas yanason zai dibi wasu dagacikin ma aikatan suje suhadu dawadanda za adiba sabbi acan suyi aiki natsawon watanni ukku dasu harwa dancan susami gogewa don hakan kowa yakasance cikin shiri sunansa zai iya fadawa 8⃣ DAME AKE ADO 3 Dawannan yayi sallama dasu yatafi kusan kowa bayason sunanshi yafada dan bamaison yayinisa da iyalinsa musamman shi Ahmad dayake da danyar amarya shakaf inazaiwuce yabarta har tsawon wannan kwanakin donhaka afili da cikin ranshi yake addu ar Allah yasa babushi din yanagab datashi daga aiki yaya Auwalu yakira wayarshi bayan sungaisa Auwalu yace idan yatashi daga aiki yabiya tacan gidan ya amsa dato sukayi sallama sanda ya isa gidan yaya Auwalu matarsa hafsa tashiga tsokanar shi tunyana ramawa harbakinsa yayi shiru datafara hadawa da matarsa yaya Auwalu yace kinga hafsa idan zaki taimaki yaron nan kibashi abinda kikace to idan kuma bahakaba yayi tafiyarshi tamike tana dariya tashiga cikin daki minti biyu hafsa tafito daga dakin hannunta rike da bakar leda takaraso wajensu tamika masa Amshi nan kakaiwa ma'u tayita karatu Haus a Novel ne yadan waro ido

See translation 28 April 2015 at 18:38 · Public Like Page · Save · More Like React Comment Share Like7 Write a comment...

· Abubakar Sa'ad Dan Allah a cigaba da wannan littafin Like · React · Reply · More · 18 Jan Ummu Khalifa Khadija Adamu Allah ya kara basira Like · React · Reply · More · 30 Sep 2018 Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah mungode Like · React · Reply · More · 20 Aug 2018 Mahmud Yusuf Adam Maje Gaskiya mugode Like · React · Reply · More · 18 Jul 2019 Mahmud Yusuf Adam Maje Agaskiya mungode Like · React · Reply · More · 13 Jul 2019 Tajudeen Aminullah Abubakar Tnx 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Hussaina Abdulhamid Abdulhamid TNX 1 · Like · React · Reply · More · 5 Feb 2017 Maryam Balarabe plz adora ynxu 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Jamilubello Bello Dan Allah abamu cigaban kallon kitse a idah manah 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Tahir M. Kaumi Cabdijam. 1 · Like · React · Reply · More · 28 Apr 2015 Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 14. yadan waro idoí ½í¸³da mamaki wai kina nufin littafan soyayyane eh sune tunda yayanka yabani lbr halinda kuke ciki da ma'u naga babu mafita bayan wadannan littafan tayita karantawa yakarba yana jijjiga kai cikin ranshi yana fadin NAYI ZATON AI BABU KOMAI CIKINSU SAI HIRAR SOYAYYA MARA KAN GADO AMMAN DAI BA AKIN TA MUTUM Yayi godiya sannan yayi musu sallama zaiwuce danyaga dare yanashirin yimasa lokacin daya isa gidan saiyatarar dayara afalon suna kallo amman yana shiga yaran sukafice domin tun randa yayi musu barin mahaukaciya suke jin tsoronsa yatsaya abakin kofa rike da labule yana kurawa ma'u kallo data kauda kanta gafe tanawasa da yatsun hannuta ma'u baki ganni bane naganka mana sannu dazuwa yafada afili aranta kuwa cewa tayi mezan maka kuma yayi murmushi don shi mailiafine a gurinta yakarasa kusa da ita yamika mata ledar dake hannunsa karbi wannan inji Aunty Hafsa tace kiyita karantawa harkigama dasu duka taleka ledar taware ido duk wannan saikace wata jaka nadai karanta wasu kawai duk yanda kika gani haka zakiyi makika dafa agidan ne dan wake mana dan wake ma'u dawannan daren yatambaita da damuwa babu kyaune cinsa dadare yaya? Tamaida masa tambayarsa A'a banceba zubomin amman kadan tamike tanufi kicin yadafa kai cikin ransa yana Addu'ar Allah yasanya ma'un tasauya sanadin karance karance kamar yadda Aunty Hafsa tafadamasa Washe gari bayan yafita aiki tayi shiru tunani duk yacika ranta domin babu yaron daya shigo mata kusan kowa yana makaranta tunanin kawayenta yafadomata arai tana tuna irin rayuwar dasukayi abaya koyaya suke yanzu ta tambayi kanta acikin zuciyarta idonta ne yaciko da kwalla damuwa fal acikin ranta can sai littafannan suka mata arai tamike da sauri tanufi daki dasauri tadaukosu tazabi daya daga cikinsu tahaye kujera tafara karantawa wasa wasa littafin yayimata dadi hartakasa ajewa koda yan hira tata sukazoma yau bata kulasuba ko Abinci rana bataciba dan bata iya tashi tagirkaba balle wanke wanke ko shara saida taga yayan nata nagab da dawowa sanna tamike tafara gyara gidan soyayyar jaruman littafin tayi matukar burgeta kuma takayatar da ita domin har sunyi aure sunfara gudanarda rayuwar aure nan gurin kam shima tadade tana tunani wannan shine rayuwar Aure kenan ? Har yayan nata yataddata bayan sallar magariba tanata karatu yayi murmushi ganin yanda tagwagwafe yakula batasan ya isoba ma yayi gyaran murya tamike dasauri tanayimasa sannu dazuwa yaya akayi kanwata dadadi kenan littafin ? Dadi yaya kayi wanka kaci abinci nabaka lbr akwaidadi wlh yakada kai kawai yawuce yanacin abinci tanabashi lbr littafin datake karantawa Ranshi yayi wasai domin tafara sakar masa jiki kuma yagane karatun zairagemata da kadaicin makaranta haka yayitajin lbr yana kada kai kwanaki kusan ukku kullum idanyadawo aiki da lbr dazata bashi yau yadawo ransa acunkushe domin yana daya daga cikin wadanda Alhaji Nura kwangila yasanya ayi tafiyar legas dukkan abinda zainisantashi da ummansa da ma'u baya kaunarshi domin kullum kafin yatafi aiki saiyabiya duk da sammakon dayakeyi itakanta umma harta saba don haka kodata idarda sallar asuba bata komawa bacci saita tashi takama aikace aikacen gidan yau ma'u tanata bashi lbr amman sam hankalinshi baya tare da ita har tagano wani abu yanadamunsa tace yayana kobada lfy ne? Dasauri yadago kai yadubeta eh banajin dadi ne ma'u gaba daya yanayinta yasauya zuwa damuwa tamike sannu yayana me zankawo maka? Kwantar da hankalinki nasha magani ma kan yadan fada inasodai inje wurin ummane yanzu Amman dai danizakaje ko? Takatseshi ciki hanzari dasauri yace A ah nikadai zanje yayi dan tunani yanason zuwa da ita amman yasan zuwa da ita din zaisanya sukasa samun natsuwa ganin bashida mafita yadubeta yace bari nakiramiki A'ilon gidan kasa kuyi kallo kinyada dasauri tace eh nayarda kirata..........Am yaya namanta yaufa hajiya tazo takawomaka kaya masu yawa nima haka kuma tace tanagaisheka bari nakawo maka kayan yasan kowace hajiyace hjy Aminansace maisonshi dasauri yace kinga bari nadawo yafice dasauri Acan gidan umman shi tashiga damuwa dajin antura Ahmad legas har tsawon wattani ukku harsaida fuskarta tanuna hakan afili tace babu kuma wani abu daza a iyayi akan dole saikunje din subasuda tausayi ne bausan kanada iyali ba? Malam yayi murmushi afili yace wai yaushe zakiyaye Ahmadu ne Deeje? Abin yabasu dariyaí ½í¸ itada Ahmad din gabadaya tace Au! Hakama zakace malam baka tunanin nisan dazaiyi? Meye abin nisa ga namiji don yatafi legas yanzu idan yasami aiki acan bazaki barshi yajeba kenan? Tayi ajiyar zuciya insha Allahu kozaisamu aiki anan zaisamu malam kadinga yin irin tunanina mana Aitunanin kowa dabanne nasan dai bazasu cinye mikishiba acan yanda yaje guda haka zaidawo guda kiyi masa addu'a dasanya albarka kawai takada kai shikenan yanzu ne tafiyar Ahmad yagyara zama wajen jibi sukace insha Allahu inatunanin kawo ma'u gidanma gobe kafin indawo! Gida kuma akanme? Malam yakatseshi da sauri A ah hakan bazai yiyuba kabarta adakinta tasaba da aure yanzu tazama matar aure dole takoyi juriya irinta mace mai aure yayi danjim kamar bazaiyi maganaba saiya daure yace gidan zaimata girma ne gashi tanajin tsoro kuma akwai kurciya haryanzu atare da ita inaga kamar zamanta zaifi tunda kwanakin dayawa. Maitama

See translation 29 April 2015 at 10:12 · Public Save · More Like React Comment Share LikeLove66 Write a comment...

· Adama Abdulkarim Kiyawa Mungode Allah ya kara basira thanks Like · React · Reply · More · 20 Aug 2018 Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah Like · React · Reply · More · 20 Aug 2018 Atika A Umar thank you so much Like · React · Reply · More · 24 Apr 2018 Faisal Sa'ad Isma'il Mun gode Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Mujaheed Ummi Ummi Mujaheed dai dai kenan Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Fatima M Bello Mun gode Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Ra'idatu El Kabeer Tnx Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Maryam Saleh tnx u Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 Mujaheed Ummi Ummi Mujaheed dai dai Like · React · Reply · More · 29 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 15. Umma kam tana bayan ra ayin Ahmad amma tagaza cewa komai Don kada malam yayi zaton hada baki sukayi Amman acikin ranta tana addu'ar Allah yasa ya amince din hakan ne kadai mafita malam yace tau shikenan tunda kana ganin hakanne mafita baijima agidanba yayi sallama dasu domin hankalinsa yanakan ma'u daya baro akwai yankallo agidan yabarsu dan haka yatada babur dinsa yanufi gida yana isa yahango kofar soron ansakayota saidai wurin bakikirin kasan cewar andauke wutar nepa yakafe babur dinsa agefe yasauka domin yatura kofar yashiga yatabbatar babu wani abu akan hanya cikin soro saida ya isa cikin soro yafara kokarin kunna yar cocilan din dake hannusa dai dai lokacin dayaji wata uwar kara yarude yafara kallon inda karar kefitowa acikin soron ne daga gefe kuma muryan ma'u ce cikin sauri yace ke menene ma'u nine Ahmad cocilan din dake hannunasa wacce yake kokarin kunnawa tafadi saboda damkar datayi masa tana sheshshekar kuka kamar zata shide cikin firgita yace ke menene meyafaru tana kankame ajikinsa take fadin wlh kamar tafiya akeyi acikin gidan nakasa zauna..........ina A'ilon take? Anadauke wuta kanenta sale yazo kiranta nayita magiyar tatsaya tace wai dukanta za ayi shine nabuya abayan gado saina dinga jin tafiya nagudo nadawo soro naboye cikin kuka take bayanin yakasa cewa komai domin rikon datayimasa tasaukarmai kasala dawani iri shauki da kyar yadake yace shikenan sakeni nashigo da babur dina babu komai tsorata kawai kikayi taki sakinsa takuma kiyin magana har lokacin jikinta rawa yake yakara kwantar da murya yace bari badauko cocilan din tadan sakeshi amman tana gabansa yasunkuya yafara laluban cocilan harya samu yakunna yahaske fuskar ta dariya takamashi ganin tayi miyau da majina yakauda da kai yana dariya Ho ma'u hankalinki saike bari nashigo da babur din nifa tsoro nakeji Allah kuwa yaya yamikamata tocin rike harnashigo dashi haka tatsaya badon tasoba haryashiga da babur din yashige gaba tana biye dashi abaya suna shiga aka kawo wuta yakalleta yana rike da babur din haryanzu yanayinata dariaya togashinan babu komai agidan matsoracya kawai itadai batace komai komaiba yadauki buta yanufi bandaki saita tashi dasauri harda dangudunta yawaigo dasauri malama bandaki zakibini kuma A a tafada dasauri yakuma fashewa dadariya kinga dun Allah kikwantar da hankalinki kiyita addu'a babu komai bari nafito dahaka yasamu yashiga bandaki yanaci gaba da dariya a zuciyarshi daren ranar tana gado shiyana kasa kwance takundundune kamar za ashigo adauketa ma'u akwai kurciya da shiririta yanason yayi maganar tafiyarsa da ita amman yanda take afirgice dinnan yasan bazaisami komai agareta ba don haka ya kyaleta dasafe baijima dafitaba yadawo domin manaja gidan man yace sudawo gida kowa yayi shirin tafiya gobe sannan yadan basu kudaden dakowa zaibarwa iyalinsa ma'u anmike kan kujera anata karatu Allah yasanya takammala aikinta gabadaya tajiyo sallamarsa tadago da mamaki tana kallon kofar dakin tamike dasauri taleko shine din kuwa damamaki tace yaya Ahmad yauhar kadawo dawuri haka 1⃣1⃣ DAME AKE ADO 3 yakada kai banyi aikiba ne nadawo nayi shirin tafiya ne tafiya kuma ta tambaya dasauri kinga shiga ciki kizauna nayi miki bayani babu musu takoma tazauna shima yasami guri yazauna yafaramata bayanin dalilin tafiyar haryakai karashen bayanin tayi shiru dadamuwa kamar zata fasa kuka amman yaya bazan iya zama nikadai agidannanba katafi dani can dan Allah yakauda kai A a bazanje dakeba anan zaki zauna kefa matar Aurece baikamata kidinga yawo ko inaba abinda bajimawa zanyiba darana saikiyita wasa dasu A'ilo idankuma dare yayi saiki kulle gidan kisanya sakata babu wanda Zaishigo ai tadafe kirji dan Allah yaya kayi hakuri wlh bazan iya kwana nikadaiba saidai idan kayarda nadinga zuwa gidansu mairon gidan kasa nakwana yabata ran wasa gidan kuma fa yakwana shikadai babu kowa banyardaba gaskiya dole kizauna kedaya tayi shiru tarasa mezatace ma amman dai idonta yafara zubo da hawaye dasauri yamike yanafadin lalala kada kiyi kuka yar Amaryata tsokanarki nakeyi tashima kishirya kayanki mutafi gidansu umma acanzaki zauna tamike tadaka wani uban tsalle tana ihu yabude baki yana kallonta lallai yariya zakija afasa tagimtse murnar yi hkr yaya nadaina bari naje nafara hada kayana ko ajikinta batajin komai akan tafiyarsa domin damar komawarta ga ummanta tafi komai yimata dadi yana kallonta tafice yana kallonta yafada kujera ya lumshe ido baison rabuwa da matar tashi ayanzu zaman dasukayi nawatannin nan yashaku da ita fiye da tsammani kobabu komai yakaso sokancinta danya dinga cindariya kawai amman yaya ya iya rabuwa tazama dole Amotar haya taxi suka tafi domin kayan dayayiwa su umma siyayya nakayan abinci da kuma kayan sawar ma'u sunada yawa ma'u kuwa murna takeyi kamar zata shide shidai kawai yake ransa babu dadi Acan gidansu umma ma haka tadinga murna tanajin kamar za asanyata agidan Aljanna umma tana kallonta tana murmushi shikuma jiyake kamar kada yatafi Anan yaci abinci har wajen karfe goma baibar gidanba saida malam yayimasa magana Ahmadu yakamata kaje kakwanta haka domin samun damar tashi dawuri tunda kace sammako zakuyi? Yayi shiru dadamuwa saiyakejin kamar yarabu dasu kenan har abada faduwar gabanshi takaru idonshi yataru da kwalla malam yayi murmushi nason basar dashi Ahmad saikace wani karamin yaro don Allah ka kwantar da hankalinka sai alokacin jikin ma'u yayi sanyi tazubawa Ahmad ido wanda kansa ke kasa itakanta umma kauda kanta tayi gefe don batason ganin fuskar dan nata Cikin rawar baki Ahmad yace naji gabana inazaton babu Alkhairi acikin acikin tafiyar nan tawa gwara nafasa nasamu wani aikin kul nakoma jin wannan maganar Ahmadu tunranda kafadamin maganar tafiyar nan nasanarda yan uwanka mukayita Addu'a saikuma da aski yazo gaban goshi sannan zakace kafasa ban amince dahakan ba sam kaje kayiwa mamanka hajiya Amina sallama tukunna naje dagacan mukayo nan tace agaiaheku muna amsawa maza tashi kawuce ya mike yana kallon ummansa da har lokacin kanta yana kallon wani sashin yace umma zanwuce sai alokacin tawaigo idonta yacika da kwalla tace Allah yakiyaye hanya kakula da kanka Ahmad kakula da Addininka da matsayinka na musulunci aduk inda katsinci kanka Allah yayimaka Albarka kalmarta ta karshe tafi komai dadi agareshi yanzu da agidan marayu yatashi waye zaidinga saiyamasa Albarka kamar haka yayi kokarin goge kwallar data zubomasa yanafadin Amin Umma nagode baba natafi Allah yatsare yakiyaye madinga gaisawa ko awayar yayanka ne 1⃣2⃣ DAME AKE ADO 3 Ma'u tanazaune tamkar andasata gabadaya murnarta takoma ciki saizare idonta takeyi saiyanzu takejin ciwon tafiyar yayanta Ahmad kalamanshi sunsanyayar mata dajiki har kwalla yacika idonta Umma tadubeta tace bazakije kuyi sallama bane? Takalleshi dasauri maganar umma tasanyata mikewa dasauri babu shiri donbin bayan Ahmad dayafice dasauri yana goge idonsa cikin gaggawa tabishi donganin yanufi soro kaitsaye dasauri yaya Ahmad takwalla masa kira sanda ta isa soron taga zaifice yatsaya gami da waigowa da sauri yakalleta ma'u yaya akayine? Cikin dakiya dakokarin boye damuwa yake maganar yaya bamuyi sallama ba zaka tafi naga kamar ranka yabaci yaya dan Allah kayi hakuri idan nayimaka laifi yayi murmushi dajindadi lallai ma'un shi tafara samun hankali da natsuwa ya isa kusa da ita yariko hannunta yanajin kamar yarungumota jikinsa amman gudun abinda zaifaru yasa yadake cikin dakiyar zuciya yace ma'u bakiyiman komaiba amman inajin kewa dakadaicin rabuwa daku naga kamar murna kikeyi domin kidawo gidansu Umma ko? Tasunkuyarda kai kunya tarufeta amman saita girgiza kanta alamar a a bahakabane ba yakura mata ido cikin hasken dayaratso soron yanaci gaba da magana kidinga yiman addu a ma'u naso kamin natafi nasaimiki waya amman banida kudi kudin danasamu nayiwa su umma siyayya nasanyamiki wasu kudi cikin kayanki idan kina bukatar wani abu kidinga siya kada kitambayi umma ko baba kinjiko tadaga kai alamar to yajanye hannunsa daga cikin nata yanadan ja dabaya yace sainadawo ma'u yajuya dasauri yafice ma'u kurawa kofar ido kamar katabishi saiyanzu takejin kaunar mijin nata haka takoma gidan babu kwari balle karsashi ajikinta Gasu Ahmad saidare suka isa garin legas kaitsaye gidan dazasu sauka suka isa dayake amotar kamfaninsu suka tafi gidane irin ginin legas amma babu laifi yanada kyau kowa da dakinsa daban akabashi dakyar suka iya cin dan abinci suka kwanta baccin gajiya washe gari kuma dasafe akakwashesu amotar kamfani akakaisu sabon gidan man maisuna YAN LEMA PETROLEUM & 10 dayake duk sunan gidajen man nasa dayane suntarar da ma aikatan gurin wanda aranar zasu fara aiki babban gidan mai yagina wanda yafi nacan kasancewar shikadai ne dashi alegas kuma nafarko ajahohin kudu kuma ance shine nafarko dayafara ginawa dayake kuma yanada kishin jama arsa HAUSAWA kusan kaso sittin naginin duk hausawane saisauran yarbawa basusha wahalar fara aikinba kasancewar anrage kudin litar dakaso biyu (2%) cikin (100%) saboda gidan man sabone haka yasanya akayita samun masu siya Awannan ranar dakyar Ahmad yasamu dan lokacin yin tunanin ummanshi da ma'unsa kida yakema lokacin dayana aikin mayakan tunodasu jefi jefi kuma aduk yayin dayatuno dasu saiyayi murmushi 1⃣3⃣ DAME AKE ADO 3 KWANAKI sukai tazuwa suna wucewa zuciyoyo nakara shiga cikin damuwa Awannan lokaci ma'u takara fahimta meye Aure meye miji domin yayi nisa acikin karance karance sannan Umma ta ajiye kunya tanayimata bayanin aure meya kunsa menene alfanunsa wannan yake karasanya takara son mijinta idantayi kwance agado saitayita tunaninsa burinta baiwuce yadawoba musamman lokaci da hajiya Amina tazo ta taddata tana karatun littafi tasayomata jaka guda tace ayitayi ananma tasamu abubuwan karuwa dayawa takaicinta daya tunda Ahmad yatafi bata tabakoda jin muryansa ba kullun sai dai yaya Auwalu ko yaya sani yazo yabasu labari yace sunyi waya dashi sungaisa tanaso tace abatashi idanyakira wayar amman vazata iyaba sam sukuma sunkasa karar subata din Ahaka har watanni biyar suka cika zuwa lokacin ma'u takoyi abubuwa masu dama yacika tazama budurwa domin tacika shekaru sha shida kenan gashi kullum umma saita bata kunun daka irin na MUTANEN NIJAR da tukudi tunbata son sha haryazame mata jiki dukkan halittar ta takammala fitowa tazama CIKAKKIYAR MACE Idan tatuno abinda tayiwa mijinta abaya saitayita dariya daganin wautar kanta gaskiya Ahmad tayi kokarin zama da ita shekara daya dawata bakwai amman baiyimata komaiba tatabbatr yayan nata namatukar kaunarta yanzu saidai abinda kedamunta baiwuce rashin dawowarsaba kullum sai umma tayi mita domin ita kanta tagaji amman sai yaya Auwalu yace ba abasu damar dawowabane saidai duk karshen wata yana aikomusu da sako wannan abin shine yake farantawa malam rai kwarai dagaske domin ayanzu kobaifita kasuwaba bairasa abinda yasanya abakinsa Albarkacin darajar iyaye Ahmad yana cikin tsananin damuwa datakura saboda rashin iyalinsa da iyayensa Ayanda Alhaji nura yayi musu Alkawari watanni ukku zasuyi amman gashi harsun shiga watanni shida kuma watan yana neman karewa ba acemusu komaiba hankalinsa duk yatashi haryarasa abinda zaice agayama ummansa da ma'unsa amman dai yasan sunacikin damuwa kwarai da gaske lokacin dasuka cika watanni bakwai yagama fusata baijin komai bayan ya isa ga ahalinsa don haka lokacin da Alhaji nura ya iso gari donya duba yadda abubuwa suke tafiya Ahmad yaji kamar dukkan matsalarsa takare dan haka lokacin da yazauna mitin dasu yakudiri aniyar fadin abinda keransa bayan yayi yabo dajindadin yadda akasamu cigaba da abinda ake bukata ga gidan man yayimusu albishir dasamun karin albashi maitsoka murna dajindadi yacikasu amman banda Ahmad domin yawanci wadanda sukazo kamar basu damu da iyalinsuba dayawa sunsaki jiki suna mu amalarsu harma dasu ajiye daduro! Bayan Alhaji nura yagama bayaninsa Ahmad yadaga hannu yana fadin idan yallabai yabani dama inada maganar da zanyi gabadaya kallo yakoma wurinsa abokinsa isuhu haryadan zunguresa alamar kada yayi magana domin yasan abinda zaice saboda kullum saiyayi masu korafi amman Ahmad baikulashiba Alhaji yakada kai kanada damar yin magana Ahmad yamike tsaye yafara koro bayani yallabai kamar yanda kafada abaya kafin muzo garin nan kace watanni ukku kacal zamuyi amman gashi harmunshiga wata na bakwai kuma watan yanagab da karewa amman babu labarin tafiya gida shine nakeson ayiman bayanin yanda abin yake Rufe mana baki mara kunya kaikadai kake da iyali kobakin magana bakaganin wasu neman aiki sukeyi sun rasa idon su arufe manajan gidan man yafadi haka bayan yakatseshi cikin tsananin bacin rai da masifa Ahmad yace hakane kasan babu wanda ya isa yabaiwa wani aiki idan ba Allah yakaddara ya aminceba Abdullahi yusuf maitama 09034598552 @whatsapp

