💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*
*🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
_Sabuwar Marubuciya, mai tafe da sabon salo💫_
*Abban Sojoji part 2*
*EPISODE 1*
Meaning Of Name *AMANI* means *wish* arabic name ne na mata🌹ina faÉ—in ma'anarsu ne saboda masu tambaya, sunaye ne masu kyau mutun zai iya amfani dashi in yana so wa baby girl É—insaðŸ˜
Ruwan sama ake yi sosai garin, yanayin yayi wani irin daɗin gaske, ga wata irin ni'imtacciyar iska wadacciyar da ta gauraye ko'ina, wurin ƙarfe 5 na marece ne amma sai kayi tunanin dare ne sosai saboda Lullumin da garin yayi, a wannan yanayin kowa na ƙumshe a bedroom ɗinsa saman gadonsa, lullu6e da bargo, baka jin hayaniyar komai ko'ina tsit a cikin gidan 😊
zaune suke acikin mota suna tattaunawa su biyu, Hafsat ce tare da wata Hamshaƙiyar mata wadda bansanta ba, jikinta na sanye da tsadadden leshi Ash colour, fara ce kana ganinta kasan taji hutu Over ya zauna mata, ita ce a mazaunin driver yayin da hafsat ɗin ke gefen ta suna tattauna wa, Hafsat ta natsu tana sauraronta " Naci sa'a da nasamu address ɗinki kuma na same ki cikin sauƙi, kuma ina fata zaki taimaka mun wurin cimma burina,' matar ta faɗi tana kallonta, Hafsat tace "ina sauraronki me kike so inyi miki ne "? Murmushi matar tasaki kafin tace "Kafin na faɗa miki abunda nakeso, pls ina so ki fara bani acct number ɗinki," Bin ta da kallo hafsat tayi cikin mamakin jin abunda matar tace, Amma batayi musu ba, ta shiga karanto mata numbar acct ɗin, ita kuma tana kwashe wa a wayarta dake hannunta, Bata jima da gama karanta mata numbar ba sai ga Alert ya shigo a wayarta ƙirrrr! Cikin sauri hafsat tasa hannu ta ɗauki ƴar purse ɗinta dake asaman Laps ɗinta ajiye, ta zugeta ta ciro wayar jiki na rawa ta duba, gabanta ne taji ya faɗi rass !! Ganin Alert na 6millions abun kamar a mafarki take ganinsa Cikin tsananin mamaki ta ɗago ta kalli matar tare da cewa "Wannan fa? Na menene? dariya matar tayi kafin tace " akwai wasu tagwayen Yara da Marshal Omar ya kawo gidan nan, Sunan su Hosana da Jahad,' Jin sunan da ta ambata yasa hafsat kallonta cikin mamaki,. Taci gaba da cewa "Ba wani aiki bane mai wahala, so nake subar gidan nan ! Suyi nesa da Marshal Omar..........' Cike da mamaki hafsat ke kallonta , babban abunda ya ɗaure mata kai shine yadda akai tasan cewa Marshal Omar ya kawo yara acikin gidan,. Daker ta iya cewa "Saboda Me za'ae hakan? "Saboda basu da amfani," matar ta bata amsa a taƙaice, Shiru hafsat tayi tana kallonta acikin zuciyarta tana Was wasi akanta, "Wacece ke? Taya akai kikasan sunan Tagwayen tare da kuma sunan Omer? "Ba buƙatar wannan, Kawai kiyi mun abunda nace in aikina yayi kyau nayi maki alƙwarin zan ninka miki abunda na baki har sau uku,
Hafsat tace "To shikenan ni zan wuce ciki sai kin jini"
Murmushi matar tasaki tare da cewa "sai mun sake haÉ—uwa," fito wa hafsat tayi daga Motar ta rufe mata sannan ta wuce cikin gidan da hanzari saboda ruwan dake sauka ajikinta,
Yayin da ita kuma Matar taja motarta ta fuce daga gidan fuskarta É—auke da murmushin nasara,