30 April 2015 at 08:53 · Public Save · More Like React Comment Share Like67 Write a comment...

· Rahma Hussain Mai Doki Thanks Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Ra'idatu El Kabeer Tnx Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Sa'adatu Ibrahim Panda tnx Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Kabiru D Shagari Tnks. Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Siyama Auwal munajin dadi Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 EL-Mansoor Mancy Dulo 10nks u Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Shahara Na Suleiman Good Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Aliyu Ibrahim Tanxx Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 Mukhtar Moh'd Mopol Muna godiya Like · React · Reply · More · 30 Apr 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 16. Inaji ajikina aikin danakeyi yanacikin kaddarata sukuma wadanda basu samu ba hakan aka rubuta alittafin kadararsu dan haka zaka iya yanke kowane irin hukunci akaina babu tsoro balle fargaba Ahmad yasake fadar maganganunsa manaja yakara fusata dajin abinda Ahmad din yafada masa batare dawani shakkarsa ko fargaba ba gurin kowa yayi tsuru tsuru cike da tsoro masamman isuhu abokinsa manaja yanuna Ahmad da dan yatsa cikin tsananin fushi da fusata kaikada kasake kayiman rashin kunya daman najima daganin take takenka dan matsiyata ba,za...........kai manaja dakata Alhaji nura kwangila yadoka masa tsawa jikin manaja yadauki rawa yaguntse baki da sauri domin yau dai asirinsa yatonu duk yanda yaso kuma yakare abin yafaskara Alhaji nura yana huci yakalli ma aikatan yace Acikinku waye yasamu manaja damaganar yanaso abarshi anan idan har za adinga bashi alawus din dazairika aikawa iyalinsa? Kowa yayi shiru ana kallo kallo manaja yafara hada gumi jiyake kamar kasa tatsage yashige cikinta saboda tsananin kunya Alhaji nura yabisu da kallo daya bayan daya yace babu sukayi shiru wanda yatabbatar masa da babudin yakada kai cikin takaici Nayi matukar bakin ciki da manaja ya aikata wannan zalunci da sunana tun lokacin dakuka wata ukku nasameshi damaganar komawarku ga iyalinku idan kuma da maibukatar zama ana legas yacigaba zamansa amman sai mutumin nan yace min aiduk kunce anan zaku zauna indai za adinga baku alawus kuna turawa iyalinku nace yaware wasu kudi yadinga baku dukkan sati ashe karyace yashirya min bahaka bane gaskiyar lamarin ba naji dadin wannan maganar dakayi Ahmad inason mutum irinka dabayajin tsoron fadin gaskiya duk dacinta kai manaja katafi gida nadakatar dakai tsawon wata ukku babu Albashi mataimakinka zaimaye gurbinka!!! Kukuma dukan maibukatar tafiya gida saiyafara shiri cikin satinnan saikuwuce sannan albashinku yana nan yanda yake dakarin danayimuku nagode manaja yadafe kai da tsananin tashin hankali dakatarwa wattani ukku babu Albashi dame zaidinga ciyarda iyalinai har wannan lokacin balle kuma kudin dazainemi mata domin duk abinda yake samu jikin matan banza yake karewa Ahmad kam yafi kowa farin ciki saigashi yafara shirya jakarsa domin babu komai acikinta sai tsarabar kayan ma'u isuhu yana zolayarsa yanda yayi magana da babban manaja babu tsoro mutumin da kowa yakejin tsoronsa da shakkarsa baisanarda kowa zai komo cikin satinba domin yanaso yayi musu bazata ne kawai Ranar assabar da daddare suka bar garin legas wajen karfe tara da rabi nasafe suka iso garin kano motarsu natsyawa yaji wani farin ciki yacikashi aranshi umma da ma'un sa kawai yake son gani yana kokarin shigowa gidan yaci karo da Amina kanwar raliya taci kwalliya tayi bilicin kamar wata karuwa gabansa yafadi domin kallota da kamannita sun tunomasa da raliya gabadaya takoma kamar raliya cikin rawar baki tace masa Ahmad sannu da zuwa batare da ya kalletaba ya amsa da yauwa yashige ciki dasaurinsa tabishi da kallon mamaki baki abude gaba daya yasauya yakara haske da kayau kamar bashiba saitakoma ciki dasauri domin tabaiwa babarta labari itada kullum take addu a Allah yasanya jirgin kasa ko mota yatakeshi yamutu koyanfashi sutaresu su harbeshi domin tafara kishi daganin yanda ma'u take komawa kullum kuma agidan ba ada magana saita Ahmad saikace shikadai da aduniya ma'u tana durkushe tana wanke wanke da T. Shirt ajikinta da dogon siket tana yar wakarta tajiyo sallamar Ahmad tadaga kai dasauri da mamaki saita fasa ihu dajindadi tana fadin yaya Ahmad dagaske kaine dan Allah tawurgarda kwanon dake hannunsa tanufeshi dagudu ta kankameshi tana ihu umma dake kicin tajiyo tafito fasauri ta leko dadi damamaki yacikata tayi wurgi da ashana tana fadin Ahmadu kaine da tsakiyar ranar nan kesakeshi mana kinbi kin kankameshi kamar zaki kadashi kunya takama ma'u tasakeshi dasauri shi kam ji yayi kamar sudauwama ahaka 1⃣5⃣ DAME AKE ADO 3 Amman dai yadake ya ajiye jakar hannunsa dasauri ya isa ga ummansa yadurkusa yana gaisheta umma tadinga kallonsa cikin farinciki dajin dadi tana amsawa jitakeyi kamar tagoya shi abayanta don dadi ma'u kuwa tsaye tayi tanata kallonsa gaba daya yayan nata yasauyamata yini akayi damurnar dawowar Ahmad su ma'u ankulle cikin daki sai hada kaya takeyi gaba daya zaman gidan umma datake doki yanzu ya isheta domin shagwabar datakeyiwa umma da yanzu duk tadaina kuma tanason gwada irin abinda take koyo alittafi agidan mijinta musamman girke girke data kware yanzu akanyinsu umma tashigo dakin daukar wani abu tahango ma'u anata hada kaya dariya taso kwace mata amman saitadake tace Asma'u menene kikeyi haka kuma? Babu kunya tace Umma kayana nake hadawa koba yanzu zamu komabane ? Umma tarike haba damamaki tana kada kai Au har zaman gidan namu ya isheki kenan? Ma'u tarufe fuska kunya takamata tana dariya umma tayi murmushi aisaiki huta da hada kaya domin bayau zakukomaba saigobe anje angyara gidan tafice tabarta murnar ma'u takoma ciki taturo baki gaba shikansa Ahmad abinda yake bukata kenan yakoma gidansa yakebe damatarsa kohira suyi amman yaya ya iya da hukunci ummansa dole yayi shirin kwanciya adakin gwaurayen gidan amman ba sukwanta da wuri ba anatashan hira dasafe kamin kowa yafito ma'u tasalara wankata sanda umma tafito domin dama koko taci karo da ita anata shafa hoda da fesa turare umma tatabe baki nashiga ukku Asma'u badai nan shirin tafiya gidan mijinki kikeyi haka da sassafe ba? Malam yadaga labule yana kallonsu bayan yadawo daga masallaci yayi murmushi tolaifi tayi kenan kefa kikaimata gori kullum yaukuma saikidamu Amman dai tabari ayi karin kumallo ko? Shima Ahmad tun da sassafe yashirya yabaiwa kowa tsarabarsa sai tamatarsa kawai yabari acikin jakarsa Umma da malam sunata zolayar ma'u da Ahmad dasuketa hada kayansu suka fice suna dariya shatar mota taxi suka dauka har kofar gidansu gidan yayi futu futu cike da tsananin kura kamar anyi shekara ba ashiga cikiba ma'u tacire gyalenta tasakale ajikin igiya tafara karewa gidan kallo tana tunanin ta inauadace tafara gyarawa ne? Ahmad yabita da kallo tunda yadawo yake mamakin irin girma da cikar da ma'u tayi saikace yayi shekara rabonshi da ita kamar ance takalli inda yake tajuya tanafadin yaya ta ina zanfarane takasa karasa maganar saboda irin kallon dayakemata tadauke kanta dasauri domin yamzu tasan irin ma anar kowane irin kallo shima yadanji kunya amman saiya dake yace wannan aikin yafi karfinki kekadai ma'u dole saina taimakamiki bari kigani saiya fara kokarin cire kayansa yana ajiyewa shima akan igiya yarage daga shi saigajeren wando da singileti tasanya hannu suka cigaba da aikintare saikarfe hudu sannan gidan yadawo hayyacinsa yanda suke bukata sunyi butu butu da kura shiya fara shiga toilet yayi wanka bayan yafito yasanya kayan da yabari akan igiya yafice domin yaje yasiyo musu take away saboda yamma tayi babu damar yin girki ayanzu yana fita itama ma'u tafada wanka bayan tafito tafara gyara jikinta dayin turare masu kamshi domin Umma wannan karon batayi sanya gurin hada mata kayan kamshi da gyaran jikiba wata kila tahimci har lokacin ma'u budurwa ce ita kamin kace wani abu gidan ya dauki wani irin kamshi maidadi dasanyaya zuciya tafara duban kayan da yayan nata yakawo mata tsaraba dukansu kananan kayane saikuma rigunan bacci saikuma kayan gyaran gashi kala kala da mayuka komai maikyau tasan yayan nata danayune amma batayi tsammanin ya iya zabe kamar hakaba saiyanzu da idanunta suka ganemata tama rasa wanne kaya yakamata tasanya domin kowanensu yanada tsananin kyau daga karshe dai ruwan idonta yakare akan wani dogon siket mai roba da alama idan akasanyashi zaikama jikin mutum rigar kuma maikama jikice kwarai dagaske koda tasaka kayan sun Amsheta kwarai da gaske kitson kanta shikune don haka yadace da kwalliyarta kasancewar tanada gashi tayi dauri dawani gyale kitson yafito tatsakiya yasauka abayanta tasanya wani dogo dankunne wanda shima yanadaga cikin kayan dayayan nata yasiyomata bayan tagama tsantsara kwalliya takoma falo tana kallo domin ankawo wutar nepa alokacin saibayan sallar magriba Ahmad yashigo gidan domin yabiya tawurin abokinsa ishak sungaisa sannan yayi yanbiye biyensa dai bata damuba domin bayan kallon datakeyi yan matan unguwar su A'ilo sunata shigowa dagaisawa suna murnar dawowarsu kaitsaye falonsa yanufa domin can yaji motsinta baifita da babur dinsaba domin yasan shima yana bukatar gyara saiwashe gari zaikaishi aduddubashi tukunna hakan yasanya ma'u batasan yadawoba saida yashigo dasallama tadago kanta dasauri ta kalleshi saitamike daga zaunen datake tanufeshi tanafadin sannu dazuwa yayana ta amshi kayan dake hannunsa tanufi cikin daki domin ajiyewa Ahmad yabita!da kallo komai najikinta juyawa yake yabude baki saikace wani sauna ANYA KUWA WANNAN MA'UNSA CE BASAUYAMASA ITA AKAYIBA ? Batasan yanayiba harya isa yazauna jikinsa yayi sanyi abinda yakeji gameda ita yadinga dawo masa ko acan legas yayi fama da irin wannan matsalar saidai yadinga dagewa da addu'a donkada shaidan yayi galaba akansa komai na ma'u yasauya cikin dan wannan lokaci kodayake kokamin yatafi yafara fuskantar wasu yansauye sauye atare da ita amman basu kai nayanzuba tamike tashiga kicin tadauko babban faranti tajuye musu Abinci dayayimusu take away takawo gabanshi ta ajiye yaya sauko muci nifa yunwa nakeji yasauko yanafadin nima haka Amman dai abaki zaki bani ko mamata? Tayi dariya takauda kai kunya tarufeta azuciyarta cewa tayi mezaihana nabaka nagwada yanda Alhaji bashir yayiwa fauziyya akanka ( TACIKIN LITTAFIN SAWUN GIWA) Amman afili bazata iyaba yayi murmushi yafara cin abincinsa yadinga janta dahira yanabata lbr abinci ikko itama tanabashi lbr abubuwan dasuka faru ahaka harasuka kammala cin abincin dukkan hankalin Ahmad yanakan ma'u ayau dai yake zaton dauriyarsa takare idan bai isa ga matarsaba komai zai iyafaruwa gareshi Ita kanta ma'u tanajin tanajin wani abu yanayawo akanta duk lokacin datakalli mijin nata domin tacika tayi dankam babu wata damuwa kota kwabo aranta amman kowa yarasa yanda zaitunkarar dan uwansa Ma'un ce tafara gudowa dakin baccinsu tasanya kayanta don akwai rigunan bacci kala kala don haka tazabi daya maikyau tasanya duk da dukkan rigunan anahango komai na mutum idan yasanya itakuma bazata iya yarda yayanta yaganta ahakaba donhaka tahaye gado takudundune ciki bargo shima baiwani jima afalo ba yabiyo bayanta saiya taddata agado kudundune ya isa kusa da ita yazauna daga gefen gado yana fadin ma'u sanyi sanyi kikejine haka? Kinga bude naga yanda rigar tayimiki dukkan kayan dabasuyimiki kyauba canzasu za ayi tayimin kyauma Allah yaya............A ah sainagani da idona bari nagani yafara kokarin janye bargon tana rikewa da yar kissa amman sai da yacire yazubawa halittar matarsa ido WAIDA GASKE DAMAN HAKA MA'UNSA TAKE? Takara kudundunewa zuciyarta nacigaba da bugawa tabbas dai abinda take karantawa cikin littafi zaifaru akanta duk da batasan awane hali yakeba shi mijinta jikinta yabata yakura mata idone don haka takara matse jikinta gabanta yanaci gaba dafaduwa yayiwata yar doguwar ajiyar zuciya yamike tsaye yace taso ma'u tayi shiru batayi maganaba kuma bata motsaba harya dan juya yafara tafiya amman saiyasake waigowa yace ma'u kina jinafa daure tashi kiyo Alwala zangaya miki abinda zakiyi bayan kinyi Alwalar Tayunkura kamar kifanya harlokacin jikinta yana nannade tarike zanin yana kallonta yakada kai yayi murmushi yawuce tayi ajiyar zuciya bayan tahango inuwarsa yagama ficewa tadafe kunci takara maida hannunta ga kirjinta dayake bugawa tayi dan murmushi sannan tamike tafito yana tsakar gida kusa da bandaki yana daura Alwala Tarakube tana jiran yakammala yayi kamar baigantaba yana gamawa yashige falo sai tanufi bandakin tashiga tajima tana sakawa da kwancewa kukan wata mage datazo wucewa daga kan soron ne yabata tsoro tashige dakin da sauri yana zaune akan sallaya ya tankwashe kafafunsa yayi shiru amman amman bakinsa yadan motsi alamar lazimi yake ta isa kusa dashi tatsaya daga bayansa yaji alamun shigowarta don haka yamike da kansa yadauko hijabin sallarta yamika mata batare da yakalletaba yace sallah zamuyi raka'a biyu ma'u yashige gaba yana kokarin tayarda sallah tabishi abaya ta tayar baija dogayen suroriba yayi sallama yajuyo yakama kanta yafara karanta addu'a ALLAHUMMA INNI AS'ALUKA KAIRAHA WA KAIRA MAJA BALTAHA AKAIHIM WA'AZUBIKA INNI SHARRIHA WA SHARRIHA WA SHARRA MA JABALTAHA ALAIHI " yayi dan shiru bayan yakammala addu'ar yana kallonta cikin kwantarda murya yace ma'u nasan kin iya farillan addini dasuka kamata kisani ko akwai wani abu dabakisaniba? Ma'u tagirgiza kai kawai yasake yin murmushi yace ma'u ai bangane mekike nufiba kibude baki kisanarda dani eh ko a'a zakicemin shine zanfahimta kuma harnagamsu eh nasani tafada da sauri yace yauwa nasan haka tashi kije kisanya rigarki dakikasanya dazu kikwanta baijira jin abinda zataceba ya mike yafice yanufi kicin dinsu yaduba yayi sa'a akwai kalanzir donhaka yadora ruwan zafi kadan yadafa shayi yasanya koren ganye shayi yashanye karamin kofi sannan ya nufi dakin yayi sa'a akwai wutar nepa fanka kada dakin nasu yanda takwanta dazu haka ta kwanta yasanya hannu yakashe kwanfitilar dake dakin yakarasa gadon yakwanta daga gefe inda yake yanajin sautin ajiyar zuciyar ma'u yadan matsa gab da ita yanadan gugar jikinta amman baishafetaba sai yace saiyace ma'u bani lbr dame dame yafaru bayan tafiyata? Tayi shiru takasa magana saidai faduwar gaban nata yadan ragu yacigaba damagana ahankali dai dai saitin kunnenta tunda kinki bani lbr bari nabaki mawa lokacin da akace andaura aurena dake sainaga abin kamar wasa kamar shiririta harna tare dake banajin komai akanki saikulawa ta kanwata sannu ahankali damuwa da tunaninki yafara shiga raina lokacin dazan tafi legas nayi tsammani nadamu darabuwa dakene domin sabo da shakuwa data koma shiga tsakaninmu saidai bayan naje nagano kaunarki ne nagaskiya yashiga zuciyata yayi dan shiru yana murmushi shidaya cikin duhu wani shauki da bakon abu nasake shigarsa yadan kara matsawa jikinta yakamo hannunta yarike kam cikin nasa yafara wasa dashi yace ma'u babu abinda nakeso aduniya yanzu bayan Allah da manzonsa da kuma Ummata kamarki tsikar jikinta tatashi yarr! Tadinga jin wani abu yanashigarta wanda bazata iya fasaltashi ba tadinga jin kamar tajuya tarungume mijinta amman saitajiyo tafukan hannunsa sun saki hannunta sunfara kaikomo cikin jikin jikinta yacigaba da magana cikin kunnenta bantaba zaton zanyiwa ma'una irin wannan soyayyarba kigayamin ma'u mekimeji akaina yanzu domin tunda nadawo naga wani abu akwayar idonki kuma gangar jikinki kamar tana nunamin wani abu nayadda.............yasake kasa da murya yana cikaba da magana ma'u kinyi wayo kinsan meye Aure kin amince nazama miji agareki nagaske ba suna ba kibarni nafara raya sunnah dake afarkon duniyata kibarni naji abinda kowa yakeji acikin aurensa ma'u yakankameta ajikinsa kamar zaimaidata cikinsa itakam tagaza cewa komai domin yayimata dukkan abin zaikashemata jikinta dazuciyarta tagamsu da amsar mijinta takaranta littafan soyayya masu dama amman bata taba karanta irin wannan soyayyar da mijinta ke gwadamata ba cikin Duniyar shauki tajiyoshi yana cigaba da sambatu da rokonta bakice komai ba ma'u kibani dama dan Allah ki amince nazama miji agareki da gaske cikin rawar baki da kyar tafurta na amince yayana domin tafuskanci yanagab da shidemata Allah mai iko kawai Ahmad yake iya ayyanawa cikin ransa Hmmm ni abdullahi kam sai ma'u other wise sai dae ku tsintoni a sambisa Abdullahi yusuf maitama 09034598552 @whatsapp

1 May 2015 at 09:23 · Public Save · More Like React Comment Share Like66 Write a comment...

· Usman Sulaiman Jahun maitama kwana biyu Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books wallahi kuwa usman ya school? Ummu Khadijah Ummu Adnan Tnx Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Usman A Umar Uhm nima haka nakeji sai dai kash banda wacce zata jiyar dani Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Aminu Ibrahim hhhhhhhhhhhhh thanks Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Ukashat A Abbakar tnx alot Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 4 May 2015 Jermeelerh Muhammad Umar Sannu Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Abubakar Ibrahim Ita kuma uwargida fa babu lbrnt ne Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Aminu Tukur Dange Hahahahaha ayi haquri ai taxama taka Like · React · Reply · More · 1 May 2015 Mohammed Bin Ahmed Hmm su maitama ayi dei ahankali saboda Ahmad nada bala in kishi . Like · React · Reply · More · 1 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 16. 1⃣8⃣ DAME AKE ADO 3 Haryakai ma'un ga matsayin dakowace mace keshiga wato CIKAKKIYAR MACE ba ma'un kadaiba shikansa yasha wahala domin tare suka bare junansu akwali amman ma'un tabashi mamaki domin tayi matukar dauriya don haka harbacci yadauketa tana kan kirjinsa yanashafar gashin kanta dajin dadi cikin ransa gami dayima Allah godiya dayanufeshi dayin Aure harya dandani zakin dakecikin Aure gajiya da kasala suka taru sukayi musu rubdugu dan haka sunkusan makara shine yafara tashi yadora ruwa yashiga wanka kafin yafito daga wanka an idar da sallah amasallaci baiji dadin hakaba amman yasan Allah zaiyafemasa tunda ba daniyya ya aikata hakan ba saida yafarayin sallah sannan yagirka ruwa maidimi yanufi dakin har lokacin ma'u tana bacci domin tasha matukar wahala dabata taba shaba cikin rayuwarta cak yadauketa kamar yar bebi sai asannan tafarka tanajinsa takara maida idonta tarufe domin kunya tagama rufeta yayi murmushi kawai baice komaiba cikin faffadar robar daya kusa cikawa da ruwan zafi yatsundumata aciki bayan cire dan yalolon zanin dake jikinta tayi doguwar ajiyar zuciya sanda ruwan yafara ratsa jikinta amman har lokacin idonta yana rufe takasa budewa yayi murmushi yajuya yabarta abandaki tayi wanka tagasa jikinta saitaji kwarin kijinta kafin karfe 8 nasafe yayi Ahmad yagama yimusu komai nakayan karin kumallo saida yayi dagaske taci domin kunyarsa tahanata sakat shikam dariya kawai yakeyimata da tsokanarta ranar haka nan suka kareshi cikin nishadi dajindadi gami da soyayyar juna Aranar tare suka fita siyayyar kayan abinci dayake akwai dankudi ahannunsa harda karamin cooker gas yasiyamata yayikuma yimata siyayyar kayan kwalliya dana shafa dai dai karfinsa Rayuwar Ahmad da ma'u tazamo abin sha'awa domin kullum soyayyar junansu kara karuwa take yi acikin ransu sun saba da juna sun shaku da juna Ahmad ya iya soyayya yakuma koyarda da ma'u soyayya da sonsa domin idan yafita aiki ta kagu yadawo donma dai karatun littafi yanadan dauke mata hankali kadan BAYAN SHEKARA BIYU Ma'u tazama CIKAKKIYAR MACE data iyarike mijinta zuwa wannan lokaci duk wata halitta da kira ta kammala fitowa Allah yayimata maitsananin daukar hankali musanman tsarin jikinta da akecewa maikirar kalangu Ahmad yakasa gano sirrin matarsa daga karshe yabaiwa zuciyar amsa kawai Allah ne yahalicceta hakan 1⃣9⃣ DAME AKE ADO 3 Yautana zaune tana gogewa mijinta kayanda ta wanke masa tajiyo sallamar maryam maryam taga labule tashigo tana fadin komatar gidan batananne ma'u tamike dasauri tana ihu farin ciki tarungume maryam suna tsallen cikin farinciki ma'u tayi murmushi tana fadin naji dadin ganinki maryam nayi zaton ai kinmanta danine wace ni kinsa makaranta ke hanani zuwa amman yanzu tunda munyi candy ai harsaikin gaji dani kamin nasamu Admission! Admission kuma maryam ma'u tatambayeta cikin da sanyi jiki maryam tabata amsa da eh kinsan babana yanason nacigaba da karatun kamar sauran yayyena dadamuwa ma'u tace kinji dadi daman nice ke niyanzu saizaman gida bansan ahalin danakeba koda ace candyn ma nayi toda da dansauki anangidan ma'u maryam tayini har saida tataya ma'u girkin dare ita ma'un tana sha'awarta ta kammala karatunta ita kuma tana sha'awar ma'u nayadda tayi sa'ar Aure duk da mijin nata bamai hali bane amman suna cikin rufin asiri saigab da sallar magriba maryam tabar gidan amman tatafi tabar zuciyar ma'u damiki wanda tayi niyar amayar dashi yau kota huta kamar yanda Ahmad yasaba dawowa yauma hakan yadawo yakaraso cikin gida yakafe babur dinsa sannan yajanyota jikinsa yamatse gaggawar tameye bayan takaceni kaikadai bamai gutsirarma to meye danna taba kayana kuma za'adamu bar maganar haka jekacire kayanka kayi wanka tukunna harsaida yaci abinci yakoshi suna falo suna kallo sannan ma'u tabijiromishi da abinda keranta alokacin kanta yana kan cinyarsa yana wasa da gashinta suna cikin nishadi yadaga kai ta kalleshi tace yaya akwai wani abu dake damun zuciyata inason gayamaka amma bansan yadda zaka dauki abin ba ya lakace mata hanci yana murmushi yaushe muka fara yar haka dake ma'una kiboye abu aranki yasanya miki ciwon zuciya idan narasaki mekike tunanin zaisami rayuwata? Tayi murmushi saika sake wata matar yargayu tayi kara saboda mintsilinta dayayi wacce mace ce zata auri mutum irina? Idan narasaki nima narasa kaina bayan su abba babu wanda zaikara bani matat aure har abada.........ya isa haka bazan mutu bama saikarigani da shekara ashirin daya yakuma mintsininta yana dariya tasanya ihu tazame tanafadin kai yaya wlh ka iya mugunta mugunta ko gaskiya yaza ayi nayarda na mutu nabarki har shekara ashirin da daya wato wani ya auremini ke ko? Naki wayon rana daya zamu mutu nida safe keda yamma yanda yake maganar babu dariya yasanya tafashe dadariya tana fadin kaji yaya kamar kaleka littafin kadararmu kasan komai nidai bazanmutu dawuriba gaskiya Anji anbarmiki duniya kiyi gadinta amman gayamin abinda kikeboyewa kona samu kwanciyar hankali don har kindagamini hankali yanzu yaya inason cigaba da karatu ne! Gabadaya annurin fuskarsa yadauke kamar baitaba dariyaba hakan yakara haifar mata dafaduwar gaba amman saitaji yace karatu kuma kamar yaya? Tana kallonshi har lokacin tace karatun boko mana dankaga abokan karatuna harsunyi candy nikuwa inata zaman banza wannan kalmar karshen tashigeshi harya kalleta dasauri yana koma maimaita maganar zaman banza fa kikace ma'u zaman auren ne yakasance zaman banza tawayance dafaduwar gaba tace bahaka nake nufiba yaya wai inanufin inazaune haka babu komai ga abokan karatun nawa harsunyi candy yayi shiru yanasauraronta kamar bazaiyi maganaba yakamata kigane shi aure yanagaba da komai garayuwat ya mace sannan inada karfi da halin dazan iyarikeki kiyi karatu amman ayanzu lokaci yakure bazan iya kallonki kinafita kullum dasunan karatuba wasu nagane mini mata dan haka kicire maganar karatu cikin kundin burikanki yanagama fadin haka yamike tsam danufin ficewa cikin dakin amman maganarta tahanashi fita haba yaya kada kazamto irin mazan nan masu daukar mace tamkar baiwa kaima kanayin abinda kakeso yakamata kabani dama kosaudaya ne arayuwata gaskiya banida burin dayawuce ganin nayi karatu yawaigo baki bude jin kalaman dasuke fitowa daga bakin ma'unsa kamar wadda tarubuta cikin littafi tana karantowa amman saiyaga bahaka shidin take kallo kyar kuma tanacigaba dazakulo abinda keranta yaso yakyaleta tacigaba da maganarta amman saiyakula kamar batacikin natsuwarta danhaka dasauri yadakamata tsawa yanafadin kikame bakinki inhar nine mijinki bazakiyiba har abada!

Kuyimin uzuri plss banda lapia ne kuma gashi ina school shiyasa. Post en yau ma kunga baida yawa............. Sannan kuma jiya Amal din nuri tace zata para kawo muku ziyar daya bayan daya. Zata para daga kan masu suna Rukayya da Amina then Abdullahi da amma pa bani Abdul en ba Abdullahi yusuf maitama 09034598552 @whatsapp

See translation 3 May 2015 at 10:20 · Public Save · More Like React Comment Share LikeWow66 Write a comment...