tana shiga cikin babban falon ba kowa kai tsaye bedroom ɗinta ta wuce, cire kayan jikinta tayi shaf shaf ta canza izuwa riga da wando, ta ɗaure gashin kanta a baya, tana tsaye gaban Mirror tana tunanin maganar Matar nan data kawo mata ziyara sai ga Aunty Babba ta faɗo ɗakin tana faɗin "Hafsat wacece waccan matar da tazo wurinki yanzu"? Juyowa hafsat tayi tana kallonta tace "Nima bansanta ba address ɗina aka mata shine tazo da buƙatarta," "Wace irin buƙata kenan"? Aunty babba ta tambaya tana kallonta, Hafsat tace "Tayi mun magana akan cewa tana so in raba twins ɗincan da Omar ma'ana subar gidan nan gaba ɗaya, Suyi nesa dashi" tsoki aunty babba taja tare da cewa "Ita kuma wacece ita isasshiya? halan Omar take so ne shiyasa ta biyo ta wurinki?. "Bana tunanin hakan, Nafi tunanin Tasan Yaran ne shiyasa take son azubar dasu," "To ke kuma kin amince da buƙatarta kenan"? Murmushi hafsar tasaki tare da cewa "eh mommy na amince da hakan, saboda anan take ta bani miliyan shida kuma tace muddin aikinta yaci ka zata ninkamin abunda tabani ynx," tuni aunty babba ta haɗe fuska rai a6ace tace "Amma ke shashashar ina ce? Kawai daga zuwan mata sai ki amince mata da buƙatarta? matar nan fa Omar take so shiyasa takeson a salwantar mata dasu," "Koma dai menene Mommy ni bazan bari kuɗin nan su wuce ni ba, saboda ina cikin buƙatarsu, daddy baya sakarmun kuɗi yadda ya dace ke kuma tanadin ki na zuwa wurin bokane kema fa bakya bani ko sisi Burinki akan hayaam da Abrah ne," . Matsawa Aunty babba tayi kusa da ita tana cewa "Hafsat Anya kina cikin hayyacin ki kuwa? Ni kike faɗama haka"? "Na faɗi wani abune daba dai dai ba? ta tambaya tana kallon mommyn nata, Ido cikin Ido Sassauta Murya Aunty babba tayi a ƙoƙarinta nata fahimtar da hafsat tace "duk wannan tanadin da nake saboda kanmu ne fa ! Ƙaruwar mu ce, in har naci nasara akan burina Hayaam tasamu RAFAYET ita kuma Abra tasamu MARSHAL OMAR mune zamu ji daɗi, don haka am commanding u ki tattara kuɗin da tabaki ki mayar mata dasu yanzun nan !!!! ta faɗi a tsawace Dariya hafsat ta kwashe da ita hada tafa hannu bayan ta tsagaita tace "Mommy kenan !! nima fa lashe Money ce kamarki, bazan bari garabasar nan ta wuce ni ba!! Akace da arziƙi a gidan wasu ƙwara agidanku, kai agidan nakuma kwara a ɗakinku, a ɗakinku ɗin ma ya faɗo akan ka, don haka ni baxan mayar mata da kuɗinta ba!!!!!!!!! Gaba ɗaya hankalin aunty babba ya tashi don alamu sun nuna cewa Hafsat fa kamar bata cikin hayyacin ta, cikin ruɗi tace "Hafsat anya kina cikin Hayyacinki kuwa"? Shu'umin murmushi hafsat tasaki sannan tace "Kwarai kuwa! nice dae ƴarki Hafsat ɗiyar general ishaq, jika ga Abban sojoji" Jinjina kai aunty babba tayi tabbas an samu matsala, domin kuwa tasan Hafsat bazata ta6a fasa abunda tayi niya ba, Huci kawai take yi tana jinjina kanta a ƙarshe ta fuce daga ɗakin, Duk wannan suratan da Hafsat su kayi da aunty babba a kunnan Hosana wadda ke la6e a ƙopan ɗakin, jin Takon tafiyar Aunty babba yasa ta gudu izuwa cikin store ɗin da suke, "Ina kika je hosana bakya jin magana ko? salon sai sun ganki? Mun