· Muazz Alawo tnks Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Sorry grp a watsapp Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Karimat Abdullahi Allah ya baka lfy 1 · Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Maymoonart Muhammad dan Allah plz ina zan samu continuation din wannan littafin DAME AKE ADO? Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Dan allah yan uwa ga number na kusani a gurp din dan allah 08065240700 Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Salees Naja'at eyyah d only maitama, wish you quick recovery broth. Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Kabiru D Shagari Tnks. Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Sadiqa Ahmad Allah baka lfya Like · React · Reply · More · 3 May 2015 حفصة أبو بكر tnx alot maitama Allah yabada lfy Like · React · Reply · More · 3 May 2015 Mukhtar Umar Daura Allah baka lpy Like · React · Reply · More · 3 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part18. don haka kisanya wannan aranki inakuma gargadinki dakar kikara yimin irin wannan zancen dagayau!!! Yanufi kofa dasauri yafice yana huci wani malolon takaici yataso yatokare zuciyar ma'u WANNE IRIN MIJINE ALLAH YABATA MAIKISHIN TSIYA DASON KANSHI KUMA YASANI SARAI KARATUNNAN AKWAI ALFANU ACIKI AMMAN YARUFE IDO YAHANATA DON YANA TAKAMAR YAFI KOWA KISHI saitafashe dakuka takaici da bakinciki cikinta yahautsine kirjinta yakama zafi don bakinciki tarike ciki tana murkusu tana kuka shikam yariga yafice baimasan abinda kefaruwa da itaba can taji amai yatahomata tayunkura tamike dagudu tanufi tsakar gida kafin ta isaga rariya tuni aman yacimmata tatsuguna anan tafara kelayashi tanadafe ciki dakirji kamar zaibiyo hancinta yafito waje takeji yashigo dauke da maganin dasauro daya siyowa yahangota durkushe tana amai yakidime yanufita dasauri yana tambayarta abinda yafaru yaya akayi ma'u? Meyasameki lafiya? Duk yarikice yarude bata iyacemasa komaiba saboda aman datake yamike yanufi robar ruwa yadebo ruwa cikin buta yanufeta yafara zubamata akanta don tajigata da aman sannu ma'u meyakemiki ciwo kuma yanzu? Takada kai muryarta adashe tana fadin babu komai saidai tashin zuciya kadan kadan zaidaina shima garin yaya kikafara aman ma? Tarintse ido bansaniba nima yayi shiru yana kallonta datausayawa saiya mike bari nasamomiki magani a chemist din sister deeje yafice da sauri itakuma taji wani sanyi yanashigarta tajanyo bargon dake gefe ta dukunkune yadawo dauke magunguna ya ajiye ya dauko ruwa yabude abinda ta lulluba dashi ya tallafo kanta yana fadin ma'u tashi kisha magani batayi musuba ta amsa tafara sha har tahadiye duka ya maidata yakwantar ya mike yafita dakayan itakuwa takara kudundunewa domin har lokacin akwai zazzabi ajikinta yanacan yanakokarin dauraye kayan databata yakuma jiyo kakarin amanta yabazamo dakin dagudu yasameta tana durkushe agaban gado ta amayarda dukan magungunan datasha yadafe kai dadamuwa kamar zaifasa ihu ya isadai yagyaran wurin ya dauko kayan yajibge akan wadancan na waje yadawo yadauko dan ruwa yana bawa matar tashi yafasa wanke kayanma yarungumeta akirjinshi yana shafa kanta da lallashi domin dabaiyi mata masifarba da bazatayi aman har hakaba hakanan suka kwana tana aman tayi yakai sau 4 cikin dare danhaka tun asubah yafara shirin kaita asibiti karfe bakwai sunfice yaso yakaita nakudi amman kuma babu kudi ahannunsa domin wata yafara nisa don haka dole na murtala muhammad yakaita Dayake sunfita dawuri sunyi sa ar ganin likita dawuri akarubuta musu magunguna harda karin ruwa da kuma gwajin fitsari harwajen karfe 3 suna asibitin saida ruwan yakare tas! Saidai harsannan Ahmad baisan abinda kedamun matarsaba donhaka dazasu tafi yasamu wata ma aikaciyar jinya yamikamata korafi yana fadin sister don Allah mekedamun matata dazu ina rude bantambayi likitaba gashi yatashi yanzu ma aikaciyar jinya tayi kamar bazata amsaba datayi ido hudu da Ahmad saitagaza yin musu domin shi mutum ne maikwarjini da haiba dawuya kakalli tsakiyar idonsa kayimasa musu bayan tagama karanta abinda kerubuce ajikin katin ta kalli ma'u tana dariya tana fadin inatayaki murna kinkusa zama mama sam ma'u batafahinci komaiba Ahmad yadan fahimta amman duk da haka sai yasake kallon ma aikaciyar jinya dasauri sister waikinanufin ciki ne da ita tayi murmushi tace kacire kalmar wai tamika masa katin tana murmushi Allah yaraba lfy ma'u kam kunya duk takamata kamar tanutse agurin takauda kanta gefe tana murmushi Ahmad yakuramata ido yana kallonta yama rasa wane irin farin ciki yakamata yayi yadan kalli mutanen dake kai dakomowa banda gudun baki daya suri matarsa yayi rawa da ita sannan yakaita har bakin titi inda zasushiga motar amman dai yadaure yariko hannunta kawai yanata wage baki tamkar mai tallan makilin yace ma'u maiyasanya kika boyemin wannan farin labarin bata iya kallon fuskarshi ba dankunya nima fa bansaniba yaya zaikara magana ta katseshi yaya muyafi gidan mutane suna kallonmu sannan kuma yunwa nakeji wannan abin data fada yasanya ya dan natsu yakama hannunta suka nufi titi shatar adai daita sahu yadaukar musu harkofar gida daman yadan tsaya yasaimata take away dan haka suna shiga gidan yafara shirya mata shi agabanta yace tacinye tas sannan tayi sallah Allurar da akayimata natsaida aman sunyi aiki ajikinta batajin aman ko tashin zuciya a yanzu dan haka tadanci abincin dayawa Ranar dai kowurin aiki Ahmad baijeba sai waya yayi yasanarmusu matarsa batada lfy agayawa manaja yacigaba da kula da ma'u kamar zai lasheta BAYAN WATA TARA kwanci tashi bawuya awurin Allah domin zuwa wannan lokaci cikin ma'u haryashiga wattani tara dukkan wata kulawa dagata tanasamunsu awannan ciki Kamar ranshi haka Ahmad ketattalin cikin nata jama'a kuwa kowa yasan ma'u nada ciki tunyana watanni 4 musamman hjy da Umma sune abokan neman shawararsu Kullum sambayajin kunyarsu indai akan cikinne ma'u takanyi mamaki yanda Ahmad ke tsananin son haihuwa kamar yayi hauka akan kula da cikin aikima don ance anabukatarashi awajenne dole shiyasa yake kyaleta yatafi yau tana kishin gide akan kujera tana kallo tayi wata irin kiba cikinta yafito sosai Ahmad yashigo falon da sallama hannunsa dauke da manyan ledoji guda biyu ta yunkura da kyar tanakokarin mikewa gamida Amsa sallamar yakaraso kusa da ita da sauri yanafadin kinga bance kitaso kitareni ba cigaba da hutawarki nagode Abdullahi maitama 09034598552 @whatsapp

See translation 6 May 2015 at 09:21 · Public Save · More Like React Comment Share Like68 Write a comment...

· Mahmud Yusuf Adam Abubakar lallai sumau ankusa xama mama Like · React · Reply · More · 24 Jun 2019 Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah mungode sosai Like · React · Reply · More · 21 Aug 2018 Sa'adatu Ibrahim Panda tnx Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Abdull Muh'd Da kyauuu Like · React · Reply · More · 7 May 2015 Abdullahi Yahya Abdullahi Yahya Don Allah adena dadewa ba'amana posting ba Like · React · Reply · More · 7 May 2015 Faisal Sa'ad Isma'il Maitama muna godiya Like · React · Reply · More · 6 May 2015 صفية علي محمد MashaAllahu,Allah Ya rabasu lhy.Lalle kam su Ma'u an kusa axama Mama. Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Aysher A Imam garkiya maitama kana qoqari thanxs alot Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Umar Abdulkadir Múwadda Malik ya batun cigaban #FARIN-CIKI-SAUDAYA Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Sadiqa Ahmad YA JIKINKA 1 · Like · React · Reply · More · 6 May 2015 Kulsum Nasir replied · 1 reply View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 19. 2â£2⣠DAME AKE ADO 3 Tayi murmushi waton kayimin haramiyar wannan ladanko yaya? Yafara kokarin fito dakayan dake ledojin dayazo dasu takatseshi yaya dakafara cin abinci kafin kayi komai ko? Bari nadaukomaka tasake yunkurawa zata daukomasa yayi saurin dakatar da ita dakata ma'una naga alamar dai sokike saikintashinnan dole toni akoshe nake Akoshe kake yaya? A ina kaci abinci kuma ta tambaya yanayin fuskarta yafara sauyawa zuwa damuwa yalakucemata hanci kada kiyi kuka matata kanwata daga gidan hjy nake bawatace tabani abinci ba itacema tabani wannan kayan wanda tatara newai yace nakawomiki tadan saki fuska tana dariya naga kayan hajiyar? Wannan tawace ninasiyosu wannan kuma na hjy ne tayi shiru tana kallon ledojin duka saitayi murmushi tanuna ledar dayace nashine kayan yayi dariya ya ajiyemata gabanta taja ledar tafara duban kayan tana fadin nasan mijina dan gayune yafi hjy iya zabe tafara daga kaya yaya kayan sunyi kyau ka iya zabe wlh amman kamar sunyi yawa ko? Inji wa? Yarinya da ace kudine dani wlh da akwatima zanciko dakayan dana ko diyaya to wai ya akayi kasami biyu ganaka gana hjy aida daya ya hakura daya yasiya? Wasu kudine damuke karamin dashe akahadamin yau awurin aiki shine naje kasuwa nayo siyayyarnan saina yanke shawarar naje nanuwa hjy abinda babu saitayamin nakaro to inazuwa tanaganina takama fada akanme dazan siyo banyi shawara da itaba domin itama tasiyo nata kayan daga karshe dai tahadoni danata kayan tace saina kara ma'u tayi dariya gaskiya tafada wlh akan cikinnan kazama wani babban mara kunya ko agaban umma da abba bakajin kunyar maganar cikinnan yayi yake yana fadin ma'u kenan laifina kikagani? Idan banyi daukin cikinnanba meya kamata nayi dokinsa kada kimanta fa shine dan uwana jinina kuma tsatsona Nakasance babu wani wanda yazamto munhada wata alaka ta daga jini awannan duniyar abinda zaki haifane kawai zaizamto min haka idonsa yataru da kwallah inason kihaifamin yara guda guda ashirin ma'u yanda zanraya sabuwar zuri'a daga bangarena nima tunda banida kowa awannan duniyar sai mahaukaciya mahaifiyata data rasu da ace tarayuma data iya zamemin abar kallo kokuma takaini wurin babana dayayimata cikin shege har akahaifeni tasanya hannu dasauri ta toshemasa baki tana kada kai..dan Allah yaya kadaina wannan maganar saikawai yafashe daí ½í¸­í ½í¸­yadora kansa akan kafadarta yana kuka sai itama tarasa abinda yakamata tayi masa sai kawai itama tafashe da kuka yayi sauri yafago ido yana kallonta yajanye jikinsa yi shiru ma'u kuka baikamace kiba kefa yargata ce kinada uwa da uba da yayye da kuma miji kuma yayanki nikuma banida kowa daya kasance jinina saiwannan abin dake cikinki ya isa haka yaya idan basokake kadagamin hankaliba yayi shiru yana ajiyar zuciya kalamanta sunratsa zuciyarsa cikin kunnensa tace gobe zanje awo yaya za ayine? Zankaiki idan angamamiki saikiwuce gida idan natashi daga aiki sainabiya tacan nataho dake saiwajen karfe biyu takammala komai da komai na awo tatako dakyar tanufo bakin kofa saitakejin duk jikinta yayi nauyi yanzu da kyar ta isa bakin titi tasami shatar mota tashiga hargidansu tabiya mai motar tashiga soro saitaja tatsaya turus dafargaba danganin Raliya abakin kofar gidansu tana waya hankalin Raliyan yayi kanta itama sukayiwa juna kallon kallo kowace mamaki yabayyana akan fuskarta ganin yar uwartata dauke daciki Amman Raliya bayan mamaki harda tsananin takaici da kishi domin bayan tadawo yaji lbr Ma'u aka aurawa Ahmad saikuma taganta kwasam da ciki babu zato babu tsammani ma'u kuma tana mamakin gani Raliya da ciki tsoho bayan tasan ba aure ne da itaba KOCIKIN SHEGE TAYO NE? Raliya ce taja dogon tsaki tajuya cikin gidansu da sauri Lami tana zaune akan benci tayi tagumi tashiga tana kwalamata kira Lami! Lami!! Lami!!! Dakarfi lami dake zaune tadago ido yakalleta dasauri cikin fargaba bakin cikin duniya duk ya isheta tace yaya akayine kike kwalamin kira haka? Ta isa gabanta tazauna tana haki tace yarinyarnan ma'u ce tashigo yanzu naganta da ciki kuma cikinma tsoho waikina nufin har ciki tasamu da mijina Lami tatabe baki bagashinan idonki yanunamikiba Raliya? Wlh koganinki bana kaunaryi Raliya nagama kuri dacika baki akanki amman kidawomin da wannan abin kunyar dawanne ido zankalli duniya da makiyana masuneman gazawata suyimin dariya? Raliya taturo baki gaba tana kumburi haba Lami saunawa zangayamiki banyi iskanci dakowa ba wannan cikin na Ahmad ne kwanciya yayi nayi zaton yafadi tuni saicikin wattanan yatashi idanke bakiyarda cikinsa bane waye zaiyarda dani harya kwatarmin yancina? Malam jibril yashigo fakan fakan ransa abace domin baikaunar kolekowa gidan don baison ganin Raliya da cikin da shege ajikinta wanda yakejin kamar yaharbeta yakashe abinda ke cikinta yanason yagayawa dan Uwansa amman baisan yadda zaidauki abinba donhaka yaja bakinsa yayi shiru amman bakinciki yanajan ransa da zuciyarsa yadebi ruwa yazuba abuta yanufi bandaki da sauri Lami tafito daga cikin daki da sauri tafara kwalla masa kira Malam! Malam!! Baiko kalletaba yashige cikin bandaki abinsa lami taja tatsaya turus tarike kugu tana masifa amman wannan wulakanci ne inaimaka magana kayi banza dani tozaka fito kasameni inatsaye inajiranka ai Raliya tafito daga cikin daki tasamu guri tazauna itama Malam jibril yafito daga bandaki yadurkusa yafara Alwala Lami tayi kansa dasauri malam waiko cutar rashin jice tafara shigarka bansaniba? Abdullahi yusuf maitama 09034598552

See translation 10 May 2015 at 07:11 · Public Save · More Like React Comment Share Like54 Write a comment...

· Maryam Adam Isah madalla Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Ukashat A Abbakar tnx alot Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Usman Aliyu Taller Tanx Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Usman Mustapha Muna Bin Ka Bashi Fah Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Abdull Muh'd Da kyaww Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Ali Baduku Toh dae Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Hussaina Idris Weldon Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Maimuna Ismail Yayi munago diya Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Muhaseen Baba Muhammad tnx Like · React · Reply · More · 10 May 2015 Yagana Ali Lalle aikin gama ya gama Like · React · Reply · More · 10 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 20. Yadaga kai afusace Allah yakiyaye saidai kiga wannan bala'in akanki badainiba! Nima din bazata sameniba aniyarka tabika ashe kanaji kayimin banza? Naga kasauya hali dalokacin shigowa gidannan tunda yarinyar nan tadawo kaki zama kaji damuwarta saifishi da kumburin dakakeyi malam yakuma fusata yadago kai yakalli lami damuwarme zanyi bayan wacce nagani manne ajikinta? Aikome yasameta kece kikasaimata da kudinki saita haifamiki shegen kiraineshi bahaka daman kikebukataba? Lami tadaga masa hannu idanunta cikeda masifa tsaya tsaya malam kadaina kiran cikin diyata da shege domin wannan cikin bashege bane da wlh da Ubansa!!! Malam jibril yamike tsaye dasauri yafasa Alwalar yana fadin Au! Kokindaura mata Aurene bansaniba? Wato tayi aure akan aure kenan laifi biyu akanta babu batun aure akan aure auren nan dai guda daya shine akanta haryanzu na Ahmad kuma cikin nasane yasan dahakashi.......malam jibril yafashe dadariya yana kallon lami wacce tafara kuluwa da irin dariyar dayakemata yace wlh nayarda lami bakida hankali yarinyar dabata tare da mijinta tsawon shekaru tatafiyawo amman tasamo cikin shege kice nasane? Ta ina yayimata cikin kokuma tawayar salular zamani? Komeye cikinsa ne idankuma bakayarda ba saikaje kayi tambaya akanhaka tunda tabar gidansa daciki tafita wanda yakwanta mata sai awadannan watanni yatashi kuma shikansa yasan tanadauke dacikin kuma kowa yasan ciki yana kwanciya acikin addininmu dagurin likitoci zamani donhaka dole ya amsa indai bazaka kwatarmata yancita ba nuzanyi duka kotun dake duniyar nan nashiyar shigarta domin kwatarma diyata hakkinta!!! Yatsaya yana kallonta kyar yanda tadage tanazuba bayani yayi kama dana masu hankali saidai kuma yana tantama tabbas mace kanyi shekaru da ciki kuma tahaihu daga baya indai dagaske Raliya daciki tagudu kuma Ahmad yasan da haka tobabu makawa wannan cikin nasane yadire butar dake rike ahannunsa yakarasa kusa da Raliya dake zaune tana kallonsu yace ke Raliya kisanarda ni gaskiya shin dagaskene kintafi da ciki ajikinki daga gidan Ahmad kokaryace kika shirya kawai? Takarkace baki wlh baba da gaskene wannan cikin na Ahmad ne domin yasan dashi tunkamin natafi ninayi zaton yazube ne danaga yadaina girma saikuma dagabaya cikin wattannin nan naga yana tashi idan kuma shi Ahmad din yamusa muje har asibiti agwada agani za'aga jininsa ne acikina malam jibril yayi shiru hankalinsa yadan soma kwanciya idan hakane lallai yasamu mafita yatsira daga daga abin kunyar dayake tunanin yashiga abaya yakada kansa shikenen bari naje masallaci nadawo saimuyi maganar dayaya inazuwa yadurkusa yakarasa Alwalar yafice daga cikin gidan Raliya tatashi tashige dakin ranta yayi fes domin abinda tatsara yatabbata babu kuma wanda ya isa yakaryatata su ma'u sunacan basusan wainar da aketoyaba sannan umma takibata hadinkai sujajanta abin sai sabgoginta takeyi ma'u takagu mijinta yazo yadauketa kosasami damar tattauna matsalar Raliya dashi Malam sule yadawo daga sallar magrib yanufi gida da casbaha ahannunsa yana lazimi yajiyo kiran dan uwansa daga bayansa yana fadin yaya! Yaya!! Yaya!!! Malam sule yaysaya cak gami dajuyowa yakalleshi har yakaraso inda yake yamike masa hannu suka gaisa malam sulemanne yafara magana inakashiga ne jibril kwana biyu banaganinka? Malam jibril yashafa keya wlh yaya inawurin yanbuge bugena daman inason muyi wata muhimmiyar magana ne dakai malam sulaiman yace to to! Mukarasa wajen dakalin can saimu zauna suka nufi wani dan tudu dake kofar gidan suka zazzauna dukansu malam sulaiman ya kalli malam jibril yace masa inajinka meyafaru ne?

Abdullahi maitama 09034598552 @whatsapp

See translation 11 May 2015 at 08:01 · Public Save · More Like React Comment Share Like51 Write a comment...

· Ihsan Zubairu Gakiya raliya ta raina mutane Like · React · Reply · More · 17 Jul 2019 Dauda Yahaya Masanawa MADALLAH Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Marcus Sebastain Otter Hmm Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Babangida Lawan Miko Da kyau Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Fateemah Hassern Phariey Hr na kosa akama raliya wlh Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Faisal Sa'ad Isma'il Sannu da aiki Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Maman Ihsan mungode Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Rahma Hussain Mai Doki Thanks Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Shamwilu B Abdullahi Tnxs Like · React · Reply · More · 11 May 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 11 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 21. Malam jibril yagyara tsayuwa yana tunanin ta inda yadace yafara bayanin nasa canyanisa yace yaya kasan Raliya tadawo gida bayan kwana hudu dasuka wuce kuwa? Malam sulaiman yadan yazabura yace Raliya kuma! Yayi wata doguwar ajiyar zuciya yakara dacewar masha Allahu yaushe tadawo kenan? Yau kwananta 6 malam jibril yabashi amsa yana in ina haba malam jibril amman kakasa sanardani tun randa tadawo din? Amman babu komai tunda kasanar dani yanzu amman kokaro bantabaci da itaba cikin wadannan kwanakin datayi dinba malam jibril yaja doguwar ajiyar zuciya yaya inadan fargabar yanda zanfada maka zuwan nata ne saboda abinda ketattare da ita wato Raliya dai tadawo daciki tsoho kuma.............malam sulaiman yazabura darudani yace cikifa kace jibril!! Ciki dai juna biyu na haihuwa? Ciki nahaihuwa yaya wannan nema dalilin dayasa bakasa sanarda kai harsaida nasami hujjar da zangayamaka don nasan hankalinka zaitashi matuka idan harkaji cikin nata nashege ne amman dayake da ubansa shiyasa nasami karfin guiwar iya tunkararka har nasanarda kai yanzu har lokacin bakin malam sulaiman yanabude tsananin damuwa akan fuskarsa cikin takaici yace Aure kakoma dauramata ne bansani ba dayasanya cikin nata yazama mai uba bashegeba jibrulu? Yanda yake maganar yasanya gaban malam jibrilu faduwa har yaji yanashakkar fadin abinda yayiniyar fadadin saida malam sulaiman yace kaifa nake saurare kacemin cikin nata yanada uba kagayamini waye uban nasa? Malam jibril yagyara zama yace kasan lokacin dabatar gidan mijinta da aurensa akanta baisaketaba.....yayi dan shiru yana kallon malam sulaiman domin yaga yanda yadauki maganar saiyaga yanutsu tsaf yana sauraronshi yacigaba dabayaninsa donhaka malam yaci gaba dabayaninsa koka manta haka yaya? Malam sulaiman ya girgiza kansa tare da fadin A'a banmantaba inasane dacewar Raliya tagudu daga gidan Ahmad batare da yasaketaba injin har izuwa wannan lokacin ma akwai Auren Ahmad akan Raliya Amman duk ba wannan bane yanzu inason naji yanda tasamu ciki halattace ne jibrilu malam jibrilu yagyara zama yana duban yayan nasa eh kafin tabar gidan shi Ahmadu din da ciki ajikinta kuma shi Ahmadu ma da kanshi yasan dashi towai cikin kwanciya yayi saiwannan karon yatashi shine tadawo gida don ashaida tahaifar masa abinsa tabashi malam sulaiman dai yayi shiru yana sauraren jawabin malam jibril saiyaji kamar yashakoshi don bakinciki yarufeshi da duka yarasa dalilin dayasanya kanin nashi yamaida kansa kamar tababbe mara hankali idan yana wani zance yadai daure yace bari natambayeka jibrilu tsawon watanni nawa mace takeyi idan mijinta yasaketa? Dasauri malam jibril yace wata ukku ne yaya malam sulaiman yakada kai itakuma macen da tagudu daga gidan mijinta tsawon shekara biyu ko ukku ma wanne hukunci ne akanta? malam jibril yayi shiru yana juya tambayar sannan yace wlh bansan irin hukunci daken kanta ba saidai ko idan malamai sunyi jawabi malam sulaiman yace to! Idanhakane kaga baikamata kaitsaye kadanganta cikin dake jikin Raliya dana Ahmad ba domin basakinta yayiba balle tace kwanakin iddarta suncika kuma tare daciki ba.......yayi shiru yanakada kai amman bari nayi shiru nafara jin tabakin Ahmad domin shi ne hakkin komai ke hannunsa konaje wajensa Amman idan kashiga gidan kagayawa Raliya tazauna cikin shiri kafin Ahmad din yakaraso malam sulaiman yamike yacema dan uwansa nasa bari nashiga daga ciki sai anjima yajuya yashige cikin gida batare dayaji abinda dan uwan zaikata cemasa ba malam jibril yabisa da kallo gwiwarsa dajikinsa gaba daya sunyi sanyi saiyamike azabure kamar wanda akatsikarawa allura yanufi cikin gidan kaitsaye babu ko sallama yafada gidan yayi wuri wuri da ido baiga kowa atsakar gidan ba saiyajiyo muryarsu cikin daki saiya juya dasauri yafada cikin daki suna zaune suna zance suna sake sakensu nabanza sukanshi yashigo dakin kamar anjehoshi gabadaya suka dago kai suka kalleshi cikeda mamaki dafargaba lami ce tayi karfin halin fara magana malam lfy babu ko sallama? Yadubi raliya kekuma nazo inason kikara gayamani gaskiya abinda kecikinki nawaye don wlh idan kika maidani karamin mutum sairanki yabaci fiye da yanda kiketsammani kinji nagayamiki ko? Raliya tazunburo vaki gaba ranta abace tace nifa gaskiya nafada wlh cikinsa ne idankuma yamusa nayarda musanya Alkur'ani ayi rantsuwa wanda yayiwa wani karya Allah yatona asirinsa tun a duniya malam jibril yayi shiru yana kada kai alamar ya yarda da abinda tace shikenan sai kizauna cikin shiri dan yanzu Ahmadun zaishigo Raliya tana kallonsu kawai tanata Addu'a cikin zuciyarta akan Allah yasanya Ahmad ya amince har ya amshi cikinnata wayarta tayi ringing dasauri takalli jakarta dakegefenta da sauri saitazura hannunta tadauko tamike tayi kofar fita daga dakin tana danna wayar gaba dayansu suka bita da kallo ganin yanda tafice bata kula da nauyin dake jikintaba Hello Rukky babby ya akayine? Dagacan bangaren Rukky tafashe dadariya tana fadin babby kin makale kinki kiranmu ko? Waime ake cikine akan dankadafen daya makalemiki ne? Raliya tamakale jikin bandaki tana hango gidan taga babu kowa saita ce shegiya saiyau kikanemeni to yaudai za'afara shirin yaki ba'ayi komaiba amman nifa nadan fara shakka kamar bazai amshi cikinnanba......kebanza ce kada kikaraya koki batamana shiri boka yatabbatar mini da lallai saiya amshi cikin nan idan kika fara karaya kuma yaya Za'ayi yayarda ya amsa? Raliya tayi ajiyar zuciya tace bakiji yanda akeyimini tambayoyiba kamar ina gaban mala'ikan kabari masu tambayar tashin hankali ne keduk natsorata wlh Rukky danasani danake kitaho dani? Aida shiri yaruguje domin suna ganinmu tare zasu yarda ribar bariki kikaci harkikasamu ciki kedai kiyi yanda boka yace kidaura layar akancikinki kuma kikuskure bakinki daruwan rubutun dole kowa yayarda fatana dai dazarar kinhaifemasa cikin ki ajiyiyemasa kidawo harka karki yarda sukara kullaki cikin gidannan maikama da akurkin kaji Raliya tace karki damu kawata bari ai itace gadonmu cinmu kuma shanmu bari nakoma sainakira ki dakarin bayani akan anda muka yi dasu takashe wayar tana murmushi amman lokaci guda murmushin dake fuskarta yadauke saboda ganin yayanta musa datayi yafito daga bandaki yanamata wani irin kallo babu ko tantama yaji duk abinda suke tattaunawa dakawarta cikin waya tayi mutuwar tsaye tama rasa meyadace tayi yadaka mata harara yana fadin sakarya kinyi asara raliya amman dasannu zaki gane shayi ma ruwane wlh yakada kai yafice talafe ajikin bango cikinta na hautsinawa tana zare idanu ta shiga ukku amman idan yasan wata aibaisan wataba Acan gidan malam sulaiman ma'u zaune akan tabarma tanacin tuwonta suna fira da ummanta dake gefe ma'u takalli ummanta tace Umma baki kula baba yashigo cikin damuwaba? Kohirar dayasaba yi dani yau baiyiba dakyarma ya iya amsa gaisuwata yashige cikin dakinsa umma tace nagani mana watakila saiyau yasami lbr abinda raliya tazo dashi daman kinsan cikin maganarta yakeyi fitowar malam sulaimance takatse musu hira gabadaya yaran suka kama kallonsa suka fara kokarin gaisheshi yana amsawa hannunsa yana rike da tabarma katuwa Ahmad ne yayi sauri yakarbi tabarmar da kehannunsa cikin girmamawa ya shimfida malam sulaiman yazauna yana kallonsu daya vayan daya kowane daga cikinsu yasha jinin jikinsa domin ganin halinda mahaifinsu keciki bayan angama gaisawa malam sulaiman yaja numfashi yadubi salisu yace kai salisu jeka wajen jibrilu kace yazo shida maidakinsa da raliya salisu yamike dasauri don cika umurnin mahaifinsu can malam jibrilu yashigo lami da Raliya nabin bayansa harda Amina ma'u dasauran yan uwanta sukabi raliya da kallo wacce tazundumo katon hijab kamar gaske Amman Ahmad yakasa kodaga kansa balle yakalleta saboda bakinciki da takaici Abin mamaki saiga raliya na kallon Ahmad dayake akwai hasken wutar nepa tanason tagano yanda yakoma shin yacigaba koyakoma baya? Takasa dauke idonta daga kansa malam sulaiman ya kallesu daya bayan daya sun zazzauna yayi gyaran murya ya kurawa malam jibril ido yafara magana yauwa kamar yanda yafaru dazu jibril yakirani akan maganar Ahmad da Raliya wadda nayi munwuceta abaya amman yau yadawo dawata sabuwar magana wacce yadace kujita daga bakinsa banawaba domin masu salon magana sunce waka ga bakin mai ita tafi dadi yawaigo yakalli malam jibril yace jibrilu kafadamusu irin abinda kagayamin dazu malam jibrilu yayi wuki wuki yana kallon mutane wajen shikansa yanada shakki akan abinda zaifada dil ballesu yanajin kamar ana izashi lallai saiyafada ya kallesu yace eh to akan maganar cikin raliya ne daman wai tace cikin na Ahmad Abdullahi maitama 09034598552 @whatsappne

See translation 12 May 2015 at 08:54 · Public Save · More Like React Comment Share LikeAngry46 Write a comment...

· Bilya Ado Sunusi gud Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Abdullahi Yahya Abdullahi Yahya Amma raliya yar reni hankalice Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Usman Aliyu Wannan labari babban darasine. Allah yakaremu dunia d lahira Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Abubakar Ibrahim Hmmmm Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Sagir Kabir Madallah maitama Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Hauwa M. Aliyu lallai Raliya ta cika mara kunya Like · React · Reply · More · 13 May 2015 Omar Uba Abbaskk tnx Like · React · Reply · More · 13 May 2015 Shahara Na Suleiman Haha Like · React · Reply · More · 13 May 2015 Abubakar Ahmad Pate Lere Hhhhm bariki xuren dandi Like · React · Reply · More · 12 May 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 13 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 22. Gabadaya suka kalleshi da mamaki jin abinda yace Umma kam har tsaye tamike tana fadin kan Uban can! Wannan wace irin maganace mara kan gado haka? Lami tayi caraf ta'amsa daman batazatayi kan gado awurinkiba deeje amman mu awurinmu agurinmu tafi maganar shahararren malami tasiri kikarkade kunnenki dakyau kiji kaimeye haka ne wannan wane irin hauka ne waye yasanya bakinki acikin wannan maganar? Malam sulaiman ne yadoka musu tsawa tahanya fadin wannan maganganu shi kuwa Ahmad baki yasa yana kallon ikon Allah sai yake ganin abin kamar shirin film din nan ma'u kam mutuwar zaune tayi zuciyarta har ta fara raya mata miyagun abubuwa kar dai mijin nata zagayawa yake yi gurin raliya sunawatsewarsu batare da tasaniba? Koda yake ai ance baisaketaba matarsa ce kenan indai hakane kuwa lalle yaci amarnata

wani tukuki yataso yatsayamata awuyanta mai daci daciwo tadinga kallon mijinta wanda shikuma yake kallon Raliya da mamaki da takaici gabadaya guri akayi tsit! Kamar mutuwa ce tagifta amman fuskar kowa tanuna abinda ke zuciyarsa afili malam sulaiman ne yacigaba dacewa kaci gaba da bayaninka malam jibrilu malam jibrulu yakalli Raliya wadda ke sunkuyarda kanta kamar tanutse akasa tana kara matsa layar dake jikinta wadda takeganin itace zatayi magana ayadda da ita babu tantama ke Raliya gayamusu suji daga bakinki mana Raliya tafara ina iana tana zare idanuwa daman..........cikin jikina............Lami ta amshe meyekike wani ina iana kifito kifadi gaskiya kada kiji shakka ko tsoron wani Raliya tadan samu kwari gwiwa tace cikin dake jikina na Ahmad ne shine ubansa " Ahmad yamike agigice yana fadin nikarya kike mini wallahi karya kike!!! Malam sulaiman yakalli Ahmad wanda jikinsa yadauki rawa yace Ahmad samu wuri kazauna karnakoma jin bakinka Umma takalli da tsananin mamaki domin tanaganin malm din kamar yanagoyamusu baya ne Ahmad dasauran yan uwansa suka rinka kallon babansu da tuhuma suna ganin komahaukaci yasan tayanda zaiyi wannan ashari'a balleshi malam sulalman yamaida kallonsa ga Raliya yace kicigaba dabayaninki muna sauraronki Raliya tadanji karfi gwiwa tana zaton tanazaton harta fara gamawa da malam dinne tace tunkafin nabar gidansa da ciki natafi kuma yasani shikuma cikin yakwanta nayi zaton yafadi amman saicikin watannin nan naga yatashi shine nace bari nadawo nagayamasa yasani akasake yin shiru dai anakallonta tana inda Umma tanajin kamar tayi zage zage ko ta huce saikwafa takeyi Lami kuwa saigyada kai takeyi tana fadin hakane kam!! " Auwalu yadaga hannu dasauri yace baba dan Allah inason inyi magana malam yace indai Raliya da Ahmad ne bakada ikon cewa komai wannan maganace datashafesu suka dai yakalli Raliya kikace kin kammala bayaninki ko tace eh nagama amman wlh baba cikinsa ne kuma yasani!!! Malam sulaiman yakalli Ahmad dake zaune baki bude kamar andasashi kai kaji dukkan Abinda tafada shin dagaske kafin raliya tatafi daga gidanka akwai cikinka ajikinta? Gaba daya akamaida ido kansa Ahmad yadukar da kanshi kasa yana kada kai yafara magana Abba kuyi hakuri da abinda zanfada dolece tasanyani fadinshi wallahi tallahi tunda aka daura aurena da Raliya ko magana maidadi bantabayi da itaba balle wata harkar aure tashiga tsakaninmu bantaba kusantar raliya amatsayin mamataba wallahi!!! Umma tayi doguwar ajiyar zuciya cikin ranta tana hamdala ga Allah sauranma duk ajiyar zuciya sukayi Raliya kam fashewa tayi dakuka bakinciki da takaici ta tabbatar shegen bokan nan yacikudinta ne abanza tunda gashi aiki baiyiba amman baridai takara jarrabawa cikin kuka tace Ahmad kaji tsoron Allah wlh wannan cikin nakane karya kikeyi bansan komai game dashiba! Cikin kuka tacigaba damagana wlh kaine cikinka ne donka auri ma'u ne kaki amsa .....musa yashigo da sauri yana fadin karya kikeyi munafuka bacikin Ahmad bane wannan gaba daya idanuwan kowa yakoma kansa ana kallonsa damamaki kamar daukewar ruwan sama kukan Raliya yadauke tafara ware ido lami kuwa fusata tayi tacika tabatse tadubeahi cikin fushi tace ubanka ne yasako bakinka cikin wannan maganar? Idan bakakiyayeniba sainayima baki tsakanin miji damata babu wanda yasan tsakaninsu sai Allah musa yacigaba da magana batsoro balle shakka lami kozaki tsine mini sainafadi gaskiya tabbas wannan cikin bana Ahmad bane domin najiyo hirarta da kawarta dazu ina bandaki alokacin tazo kusa da bandaki batasan inacikiba suke tattaunawa akan maganar cikin nan yakwashe labarin dukkan abinda yaji suna tattaunawa awayar itada kawarta yasanarda su Raliya takara rudewa kunya duk tacikata kamar kasa tatsage tanutse cikinta Umma tadaga hannu sama tana fadin Alhamdulillah yau SAKAYYA tabayyana ga SHEGE yatabbata a inda ake ambatonsa kullum!!! Lami kuwa wuki wuki tayi cike da tsananin kunya tana muzurai RALIYA TAGAMA CUTARTA ! Shi kam malam jibril fashewa yayi dakuka yana fadin kincuceni Raliya kinzubarmin da kima!! Allah ya isa banyafemiki ba!!! Allah ya..............."malam sulaiman yadaka masa tsawa yana nunashida dan yatsa kai rufemin bakinka ahaka ma bakayimata bakiba ta aikata wannan shedanci inakuma ga kayimata bakin? Kabarta kawai duniyace ta isheta riga dawando Ammandai yaya saika hanani la'antar wannan yarinyar wacce keyawon duniya da aurenta? Malam sulaiman yace aimaganar aure ta kare kai Ahmad saketa yanzunnan duk da daman tasaku Ahmad yaji wani farinciki yabaibayeshi wanda baitaba jinsaba atsawon rayuwarsa NI AHMAD NAJANYE DUKKAN IGIYOYIN AURENA AKAN RALIYA HAR ABADA Raliya taja baya atsorace sannan tafashe dakuka maikarfi lami kuwa kamar tasanyama gidan fetur dawuta sukone gabadaya kowa yahuta tatashi tafita fuu suka bita da kallon mamaki malam sulaiman yayi murmushi kawai don lami bazata sauyaba itakam ma'u tunanita akan ace Raliya tacigaba da kasancewa matar Ahmad ne da yaya zatayi da rayuwarta? Ahaka suka isa gidansu batareda wani yayiwa wani maganaba Ahmad yajima akan gado yana game awaryasa amman ma'u batashigo dakinba yamike tsye san da ya ankara da jimawarta bata shugoba yafito falon yajiyo muryarta tana amsawa da kyar muryarta kasa kasa yashigo falon da sauri ma'u kina ina? Can bayan kujera yajiyota tana fadin gani nna yaya cikina da bayana zasucire ya isa gurin datake dasauri yana salati yatarar da ita kankame jikin kujera tahada uban gumi sai kada kai takeyi kamar tahadiye kunama cikin fargaba yace yaya dai ma'u lafiya meya faru cikin karfin hali tace tun agidansu umma naji cikina naciwo Ahmad yamatsa gabanta sosai yafara kokarin tayarda ita zaune komota zan nemo muje asibiti? Yaya bazan iya tashiba wani abu yarikemin kafa wash! Innalillahi wayyo yaya.........!!! Ahmad duk yagigice yasaketa ya ma rude yarasa mai zaiyi yanufi kofar fita yana fadin bari na kirawo babar A'ilo karkafita kazo na mutu a gabanka yaya......ka zodon Allah!!! Yadawo dasauri da tsananin tashin hankali ya runguneta gaba daya yafita daga cikin hayyacinsa labarin yanda mahaifiyarsa tahaifeshi kawai keyawo aransa yanzu idan ma'u ta mutu yaya zaiyi da rayuwarsa? MUHADU ALITTAFI NA HUDU

Abdullahi Yusuf maitama

See translation 14 May 2015 at 07:48 · Public Save · More Like React Comment Share Like60 Write a comment...

· Ummu Suhairat Mungode Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Jameeylarh Dalhart tenxs Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Halima Abdullahi JAXAKALLAH Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Jermeelerh Muhammad Umar Tnk Q! Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Sardaunan Telolin BG tñc Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Ummu-rumaisa Abubakar MUNGODE Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Nerjer'ert Bint Erbdoullerh Tnx alot Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Isah Shaaibu Anayi munajin dadi Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Fatima M Bello Mun gode Like · React · Reply · More · 14 May 2015 Babangida Lawan Miko Ok Like · React · Reply · More · 14 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 23. BOOK 4*1 Ma'u kam tana durkushe kankame da kujera saigyada kai take tana nishi, shikuma Ahmad yama rasa mai yakamata yayimata cikin ikon ubangiji tazabga wani irin nishi cikeda kabbara saiga yarinya tafado facal! Ihun yarinyar ne ya ankarar da Ahmad yazura hannu yajanye yarinyar gefe ahankali donyaga kamar zata zauneta saiga mahaifa tafito itama gaba daya ma'u takwantarda kanta ajikin kujera tana maida numfashi Ahmad yarasa maizaiyi saboda ihun yarinyar keyi gamahaifa ajikinta yakalli ma'u yace ma'u mezanyimata ne? Tadan kalli yariyar nima bansaniba yaya kakirawo babar A'ilo dasauri yafice yanufi gidansu babar A'ilo yatarar kofar gidan akulle danhaka yafara bugawa baijima dafara bugawaba suka bude mahaifin A'ilo ne yafito yanatambayar wanene? Yanabudewa yayi arba da Ahmad hankalinsa atashe nan take Ahmad masa bayani yajuya gida yasanarda babar A'ilo suka fito dahanzari suka garzayo gidan Allah yasa baijima dayin siyayyar haihuwaba harda reza acikin kayan kafin karfe dayan dare babbar A'ilo ta kammala komai tagyara maijego da jaririya da kuma dakin Ahmad kam shiya wanke dukkan kayan dasuka baci cikin ransa yanajin son ma'u da tausayinta nakuma shigarsa cikin daren su Umma sukaji lbr donhaka danhaka ana idarda sallar asubah Umma ta iso gidan tun gari baiyi sha ba tatarar da diyarta fes! Ranta yayi tas! Shikuwa Ahmad kwana yayi idonsa akan diyarsa komai dake jikinsa shine ajikin wannan yarinyar ya rungumeta kamar zaimaidata ciki yayita yimata addu'a duk wadda tazo bakinsa Duk wani duba anyiwa ma'u batasami matsalar komaiba sukansu likitici Sunyi mamaki domin ganin ma'u tanada karanci shekaru amman dai sunsan kowace mace da irinjikinta musamman itada tahaihu durkushe daga karshe dai sunbata magunguna itada diyarta suka wuce gida matan yayyenta dasu yayyen nata dukkansu suna jiran dawowarsu Ahmad saibasu labarin kammanin diyar yake yi anata dariya kowa yakagu sudawo din sanda suka iso gidan yacika da murna da hayaniya akadinga shigowa barka hayaniyar ce tasanya lami da diyanta suka gano wani abu yana faruwa agidan Amina tadawo ranta abace takasayin koda magana lami tadubeta tace malam kigaya mana abinda yafaru mana kishigo sum sum saikace tinkuya tome zangayamikine wai waccan banzarce tahaihu.....lami tatashi agigice cikin firgici tace badai ma'u ba? Itamana sunckawa mutane gida da ihu banza kawai!!! Lami takoma tazauna tana huci kamar zatafaahe da kuka Raliya kam takasa cewa komai sai kallonsu kawai take itakadai tasan metaki cikin ranta lami tsinuwa da baki babu wanda batayiwa diyar da aka haifaba ma'u kam taga karamci daga gurin yan uwanta da mijinta don duk yankudin hannunsa da wanda yake tarawa akan diyar nan yakarar dasu itama hajiya amina tadauki soyayya tadora akan diyar nan kullum saitazo ganinta saitake tunamata da Ahmad lokacin dayana jariri Rashin shigowar lami dadiyanta barka yadaurewa Umma kai kwarai dagaske amman tadanne abin acikin ranta gurin yiwa diya huduba saida akasamu sa insa domin shi Ahmad sunan Umma yakeso asamata itakuma Umma tadage sunan mahaifiyarsa za asanya domin ita akwai sunayenta dayawa Auwalu yasaka sani yasaka itakuwa ma'u babu maisunanta dakyar ya amince da hakan akasanyawa diyar sunan Asma'u saiyakejin kamar mahaifiyarsa tadawomasa son diyar yarika shigarsa Ranar suna anyi suna maikayatrwa namasu rufin asiri anci ansha dai misali wannan abu yakoma konawa lami rai Raliya kam har kuka tayi takunshe cikin daki takasa kolekowa waje datuni itace zatahaifi wannan diyar ta halak tayiwa kanta tabbas tashiga cikin tsananin tada sani wacce hausawa sukecewa keyace Adaren ranar suna ciwo yakumeta cikin daki tuntana abin itadaya hartafara kiran mahaifiyarta lami tashigo dakin sukaci gaba amman shiru babu haihuwa sai azaba tun lami naganin abin wasa ne hartafara tsorata shikam malam jibril tunda yafuskanci abinda kefaruwa yashige dakinsa yarufo kofa da lami taga bahaza taje tabuga masa tanakuka yavude kofar ransa abace yaya akayi lfy dai ko? Cikin kuka tace Raliya zata mutu jibril kataimaka mini yagalla mata harara Rayuwar raliya da mutuwarta duk dayane agurina lami don gwara ma tamutu kona huta da abin gori yajuya yashige dakinsa avinsa yaja kofa lami tafashe dakuka gami dajuyawa dakin da gudu savoda jiyo kuwar diyar tata datakeyi sukacigaba da fama amman har tsakiyar dare shiru shikansa jibril saida yakaraya yaleka dakin halin dayaga diyar tasa yadaga masa hankali kwarai dagaske yagigice yanafadin yayazasuyi? Lami tana kuka tace asibiti za'akaita kawai yadan waro ido agigice asibiti gashi banida ko kwandala kuma shi asibiti saida kudi kinsani

Abdullahi Yusuf maitama

See translation 19 May 2015 at 08:37 · Public Save · More Like React Comment Share Like63 Write a comment...

· Jamila Umar Tanko Books 10x@maitama ya skul? 2 · Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books lapia klau surry kepa? Mukhtar Umar Daura muna gdy Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Nafeesah M Adamz Littafin ga dadi amma guna ja muna rai dayawa akai Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Mukhtar Umar Daura muna gdy Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Abdull Muh'd Mumbers ku taimaka ahada musu kudin asibity!! Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Salees Naja'at Allah sarki dan uwa, sannu da kokari. Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Abashiyyah Umar tnkx alotx Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Ummu Suhairat Godia marar adadi Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Abdulrahaman Jumeh Muna godiya Like · React · Reply · More · 19 May 2015 Saa Zakka Ta mutu kawai yar bnxa Like · React · Reply · More · 19 May 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO part 24. Book 4*2 Kaje wurin yayanka mana agidime yanufin gidan yajima yana buga kofa can jimawa malam sulaiman ya iso yana tambayar waye? Jibril yace nine malam sulaiman yabude masa kofa cikeda mamaki dalilin zuwansa cikin dare agidime jibril yayi masa bayanin abinda kefaruwa malam sulaiman yace to aisamun mota cikin wannan daren shine aiki amma bari yashiga yayiwa Umma magana ko akwai dazata iya yi akai? Sanda malam sulaiman yasanarda Umma abinda kefaruwa tayi tsalle tadire tace babu inda zani nima diyata tahaihu yauhar kwana bakwai amman daga lami har yayanta babu wanda yaleko danhka itama babu inda zata tunyana mata fadan har saida yafara yimata magiya dakawo mata hadisai wadanda suka sanyayarmata da guiwa tanufi gidansu lami tana zuwa taga halin da Raliya take ciki tasan lallai tajigata takwanta shabe shabe ga kanda yana yunkurowa yana komawa yakasa nishi lami saikuka takeyi itada Amina Umma takalli lami tace kunada koko? Dasauri lami tace akwai tafice tadauko Umma ta amsa tayi addu'a tatofamata aciki sannan tace adagamata Raliya zaune suka kama Raliya dakyar suka durkusarda ita Umma tace tadafa kujera tatokare kafafuwanta akasa takafamata wannan kunun cikin katon kwanon sha tadinga sha harsaida tashanye shi tas! Cikin ikon Allah saiga karfi yazowa Raliya tafara wani irin nishi da karfi Umma tariketa saiga diya tafado cikin ikon Allah kuma harda mahaifa baki daya lami tafashe murna Umma tadallamata harara keda zaki godewa Allah saikuma saikuma kikama guda? Saiki kawo reza lami tazura da gudu tafara nemo reza da zare Umma ta amsa tayanke ta kulle cibiyar bayan ta yanke Raliya tayi zaune takasa ko motsawa saboda abu biyu keyawo aranta murna darabuwa da abinda kecikinta dakuma abinkunyar dazaifara bibiyarta harkarshen Rayuwarta malam jibril natsaye jikin kofar dakin dadamuwa akan fuskarsa yanajiyo sautin kukan jaririya yazame yazauna yanasallami da damuwa Shikenan shege yatabbata agidansa diyarsa ce tahaifamasa shege yashiga Ukku!!! Umma dai tanagama abinda zatayi takalli lami datayi wuki wuki tace to lami ga Raliya tasauka tasami irin abinda kikajima kinagorantawa Ahmad akai sainace Allah yaraya Ameen lami tabude baki dabakinciki amman batada abincewa dazaiyi daidai da irin maganar Umma tafada mata hartafice daga dakin lami takalli raliya dake zaune kamar tashaketa don bakin ciki takalli diyar wacce kekuka wutsil wutsil da kafafuwa saitayi tsaki tajuya tafice daga dakin dasauri Raliya tabi yarinyar dakallo tamika hannu tadauketa ta kuramata ido fatanta baiwuce tagano dawa diyar kekamaba wanda zatace shine ubanta domin maneman nata nada yawa amman iyakacin kallonda tayiwa yarinyar takasa gano dawa yariyar tayi kama hawaye yakama fitowa daga idanunta soyayyar yarinyar tanashigarta ahankali meyasanya batazauna gidan Ahmad tahaifi wannan yarinyarba kobayan hakanne tabar gidansa Datahuta dagori daduk abinda zaibiyo bayan rayuwar wannan yarinyar data haifa yanzu dakyar lami ta iyadaura ruwan dumi domin takaiwa Raliya tayi wanka basu sami kwanciyaba saiwurin karfe 4 nadare sannan suka kwanta kiran sallar farko Raliya tamike tsam tadauko jakar kayanta tafara zubawa dukkan abinda tasan natane daman sugama yin waya da Ruky tuncikin dare sungama shirya abinda zasuyi bayan takammala shityawa ta juya ta kalli jaririyar dake bacci hawaye yazubomata taji kamar kada tagudu tabar diyarta amman bazata iyacigaba daharka yanda takesoba matukar tanatare da wannan jaririya tagoge idonta dasauri tadauki jakarta tafice har gari yawaye rana tafito lami bata leka dakin da Raliya takeba can yarinya tafara kuka daga cikin daki daga lami har amina babu wanda yakula dakukan datakeyi domin suna tunanin mahaifiyarta nakusa da ita shikam daman malam jibril tunda yafita baidawo gidaba musa kuma tunda akayi rikicin nan baidawo gidaba saiyatare can wani dakin abokinsa dan baisan abinda zaifaru dashiba idan sukaci karo da lami kukan ya ishesu lami tamike afusace tanufi dakin tana fadin Raliya wai uban me kike yine kikabar yarinyar nan tana kuka haka? Tadaga labulen dakin afusace saidai ga mamakinta saitaga dakin wayam babu kowa saijaririya dake tsala kuka tashiga dakin dasauri tafara bincike Raliya! Raliya!! Raliya!!! Amman taji shiru babu ita babu alamunta tafito dasauri takalli Amina cikin ihu kedubaman bandaki ko Raliya tashiga Amina tamike dasauri domin taga mahaifiyar tata arude take tace lami batanan lami tadafe kirji agidime tana fadin nashiga ukku kardai ace yarinyarnan tagudu tabarman diyar nan? Ihun jaririyar yacikamata kunne takoma dakin dasauri tadaukota tarungume tana jijjiga dafadin kemaza dubamana gidan nan sosai harcan gidanu deeje kigani intana can Amina tajuya tanufi hanyar fita lami tacigaba da jijjiga jaririyar hankalinta atashe kamar tazabga ihu taji sanyi aranta Abukamar wasa karamar magana tazama babba! Domin duk inda aketunanin za'asamu Raliya anduba babu ita babu alamunta dole lami tanaji

See translation 1 June 2015 at 10:27 · Public Save · More Like React Comment Share Like41 Write a comment...

· Ammatullah Suleiman Dan allah ku tayasu nemanta mana kilan adace Like · React · Reply · More · 14 Dec 2019 Babangida Sulaiman Muhammad Assalamun alaikum ina ci gaban ban gane ba Like · React · Reply · More · 2 May 2019 Dauda Gimba Tnx Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Usman Aliyu Taller mungode Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Musa Muhd Hmm Like · React · Reply · More · 16 Jul 2015 Mubina Bind Muhammad Mungode Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Ahmad Sabo Ai ni da naji shiru, na yi tunanin ko saceka akayi! Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Aslamiyya Usman Mun gode 1 · Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Munirat Rayyan Gud Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 Ummu Abulkhair Gud Like · React · Reply · More · 1 Jun 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**2

tun ina boye halin da nake ciki har iyayena suka fuskanta don na rame na fita daga hayyacina bani da kwanciyar hankali sam ga danbanzan duka danake sha ahannun salim, iyayensa kuma kamar kurame domin sun toshe kunnuwansu daga duk wani kuka na game da dansu, sai asannan nagano salim dan iyayene marasa tarbiyya. shekararmu biyar ina cikin wuya da tashin hankali danmu daya, kwatsam! wata rana salim ya dawo gida abuge daga yin magana ya rufeni da duka har da karaya ahannu wannan shine ya kawo karshen aurenmu domin na gaji da azaba iyayena ke tausaya....... Tayi shiru tana maida numfashi idonta ya cika da kwalla ta cigaba, shekaru uku da mutuwar aurena nakasa samun wanda ya dace dani da burikana, Ahmad ka tuno ummi da soyayyarta cikin ranka? Gaban Ahmad ya fadi ummi ta dawo dashi ruwa tsumdum! amma ya dake yace ummi ko kin manta kina magana da Ahmad SHEGE ne dan gidan asma,u mahaukaciya ne? Nine dai yadda kika sanni ba,a sauyani ba bakuma a siyomin uba a kasuwa ba, me zakiyi da shege ummi? Hankalinta ya tashi ta mike daga inda take kishingide ta kankame wayar tana fadin wallahi bazan ga laifinka ba akan dukkan abinda zaka fada ba, amma ka sani ko mahaifana sunyi da sun sanin rabamu, don sun gano wani mara iyayen ma yafi mai uwa da uba daraja da hali na gari. kayi hakuri Ahmad ka manta da dukkan abinda ya wuce ko bakayi magana ba Allah ya saka maka cikin ruwan sanyi Yayi shiru baice mata komai ba yana maida numfashi har sanda muryarta ta kara sauya masa tunani da fadin ka yafemin Ahmad! Yanda ta furta maganar ya sanyaya dukkan gabbansa baisan sanda yace nayafe miki ummi Wani irin dadi ya cikata tace nagode Ahmad ina fatan zamu dora daga inda muka baro asoyayyarmu? Yayi wani tari da bai shiryaba yace "Nan fa daya! Ai ma,u ce kadai matata ta duniya insha Allahu Farin cikinka ya gushe lokaci guda, cikin damuwa tace kayiwa ma,u alkawari ko rantsuwar bazaka mata kishiya ba kenan Ahmad? Ya kada kai, ko daya ban taba yi mata wannan alkawarin ba amma na sanyawa raina hakan, iyayen da suka rikeni suka maidani mutum kamar kowa suka raineni sanda bansan kaina ba suka bani aure sanda na rasashi yaushe zan iya hada son diyarsu da na wasu matan? Bazan iya ba! koda ace ma,u tana azabtar dani bazan iya hadata da kowacce mace ba, balle ina cikin mazan da ke cikin sa,ar aure da iyali a duniya, don haka bana bukatar kari sai dai nayi miki addu,a ummi Allah ya baki wani mijin daya fi mijinki na farko alkhairi dani kaina......... Sai ta fashe masa da kuka tana fadin don Allah kada kayimin haka Ahmad kada kace zaka rama dukkan abinda na aikata maka, ni mace ce bazan iya dauka ba. Jin kalamanta zai iya karya masa zuciya, bayan kuma yasan ko kukan jini zatayi bazai taba iya yi mata abinda take bukata ba don da ma,unsa tayi kuka gara kowacce mace a duniya tayi kukan jini in ancire mamansa, dan haka da sauri yace kiyi hkr ummi sai anjima! ya kashe wayar. Ya koma jikin kujera ya kwanta tausayin ummi da sautin kukanta suna turereniyar shiga zuciyarsa har baisan sanda aka turo kofa aka shigo ba, sai da aka daki tebur dinsa sannan ya daga kai da sauri kamar wanda ya farka daga barci. Nana ce tsaye ta rike kugu tana kallonsa. Ya wayance Sorry hajiya na tafi wani dan tunani ne. Ka tafi babban tunani dai, wannan tunanin naka baiyi kama dana komai ba bayan na soyayya, ko ka tuna da tsohuwar budurwarka ne? Yayi yake me ya sanya tayi saurin ganoshi? Amma sai ya dake yace waya gaya miki haka? Mubar wannan chapter mu koma ta aikin daya shigo dake. Taja kujera ta zauna ta dora kafa daya kan daya tace. Yau ba aiki na shigo yi ba hira ce ta kawoni, sai kuma nayi katari da samun babban labari akan fuskarka. Don Allah ka gayamini ka taba soyayya Ahmad? Tambayar tazo masa a bazata cikin mamaki yace maiyasa kikayi min wannan tambayar? Ta gyara zama domin nagano da gaske akwai kalmar soyayya a doron kasa, idan na rantse maka bazan kaffara ba ban taba soyayya ba, bantaba jinta cikin jikina ba a baya dukkan rayuwata na karar da ita ne haka bantaba surkata da soyayya ba, bantaba son wani ba, hakan ne ma yasa iyayena da dangina suke zaton ina da mutanen boye (aljanu) musamman da wasu malaman da suka sha fada musu wai bakin aljani ne ya aureni, sunce sai anyi da gaske zai barni nayi aure, su fa sun yarda da hakan shi ya sanya suke lallabani da banka min magunguna a tsawon shekaru ashirin da wani abun da haihuwata babu wanda ya taba matsa mini nayi aure, don ance musu da sun fada ko sun matsamin zasu iya rasani daga lokacin don aljanin wai zai gudu dani. Tayi shiru tana kallon Ahmad dake kallonta da mamakin jin abinda take fada, tayi ajiyar zuciya ta cigaba da magana. Ahmad babu abinda iyayena ke bukata yanzu a rayuwarsu bayan ganin aurena, amman suna tsoron fadamin haka, nasan dukkan abinda aka gaya musu na kuma san karya ne, amma na bisu ahaka don ni a karan kaina bana bukatar auren, ban ma taba jin naga wani mutum ina sonshi ba sai cikin shekarar nan