samu yau sun ƙyale mu basuyi mana komai ba, Jahad ce ke wannan maganar wadda ke atsaye tana kallon hosana, Murya na rawa hosana tace "Jahad naji abunda su Hafsat ke cewa ita da Momynta," "Me suke cewa ne"? Ta tambaya tare da matsawa kusa da Hosanar don taji dakyau, Hosana ta kora mata bayani tun daga farko har ƙarshe, Jahad ta jinjina kai tare da cewa "Ashe buri yayi kama da mutun, shiyasa ta tsane mu kenan saboda tana tunanin cewa Omar zai iya son ɗaya daga cikinmu, ran nan tace mun batason mune saboda mun shiga tsakaninta da abun harin ta, Yanzu nagane inda ta dosa, To amma wacece matar da hafsat ta haɗu da ita yau? Wadda ke son A zubar mata damu!? "Ni inaji araina jahad so suke su rabamu da ƴa'ƴa Omar kawai," hosana ce tayi maganar ido cike tab da kwalla don bata son duk wani abu yanzu dazai rabasu da Omar, "Insha Allah burinsu bazai ta6a cika ba Hosana, baza su iya raba mu ba da yaya omar ɗinmu," tayi maganar tare da janyo hosana suka rungume junan su __________________________________________
Tuni sun kammala aikin su na dinner, har sun kammala jerawa a dining Kowa ya bama cikinsa an ware, yanzu gidan ya ragu ba laifi kasancewar tun week ɗin daya wuce aka tura mutun Huɗu Aiki, Irfan jabeer, khaleed da Fawan duk basa nan, yanzu wanda suka ragu Acikin gidan Haroon, twins, junaid, Sai Marshal Omar da Sgr duk da basu cika zama cikin gidan ba suma, always working saboda suna bada gudummuwa sosai shiyasa koda yaushe suna headquater ɗinsu don ana buƙatarsu sosai game da insecurity ɗin qasar tamu, kasancewarsu kwararrune a6angaren aikin soja dama sun kasance international Armies, kowace ƙasa aduniya suna bada gudummuwarsu wurin kame tantirai sune maganin ƴan Iska, shiyasa sunansu ya shahara a faɗin duniya duk inda suka je, ansansu girmamasu ake gani kamar kamar me (Tiger da Lion) Kenan ba wasa 😇😇😇
SEHRISH Shiga bedroom É—inta tayi Wurin isha prayer, duk ta rame kamar ba Reeshi ba, alwala ta É—aure a toilet, ta shimfiÉ—a sallaya, ta gabatar da salla, bayan ta kammala ta naÉ—e hijab da sallayar ta tura a wardrobe É—inta, komai nata a slow take yinshi saboda rashin kwarin jikinta da fargabar da take fama dashi na Haroon,
Haye wa tayi saman gadonta tare da janyo pillow ta rungume tunani kala kala a ranta, hawaye ne suka soma gangarowa daga idonta sbd tuna yadda haroon ke ta6a jikinta, hannu tasa tana share su, daga bisa ni tayi lamo tana tunanin duniya, Tana cikin wannan halin taji an kwankwasa ƙofa, shiru tayi bata Yi magana ba cike da tsoron waye ke mata knocking, ji tayi an sake buga ƙopar muryar na rawa tace "wanene"? Muryar junaid taji yana cewa "Sehrish ni ne," Ajiyar zuciya tasaki jiki na rawa ta sauko tare da karasawa wurin kopar ta buɗe, Gabanta ne yayi mugun faɗuwa ganin haroon hankali tashe tace "Kaineeee !!!!" a tsorace tayi maganar jikinta na rawa,. Fashewe da dariya haroon yayi tare da wuce ta yashi ga ciki yana cewa "ƴar shila ni ne, ae nasan bazaki buɗe ba shiyasa nayi maki muryar junaid don na lura kuna good time dashi,' juyowa tayi tana bin shi da kallo a razane,. "Me ya kawo