14 August 2015 at 08:56 · Public Save · More Like React Comment Share Like28 Write a comment...

· Amirah Muh'd Tnx Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Aisha Dalhatu Sannu da kokari Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Autan Fazebuk So masu gari Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Ibrahim Ubali GD Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Zaharaddeen Abdullahi muna godiya sosai Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Ummu Suhairat Sae kuma muka ji shiru wae malam yaci shirwa. Like · React · Reply · More · 14 Aug 2015 Abdul Umar Katuka Meye haka wnnan labari ba kai? Like · React · Reply · More · 24 Feb 2016 Ibrahim Al-hassan Naja buk din yahadu Like · React · Reply · More · 23 Feb 2016 Usman Aliyu Taller Nice Like · React · Reply · More · 15 Aug 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO.... 4**6

ya kwanta tausayin ummi da sautin kukanta suna turereniyar shiga zuciyarsa har baisan sanda aka turo kofa aka shigo ba, sai da aka daki tebur dinsa sannan ya daga kai da sauri kamar wanda ya farka daga barci. Nana ce tsaye ta rike kugu tana kallonsa. Ya wayance Sorry hajiya na tafi wani dan tunani ne. Ka tafi babban tunani dai, wannan tunanin naka baiyi kama dana komai ba bayan na soyayya, ko ka tuna da tsohuwar budurwarka ne? Yayi yake me ya sanya tayi saurin ganoshi? Amma sai ya dake yace waya gaya miki haka? Mubar wannan chapter mu koma ta aikin daya shigo dake. Taja kujera ta zauna ta dora kafa daya kan daya tace. Yau ba aiki na shigo yi ba hira ce ta kawoni, sai kuma nayi katari da samun babban labari akan fuskarka. Don Allah ka gayamini ka taba soyayya Ahmad? Tambayar tazo masa a bazata cikin mamaki yace maiyasa kikayi min wannan tambayar? Ta gyara zama domin nagano da gaske akwai kalmar soyayya a doron kasa, idan na rantse maka bazan kaffara ba ban taba soyayya ba, bantaba jinta cikin jikina ba a baya dukkan rayuwata na karar da ita ne haka bantaba surkata da soyayya ba, bantaba son wani ba, hakan ne ma yasa iyayena da dangina suke zaton ina da mutanen boye (aljanu) musamman da wasu malaman da suka sha fada musu wai bakin aljani ne ya aureni, sunce sai anyi da gaske zai barni nayi aure, su fa sun yarda da hakan shi ya sanya suke lallabani da banka min magunguna a tsawon shekaru ashirin da wani abun da haihuwata babu wanda ya taba matsa mini nayi aure, don ance musu da sun fada ko sun matsamin zasu iya rasani daga lokacin don aljanin wai zai gudu dani. Tayi shiru tana kallon Ahmad dake kallonta da mamakin jin abinda take fada, tayi ajiyar zuciya ta cigaba da magana. Ahmad babu abinda iyayena ke bukata yanzu a rayuwarsu bayan ganin aurena, amman suna tsoron fadamin haka, nasan dukkan abinda aka gaya musu na kuma san karya ne, amma na bisu ahaka don ni a karan kaina bana bukatar auren, ban ma taba jin naga wani mutum ina sonshi ba sai cikin shekarar nan shine ya dawomini da rayuwata irin ta sauran mutane wadanda ke dandanar kalma da aman soyayya. Gaban Ahmad ya kama bugawa ganin irin kallon da take masa amman sai ta basar ta kauda idonta daya ciko da kwalla tace ka manta da wannan bani labarin tsohuwar budurwarka ko ita ce matarka ne? Yayi murmushi yana kallonta ta kauda kanta gefe. Yace ke da baki san amo da dandanon soyayya ba yaya kika gane ina cikin soyayya, ko kuma na tuno da tsohuwar budurwata ta da? Tayi murmushi kuma fa hakane kanada gaskiya. Amma ina zaton na gano hakan ne cikin littattafan soyayya na turawa da nake karantawa ko kuma ayawon kallon fina finansu. Koma dai meye sai ka bani labarin nan yau. Yayi dariya lallai da gaske kin shiga cikin soyayya amman babu abinda zan gaya miki bayan nace miki ummi ce tsohuwar budurwata ta bugomin waya bayan ni kuma na ma,u ne ita daya. Gabanta ya fadi yanayinta ya sauya zuwa damuwa da kyar ta iya daurewa tace wacece ma,un? Ya jingina da kujera yana murmushi tamkar ta masa albishir da gidan aljanna. Yace ma,u ita ce matata, mai sona mai darajani fiye da yanda yakamata ta mini, ban hadata da kowa cikin raina da al,amuran rayuwata ba. Cikin gaggawa da rashin sanin abinda ta fada tace Har ni ma? Shirun da yayi yana kallonta ne yasa ta gano ta fadi wani abun daya jima aranta tana nuku nuku dashi. Sai ta dauke kanta daga kallonsa da sauri ta kalli gefe gabanta na faduwa dakin yayi shiru sai karar A.C da ta bugawar zuciyoyinsu. Ahmad kam addu,a yake cikin ransa Allah ya sanya abinda ta fada bashi take nufin fada ba, amma sai ya jiyo sautin muryarta ya cigaba da fadin. Maza da dama sun soni masu kudi da masu mulki da sarauta, amman bantaba kallon kowa da mutunci ba tunda bansan meye so ba, sai kwatsam watarana naci karo da wani tsageran matashi a gidan mai wanda ya tsaya cikin raina har ya karya tarihin zuciyata, tun ina yaudarar kaina da zuciyata karya takeyi bazan taba son mutum irin haka ba har daga karshe na yarda na sallama ina sonka Ahmad. Ta waigo ta kalleshi yayi mutuwar zaune. Ta cigaba da magana idonta na zubda hawaye Nasan ka jima da gano ina sonka domin na gwada maka abubuwa da dama irin na masoya amman kana basarwa nasan badon komai bane sai don ma,unka! Sai dai ina fatan zanci albarkacin ma,un ka sammin kadan daga cikin son da kakeyi mata Like· Report·Jun 14 Nusaybarh Mustapha Ibraheem 123. Tana kaiwa nan ta mike tsam da sauri ta nufi kofar fita Ahmad yana zaune kamar an dasashi ya kasa motsawa daga inda yake yana jin kamar bashi bane ba. Ya bi nana da kallo wacce ta kama kofa zata bude har saida ta bude sannan ta kuma yin magana ba tare data waigo ba. Ahmad ka sanya aranka ba karamin abu ne zai sanya mace kamata mai cika da daraja da kyau da arziki ta fuskanci namiji kamarka ta sanar dashi tana sonshi ba. Tana fadin hakan ta fice. Ahmad ya doki tebur ya dafe kansa dake juya masa yana fadin Ya subahanallah! Lallai lokacin barina cikin wannan

So naga kuna korafi dayawa, bari na wakilci@maitama nakarasa muku.

Surayya

10 October 2015 at 11:27 · Public Save · More Like React Comment Share Like26 Write a comment...

· Jamila Umar Tanko Books thañk you sury 1 · Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Sarauta Ta Tnx Like · React · Reply · More · Yesterday at 23:21 Amina Abdullahi Good Like · React · Reply · More · 30 Nov 2018 Mubeenat Muhammad Muna godiya Like · React · Reply · More · 30 Nov 2018 Kamaluddeen Sulaiman Agaida suryy 1 · Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Tahir M. Kaumi No, pls continue this. Like · React · Reply · More · 10 Oct 2015 Abubakar Ibrahim tnx alot Like · React · Reply · More · 10 Oct 2015 Salisu M. Mu'azu Dankado Him Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Ibrahim M-Gani Yariman Fcbk Tanx surry Like · React · Reply · More · 10 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Mungode Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO....4**8

Haka ranar ya koma gida sukuku ba walwala har sai da ma,u ta fahimci yana cikin wani hali, bata matsa masa da tambaya ba don ya sanar da ita tuntuni akwai matsala a ofis dinsu, don haka addu,a kawai takeyiwa mijin nata. Duk yadda taso faranta masa ta sanyashi cikin farin ciki ta kasayi dole ta barshi shi daya cikin daki don ta kula abinda yafi bukata kenan. Nana kam da kyar takai kanta gida domin kanta wani irin ciwo yake yi da juyawa. Tana yin parking ta nufi gidan da gaggawa, amma bata kai ga ainihin sashinta ba ta yanke jiki ta fadi kasa. A dai dai lokacin hajiya batula mahaifiyarta ta fito daga sashinta ta hangota. Hajiya batula ta fasa kara ta nufeta da gudu tana salati, ta kamata ta dagota sai taga idonta ya juye alamar ta suma. Ta fasa ihu tana kwallawa masu aikin gidan kira. Da gudu suka iso kowa a rude jin kiran da hajiya batulun ke musu, ganin halin da nana ke ciki ya kara daga musu hankali suma. Hajiya batulu cikin kuka take cewa kubani ruwa na yayyafa mata, daga daga cikin matan ta kwasa da gudu sakwanni kadan ta dawo dauke da ruwan robar swan mai sanyi.. Hajiya batulu ta karba saboda tsabar gigicewa ma kurzawa nana shi tayi ajikinta gaba daya. Nana tayi wata doguwar ajiyar zuciya ta bude idonta a hankali. Hajiya batula tayi doguwar hamdala sannan ta kalli yan aikin tana cewa ku taimaka mini ku kamata mu kwantar da ita akan kujera. Suka ciccibi nana aka kwantar da ita ta dauko wayoyinta ta fara neman layin wayar mijinta wanda yake abuja. Bugu daya ya dauka, cikin tashin hankali hajiya batulu tace masa Alhaji nana bata da lafiya, yanzu ta fadi har da suma. Alhaji nura kwangila ya gigice yace, suma kuma me ya sameta? Ta kalli nana dake kwance akan kujera tana kallonta tace bansani ba, dama cikin kwanakin nan na kula bata jin dadi, amma danayi mata magana sai tace babu komai..........Kinga bar bayanin nan haka zanyiwa likita waya yanzu yazo ni kuma zan hayo jirgi na taho yanzu, ki kula da ita kafin nazo. Ya kashe wayar da damuwa a take a lokacin yayi waya a tanadar masa ticket mai zuwa kano. Like· Report·Jun 14 Nusaybarh Mustapha Ibraheem 127. Hajiya batula ta isa ga nana ta zauna ta dora kanta bisa cinyarta tana shafa kanta. Sannu nana, meke damunki? Nana ta rintse ido hawaye ya zubo mata , batason tunawa amma bazata taba mantawa ba domin soyayyar Ahmad ta zame mata masifa, bazata iya rayuwa ba Ahmad ba. Ganin tana hawaye ya kara tayar da hankalin mahaifiyarta ta tace shikenan ya isa daina kukan. Mintuna goma baya sai ga likita ya iso gidan masu hidima sukayi masa jagora har cikin gidan da yake kowa ya sanshi a gidan. Hajiya batula na ganinsa ta mike da sauri tana fadin yauwa karaso doctor ka dubamin ita. Likitan ya isa da sauri ya sauke jakarsa da yake rataye da ita ya fara fiddo kayan awo kala kala. Cikin yan mintuna kadan ya kammala auna nana yayi mata wasu yan tambayoyi ta bashi amsa, daga karshe yace da hajiya batula dole sai sunje can asibitinshi anyi mata wasu gwaje gwajen. Hankalin hajiya batula ya kara tashi sosai ta dubi likita tace likita gaya min meke damun diyata? Cikin kwantar da murya likitan yace kwantar da hankalinki hajiya ba wani abu bane ba, ina dai so nasami sakamakon da nake bukata ne. Babu musu ta fara shiryawa aka dunguma zuwa asibiti.

11 October 2015 at 16:52 · Public Save · More Like React Comment Share Like26 Write a comment...

· Salisu M. Mu'azu Dankado Gud Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Weldon Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Asabe Ali 10x Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Abubakar Ibrahim pls continue Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Nice Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Dauda Yahaya Masanawa Madalla Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Adamu Safeeyarh tnx Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Tahir M. Kaumi Next pls Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Muhd Dawud Rano Muna tare Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**9

daga karshe yace da hajiya batula dole sai sunje can asibitinshi anyi mata wasu gwaje gwajen. Hankalin hajiya batula ya kara tashi sosai ta dubi likita tace likita gaya min meke damun diyata? Cikin kwantar da murya likitan yace kwantar da hankalinki hajiya ba wani abu bane ba, ina dai so nasami sakamakon da nake bukata ne. Babu musu ta fara shiryawa aka dunguma zuwa asibiti, Acikin mota tayiwa Alhaji nura kwangila bayanin sun wuce asibiti, alokacin shi kuma yana cikin airport hankalinsa ya kara tashi kwarai da gaske amma ya dake. Dukkan gwaje gwajen daya kamata anyiwa nana, sai dai sakamakon ya dan girgiza likitan don haka yaja bakinsa yayi shiru don bai kamata ya sanar da mace wannan labarin ba. Ana kiran sallahr isha,i alh nura kwangila ya iso garin, kai tsaye asibitin dr musa ya wuce har dakin da nana take ciki lokacin anyi mata wata allurar barci idonta yana rufe, hajiya kuma tanayin sallah. Alh nura ya isa gadon da nana ke kwance ya tsaya yana kallonta sai kuma ya fara lalubar wayar Dr. musa daya tabbatar masa yana cikin asibitin sai ya fita ya nufi ofis dinsa. Yana shiga Dr. musa ya mike cikin girmamawa yana gaisheshi amma bai kula da wannan ba cewa kawai yakeyi Dr meke damun diyata me ya faru da ita? Dr. musa ya jinjina kai yace kwantar da hankalinka alh zauna na maka bayani. Alh nura kwangila kamar bazai zauna ba amman dai ya hakura ya zauna yana kallon likitan. Dr. musa ya zauna ya dakko masa envelop a rufe kamar guda uku ya fara dubawa yana kallon alhaji nura wanda ya kagu yaji abinda zaice. Dr. musa ya fara bayani. Da farko na fara yiwa nana gwajin jini ne na tadda jininta ya hau........... Nanar me zai sanya jininta hawa kuma? Alh nura kwangila ya tambaya a gigice. Dr. musa yace wannan shine abinda ke bani mamaki. Sannan yanayin bugun zuciyarta ya sauya yana dudu fiye da yanda ka,idarsa take wannan dalilin ya sanya nace mu taho asibiti don ayi mata sauran gwaje gwajen, ga mamaki na sai naga zuciyarta ta dan sami matsala don ta buga fiye da yanda ya kamata ta buga musamman lokacin da ta fadi, Allah ya taimaka anyi gaggawar kawota asibiti da wani mummunan abu ya faru da ita. Hankalin alh nura kwangila ya kuma tashi yace. Abin mamaki meye zai sanya zuciyar diyata bugawa har akusa rasa rayuwarta? Kwantar da hankalinka alh, wannan ba wata matsala bace insha Allahu komai zai zama dai dai zata dawo dai dai musamman idan anyi gaggawar gano abinda ke damunta an kuma magance mata shi da wuri. Alh nura kwangila ya gyada kai yana fadin, na gode Dr. bari naje wajen mahaifiyarta. Ya tsare hajiya batula da tambayoyi, abinda ta fada masa yana can kafin yazo shi ta kara fada masa yanzu ma, dole dai su bari diyar tasu ta sami lafiya. Washe gari tunda safe Ahmad ya sami labarin abinda ya faru, hankalinsa yayi matukar tashi, don haka da wuri ya wuce asibitin ya tadda mutane anyi dandazo kama daga kan yan fadanci zuwa dangin hajiya batula dana alhajin, amma ba,a barin kowa ya shiga sai dai ko su gaisa da mahaifan nata ka juya ka tafi. Shima Ahmad din sun gaisa sai dai bai samu ganin hajiya batula ba tana ciki da yake dakin irin na masu kudine har da wani katon falo. Nana tana barci kamar cikin mafarki ta dinga jin muryar Ahmad. Nana tana bacci kamar cikin mafarki ta dinga jin muryar Ahmad lokacin da yake sallama da alh nura kwangila. Da sauri ta bude idonta ta kalli mahaifiyar ta da ke zaune a kusa da ita tayi tagumi cikin sanyin murya tace mummy ba Ahmad ne yazo ba? Hajiya batula tace bansani ba ko kinason ganinsa ne? ta gyada kai alamar eh da sauri hajiya batula ta mike ta nufi falon. Alh nura ya kalleta da sauri ganin ta fito arude yace yaya dai lafiya hajiya? Cikin karewa mutanen wajen kallo tace nana ce tace taji kamar muryar Ahmad wai. Ba wai bane shine yanzun nan ya fita bari na kirashi idon tana son ganinsa ne. Ya dauko wayarshi ya fara neman layin Ahmad bugu daya ya daga har ya tayar da motarsa, amma yace masa ya dawo maza maza nana nason ganinsa. Gaban Ahmad ya fadi yaji kamar kada ya koma din, amma bazai iya kin zuwa ba, don haka dole ya fita daga motar ya nufi dakin gabansa na faduwa yana ta addu,a a cikin ransa. Kai tsaye Alh nura ya shige dashi cikin dakin da nana ke kwance , mutanen dake zaune agurin suka dinga mamakin irin matsayin da Ahmad yake dashi a gurin Alh nura kwangila din daya samu shiga gurin nana. Nana ta kurawa kofar dakin ido dai dai lokacin da Ahmad ya shigo sukayi ido hudu, tayi doguwar ajiyar zuciya murmushi ya bayyana akan fuskarta. Ahmad ya matsa kusa da gadon nata ya tsaya da damuwa akan fuskarshi yace sannu hajiya nana, yaya jikin? Tayi murmushi da sauki nagode da kazo dubani ka kula da komai kafin na koma. Azahiri kowa zai zaci tana magana ne ko taso ganinshi don kamfani da gaske sai dai kasan zuciyarta tayi hakane don ta ganshi kawai. Alhaji nura kwangila da hajiya batula suka kalli juna da mamakin abinda tace.

Surayya

11 October 2015 at 18:02 · Public Save · More Like React Comment Share Like26 Write a comment...

· Son Guy Bin Abdallah Ana ahaka Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Salisu M. Mu'azu Dankado Him Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Son Guy Bin Abdallah Ana haja Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Tahir M. Kaumi Next pls. Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Amirah Muh'd Tnx Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Umar Dahiru Tnx Alot Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Tnxxx Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Ahmad Sabo Good. Sury Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Dan Allah aci gaba Like · React · Reply · More · 11 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO....4**10

Ahmad yayi tsaye kamar bazai tafi ba sai da ya dan jima sannan ya musu sallama ya wuce idonsa ya ciko da kwalla saboda ganin irin halin da nana ta shiga, idonta yayi jawur hawaye ne kawai ke zuba daga cikinsa. Ko da ya isa ofis kasa komai yayi sai tunanin halin da nana ke ciki da ace zai iya taimakonta da yayi, amman bazai iya bari rayuwar nana ta lalace ba dole zai san abin yi. Kwanaki hudu tana cikin asibitin amma babu sauki sai abinda ke karuwa, musamman hawan jininta gashi anyi anyi ta fadi abinda ke damunta ta ki sai kuka. Shi kansa Ahmad tun zuwansa na farko ya kasa kara komawa, don bai son ganin nana cikin halin da ya san bazai iya taimakonta ba. Bayan kwana uku Abangaren nana dai hankalin iyayenta atashe yake kullum yau kam Alhaji nura kwangila ya tabbatarwa kansa da sai yasan abinda ke haddasawa diyarsa wannan halin da take ciki, don suna jin kukan da take kusan kwana tanayi indai ba,ayi mata allurar barci ba. Tana zaune atsakiyar gado tana shan ice-cream ya taso daga inda yake ya dawo kusa da ita ya zauna agefen hadadden gadon dake kama dana gidan wani hamshakin sarki don ya sha gyara. Cikin sanyin murya Alh nura ya kirawo sunanta ta dago kai ta kalleshi gabanta yana faduwa ta amsa. Ya sake kwantar da murya yace nana ki taimakeni ki sanar dani gaskiyar abinda ke damun ranki? Nana ki tuna bani da kowacce diya a duniya sai ke, ke kadai Allah ya bani dan uwana guda daya ne yana kwance cikin jinya ke kadai nake kallo adangina kuma yata, idan kika bari na rasaki bazan yafe miki ba, don babu makawa nima karshen rayuwata yazo...... Yayi dan shiru yana kare mata kallo sannan ya cigaba Nana ki taimaka ki sanar dani abinda ke damunki, ina da kudin da zan siyo miki dukkan abinda kike bukata awannan duniyar, idan kuma ya fi karfin siya zan tayaki da addu,a Allah ya baki shi ko kuma ya sanya sanyi da salama azuciyarki ki fadamin abinda ke damunki nana.. Nana ta sunkuyar da kanta kasa hawaye na zubowa daga idonta tace. Daddy idan na gaya muku abinda ke damun zuciyata zakuji haushina da abin watakila hakan ma ya sanya ku daina tausayamin. Injiwa yagamiki? Dukkan abin da zai sanya ki cuta irin wannan ya wuce mu d'aukeshi k'arami. Ki gaya min Nana ko kin manta nine Daddy d'inki da kike gayawa dukkan damuwarki?" Ta d'ago kai ta kalleshi kamar ba za ta fad'a ba, sai ta ce, "Daddy tun randa na yiwa Ahmad wulak'anci a Gidan mai na fara kamuwa da sonsa, nayi zoto wasa ne ko zan rabu da son a hankali, amma sai abin ya cigaba da hauhawa, cikin raina har ta kai na zamto bani da buri bayan ganinsa kullum, don haka kullum sai naje Gidan Man su, daga baya nayi hanyar da ya sami aiki kusa dani, wannan ya sanya na sami sanyi cikin raina, ban ta6a zaton idan na bayyanawa Ahmad buk'atata zai juya mini baya ba, sai dai na gano halin Ahmad bai sanya akan komai don na gwada masa dukkan abin da zai sanya ya gane ina k'aunarsa amma ya kauda kansa, daga k'arshe da naga sonsa yana neman hallakani ya sanya na sanar da shi amma sai ya gaya mini bai sona bai kuma ta6a sona ba....." Ta fashe da kuka maganar ta kasa ciga da fitowa. Hajiya batula da Alhaji nura kwangila suka bita da kallo da tausayawa basu taba zaton abinda ke damun yarsu kenan ba. Wato hakan na nuna musu ta warke daga cutar dake damunta tun tana da kuruciyarta, wacce suka kashe makuden kudade gurin ganin sun samar mata lafiya. Alhaji nura kwangila ya riko hannunta ya dora kanta akan kafadarsa yace. kwantar da hankalinki diyata nasan illar da soyayya ke yiwa zuciyar dan adam dan ta taba illata rayuwata amma indai akan Ahmad ne kukan ki ya kare da damuwa zan samar miki shi da ikon Allah. Ya mike da sauri yanzu zanje gareshi insha Allahu damuwarki sun kare. Idon nana na zubar da hawaye tana kallon baban nata daya nufi kofa kai tsaye zai fita cikin sanyin murya tace. Daddy don Allah idan yaki yarda kada kace zaka koreshi daga aiki, ganinshi kadai abin jin dadi ne agurina kada ayi masa dole akan sai ya soni. Alhaji nura kwangila yayi shiru bai juyo ba amma tabbas maganar diyar tashi ta shigeshi tausayinta ya kara kamashi ashe akwai wani abu da diyarsa zata iya rasawa awannan duniyar yana raye? Lallai iko yana gurin ubangiji ya kada kansa ya fice. Hajiya batula ta matsa kusa da nana don rarrashinta. Ahmad yana zaune a ofis wayarsa ta fara kira ya dago da sauri ya na kallon screen din wayar lambar Alhaji nura kwangila ya gani gabansa ya fadi amma dai dole ya daga, yana shirin gaida Alh nura sai ya katseshi da cewa kana ofis ne Ahmad? Da hanzari Ahmad yace ina nan Alh. Alhaji nura kwangila, ok to ganinan zuwa. Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake kamar ya gudu kada Alhajin ya sameshi amma babu halin yin hakan dole ya zauna ya jira zuwanshi. Lokacin da Alh nura kwangila ya turo kofa ya shigo Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar saboda wani bugu da yaji kijinsa nayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana wa.

12 October 2015 at 13:56 · Public Save · More Like React Comment Share Like27 Write a comment...

· Hauwa Muhammad Friends y Kke d ftn kowa Lfy dn Allah angama tattalin so ne wlh baba na ne y rasu bana Hawa online ngde Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Jamila Umar Tanko BooksJamila Umar Tanko Books Allah ya jikansa da rahama, mu kuma intamu tazo... More Al-Rayyan... replied · See all 4 replies Sumayya Nasir Abdullahi mungode acigaba Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Dahir Uthman Tend Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Khadijah Aliyu Tnx Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Al'amin Khalid Sulaiman Mungode, Dan Allah acigaba Dakyau, Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Muna godiya Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Nafisa Danladi Danladi Allah jikan sa.ya.jikan iyaye mu ,ya jikan alumar musulmi Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Abban Husnat replied · 1 reply Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Ahmad Sabo Dai dai kenan! Like · React · Reply · More · 12 Oct 2015 Hauwa Muhammad Ameen nagode sosai Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO...4**11

Gaba daya hankalin Ahmad ya gama tashi ji yake kamar ya gudu kada Alhajin ya sameshi amma babu halin yin hakan dole ya zauna ya jira zuwanshi. Lokacin da Alh nura kwangila ya turo kofa ya shigo Ahmad ji yayi kamar akan kirjinsa aka mako kofar saboda wani bugu da yaji kijinsa nayi. Da sauri Ahmad ya mike tsaye yana wa Alhaji sannu da zuwa. Alhaji Nura ya dubeshi yana murmushin yak'e yace, Zauna Ahmad inason yin magana dakai ne, kuma magana ce mai mutuk'ar muhimmanci a garemu. Ahmad ya koma ya zauna cikin sanuyin jiki, gabansa na dukan d'ari- d'ari. Alhaji Nura ya janyo Kujera dake fuskantar wandda Ahmad ke kai azaune shima ya zauna ya tsare Ahmad da ido yana fad'in, Ba sai naji komai daga bakinka ba na san Nana ba ta yin k'arya, ko yaudara, abinda na ke fata daga gareka kawai shi ne ka amince Ahmad, bani da Kud'i ko ikon da zaniya siyan soyayya, domin da zan iya da tuntuni na siyuwa wani soyayyar Nana na aurar daita. Tunda Nana ta taso ta k'i jinin kula Saurayi har zuwa girmanta, hakan ya jagoranci tunaninmu da kuma fad'hn wasu Malamai cewar wai aljani bak'i ne ya aureta, yanzu kuma sai gashi allah ya kawo mana maganin abin rana d'aya, nana ta furta da bakinta cewa tana sonka Ahmad. Ahmad kayi duba da kyau ga wannan lamari, nana yarinya ce mai kyau da tsari kamar nana ace ta tunkari namiji tace masa tana sonshi ka san ba k'aramin abu bane, Kamar nana ace ta tunkari namiji tace tana sonshi ba karamin abu bane, ka taimakeni Ahmad ka auri nana don Allah. Ahmad kansa yana kasa tunda alh nura kwangila ya fara magana, da ace akwai mutumin da zai iya yiwa wani abu ko da ranshi bai so ba to bai wuce Alh nura ba, amma bazai iya yiwa ma,un shi kishiya ba dan yiwa ma,u kishiya kamar yiwa ummansa ne, mutanen da suka raineshi suka bashi mace yaya zai iya yi musu haka? Bashi da amsar da zai iya baiwa Alh nura kwangila dan haka ya dukar da kansa kawai. Alh nura kwangila ya zuba masa ido da mamaki sannan yace. Ahmad ko akwai wani abu da nana take wanda ranka bai bukata ko kuma tana da wata illah ne gaya mini don banyi zaton wani namiji zaiki diyata ba a wannan lokacin. Ahmad ya girgiza kai yana fadin, ko daya babu wani abinki dana gano a wajen nana amman..........Sai kuma yayi shiru ya sara ma mai zaice. Lallai Ahmad ka nunamin kai namijin duniya ne, hakan kuma ya sanya na kara yarda nana tayi zabi, don nayi imanin wani zai so nana ko don arzikinta ko kyanta ko dan nasabarta amma ko daya bai burgeka ba daga cikin wadannan abubuwan. Ahmad ya kada kai tunda nake ban taba sanya kwadayin abun kowa araina ba na wadata da abinda nake samu, amma kayi hakuri Alhaji ina cikin halin da ba zan iya aurar wata ba. Alhaji nura kwangila ya sake kallon Ahmad da tsananin mamakin karfin halinsa amma hakan kara birgeshi yake da kuma nuna masa shine mijin daya dace da diyarsa nana.Cikin kwantar da murya yanzu Alh nura kwangila ya cigaba da magana. Yanzu kam alfarma nake nema ka dubi halin da nana take ciki, bani da kowacce diya sai ita kadai zan iya rasata saboda sonka ka ceci rai Ahmad, ka ceci rayuwarta daga cikin bakin cikin dake damunta. Jikin Ahmad yayi sanyi lallai yakamata yayi wani abun akai, amma kuka bazai iyayin abun kai tsaye ba don haka yace da Alh nura Alhaji ka bani dan wani lokaci zan yi shawara tukunna. Ran Alhaji nura yayi dan sanyi , ko ba komai ya samu magana mai dadi amma cikin ransa mamaki da tu,ajjibi ne ke cikashi yau kuma haka Allah ya kaddara masa kamar shi ya buge da rokon wani akan wani abu da bai da iko akansa, bayan da shi kullum ake roko. Wannan kadan kenan daga ikon Allah. Alhaji nura kwangila ya girgiza kai ya mike yana fadin. Hakan ma yayi, amma bazan baka dogon lokaci ba gobe kamar wannan lokacin zan dawo dan jin shawarar daka yanke nagode. Alh nura ya juya ya fice, Ahmad ya bishi da kallo da fargaba da tsoron abinda zai biyo baya. Yau kam ransa asake ya isa gida, halin daya ga ma,un ya kara sanya ransa yin dadi, ita da yayansa suna cikin kyakkyawar shiga gwanin sha,awa. Ma,u ta mike ta taroshi da jin dadin yadda ta ganshi cikin farin ciki, ya mannata akirjinsa yana sumbatarta suna dariya, tayi masa duk abinda ta saba yi masa suka wuce daki. Yau suna cikin farin ciki gurin cin abinci take bashi labarin zuwan amina gidan dayake tayi aure shekaru hudu da suka wuce, Allah ya hadata da wani dan kasuwa akantin kwari da yayi mata karyar shi mai kudi ne yana da katon gida da mota. Akayi aure sai gashi ta kare a daki falle biyu a gidan, hakanan ta tarar zaman da zatayi ita da kishiya ne da kuma tarin yaya guda shida tayi kuka da bakin ciki amma ba ta da zabi bayan zaman auren. Malam sulaiman shi yayi komai na auren nata tare aka hada da musa wanda yanzu yake zaune a gidan Ahmad daya bashi aro saboda yawon haya ya ishesu, kuma tunda taje gidan mijin Allah ya jarrabeta da haihuwa ga babu don kuwa karya yayi irin mutanen nan ne yan kayi nayi masu tsayawa abakin hanya,

13 October 2015 at 15:22 · Public Save · More Like React Comment Share Like27 Write a comment...

· Salisu M. Mu'azu Dankado Gud Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Hajaru Sani tnx alot Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017 Hauwa Muhammad Aunty j muna gdia Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Hajaru Sani tnx alot Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017 Abubakar Ibrahim Tnx Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Aisha Ahmad Dayyab Thanks Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Hauwa Abdullahi Godiya muke Like · React · Reply · More · 25 Feb 2017 Usman Aliyu Taller Thanks 1 · Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Plz aci gaba mana Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Umar Abdulkadir Múwadda Malik good but typing erro Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**12

mutanen nan ne yan kayi nayi masu tsayawa abakin hanya, wadanda suke tsayawa idan mutum zaiyi siyayya su nuna masa shago wataran ma sai aje a wuni ba,a samo komai ba, ga iyayenta suma babu ta ko,ina su abarsu suji da hidimar diyar dake gabansu wacce suke kiranta da yar raliya saboda ba,ayi mata radin suna ba balle ragon suna ko wani abu. wannan kadai ya zamewa lami ishara. Sai da yakai loma bakinsa sannan ya kalleta yace ina jinki ma,u, yaya tazo nan gidan kuma ita da tace har abada babu ita babu mu? Ma,u tayi murmushi tace bari kaidai yaya yunwa da bala,i ne suka isheta taje can gidansu babu shine tayo nan tana zubar da hawaye da fadin na taimaka mata bayan ni babu mai bata cikin dangi tasan tayi abubuwa marasa kyau ita da mahaifiyarta garemu amma hannunka bai rubewa ka yanke ka yar don kwanansu biyu babu abinci sauran yan hayar gidan dama basa shiri sam da ita kishiyar sun hade mata kai don haka dole tayo nan. Kai bakaji zance ba sai kace ta sami tabin hankali. Kai talauci baiyi ba sam aduniya haka na harhada mata kayan abinci harda na sawa dana yara ta dinga kuka tana godiya. Duniya kenan. Ahmad ya gyada kai, kadan ma suka gani, duk wanda bazai iya kallon ikon Allah yayi shiru ba sai ya tofa tashi ko yayi kazafi akai ai yana tare da jin haushi da bakin ciki indai awannan duniyar ne. Suna ta cin abinci yana tunanin ta inda ya kamata ya bullo mata da abinda ke ransa can ya daure yace wai ya ya naji shiru ne anyi watanni da yaye malam fa? Ta dafe kirji Don Allah yaya kada kaja mini ina zaman zamana Allah ne yace na huta ka barni kawai. Yayi yake hakane idan kin gaji basai na kawo miki kanwa tayi ba. Ta kalleshi da sauri da mamakin abinda yace amma ta kasa furta komai sai kada kai da yake kawai. Ganin haka ya sanya yace ma,u yanzu ace ga wata mace tana shirin rasa rayuwarta saboda ni da kaunata har ta dinga shiga cikin mawuyacin hali na jinya zaki iya yarda na aureta? Gabanta ya kuma faduwa duk da tasan wasa yakeyi tace watakila na iya watakila kuma bazan iya ba. Dadi ya cikashi jin ta dan sakko har tana murmushi yace. Wani abu ne ke faruwa mai ban mamaki ma,u wai kamar ni Alhaji nura kwangila ke roko har da durkusawa kamar zai yi kuka, ko da yake yana da gaskiya. Akan me yake rokonka kuma? ta fadi da fargabar jin abinda zai fada. Ya kalleta ganin har lokacin babu wani tashin hankali ko bacin rai akan fuskarta ya sanya ya cigaba da magana. Bazan boye miki komai ba ma,u nana ta nuna tana sona naki bata fuska har ta gaji da nuni ta sanar dani da bakinta. Ma,u tayi mutuwar zaune akan kujera sai taji kamar ya faskara mata gatari ne akan tsakiyar kanta ta kasa motsawa. Ganin bata ce komai bane yasa Ahmad ya cigaba da magana. Ban boye mata ba na fada mata gaskiya ban sonta, hasalima bazan iya hada matata da kowacce mace ba, bazan iya mata kishiya ba, ranar da bacin rai tabar ofis dina ashe wau faduwa tayi a gida bayan anyi bincike aka gano tana dauke da ciwon zuciya daya kamata cikin dan lokaci. Bayan mahaifanta sun gano dalilin faruwar hakan suka tsirani da magiya kamar zai mini kuka akan na auri diyarsa na rasa mai zance masa tunda na fada masa gaskiya bana son diyarshi amma ya tsaya yimin magiya daga karshe nace ya bari nayi shawara da iyalina tukunna. Har ya kammala bayaninsa ma,u tana jinsa kamar cikin gajimare yake mata ihu cikin kunnuwanta. Ta daina fahimtar komai, bugun zuciyarta ya sauya abinda ta jima tana zargi ya tabbata kenan ta kuma tabbatar karya Ahmad ya shirya mata yanzu don ya sami auren nana don haka sai tayi murmushi cikin ranta tace zaka iya rubuta littattafan hikaya lallai amma a fili cewa tayi. Amman bai kamata ka bar nana ta rasa rayuwarta ba bayan dumbin alkhairan data aikata maka. Tana gama fadin hakan ta mike ya bita da kallo baki bude ya gaza gano inda zancen nata ya dosa shin da gaske takeyi ko kuwa gatse ta masa yakamata yaji cikakken bayani daga gareta. Taku uku ma,u tayi ana hudun juwa ta debeta ta fadi kasa tim! Ahmad ya tashi da gudu a gigice ya nufeta yana kurma salati, ya tallafota yana jijjigata gami da kiran sunanta amma ma,u ta suma. Ya mike da sauri ya samo ruwa ya tallafota ya zuba mata afuskarta ta bude idonta da sauri tana ganinta a rike ajikinshi ta fashe da kuma ta fara kokarin kwacewa daga jikinshi amma ta kasa domin jikinta ya mutu lubus! Cikin kuka take fadin me ya sanya baka barni na mutu ba Ahmad? Mamaki ya kamashi har ya kasa boyewa ya waro ido yau shi ma,u ke kira da Ahmad kai tsaye abinda bata taba fadi ba tsawon rayuwarta. A fili yace Ahmad fa kikace ma,u? Ta yunkura ta mike da kyar tana kuka tace. Na fada me kuma ya rage tsakanina da kai tunda ka zama mayaudari azzalumi, ni zaka yaudara? ni zaka cuta? Bayan ka tauyemin rayuwa kaje kuma yanzu zaka auro yar masu kudi da ilimi banson kara ganin fuskar macuci irinka. Juwa ta kara dibanta tayi tagal tagal zata fadi ya mika hannunsa zai tareta yana fadin ki yi hakuri ki zauna ma,u ki bari nutsuwarki ta dawo tukunna.

13 October 2015 at 15:31 · Public Save · More Like React Comment Share Like28 Write a comment...

· Usman Aliyu Taller Mhmmm mata dangin Fatima na annabi masu rikirkida Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Aisha Ahmad Dayyab Uhm MTA kenan Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Abubakar Ibrahim wannan kishin yayi Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Ummin Mustafa Muhd acigaba Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Weldon Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Ahmad B Aminu Kishin Bala'I sae mata Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Sa'adeeyer Zarah Lalle yusup ko naku kishin yayake ka pada mana Like · React · Reply · More · 14 Oct 2015 Muhd Dawud Rano Muna tare Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Umar Dahiru Tab Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Plz aci gaba Like · React · Reply · More · 13 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**14

Mahaifinmu ya fara gano amfanin ilimi. Mahaifinmu ya rasu lokacin Yayana Abdullahi yana da mata biyu ya zama cikakken d'an kasuwa, Yayana Alahaji Abdullahi ya sami nasibi akan harkar kasuwancinsa da ya gada gurin Mahaifinmu da yake ya d'an sami ilimi k'alilan na zamani, kuma yana da nasibi akan Kasuwancin. Yayana shi ne ya d'auki dukkan nauyin rayuwata, naji dad'i fiye da lokacin da Mahaifiou yana, sai na kasance matsayin d'ansa kuma k'aninsa. Uwargidanshi ta kasa zama saboda rashin haihuwawarsi da kuma fitinar matarshi ta biyu HAJIYA LAMI wacce ta kasance Mace mai fad'an tsiya da iko, Hatta ni kaina ina samun matsala da ita, fitar Uwargidan ya sanya Hajiya Lami ta k'ara mik'e kafa tana yin duk abinda ta ga dama tsawon shekaru. Da yake Alhaji Abdullahi bai da fad'a balle fishi, shi ya sanya ta rami abinda take so. Sannan Mahaifiyarmu ma mace ce mai kau da kai, a haka har shekaru suka ja. lokacin da na kammala karatun sakandire yayana abdulahi ya fara neman auren ASMA'U, wacce ta kasance 'yar d'au uwan mahaifinmu, wato da kakanta da namu bokan wasa ne. Dangi sun yi murna da hakan, don kwata-kwata baza a iya cewa ga auren da aka yi na ZUMUNCI a cikin wannan Iyali namu. Sai dai Hajiya Lami ta tayar da hankalinta ta kuma yi dukkan abinda zata iya ganin hana auren, amma sai da Allah Ya k'addara akayi auren. Bayan anyi auren anan ma tsugune bata k'are ba duk da ba gidansu d'aya c, a wannan lokacin Yayana ya biya minh kud'i na fita k'asarwaje karatu, * amman ina jin labarin gida. Hajiya Lami ta d'an sassauta bala'inta ganin shekaru sun ja har kusan biyar Asama'u bata sami haihuwa c, sai take ganin kowa zai zauna haka me. Shekarar da ma dawo daga karatu ma had'a Degree da Master's a shekarar komai ya faru, kasancewar Yayana Abdullahi ya gina k'aton Kamfani a Kano wanda shi ne ya zama na sarrafa Mai da Kayan Abinci. Kuma Allah Ya sanya Nasiai akai. Hakan ya sanya ya d'auko Asma'u ya ajiyeta anan ita kuma Hajiya Lami tana can garin mu na Yan Liman cikin Jigawa. Allah Ya sanya nasibi da albarka akan wannan dukiya ta Yayana a garin Kano, sa6an kuma Allah Ya k'ara saukar masa da rahamar samun cikinka Ahmad. Babu wanda ya san Mahaifiyarka Asma'u tana daciki har yayi wata uku a jikinta saida ciwo ya dameta na kaita Asbiti daga nan aka tabbatar da ciki ne da ita na tsawon wata uku! Yayana yayi farin ciki da jin wannan labari, har ya kasa 6oye murnarshi ya sanar da Dangi na can yan Liman. Cikin k'ank'anin lokaci labari ya fasu har ya isa kunnen hajiya lami. Like· Report·Jun 21 Nusaybarh Mustapha Ibraheem Tayi mutuk'ar bak'in ciki da jin wannan labarin, ta kuma k'uduri aniyar ganin bayan cikin nan. Kwatsam! Watarana ina 'Dakina kasancewar ina Kano Gidan Asma'u, lokacin Yaya yana can Yan Liman daga ni sai ita a Gida. Cikin dare daga 'Dakina na dinga jiyo ihu da hargowarta, abin ya bani mamaki don na san ita ba ma'abociyar rigima ba ce ba, don haka na fita da gudu, sai na taddata cikin Falonta tana ihu tana wurgi da duk wani abu dake cikin 'Daki. Na nufeta da sauri da mamaki ina tambayar abin da ya faru, amma sai na kula sam bata cikin hayyacinta na fara k'ok'arin rik'eta amma abin ya faskara, don watsi tayi dani gefe, na kuma mik'ewa da sauri na rake k'ok'arin rik'eta, a wannan karon ma ta k'ara watsar dani. Da abin ya faskara sai ma fice gurin masu Gadin Gidan suma suka kawo mini d'auki muka turata cikin d'akin Baccinta muka kulleta aciki. Nayi ta buga Wayar Gidan Yaya Abdukahi Land line amman ba a d'auka ba. Haka muka kwana cikin damuwa da tashin hankali, sai da gari ya waye sannan hajiya Lami ta d'aga kiran Like· Report·Jun 21 Nusaybarh Mustapha Ibraheem Ta sanar dani yayan baya nan, da yake wancan lokacin babu wayar hannu, haka na hau mota na nufi garin 'yan liman na sanarwa da Iyayenmu da Yayana. Muka d'ungumo gaba d'aya cikin tashin hankali da tsananin damuwa muka dawo Kano. kai tsaye aka wuce da ita Gidan masu TABIN HANKALI,

17 October 2015 at 11:03 · Public Save · More Like React Comment Share Like34 Write a comment...

· Adama Abdulkarim Kiyawa Allah sarki rayuwa mungode Like · React · Reply · More · 21 Aug 2018 Abubakar Aminu Nadabo Jaxakumullahu khayran Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Adama Adam Maidala Welldone Like · React · Reply · More · 19 Oct 2015 Sardaunan Telolin BG Tnx Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Jamila A A Jatau tnx Like · React · Reply · More · 19 Oct 2015 Dauda Yahaya Masanawa Madalla Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Hassan S Saddiq tnx Like · React · Reply · More · 18 Oct 2015 Zaynarb Abdullahi tnx Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Hajara Abubakar MUN GODE Like · React · Reply · More · 17 Oct 2015 Haleemart Abbakar Muna fa godiya allah yakaremu da sharrin mahassada ameen. Like · React · Reply · More · 20 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**15

da aka samu na game da warkewarta kullum sai dai a kulleta a cikin 'Daki sai da kyar ake samu ta d'an daina buge'bugen da take sai Rawa da Wak'a. Ga kuma Ciki a jikinta. Daga k'arshe dai Likitocin Asibitin suka bamu shawara akan gsky mu gwad na Aljanu don abin nata yayi kama da sanmu, amman sun ce zasu yi mata Allurar bacci yanda zamu ji dad'in tafiya da ita Gida. Hakan ko akayi, bayan anyi mata Allurar baccin muka sanyata a bayan Mota muka d'auki hanyar 'Yan Liman, muna tad nine ke vk'a Motar Yayana yana baya kusa da Asma'u ya d'ora kan Asma'u akn Cinyarsa. Muna tafe muna hira har bacci ya d'auke Yayana ya jingina da kuera ya fara bacci sosai. Kwatsam! muna tsaka da tafiya sai naji an shak'o wuyana an rik'e k'am. na fara k'ok'arin k'watar kaina na saki kan mota ina salati da kiran yaya don na gano Asma'u ce ta shak'o min wuya. yaya ya tshi a gigice yaga abinda ke faruwa ya fara k'ok'arin 6an6areta daga wuyana amma abin ya faskara, motar ta k'ara gudu tana yawo akan titi, muna ta ihu da salati har hatsarin ya afku. bamu farka ba sai a gadon Asbiti, ni kam bayan buguwa babu abinda ya sameni, shi kam yayana ya sami karaya da buuwa a baya, sai dai bayan ya farka Matarshi da cikin jikinta ya fara tambaya, sai dai mummunan labari ya riskemu cewar mu kad'ai aka gani zube a gefen titi motarmu ta kama da wuta. Wannan ya sanya jikin yaya k'ara rikicewa don ance matarshi ta mutu da kuma cikinsa wanda ya sanya rai da shi. Tun daga wannan lokacin har yau ba a kuma samun lafiyar yaya ba, shi da kanshi ya ce a maidashi Saudiyya don yafi jin dad'in Likitocin can da kuma zama acan. Hakan ya sanya aka sai masa gida mahaifiyarmu ma ta koma can gurishi da zama. Bayan Allah ya toni asirin Hajiya Lami ta hanyar zuwan wani d'an uwanta Gidan suna hira naji ashe ita ce ta shiryawa Asma'u wannan ciwo da Bokanta. Nayi kuka saboda jin irin mugun tuggun da Hajiya Lami ta shiryawa Asma'u, na sanar da Yaya abin da ya faru aka had'a meeting na gaggawa na Iyalinmu da Hajiya Lami na fara fad'in dukkan abinda naji tana fad'a, nan da nan hankalinta ya tashi ta fashe da kuka tana fad'in Tsautsauyi ne ya kaita ga aikata hakan. Yayana yana kuka ya ce za saki Hajiya Lami saki uku!! Ta sanya hannu aka tana ihu da rak'on ayi hak'uri ba zata k'ara ba, wannan ma wai tsautsayi ne da sharrin Shaid'an! babu wanda ya kulata don ta illata rayuwar yayana, ba zai k'ara samun macen da zata aureshi ba tunda ya zama mara lafiya. wannan shi ne dalilin rabuwar yayana da Hajiya Lami wacce yanzu take cikin mugun hali na ciwon hauka ga rashin gata.... Alhaji Nura Kwangila ya goge hawayen dake zubo masa yana dariya lokaci guda. Naji dad'i, na godewa Allah daya k'ddara Asma'u bata rasu ba saida ta haihu. Ina zaton ganinka Ahmad zai iya sanya Yayana ya sami sauk'i daga ciwo da azabar da yake ciki tsaawon shekaru, Don ya kasa mantawa da Matarshi Asma'u, Mace tagari, mai KARAMCI. Saboda kyautayi da gatan da ta nuna mini ya sanya da na haifi d'iyata na mai da sunanta akanta, watoNANA ASMA'U! Wani irin dad'i da farin ciki ya mamaye Ahmad, har ma ya rasa abin da zai farta, sai yak'e kawai yake, k'aunar Nana ta fara shga ransa! Ganin abin ya ke kamar a cikin Mafarkim da ya saba idan ya kwanta bacci. Wai yau shi ne ya san asalinsa da dalilin haukan Mahaifiyasa? Ashe Mahaifiyarsa bata aikata wani abu na sa6on Ubangiji ba? Malam Sulaiman yayi doguwar Kabbara da godiya ga Allah cikin tsananin farin ciki da murna. Umm kam bakinta yak'i rufuwa ashe zata ga wannan ranar a rayuwarta? Kowa jinsa yake wani iri daban, kallo d'aya za ka yiwa kowa kaga mamaki da farin ciki k'arara akan fuskarsa.. Atake anan aka yiwa Hajiya Amina waya ta iso Gidan. Itama tayi mamaki da farin cikin jin Ahmad d'an gidan manya ne! Aka dinga murnaHatta Malam Jibril sai da ya shigo da yaji hayaniya tayi yawa, don duk Mazan Gidan sai da aka kirawosu a Waya suka zo. Mamaki da tu'ajabi ya kamshi saboda ganin Alhaji Nura Kwagila a cikin Gidan a zaune a tsakiyarsu Malam Sulaiman suna tattaunawa, don duk wanda ya kwana ya hantse a garin nan ya san Alhaji nura Kwangila! Yau kuma musu dukiya babu iyaka ne suka zo Gidansu?" Ya ayyna hakan a cikin ransa Sai kuma yaji wai k'anin Baban Ahmad ne, iko sai Allah. Da kyar Alhaji Nura ya iya barin Gidan, amma da rok'om gobe za a bashi dama ya tafi da Ahmad can garinsu na 'Yan Leman sannan zai yi masa Visa shi da Iyalinsa su tafi Saudiyya gurin Mahaifinsa da Kakanrsa. Wannan dare mai muhimmanci ne ga Ahmad da duk wani mai k'aunarsa. Bayan sun koma Gida ya k'ank'ame Ma'u yana kukan dad'i da farin ciki. Ma'u ashe ina da rabon ganin Dangina da Mahaifata?