ka"!? "Abunda yasa ba kawo ni, Yau nazo ne ayi ta taƙare, Haƙƙina nake son ki bani," Cikin shessheƙar kuka sehrish tace "Me kake nufi wai !!! Wani haƙƙi ka ke dashi akaina? Dan Allah kabarni nayi rayuwata cikin salama !! Ka rabu dani mana !! ta6e baki haroon yayi tare da cewa "Na amince zan rabu dake, amma bisa sharaɗi ɗaya"? Ya faɗi yana kallonta fuska a ɗaure, a lokacin tadawo tsaye front of side drawer ɗinta tana facing ɗinshi, Gabanta na faɗuwa tace "Menene shi"? Cikin sanyin murya tayi maganar Haroon yace "Your Virgin!! shine abunda nake so,and if u do so i wll be out of ur life" Fashewa da kuka sehrish tayi cikin tsananin jin ƙunci da raɗaɗi aranta, tuni zufa tagama wanko mata kamar wadda aka tsamo daga cikin ruwa, tsanar haroon take ji kamar kamar me, tarasa amsar da zata bashi sai faman kerma take, A tsawace haroon yace "Ke !!! Ki amsa mun kin amince ko baki amince ba"!? A Firgice tace "Na'amince" ita kanta batasan ta bashi amsar ba saboda tsoratar da tayi da tsawarsa, Wani irin shu'umin murmushi haroon yasaki, bin shi da kallo tayi ganin yasa hannu yana zare belt ɗin wandonsa, tuni ta runtse ido ganin gashin jikin shi, bakomai ya faɗo mata arai ba fa ce Sgr shine namijin da take so tafara kasancewa dashi arayuwarta bata buƙatar wani namiji in ba shi ba, shi take so ta mallakawa komai nata muddin ta mallake sa, Jiki na rawa ta zura hannunta ta baya, taci sa'ar damƙar fititalar Kwan dake gefen gadonta, kafin haroon ya ɗago ta daddage da iya ƙarfin ta na ƙarshe ta ɗago da fitilar dake hannunta ta kwaɗa masa a tsakiyar kai !!!!! Ji kake KWASSS !!! A razane haroon ya ɗago jin saukar fitilar kafin yayi wani yunƙuri tuni Sehrish tabi ta gefensa ta watsa da gudu sai cikin toilet ta datse ƙopa sosai, ta sulale daga jikin ƙopan zuƙunne tana kuka don tasan dole haroon ya ɗauki matakin abunda tayi masa, Ba ƙaramin buguwa haroon yayi ba, don wurin harya fashe Ae kuwa rai a tsananin 6ace yace "Ke don ubanki ni kika fasa ma kai"? Sehrish dake acikin toilet murya cike da kuka tace "Ba dai ubana ba sai don Uban Mai zagi !! Fasiƙi ɗan iska insha Allah bazaka ta6a cin nasara akaina ba, sai Allah ya nuna maka iyakarka, wulaƙantacce kawai ƙazami mai warin baki," Tuni idon haroon sunyi jawur kamar garwashin wuta, ransa yayi mugun 6aci bai ta6a tunanin yarinyar zata iya mayar masa da martani ba, amma sai gashi yau ta zage shi tass, "Bazan ƙyaleki ba, sai na wulaƙanta rayuwarki ba dai kina acikin gidan nan ba kuma zaki fito ba, zamu haɗu ne wlh," Ya faɗi tare da tunkarar hanyar fita yana mayar da belt ɗin wandonsa daya fara cirewa,.(ba'aci nasara😂) Sehrish batayi shiru da bakin ta ba taci gaba da cewa " Ta Allah bata ka ba wlh !! Mugu azzalumi mummuna kawai, da wasu idanuwan ka kamar na Mujiya ni ina kokwanton Cewa anya kai Jinin Abban sojoji ne !! Sbd duk ƴa'ƴansa ba Fasiƙi irinka," Jinjina kai haroon yayi kawai yana huci, ya tura ƙopar ɗakin ya fuce,
Wani sabon kukan ta sake fashewa dashi, tana faɗin "wayyo Allah na nasan haroon baxai ƙyale ni ba, nashiga uku........' Jiki na rawa ta miƙe ta nufi wurin bathroom cabinet ɗinta, akwai wasu Chemicals dake ajiye cikin toilet ɗin masu illah ga jikin mutun tamkar poison suke, ta riga ta yankewa kanta shawarar kwara ta kashe kanta ta huta da fitinar haroon, Hannunta har kerma yake yi, wata ƙaramar roba ta ɗauko mai ɗauke da chemical ɗin, buɗe murfin tayi yayin da idonta ke zubar da hayawe, bakowa ya faɗo mata arai ba face Hosana Jahad, junaid, Aunty azmee uwa uba Burin ranta, yanzu shikenan duk zata rasa su? Zata mutu tabarsu? Runtse idonta tayi aranta tana faɗin "bani da wata manufa face wannan, kuyi haƙuri ku yafe mun bazan Iya cigaba da rayuwa a wannan duniyar ba mai cike da tashin hankali, ban ta6a cutar da kowa ba, amma gashi wani nason cutar da rayuwata ....................." Cikin sauri ta shiga zazzaga hodar abakinta
A dai dai lokacin Motocin Sgr da marshal Omar suka shigo cikin gidan atare jiniyarsu ta karaɗe ko'ina har cikin kunnan Sehrish Zuciyarta ce taji tayi wani irin bugu, nan take kuma zuciyarta tace "Yanzu kin amince ki mutu baki cika burinki ba!? ke fa musulma ce ! Kin kuma son hukuncin wanda ya kashe kansa da gangan!! Runtse idonta tayi hawaye na zuba, fuskar sgr kawai take tunawa da fuskar su hosana da jahad, "Ina son sake sashi a idona," ta furta da wani irin sound, nan take tayi wurgi da robar chemical ɗin dake hannunta, cikin hanzari ta shiga amayar da wanda ke bakinta agaban basin, fanfo ta kunna tashiga kuskure bakinta da hanzari ta kora aman, sannan ta wanke face ɗinta ta fito, tana tafiya zuciyarta na ƙara bata ƙwarin guiwa da cewa "Saboda wani shashasha zaki halaka kan ki, share hawayenki sehrish kina da damar rayuwa, wani banza bai isa ya tarwatsa miki burinki ba," Gyara jikinta ta shiga yi saboda tana son zuwa kai mishi dinner ɗinshi shi da Omar don ta son da yunwa suka dawo, duk da tana tsoran kada suci karo da haroon a fitarta, dama riga da wando ne ajikinta, gashin bakinta kawai ta manna, ta gyara hular kanta da mayafin da take naɗe hular dashi, bayan ta kammala ta buɗe kopan cikin fargabar ta fuce,. Ko'ina haske fauuu gidan cikin sanɗa ta wuce kitchen taji sanyi aranta ganin babu kowa, Cikin hanzari ta shirya ma Omar nasa a tray, a palor ɗinsa takai masa babu kowa aciki alamar yana cikin bedroom ɗinsa, ajiye masa kawai tayi ta fuce, izuwa kitchen ta sake shirya wani a tray sannan ta wuce upstairs part ɗin BABBAN YAYA
Haryanzu jikinta kerma yake, kuma bata fasa maganar shan poison ɗin nan ba, burinta ta sanya Sgr a idonta 4 the last time before tabar duniyar, Baiwar Allah Babu kowa a palor ɗinsa tsit kake ji sai ƙamshin dake tashi, shiga ciki tayi ta ajiye masa a saman table ɗinsa, Tsayawa tayi tana faman sauke ajiyar zuciya yayin da idonta ke cike taf da hawaye, kamar daga sama taji muryarsa ta cikin bedroom ɗinsa yana faɗin "who's There"? Runtse idonta tayi saboda jin sanyayyiyar muryarsa, daker ta dai daita natsuwarta tace "Tukur ne mai aiki," Voice ɗinsa tasake ji yace "Come In! i wanna see YOU Right now," zaro ido sehrish tayi jin abunda yace wato ta shigo ciki yana som ganinta 😳😳😳😳😳