Kuyi hkr wlh banda lpia ne 2dayz

21 October 2015 at 14:43 · Public Save · More Like React Comment Share Like27 Write a comment...

· Bakoji Lamara Misau Allah ya kawo sauki ameen Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Maman Khayrat Da Abulkhayry Allah Y Kara Sauki Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Dahir Uthman Allah yakara sauki Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Allah ya kara lfy, mungode Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Dauda Yahaya Masanawa Allah ya bada lafiya Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Umar Dahiru Wshg U Bst Rcbry Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Fatima Umar Zubairu Allah yabaka lfy, Ameen Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Ahmad Sabo Allah ya sauwake. Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Hajara Abubakar Allah yakara lafiya Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise Allah ya kara sauki amma dan Allah a dinga yi da dan yawa Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**16

Ma'u yana kukan dad'i da farin ciki. Ma'u ashe ina da rabon ganin Dangina da Mahaifana har da Kakata? Ashe ina da rabon yin farin ciki da alfarin yanda kowanne d'a keyi da iyayensa da danginsa? Ma'u me yafi wannan dad'i a gareni? Me zan yi na godiya ga Allah? Tabbas ni d'an gatan Ubangiji ne, bai ta6a tozarta rayuwata ba bai ta6a wulak'antani ba. me zan cewa Allah? Yana magana yana kuka, amman daga gani kukan farin ciki nd. Itama Ma'u kukan take yi na taya Mijinta murna da kuma rarrashinsa. Tace masa, Sallah zamu kwana muna yi da yin godiya ga Allah da Ya k'addara mana ganin wannan lokaci. Wannan shi ne kad'ai hanyar da zamu nunawa Allha farin cikinmu. Ya kad'a kai yana fad'in "Haka ne, tashi mu fara. idan su Lami kuwa, wuk'i-wuk'i Lami tayi jin aslin Ahmad tana zare ido. Lallai taga d'umbin darasi a rayuwarta. Malam Jibril yace mata, Shi ya sanya kullum nake gaya miki babu kyau wulak'anta d'an Adam. Yau dai ga iyayen Ahmad da kike yiwa gori kullum shi SHGE ne? Danginsa dangi ne masu asali da arziki. Ke yanzu ina dangin jikarki d'iyar Raliya suke? Kinga hakan ya tabbatar miki kece mai SHEGE ba shi ba. Sai kawai Lami ta fashe da kuka tana fad'in, Lallai nayi kuskure da ba zai gyaru ba, me ya sanya na biyewa zuciyata har na aikata wannan abun? Kaicona!!!" Malam Jibril yace, Lami ai baki daima kuka ba tunda har yanzu baki san halin da d'iyarki Raliya take ciki ba. 'Diyar Raliya ta iso ta zauna akan cinyar Lami tana fad'in Ke Lami me akayi miki kike kuka?" Lami ta kalli Yarinyar da tausayin halin da ta janyowa rayuwarta, da yanzu itace zata kasance cikin wannan Daular. AGidan Alhaji Nura kam d'an k'arimin falm aka yi, domin yanda ya shiga da farin ciki yana k'wallawa Matarshi da d'iyarshi kira ya basu mamaki, don ba halinsa bane ba. Suka fito da tsananin mamaki suna tambayar abinda da ya faru. Hajiya Batula tace, Duk yanda akayi an taida lokacin auren nan da Ahmad. Dad'i yacika Nana Alhaji Nura Kwangila ya kad'a kai, "Wannan abum yafi auren Nana da Ahmad, fara cikine akan farin ciki, ku zauna na gaya muku abin da ya faru. Ba musu suka zauna. Alhaji Nura Kwangila ya kallesu yana murshi yace, Ashe Ahmad d'ana ne, d'an d'an uwana ne! Shi ya sanya ni da d'iyata Allah Ya jarrabemu da tsananin sonsa da k'aunarsa!!" Hajiya Butla ta cika da mamaki, domin ta san duk abinda ya faru ga Yayan Mijinta, duk da lokacim ko taunanin aurenta ma ba'a yi ba, amma ta yaya hakan zata kasance? Nan Alhaji Nura Kwangila ya kwashe labarin duk abinda ya faru ya sanar dasu Nana ta dake tsalle ta rungume Mahaifyarta wucce ke yin dariya tana fad'i, Sakarya kina manta ba ki da laya ne? Sanan ta kalli Mijinta da farin ciki. Bam ta6a jin irin wannan labarin ba ko cikin Littattafan Hikaya ko kuma cikin fina-finai da ake yi ba. Wato a sam da ake tunanin Asm'u ta mutu, ashe ita tana can cikin mawuyacin hali, sai da Allah Ya cika lamarin sa na haihuwar Ahmad sannan ta cika? Lallai wad'annan mutane da suka rik'eshi sun cancanci yabo. Ya ce, Lallai kam. Shi ya sanya ya kasa had'a d'iyarsu da kowacce Mace a duniya, domin sun bashi aure ne sanda kowa na duniya suka k'i bashi d'iyoyinsu. Tsarki da iko sun tabbata ga Allah Mahalinccin kowa da komai, mai yin yanda yaso, kuma a lokacin da ya so! Nana tafi kowa farin ciki, wato bayan Ahmad zai zama mijinta kuma zai kasance d'an uwanta na jini, koma ya kasance. Suma dai a haka kowa ya kwana da abin da yake sakawa a cikin ransa, amman duk Umman Ahmad tafi kowa farin ciki, don d'anta ya fita daga sunan SHEGE daga masu yi masa kallon hakan. Washe gari da sasafe Alhaji Nura Kwangila da Iyalinsa suka nufi Gidan Malam Sulaiman. Lokacin Ahmad bai k'aso ba shi da Iyalinsa sai da aka kirasu a waya sannan suka taho. Alhaji Nura ya tahu da manyan motoci don tafiyar harda su Umma da Hajiya, Su Ahmad suka iso aka fara gaggaisawa. Ma'u da Nana aka had'a ido kowacce gabanta ya fad'i da ganin 'yaruwarta. Shi kam Ahmad dakewa yayi yakasa kallon inda Nana take duk da yana jinta a jikinsa amatsayin 'yar uwarsa a yanzu, amma yana jin kunyar Ma'u don ba zata zaci haka ba. Nana ce da kanta taisa inda suke ta kalleshi tana murmushi da fad'in, "Yayana wannan ce Antina Ma'u? Ya kalli Ma'u yana murmushi wacce tad'an saki ranta yace, "Eh ita ce, kin ganta nan Maman Yarana. Nana tayi yak'e tana fad'in, Antina ina kwana? Ma'u ta d'an saki jiki suka gaisa, amma zuciyarta na bugawa. Ashe Nanan ma bata wuce tsarrarta ba, tayi zaton wata k'atuwar Macce iri KISN BOKON nan. Nana kam ji tayi ta d'an tsorata don ta kula Ahmad yana balain son matarshi Ma'u daji da ita, kuma babu wani abu da zata nuwa Ma'un, don babu wanda zai ta6a yin zato Ma'un tayi auren fari balle ace har ta haifi 'ya'ya. Da aka tashi shiga Mota sai tace ita Motar Ahmad zata shiga, yaran suka koma motar Alhji Nura wanda shi ya buk'aci hakan da kansa,.

21 October 2015 at 15:29 · Public Save · More Like React Comment Share Like29 Write a comment...

· Adama Abdulkarim Kiyawa Masha allah mungode Like · React · Reply · More · 21 Aug 2018 Abdullah Fatima thanks Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Son Guy Bin Abdallah 9ce ana haka Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Abubakar Ibrahim Thanks Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Falmata Nahista Gub Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Weldon Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Amira Lawal Bello Yayi kyau Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Itx Mùhãmmâd Adam TK Like · React · Reply · More · 7 May 2016 Abubakar Habu Rahama allah yakara miki basira Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 Muhd Dawud Rano Mungode munatare Like · React · Reply · More · 21 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**17

don kallonsu faranta masa rai yake yi, don yana ganin suna fara yawa ke nan cikin iyalinsu, don duk yanzu sai tsffi da dangi na nesa can. Ma'u bata so hakan ba, amman bau yanda za tayi iya, sai dai kishinta ya gaza 6oyuwa akan Nana, duk da Ahmad yana nunawa ita ce fa Matarsg ta gaskiya abar sonsa. Shi ne mai tuka Motar Ma'un nakusa da shi, Nana tana baya sai suka yi kamar basu san da ita ba suka dinga hirarsu sai jefi-jefi Ahmad ke d'an tsomata yace, "Ko Kanwata? Sai tayi murmushin yak'e kawai, har sai da tayi dana sanin shiga Motarsu a yanzu ta kuma gano waye Ahmad da kuma yanda ya d'auki Ma'u cikin ransa ba ta da had'in da kowacce Mace, don haka Addu'a kawai ta rink'ayi akan Allah Ya kaisu lafiya zuciyarta bata buga ba. Wannan abin da yayi shine ya sanyayawa Ma'u ranta, ta tabbatar Mijinta bai son Nana kwata-kwata, kuma dukkan abinda yake gaya mata gaskiya ne. Lokacin da dangi suka ji waye Ahmad sun yi ta murna da mamaki, musamman Gidan kakanninsu don har yanzu matan nasa sua man cikin gidan gadonsu, Alhaji Nura Kwangila shi ke musu komai tunda Allah bai basu haihuwa ba, aka yi ta yawo da Ahmad ana nunashi da sanya masa albarka, sai da suka kwana biyu a garin sannan suka koma Gida. Cikin wannan kwanakin kuma Nana ta gano lallai Ahmad da Ma'u sun yi nisa, amman bata karaya ba tana nan akan bakanta don tasan idan ta zamo Matarsa dole ya sota kuma yayi adalci tsakaninsu. Duk wani mutum dake Kamfanin saida yayi mamakin jin wai Ahmad d'an Gidan Alhaji Abdullahi yayan Alhaji Nura Kwangila ne, randa suka suka shiga ofis Alhaji Nura ya mai da masa muk'amin D.G. hannunsa, Nana kuma ta koma kan Kujerarsa, don yace shi ya fi dacewa da Kujerar, sannan ya fara nemar musu Visa da Passport, musamman Ahmad da Iyalinsa, ya kuma bayar da izinin gina wani k'aton Gidansa daya fara yace a ci gaba da aiki. Babban Gidane sosai. Sannan aka sauyawa Ahmad Mota mallakinsa ta kansa tare da bashi kwautar Kud'i masu yawa yafara gyara gidanshi da iyalinsa kamar yanda Alhaji Nura ya ce. A dukiya irin ta Mahaifnka ya kamata ace ka sauya. Shi Ahmad rasa me zai yi da Kud'in ma yayi, sai kawai ya dinga yiwa Iyayensa da 'yan uwansa da Ma'u abin alkhairi da su, har Ma'un ta dinga fad'a akan irin kashe Kud'in da yake mai yawa haka. Ahmad yace bai yi yawa ba don bai ci ko rabin Kud'in da Baffansa ya tura masa cikin Rkawun d'insa ba. Rayuwa ta sauya. Daman dare d'aya Allah kan yi Buture! Sun sami tafiya Saudiyya gaba d'ayansu Nana da Ma'u da Ahmad da Yaran da Alhaji Nura. Idan akwai wani abu da ke burge Ma'u ga Nana bai wuce yanda take son 'yayanta daji dasu ba, tunda suk had'u da Yaran ta share iyayen, bayan gaisuwa bata k'ar bi takansu ba, don ta kula suna gab da haddasa mata dawowar ciwonta, suka dinga hirarsu da yara. Alhaji Nura kwangila na kallosu da dariya, ba ya ganin laifin Ahmad, ganin son da yake nunuwa Ma'u, don Iyayenta da ita kanta Yarinyar sunyi masa halaccin da bai kamata yajuya musu baya lokaci guda ba. Sannan akwai SOYAYYA DA SHAK'UWA mai k'arfi a tsakaninsu kuma. Sunisa Gidan Alhaji Abdullahi wanda yake babban gaske tun daga waje, sun isa Gidan suka tadda Hajiya Ruma a Falonta tana kallo, Tsohuwa mai Ran karfe! Jin dad'i da kwanciyar hankali sun bayyana a jikinta, duk da fatarta da jikinta ya nuna tsufanta. Tayi matuk'ar mamaki da ganinsu, zuwan babu zato. Bayan an gaisa ta janyo yaran gurinta cike da sha'awa. Alhaji nura Kwangila yace, "Hajiya da da hali hutune ya kamacemu, amman abum da ke tafe damu ba zai barmu mu huta ba idan bamu fad'a ba. Ina Yaya Abdullah yake? Tace, Tun safe masu hidama suka tafi Harami da shi...." Tana cikin mamaganar sai ga shi nan an shigo da shi cikin wani Keken Guragu irin na masu hali mai amfani da wutar Lantarki, da kansa kuma yake tafiya. Farin ciki ya cika fuskarsa da ganin Alhaji Nura Kwangila da nana, shi kuwa Ahmad zabura yayi ya mik'e da sauri yana kallon Mahaifinsa. Tabbasa babu makawa wannan Mahaifinsa ne! sai yanzu ya gano da waye yayi kama, don yana kalloo hoton Maiaifiyarsa ya kasa gano kamarsu, ashe da shi yayi kama. Shi kansa Alhaji Abdullahi yaran ya fara yiwa magana suje gurinshi, Suka tafi da gudunsu suna dariya da mamakin kekensa. Sai da bka nutsu sannan aka fara gaisawa, sannan Alhaji Nura ya kalli Yayansa ya ce, Yaya dawa wannan Matashin yayi kama?" Alhaji Abdullahi ya kalli Ahmad sai sauri wanda bai maida hankalinsa akansa ba tunda ya shigo. Ya k'ura masa ido, rai idonshi ya ciko da k'wallah yace, Da ace NANA ASM'U ta haihu da zan ce d'anta ne wannan, domin babu abinda ya raba kamanninsa da nawa sanda ina cikin k'uruciyata! Duk inda wannan yaron ya fito jininmu ne, jinin Buba Wali wanda muka had'a Kaka na had'u da shi, don iyalan Gidansa ne ke kama dani. Hajiya tace Wannan haka yake. Ahmad yayi ajiyar zuciya da jin dad'i. Lallai ya k'ara sakankan cewa Mahaifinsa. Alahaji Nura ya mik'e yana musmushi ya ciro Hoton Asma'u wanda take mace ya nufi Alhaji Abdullahi da shi ya nuna masa ya ce, Yaya ka shaida wannan wace ce? Alhaji Abdullahi ya kar6i Hoton

22 October 2015 at 14:27 · Public Save · More Like React Comment Share Like38 Write a comment...

· Usman Aliyu Taller Sannu fa Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Saidu Maimuna masha allah Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Aisha Humairah shukran Like · React · Reply · More · 23 Oct 2015 Amirah Muh'd Tn Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Dahir Uthman Tenx Like · React · Reply · More · 23 Oct 2015 Khadijah Aliyu Tnx Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Firdaus Feedy Paradise DanAllah aci gaba Like · React · Reply · More · 24 Oct 2015 Tahir M. Kaumi Next pls. Like · React · Reply · More · 24 Oct 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 22 Oct 2015 Sa'adeeyer Zarah Kai mun gode Like · React · Reply · More · 23 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**18

Alhaji Nura ya mik'e yana musmushi ya ciro Hoton Asma'u wanda take mace ya nufi Alhaji Abdullahi da shi ya nuna masa ya ce, Yaya ka shaida wannan wace ce? Alhaji Abdullahi ya kar6i Hoton ya k'ura masa ido, sai ya hau Salati yana fad'in, Subhanallahi! Wannan ai Asmu'u ce Nana Ma'una ce! Hajiya Ruma ta mik'e da gaggawa ta amshi hoton, sai ta koma ta zauna tana salati tare da fa'in, Nura ina ka samo Hoton Gawar Asm'u, Yarinyar da aka ce mana ta rasu cikin Mota ta k'one k'urmus! ko Tokarta ba asamu ba?" Alhaji Nura yayi murmushi yana kallonsu ganin duk sun gigice sannan ya fara basu labarin abinda ya faru da Asma'u da d'an da ta haifa har zuwa yau. Yana kaiwa k'arshe Alhaji Abdullahi ya kalli Ahmad ya ce, Wlh wannan shi ne d'ana! kai jinina ne!! Zo nan na rungumeka naji dad'i don Allah!!!" Ahmad ya mik'e da sauri yaisa ga Mahaifinsa ya d'ora kansa bisa cinyarsa yafashe da kuka yana goge kan kamar wani k'aramin yaro. Alhaji Abdullahi ya shafa kansa yana hawaye shima. Ahmad ke fad'in, ashe inada Iyaye masu daraja haka na dinga shan gori da hantara sboda rashinsu? Ashe nid'an gatane gaba da baya? Amma na godewa Allah da Ya sanya Iyayena dana rayu a gurinsu basu tagayyara rayuwata ba! Na godewa Allah da ya had'ani daku sanda nake tsananin buk'atarku. Maganganunsa sai da suka dinga sanya kowa kuka. Alhaji Abdullahi yace, Ka daina kuka Ahmad, wallahi ban ta6a jin dad'i da jin jinin jikina yana tafiya dai-dai kamar na yau ba. 'Dana ina jin kamar zan iya mik'ewa tsaye yanzu, kamani na gani zan tashi, domin naji kamar na warke babu rauran wani ciwo a Jikina! Ahmad ya mik'e da sauri ya kama Mahaifin sa, sai ya mik'e tsaye da k'yar! Amm ya kasa tsayuwa sai ya kwanta jikin d'an nasa yana fad'in, ashe zuciyata ce ta mik'e ba gangar jikina ba, Nayi zaton na tashi daga yau. Alhaji Nura ya isa kusa da shi ya kamoshi zai zaunar da shi, sai Ahmad yace, "Barshi Kawu zan iya. Wannan kama da ya gayawa Alhaji Nura Kwangila ya sanya shi jin wani irin dad'i da nishad'i. Yace, "Lallai yaya yanda zuciyata ta warke insha Allahu k'afafuwanka ma zasu warke da yarda Allah. Hajiya Ruma da Ma'u sun kasa koda mutsi sai hawaye. Ita kuwa Nana kallon Ahmad kawai take yi da jin dad'i. Dukkan sakwan sonshi na k'ara shiga ranta. An jima ana hira Sallah ce kwai ke tashinsu, sai da dare yayi sannan kowa ya nemi Makwancinsa. Alh Abdullahi yana jin kamar ya lashe Ahmad da Iyalans. Hajiya Ruma kuwa ta rik'e Ma'u katamau a jikinta suna jin kamar su cinyeta saboda kasancewarta Mata mai son d'ansu, don Ahmad ya basu labarin irin son da Umman Ma'u da Iyalin Gidanta ke masa. Sai dare kowa ya nemi makwancinsa. Cikin gidan nan kowa ya koma sashinsa da yake babban Gida, Ahmad ba zai iya rabuwa da Ma'unsa ba, don haka sashi d'aya suka d'auka, amman yaran runa gurin Hajiya Ruma, amman yini suke yi gurin Alhaji Abdullahi. Su kansu Likitoci sun yarda Alhaji Abdullahi ya sami lfya, daman sun san ba ainahin Ciwonshi ya hanashi tafiya ba sai bak'in ciki da CIWON ZUCIYA ne wacce ta warke yanzu garas! Babu sauran rauni a tattare da ita. Kafin sati guda sai ga shi ya fara k'ok'arin mik'ewa tsaye. Ahmad ya maida rayuwarshi gaba d'aya ga Mahaifinsa yana taimakmsa, shi ke yi masa komai, wanda hakan kullum ke k'ara faranta masa ranshi yana sanyashi nishad'i da sa samun suk'i, Ga Ma'u kuwa, tun bata sakin jiki da Nana har ta hak'ura ta sakar mata. saboda yanda take k'aunar 'ya'yanta da janta a jikinta, da taga kuma kowa ya gane tana kishin mijinta ne, bayan ko babu komai k'anwar Ahmad ce wacce ta dalilinta Mijinta ya gano dansa. Kuma taga babu wani aibu na soyayyar da Ahmad ke yiwa Nana, ko ita keyi masa, hakan ya sanya ta ga babu amfanin cigaba da shariyar. Nanan ce ta dinga janta zuwa Harami suna Addu'a da Salloli. Cikin zuciyar Nana Addu'a take yi akan Allah ya sassauto zuciyar Ma'u ta bata aron Mijinta ko da sau d'aya ne cikin sheka. Ita kuma Ma'un godiya take yiwa Allah bisa rahamar da yayi musu. Wai yau ita ce a gaban 'Dakin Allah mai girma, ne yafi wannan dad'i? Satin su uku suka fara shirin komawa Nigeria, amma Alhaji Abdullahi da Hajiya Ruma suka dage suma sun gama zaman Saudiyya tunad mai jinyar ya sami sauki yanxu har yana tafiya da sanduna biyu irin na masu kud'in larabawa, don haka tare suka tattara suka dawo Nigeria. Dayake Alhaji Abdullahi yana da Gidanshii bai sauka a can ba, sai ya sauka a Gidan d'an uwanshi aka bada umarnin a gyara mashi nasa. Cikin kwanaki biyu aka sauya komai na Gidan, xa koma sabo dal! hatta Fenti suka koma shi da Mahaifiyarsu da masu Aikinsu wad'anda daman dasu suka tafi can K'asa mai Tsarki (Saudiyya). Lokacin da aka had'u da su Malam Sulaiman da Alhaji Abdullahi kuka kawai Alhaji Abdullahi ya fashe da shi, don ya rasa bakin da zai yi godiya gasu Malam Sulaiman, k'arshe yace dole zasu bar wannan Gidan nasu cikin sati guda su koma wani sabo cikin rukunin Gidajen da ya gina.

26 October 2015 at 11:15 · Public Save · More Like React Comment Share Like37 Write a comment...

· Muazz Alawo tnks Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Salisu M. Mu'azu Dankado Gud Like · React · Reply · More · 27 Oct 2015 Khadija Mohammed Tanxs Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Amirah Muh'd Tn Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Ibrahim Ubali GD Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Maryam Abdul Tnx Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Usman Aliyu Taller Allah ya kara basira Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Ahmad Sabo Yayi kyau Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Abubakar Ibrahim good Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 Balkisu Muhammad Bashir Bashir

Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO.. 4**20

Sai tace babu komai kawai, don ko me zai yi mata ba zai wanke kansa ba a wajenta. shi da kanshi ya gano rashin kyautawar da yake yiwa Nana. Bai ta6a zuwa Gidansu da sunan zuwa Zance ba duk kuwa da halaccin da Mahaifinta yayi masa ya kamata yayi musu d'an wani abu da zasu ji dad'i. Don haka xau daga ofis yace da Ma'u ya wuce Gidan Babansa ne, amman sai ya wuce can. Yatarar da Hajiya batula da Alhaji Nura suna ta hira, yawanci akan Bikim ne wanda ya rage saura sati uku. Sun yi farin ciki da ganinsa ya ya zauna suka gaisa suka d'an ta6a hira cikin 'yar kunya ya ce, "Kawu wai ina Budurwar K'auyen man tayi ne ban gamta ba?" Alhaji nura Kwangila ya kalli Hajiya Batula da farin ciki fal fuskarsa yace, Tana can shashinta ko tana kallo ko bacci Ahmad ya mik'e tsaye yace, bari naje na tsokanota. Ya nufi sashin nata kai tsaye, Dad'i ya cika su Alhji Nura, wannan shi ne karo na farko da Ahmad ya ta6a numa wani abu ma kulawa akam 'yarsu Nana. Alhaji Nura ya dubi Hajiya Batula ya ce, "Kin gani ko na gaya miki? Watarana za a wayi gari Ahmad yana son Nana Ai jini guda ba k'arya bane ba. Hajiya Batula tayi dariya da jin dad'i ta ce, Lallai na yarda da fad'inka Alhaji. Nana tana Bam'Dakinta tana Wanka Ahmad ya shigo yana k'walla mata kira. 'Ke budurwar K'auye kina ina ne? Sam bata jiyorhi ba har ya shigo uwar 'Dakinta. Dai-dai lokacin ta fito daga Ban'Daki suka yi ido hud'u da juna, gaba d'aya jikin Nana a waje yake, don d'an Tawul d'in da ta d'aura bai kai ko rabiin cinyarta ba, ga kanta da wuyanta a bud'e, duk wanda ya san siffar kyau da tsarin mutane ba zai tsaya mamakin halittar nana ba wanda Ahmad bai ta6a kula da ita ba sai yau. Ko don hankalinsa bai ta6a kawa kanta bane oho! dukkaninsu suka yi saranda kowanne na k'ame. Ita kunya ce, Shi kuma wani abu yaji ya daki zuciyarshi wanda babu makawa yasan sha'awa da sontane yake ratsashi. Lallai ya yarda Ubangiji gwanin hikimane daya halittawa Maza auren Mace sama da d'aya, don zuciyarsa zata iya son Mace fiya da d'aya, da yaso ya cuci kansa. Canin yanda ya k'ura mata ido ya sanya tayi gyaran murya, sai alokacin ya farga, kunya ta kamashi, ya juya da sauri yace, "Ina jiranki a Falo idan kin gama shiryawa. Wani irin dad'i ya shigeta. Lallai ta yarda Mahak'urci. Mawadaci ne watarana. Bata ta6a ganin irin wannan kallon daga idon Ahmad ba sai yau. Lallai ta yarda a yanzu Ahmd d'in ya fara somta kamar yadda itama take tsananin sonsa da k'aunarsa. Tayi tsalle ta fad'a kan Gado tana ihun da murna, tare da yiwa Allah godiya da Ya nuna mata wannan lokaci. Ta ma rasa wacce irin kwalliya zatayi, ta jima tana za6e har ta k'are akan wata doguwar riga mai kama jikinta ta atamfa mai had'i da Yadi da ake kawosu daga Dubai masu d'an duwatsu. Rigar na dacewa daita k'warai da gaske, kuma tayi masifar yimata kyau Ta fesa turarruka masu k'amshi ta nufo Falon data tabbatar Ahmad yana ciki yana jiranta tana rangwad'a. Kamshin Turaren da yaji mai sanyi da dad'in shi yasa shi yin saurin d'ago kai yana murmushi. Koda ya kalleta sai ya sake yin murmushin ya ce, "Ee, lallai Budurwar kauye, ashe kin iya kwalliya? ta turo baki gaba tana fad'in, "Gaskiya Yaya Ahmad ba naso ka daina ce mini budurwar Kauye. Cikin shagwa6a take maganar. Yayi dariya da jin dad'i ya ce, "Shi ke nan na daina, zo man ki zauna ki bani labarn k'uruciyarki naji. Ta fashe da dariya ta zauna suka kama hira. Bai farga ba sai da kiran Ma'u ya shigo Wayarsa, ya dubi Agogon bango dake kafe a falon ya ga k'arfe goma na dare har ta gota, ya mik'e da sauri yana fad'in, Ya Salam! Ma'u ta gaji da jirana har tayi kirana Bari na wuce. Nana ta had'e rai da takaici, a yau tana murna ta d'an fara samoshi amma Ma'u ta 6ata mata bajat! Bai kula da halin da Nana ta shiga ba sai ya nufi Kofar fita daga Falon. A lokacin su Alhaji Nura Kwangila sun bar Falon da ya samesu d'azu hakan yasa Ahmad ya sake tabbatarwa lallai hirar tasu da Nana tayi nisa. Koda ya isa Gida Ma'un bata gano komai ba, domi haka ya rink'a bata labarin Yaranta da ba babanshi da Kakarshi da irin Diramar da suke yi tana ta dariya. Tunda daga wannan ranar kullum dare sai yace zai je gurin Babansa ya wuce gurin Nana, amma yana fara biyawa ya gaisa da Baban nasa yaga yaransa sannan ya wuce gurin Nana. A hankali SABO DA SHAK'UWA ya fara shiga tsakaninsu, amman ko da wasa bai ta6a yarda Ma'u ta gano ba. Ita kanta Nana ta gano Ahmad yana balain kaffa-kaffa da duk wani abu da ya shafi Ma'unsa, shi ya sanya ma bata had'a kanta da ita kwata-kwata. Rana cta k'arya sai dai uwar d'iya taji kunya! inji masu iya magana, domin lokacin auren Nana da Ahmad yayi, Alhaji Nura ne yayi komai, sai dai yayi adalci, don duk wani abu da aka sanyawa Nana a cikin Kayan Lefe an sanyawa Ma'u shi, sai k'alilan ne suka ban-banta, don haka kamar sabo Lefe aka sanyawa Ma'u a matsayi kayan fad'ar Kishiya.

30 October 2015 at 11:31 · Public Save · More Like React Comment Share Like34 Write a comment...

· Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 1 Nov 2015 Hussaina Abdulhamid Abdulhamid namiji kena Like · React · Reply · More · 6 Feb 2017 Muazz Alawo kakyauta Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Tahir M. Kaumi We need on time. Like · React · Reply · More · 31 Oct 2015 Dayba Seyoji Hmm namiji kenan Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Musa Abdullahi Dakyau Like · React · Reply · More · 31 Oct 2015 Hadiza Umar Abubakar Tnx Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Shafiu Shanabash DAME AKE ADO...? Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 Babangida Musa Ahmad Rijiyarlemo Ammma gaskiya namiji sai Allah Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 30 Oct 2015 View more comments…

Tanx Like · React · Reply · More · 26 Oct 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**20

Biki ne irin na masu kud'i da gata, abin dake bawa Ma'u bak'in ciki shi ne, ta rasa wanda zai tayata bak'in ciki, don Gidajen 'yan uwanta dake cikin Kwatas d'in nan kowa hidimar Bikin ce a gabanshi, haka Gidan su, haka Gidan Alhaji Nura Kwangila, haka Gidan su Hajiya Ruma, idan akwai mai tausaya mata da nuna mata damuwa bai wuce Hajiya ba sai kuma Ahmad da bai nuna damuwarshi ko zumud'in auren a gabanta sam har ta kanji kamar dole aka yi masa a ranta. Hankalin Ma'u bai tashi ba sai da aka zo d'aura aure taga irin d'umbin jama'ar da aka tara sannan da irin kud'in da yaye ke kashewa da saboda bikin. Sai da aka zo jeren Nana hankalinta ya gama tashi don bata ta6a ganin kaya irin na Nana ba ko cikhn Fim, don Hajiya Batula da kanta ta dinga nuna irin abinda za a yiwa d'iyarta a k'asar Dubai, duk da tana ganin matuk'ar kyau da tsarin gidan sai da ta ranna kanta da taga irin kayan da ake shigowa da su gidan da irin hidimar da ake yi kamar ba a son kud'in. Shi kanshi Ahmad irin shigar da yak'e yi sai take ganin kamar yanzu yafi k'arfinta, don wasu dakakkun Shaddoji ya yaduka Alhaji Nura Kwangila ya d'anko masa a Dubai, kuma a can Gidan yake shiryawa sai dai ya shigo mata. Ran da aka d'aura aure farin cikinsa ya kasa 6oyuwa dom ganin Mahaifinsa ya taka K'afarsa babu Sanda yana hawayen farin ciki, sannan Danginsu daga can 'yan Liman sun zo, yaga duk wannan taron don shi ake yi, don haka ya gaza 6oye farin cikinsa sam! Wannan shi ne abin da ya k'ara tayar da hamkalin Ma'u don ranar Ahmad bai kula ta kanta ba, tunda ya fice tun safe sai kwanciyar bacci ta dawo da shi Gidan. Can Gidan Baban nasa ya zauna ana ta hira da wasa da dariya da 'yan uwansa. San da ya dawo ya tarar da gidan cike da mutane, don haka kai tsaye 'Dakinsa ya wuce ya watsa ruwa ya fito yana shirin kiran Ma'u sai kuma ya kama Waya da Nana data kirashi. Anan ya shantake har bacci ya d'aukeshi bai nemi Ma'u ba. Yana tashi da safe ma da shirn fita yafito, kasancewar Abokinshi Jabir yashir yamasa'Yar walima suda Abokansu da suka yi Karatu, san da ya riga 'Dakin Ma'u don yin magana da ita aka ce tana Wanka, shi kuma ba zai iya tsayawa jiranta ba, saboda an dameshi da kiran a Waya, don haka ya juya ya fice. Wannan abin ya k'arawa Ma'u tsoro a ranta har take ganin tata ta k'are guqin Ahmad, ba shi da sauran lokacinta, kuma yanzu bata k'ara ganinshi a Gidan ko jin Wayarshi ba har dare sai 'yan kawo Amarya suka fara jerin gwano da Motoci, tun tana iya ganin adadin motocin da suke ta zuwa har ta kai ga gaza yin hakan, harabar Gidan k'ato ne zai iya cin motoci k'anana hamsin, kuma 6angare Nana da Ma'u daban, akwai 'yar tazara mai nisa ma. Asalin Gidan Alhaji Nura Kwangila ne da ya 6ata shekaru yana ginawa ya bai wa Ahmad da zummar shi zai k'ara gina wani Gidan nasa. Gud'ar kawo Amarya da ake yi kamar cikin ran Ma'u ake yinta, gashi lokacin babu kowa a Gidan, duk jiya aka zo mata, daga ita sai musu Aiki sai ta fashe da kuka ta had'a kai da bango tana kuka. Gabaki d'aya Gidan yayi mata zafi da kunci, Babu abinda take so illah ta fita ta barshi ko yata huta. Tana nan har 'yan kawo Amarya suka watse. Can wajen k'arfe goma da 'yan mintuna Ahmad ya iso Gidan. Kai tsaye 'Dakin Ma'u ya nufa, ya sha mamakin ganin bai ga komai akan fuskarta ba na 6acin rai, don ita kad'ai ta san abin da ta k'udurce a cikin ranta. Ya d'an zolayeta tana murmushi ya buk'aci suje sashin Amarya tace ba dai yau ba sai gobe. Ya ajiye mata kasonta da ya shigo da shi yayi mata sai da safe ya nufi sashin Nana cikin d'okin da yakasa 6oyuwa akan fuskarshi don yau kusan tare ya yini da nana, Kwalliya ta dinga yi ta tsumashi k'warai da gaske, wannan abin ya yiwa Ma'u ciwo k'wari da gake, yana fita ta k'ara fashewa da kuka. Wai yau Ahmad d'inta ne ke nuna zumud'in akan wata mace ba ia? ta dinga kuka, kusan haka ta kwan da damuwa. Shi kam Ahmad yana shiga 'Dakin Amaryarsa ya d'an zolayeta tak'i sakin jiki sai ya sureta cak suka yi ban'aki yin alwala idnta a rufe da kunya. A gsky a matse yake da Nana don tun randa ya ganta kusan tsirara sha'awarta ta gama nuna a cikin ranshi, don haka suna idar da Sallar ya fara nuna mata buk'atarshi da yake itama ta jima da jiran wannan lokaci bata yi wani nok'e- nok'e ba ta bayar da kanta. Abin da ya bashi mamaki bai wuce ganin bai sha wata wahala kamar yadda ya sha akan Ma'u ba, nan da nan yaji ya gamsu. Bayan ba haka yake so ba, yayi kykkyawan shirin da zai yi yanda yaso, sai dai bai samu ba yanayin shekarun Mace 'yar shekar 16 17 da mai shekara 23 da 24 akwai bambanci, don ita 'yar 17 komai nata k'ank'ani yake bai saki ba, sa6anin na wacce ta d'an yi shekaru 20. Sannan kuma a daren ya fuskanci Nana tana da tsawon buk'ata, sai yayi mamakin dalilin da sanya ba tayi aure da wuri ba. Ko da yake da alamunta bata ta6a yin mu'amala da wani na.

3 November 2015 at 10:02 · Public Save · More Like React Comment Share Like38 Write a comment...

· Samira Umar DAMAHAKA SUKE Like · React · Reply · More · 4 Aug 2019 Abdul Zuhra Mun gode allah ya kara kaifin basira Like · React · Reply · More · 4 Aug 2019 Usman Aliyu Taller Godiya mai yawa Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Rukayyah Abk tnx Like · React · Reply · More · 28 Feb 2017 Ibrahim Ubali GD Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Binta Binta Muna godiya Like · React · Reply · More · 27 Feb 2017 Muazz Alawo tnks Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Abubakar Ibrahim Good Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 Isah Aisha Hmm ai maza dama haka suke mtswwww Like · React · Reply · More · 27 Feb 2017 Hafsat K Dawud Godiya muke Like · React · Reply · More · 3 Nov 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**21

Ko da yake da alamunta bata ta6a yin mu'amala da wani namiji ba don ta d'an wahala, amman sai yaji daren farkonshi da Ma'u yafi wannan nesa ba kusa ba, amman ya bar abin a cikin ranshi. Ita kuma Nana wannan shi ne dare mafi alkhairi a rayuwarta. Sai a yau ta gano ashe tana k'warar kanta da rayuwarta, jikinta yana bukatar wani abu da take tauye masa lallai Ahmad ya kai ta gurin da baa ta6a zuwa ba, bata ma ta6a Mafarkin zuwa ba. Da safe duk da Ma'u tana ranshi gajiya da kasala bai barsu sun fito da wuri ba rai wajen karfe goma sha daya na safe. Lokacin sun shirya ya ce da Nana tazo su shiga gurin Ma'u su gaisa suka jera suka nufi shashin nata. Masu aiki suna ta hidimarsu, suka shiga suka dinga gaishesu, sai wata Yaya abu ta fito daga Kicin da sauri ta mik'awa Ahmad wata takarda tace inji Hajiya tace a baka. Da mamaki yace "Wacce Hajiya ke nan? Ciki ldabi tace, 'Hajiya Ma'u mana...." Tana ina yanzu, tana cikin 'Dakin ne?" Tace, "Eh ta fita tun wajen Asuba....." Ya katseta da fargaci "Ma'un! ina ta tafi? "Wallahi ban sani ba nima Alhaji. Damuwa da tashin hankali suka bayyana akan fuskarsa, sai ya ce Babu damuwa jeki kawai. Ya kalli Nana dake kallonsa da fargaba sannan ya maida hankalinsa ga wasikar ya bud'e. Ga abinda ta k'unsa, Mijina Ahmad. Nayi iyakacin kokari na danne zuciyata na zauna da kai, amman na kasa don na gano a yanzu kayi mini nisa, ka girmi rayuwata, wancan Ahmad din Mijina da muke dai-dai shi ne Talakan nan mai kula dani, da cina da sha na, mai kula da yanda na kwana da yanda na tashi, ba kai ba babban mutum! A yanzu rayuwarka tafi dacewa da d'iyar masu Kud'i da arzik'i irinka ba wadda kake taimako ba, mai ilimin degree da Master's da wayewa. Rayuwarka ta girmi ta Ma'u yanzu, don haka naga yafi dacewa na matsa na baku guri, na san ba zaka iya sakina ba saboda kunya da tunanin kad duniya ta zageka, don haka na hutar da kai na tafi inda ba zaka k'ara ganina ba, ba zakaji kunyar iyayena ka sakeni ba, amma ina son wata rana ka furta sakina ko cikin ranka ne, don kada nayi ta yawo da aurenka. Ga kuma amanar 'ya'ya nan, wata k'ila zan gansu watarana. A lokacin daza ka ci karo da wannan wasik'ar tawa tuni nayi nisa daga inda kake! ina yima ka fatan alkairi kai da Matarka! -ASAM'U MATARKA A BAYA Wani irin abu yabi ta jininshi ya wuce zur! Kamar wutar nepa taja shi, ya waro ido da fad'in, "Wht? Me kika aikata haka Ma'u, yaya kike tsammanin zan rayu babu ke?" Nana ta kalleshi ganin kamar yana shirin zarewa ne tace, Yaya Ahmad lfy, me ya faru?" Cikin kid'ima tace, "Ma'u ta gudu! Tabbas cikin satin nan na wofintar da rayuwarta, ban damu da damuwarta ba, hakan ya sanya ta yi zaton na daina sonta ne! Yaya zan yi, na shga ukuna, wallahi idan babu Ma'u ba zan rayu ba, bari naje na gayawa Abba da Umma....." Sai ya juya ya nufi hanyar fita daga Falon, nana tayi hanzarin ruk'oshi da sauri tace, "Haba yaya Ahmad, wannan matsala ce tsakaninka da Matarka, ka san ko ina Ma'u zataje ba zata yi nisa da kai ba, 6acin rai ne ya sanyata tafiya, idan ka gayawa iyayenta kamar ka tona muku asiri ne, zaka iya janyowa su yi fishi da ita" Maganganun Nana suka shgeshi yace, Haka ne, Yanzu me ya kamata nayi? Don Allah gaya mini Nana, kaina ya kulle, ina tsananin son Matata!" Ta ciza baki tace, Kaje kowanne Gida da kasan zataje Bada sunan cigiya ba da sunan kaje gaishesu ne, ta haka zaka gano inda ta shiga..." Yace, "Yauwa haka za ayi Bari na dawo. Yafice da sauri a rud'e, ta bishi da kallo idonta ya cika da k'wallah. Lallai Ma'u tayi nisa a zuciyar Mijinta, idan kuma tace sai tayi gasa da ita zata iya zamantowa a cikin takaici, abu d'aya ne zai janyo sonta ya zama d'aya dana Ma'u ko ma ya fishi shi ne Asiri, wanda bata ta6a sha'awar yin sa ba, don wad'anda taji labrin sun yi ma bai amfana musu da komai ba. Ta goge hawayen dake zubo mata ta nufi sashinta. GA AHMAD kuwa, dukkan inda ya san zai samu Ma'u sai da yaje har yamma tayi masa ya gaji lik'is ba tare da ya gano inda take ba, ya fara sarewa da tunanin ko ya sanar da iyayensa, don duk Wayoyinta Ma'u a kulle suke. TUN DA MA'U ta isa garin zaria gidan k'awarta Maryam wacce tayi aure kusan shekaru uku da suka wuce ta auri wani Soja take kuka da k'yar Maryam ta rarrasheta ta sanar da ita abinda da ya faru ta had'a da rok'onta akan ta rufa mata asiri ta barta kada ta gayawa kowa tana gurinta har zuwa sanda zata san inda zata tafi don ba zata ta6a komawa gidansu ba ko gurin damginta ba har abada! Maryam tayi matuk'ar mamakin jin labarin da Ma'u ta bata, amman sam bata ga laifin Ahmad a cikin wannan labari ba, ko don ita ma tana da Kishiyar ne? ita ce Amarya. Da Ma'u ta san irin halin da Kishiyarta ta shiga san da zai aureta da ta ce Ahmad d'an Aljannah ne, don haka ta fara baiwa Ma'u hak'uri da bata labari kala-kala na Mazajen da zasu yi aure,

4 November 2015 at 11:34 · Public Save · More Like React Comment Share Like47 Write a comment...

· Muhd Dawud Rano Mungode Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Ibrahim Dm Naimat good nd 5n Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Abubakar Sulaiman Kaura Yar shegiya kawai Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Rabi'u Khulsum Inuwa replied · 3 replies Hassana Gwarmai Nice Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Umar Dahiru Tnx Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Abubakar Ibrahim Hmmm Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Hasana Auwal Abbakar karkaga laifinta Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Ummu Khadijah Ummu Adnan Hmmmm Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 Azinatu Umar TNX Like · React · Reply · More · 4 Nov 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**22

duk da jikin Ma'u yayi sanyi amman tace ma ta ita dai ta kyaleta. Daga k'arrhe ta d'ora da ce mata. "Yanzu haka mijin nata yana gidan Uwargidan zai mata kwana biyu ba zata k'ara ganinsa ba sai bayan kwana biyu koda cuta zata kasheta ita da d'anta kuwa, ga rashin wadatasu da yake yi, aikinta shi ne gatanta (Da yake tayi Karatu mai zarfi har digiri) amman tana lalla6a aurenta domin ta jima bata sami yin saba. Duk da maganganun Maryam sun shigi Ma'u amman kishi ya rufe mata ido tace ta kyaleta, Sai ta rok'eta ko Massage ne ta yiwa 'yan Gidansu ta sanar da su inda take don hankalinsu ya kwanta, sai Ma'u tace ashe tana fatan Ahmad ya dawo mata ma ke nan? Haka suka dinga tata6uza har dare yayi. Sai dai wani abu da yake bai wa Maryam shi ne, tsawon yinin wannan Rana Ma'u tana kallon huton Ahmad Mijinta a cikin wayarta da ta sanya sabon layi, abin sai ya bai wa Maryam dariya. Wajen k'afe gama na dare aka fara buga K'ofar gidan da yake Gida ne irin na k'ananan masu rufin Asiri, babu Maigadi. Da sauri Maryam ta d'auki Wayarta tace, "a k'araso? yauwa gani nan zuwa. Ta nufi Kofa, sam Ma'u bata kawo komai a ranta ba. Tana kwance akan Kujera ta rintse idonta har suka turo K'ofa suka shigo. K'amshin Turaren da taji ne ya sanyata bud'e ido da sauri, Turaren Ahmad daya ne, tun yana talakansa har zuwa yanzu da yayi kudi, don haka ko cikin Bacci ba zai 6ace mata ba. Yana tsaye jikin Kofa idonshi yayi jajir! kamar Gauta, duk yayi bak'i yarame, yini daya tal! Bak'in ciki ya cika Ma'u, ta kalli Maryam da tsananin takaici da harara. Maryam tace, Kiyi hak'uri Ma'u, idan har na bar Mijinki da iyayenki cikin damuwa bayan na san halin da kike ciki ban yi musu adalci ba, ban kuma cika masoyiyarki ta gsky ba. Ma'u ta mik'e a fusace ta nufi K'ofar fita, amman Ahmad ya cafkota ya matseta tsam a jikinsa, ta dinga fisge-fisge da k'ok'arin k'wacewa amma ta kasa, sai ta fash da kuka tana fad'in, Me ya sanya ka biyoni, nace bana son aurenka, kaje ka zauna da 'yar uwarka. jininka, ka barni na tafi dom Allah Yaya! Ka tafi Yaya!!" Tana magana tana kukka, amman tana rik'e gam a jikinsa ya ki sakinta. Sai da tayi mai isarta tayi shiru tana shesshek'ar kuka, Maryam tana tsaye tana kallon ikon Allah, soyayyar Ma'u da Ahmad na burgeta. Cikin sanyin murya Ahmad ya fara magana, Wallahi Ma'u da Maryam bta sanar dani kina gidanta ba da babu abnda zai hana zuciyata bugawa, tun daga lokacin dana gano baki tare dani ban huta ba, ban sha ruwa ko mukurwa goda ba, ban ci abici ko loma daya ba, Na gode kwarai da gaske, Allah Ya bar zumunci. Ya dauko Bandir d'in Kudi da bai san adadinsu ba ya bata ta amsa da zumud'i tana godiya, don daman wata yayi nisa bata da kud'i, kuma komai nata ya kare. Har gaban Mota Maryam ta rakasu, sai da taga tafiyarsu sannan ta juya ta nufi gida. Bayan ta kulle gidan a ranta tana cike da sha'awar soyayyar Ma'u da Mijinta Ahmad su dai kam basu yi sa'ar aure ba sam! A can hotel d'in Ahmad ya dinga lalla6a Ma'u da k'yar ta yarda zata yi wanka tace amman ba zatayi tare da shi ba, dole ya kyaleta. Tana daga Ban'Dakin taji kira ya shigo Wayarshi, don bai jima da kunna Wayar ba, sai ta jiyoshi yana "Eh na ganta...!!" Ban san sanda zamu dawo ba gaskiya....Sai da safe...!!" Daga yanda yayi maganar ta san da Nana yake, sai taji tausayin Nanan ya kamata tana bin Namiji yana mata yanga. Shi kuma haushin Nana yake ji yanzu don yana ganin kamar itace ta janyo masa duk wannan matsalar ma. A6angaren nana har sai da tayi hawayen takaici. Duk da Ahmad yaso samun wani abun a wajen Ma'unsa amma sai yaga ta had'e rai ta kwanta a Falo ma, dole ya k'yaleta. Washe gari da safe suka wuce Kano. Nana taji dad'in ganinsu taji dad'i, tay murna, ya had'u guri d'aya yayi musu nasiha da rok'on arzik'insu su zauna lafya. A gurin ne Ma'u tace ta bai wa Nana kwananta na Wata guda, Ahmad bai ji dad'in haka ba, amman babu yanda ya iya tunda lalla6ata yake yi. Ita kuwa Nana dad'i ne ya kamata har farin ciki ya bayyana akan fuskarta. Cikin wannan Watan Ahmad ya shiga tsananin damuwa da tashin hankali, ya yin da Nana ta more Amarcinta yanda taso. Mijinta ya d'ebe mata dukkan damuwa da kewa. ita kuwa Ma'un da wannan damar tayi amfani gurin neman NAFISA LILI 'YAR NIJAR ta harhad'a mata Magunguna na gyaran jiki, wato MAI DA TSOHUWA YARINY! Ta dinga Sha da Tsarki dana Turare. Cikin wannan lokacin ita kanta ta san ta sauya, don haka Ahmad idan ya ganta kamar ya cinyeta, Don akwai sanda ya gaza hak'uri ya matseta a d'aki suka dinga rikici tace wallah ta d'auki alk'awarin bazata ci amanar nana ba sai dai suje gabanta ya gaya mata shi ne yace sai ta karya, abinda ta san ba zai iya ba. Haka dole ya hak'ura ya kyaleta don ba yai iya yin Raping d'in Matarsa ba, don yana matse k'warai da gaske, dole ga nana ya kai bukatarsa.

5 November 2015 at 10:51 · Public Save · More Like React Comment Share Like37 Write a comment...

· Shuraihat Ummu Ammar da kyau ma'u but nana kina bani tausayi nd i love u oll!! Like · React · Reply · More · 16 Oct 2019 Rahmat Mums Tnks Like · React · Reply · More · 15 Aug 2018 Safiyya Hussain INA YINKI MA,U Like · React · Reply · More · 22 May 2019 Habibu Abubakar TNX.PLS LETS GO AHEAD Like · React · Reply · More · 18 Oct 2018 Firdaus Feedy Paradise Tnx Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Hafseeyat Hafseeyat Abubakar Namadi Dan allah acigaba allah qara hazaqa Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Umar Sg Asma'u Aci gaba pls Like · React · Reply · More · 9 Nov 2015 Umar Dahiru tnx Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Bakoji Lamara Misau Gud Like · React · Reply · More · 5 Nov 2015 Hafsat Ibrahim Garba Tanx Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 View more comments… Free Mode See Photos Facebook logo Go To Home Jamila Umar Tanko Books DAME AKE ADO 4**23

Dole ga nana ya kai buk'atarsa. Wannan ya yiwa Nana dad'i, wannan abu da ma'un tayi mata ya sanya take girmamata k'warai da gaske, sannan ta rik'eta kamar 'yar uwa, za a gaisa ayi wasa da dariya dai-dai gwargwado. Ammam ranar da Ahmad zai koma 'Dakin Ma'u Nana ta raina kanta ganin yanda yake ta zumud'i da rawar k'afa har taji Kishi ya rufeta a ranta tace sai kace ba gurin tsohuwa zai je ba. Tun daga iri rigar baccin da Ma'u ta sanya ta tsokanoshi ya dinga binta da kallo tana wani kwarkwasa da yanga har dai ya gaji ya janyota yana fad'in, "Yarinya wallah baki isa haukatani ba. Ta fashe da dariya don ta gano ya shiga tarkonta.Ranar kam saida ta raina kanta don a daren nan saida ya fanshe watanshi guda, musamman da yaji ta kamar ba Ma'unshi ba ta koma masa wata 'yar Budurwa kamar daren Amarcinsu. Wannan daren kam sun k'arar da shi gurin nunuwa juna yanda suka yi rashin juna. AHMAD ya gama gano yanayin Matansa, don haka yaci Maganin zama da kowacce dai-dai halinta. Ita dai Nana tana da tsananin buk'ata, don haka kafin girkinta ya fita sai ta isheshi, ita kuma Ma'u shi ne yake da tsananin buk'atarta saboda gyara da kuma yanayin halintarta, don haka har Nana ta ganoshi dole ran Girkin Ma'u d'okin yake yi da zumud'i, ita kanta Ma'u ta gano hakan, sai dai yana iyakacin k'ok'arinsa gurin ganin ya kamanta gsky da adalci a tsakaninsu, sai dai bai isa ya 6oye soyayyar ma'u ba, duk da itama Nana yana bata wani matsayi na ita ce jininsa, 'yar uwarsa da yake sun fahimci juna sai suka zauna lfya. Cikin shekarar ne duk Allah Ya albarkacesu da smun juna biyu, tsakaninsu wata guda ne kacal, Nana ce tafara haihuwar k'aton Namiji yaci sunan ABDULLAHI (Mujahid), Yaron da yaga soyaya da gata gurin dangin 'Yam Leman. Sai kuma Mau da ta kara haifo Mace. Itama ta sami gata, Ahmad dai shi ne mutumin da ya karya alk'adarin canfin danginsu na haihuwar d'a d'ya ko biyu, sai gashi da biyar cur! wannan ya sanya iyayensa jin dad'i. Adalci da Ahmad yayi a Gidansa da ya kwantarwa da Ma'u hankali shi ne hana Nana yin aiki ya ce shi ya dace ya nemo, duk da Nana ta damu da farko, rigima har gurin Babanta, amman da bata sami goyon baya gurin Iyayenta ba dole ta hak'ura, don Babanta yace ita kanta Mahaifiyarta digiri biyu gareta, kuma saboda k'warewarta a makaranta suka had'u suka yi aure, amman bata aiki saboda su Family d'insu suna da tsananin kishi, wanda tayi a baya ma Allah Ya amfana. Hakan ne ya sanyayar mata da guiwa, Ahmad ne yayi k'ok'arin k'ulla auren Mahaifinsa da Hajiya Amina don Mijinta shekaru biyu ke nan da rasuwarshi. Hakan ya yiwa kowa dadi Musamman kakarshi data damu yayi aure. Ita dai nana tun daga haihuwa 1 shiru babu k'ari da yake itama jinin iyalin ne suke ta6ata. GAME DA UMMI kam a yanzu ta yarda Ahmad yafi karfinta da ta gano matsayinshi dole ta samarwa kanta lafya, amman Iyayenta sun yi da sun sani da takaici, musaman da Mahaifin nata ya gano mahaifin Ahmad tsohon Ubangidansa ne, shi ke bashi kaya kafin kaninsa ya cigaba da bashi. wata rana kafin tayi aure ta hadu da Ahmad a Super Market ta gaya masa shi kadai take so amman ta hakura da shi zata auri wani ta bashi tausauyi kwarai da gaske, sai dai ya san bai isa ya karawa Ma'u kishiya ba, sai ya amshi lambar Accunt dinta ya tura mata kudi masu yawa wanda dasu ne tayi komai na auremta. WATA RANA sunje Gidansu da yamma ana ta hira sai suka jiyo kuka a harabar gidan, suka fito da sauri dasu Umma dasu Ma'un da Yaya Auwal da sauransu da yake duk ranar Lahadi da yamma annan ake hake had'uwa ayi ta hira. Lami suka gani dawata k'armasashiyar Mata kamar Fatalwa, Matar ta fadi Lami na kokarin tashinta tana kuka, ta lalla6a ta tasheta ta rungume a jikinta tana takawa da kyar! har ta isa kusa dasu ana tsaye cirko-cirko. Mal. Sulaiman ne yace, Lami wace ce kuma wannan? Cikin kuka Lami tace, "Yaya Raliya ce! Kusan Wata hud'u ke nan da aka kawota da cuta mai karya garkuwar jiki (H.I.V) dukkan abinda nake da shi ya k'are gurin Magani, kullun Mahaifinta idan zai zo gurinka sai nace ya gaya maka sai yace a'a shi ba zai fad'a maka ba, shi ne ni kuma da naga kamar zata mutu ne na kwasota tafiya bata iya yi don ku taimaka mata. Yaya Auwal yace, Raliya ce wannan Lami Subuhanallah!" Kowa ya tsorata da ganin yanda Raliya ta koma Yaya Auwal yace a kaita Asibitinshi zai yi mata komai kyauta, shi kuma Ahmad ya basu Kud'i mai yawa yace kuma duk k'arshen Wata ta dinga zuwa gurin Ma'u tana amsar Kud'i. Raliya da Lami suka fashe da kuka. Umma tace "Ato, duniya ke nan, tafi duk yanda ka d'auketa, sakayya ce take zuwar muku. Suka lalli juna da mamaki. TAMMAT BIHAMDILLAH!.

Surayya

6 November 2015 at 12:10 · Public Save · More Like React Comment Share Like35 Write a comment...

· Saihanatu Umar Umar Mun gode sosai Like · React · Reply · More · 6 Mar 2019 Adama Abdulkarim Kiyawa To alhmdllh mungode kwarai da gaske Allah ya kara daukaka da basira ubangiji yayi jagora Allah ya saka da alheri masha Allah Like · React · Reply · More · 2 Sep 2018 Sa'adeeyer Zarah Muna godia. Kuma muna jin dadin shi ... Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Muhd Suhunun Muhd Tank Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Maryam Abdul tnx Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Rahama Adamu Allah ya taimaka Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Bakura Sheriff Kayima allah yabadasa,a Like · React · Reply · More · 11 Nov 2015 Aisha Saleh Aliyu TNX Like · React · Reply · More · 6 Nov 2015 Zaynarb Abdullahi tnx Like · React · Reply · More · 11 Nov 2015 Amirah Muh'd Tnx sury allah yabar zumunci Like · React · Reply · More · 7 Nov 2015 View more comments…

End of current loaded text.