Dake ta dai dai ta natsuwarta, ta tafi izuwa cikin bedroom ɗinsa kamar yarda ya umarta ta shiga da sallama"Assalamu alaikum" "Wa'alaikum salam" ya amsa mata, tsaye yake agaban mirror jikinsa sanye da sleeping dress riga da wando Milk colour masu ɗigon² baƙi ajikinsu ba ƙaramin kyau su kayi mishi ba, turarurruka yake ta fesa ma jikinsa, Sam tagaza janye idonta akan shi daker ta iya cewa "barka da dare" ya amsa mata da "Yawwa" sannan ta ƙara da cewa "Gani" Hannu yakai ya ɗauki kalbar turaren SHUMUKH ya feshe shi sannan ya mayar ya ɗauki wani turaren na Jar yana fesawa, mutun ne mai tsananin son ƙamshi shiyasa baya gajiya da bin jikinsa da turare, Shiru sehrish tayi zuciyarta na ɗar ɗar, kusan 15 minsa sannan Boss Man ɗin yace "Ni zan zo ne"? Ya tambaya yana jiran amsa, Cikin sauri sehrish ta ƙarasa hankali atashe ta tsaya daga bayansa jikinta na rawa, Cikin natsuwa yaso ma magana" Wacece ke"? Waro ido waje sehrish tayi jin abunda yace murya na rawa tace "Ni.....mai.....aiki...ne ...." a wani irin slow sgr ya juyo kai tsaye ya tunkare ta gadan gadan, a tsorace sehrish ke ja da baya tana kallonsa tuni zufa ta gama wanko mata sharkaf a jikinta, Sam idonsa basa a kanta ƙasa suke, har sai da suka ƙurewa bangon gaba ɗaya, yarfa hannu sehrish ta shiga yi a tsananin tsorace take karanto addu'o'in da duk suka zo mata abakinta, kuma abayyane take yi saboda tsaban ruɗi tuni ƴan hanjin cikinta sun motsa, gaba ɗaya jikinta rawa yake yi kamar wadda sanyi yakama, Hannunsa yasa ya daki wall ɗin data ke manne ajikinsa ya aza hannun anan jikin bangon ya dafe sannan yace "ƙarya ke bana so arayuwata, am gonna ask u some questions idan aka min ƙarya za'a fuskanci matsala," Ya faɗi yayin da idonsa ke a lumshe tamkar a datse suke ba don komai ba sai don gudun kada mai aikin ya Sume a ƙaro na biyu saboda launin ƙwayar idonsa dake razanar da shi, . Kallon shi kawai take yi zuciyarta na bugawa da ƙarfi, daker take haɗiye yawu ga wani fitsari daya matse ta tunda taji ya ambace ta da mace tasan cewa ya gano ta kenan, "maca ce ko Namiji"? ya tambaya yana jiran amsa, Shiru tayi tana tunanin amsar da zata bashi, muddin tamasa ƙarya wannan ba ƙaramin shaqa zata sha ba, Wannan shirun da tayi masa shiya fusata shi, buɗe Blue eyes ɗinsa yayi duka akanta , ta firgita sosai amma sam ta sanƙare ta gaza motsi da alama suman tsaye tayi Hannunsa yasa ya damƙi hular kan sehrish yayi wurgi da ita tare da mayafin duka, nan take sumar kanta tasoma warwarowa tana saukowa saman kafaɗarta, kyakkyawan sumar kanta mai matuƙan kyan gaske ga laushi, mayar da hannunsa yayi saman gashin bakin da take sawa ya cire shi shima, nan take ainihin kyakkwar fuskar reesh ta bayyana a matsayim mace 😊😉 sam fa bata motsi idonta sun kakkafe sun ƙame, kamar wata saƙago haka tayi, jinjina kai sgr yayi maganar Adams ta tabbata, yayi mamakin ganin yarinya ƙarama kamar wannan da ƙarfin halin Yin shigar Maza tazo gidan sojoji aiki, ko nawa aka biyata don tayi hakan? Ya tambaya aransa, sam shi baya tunanin ta haura 12years saboda ƙarantarta dayake gani agabansa Ko shouder ɗinsa tsayin sehrish bai kai ba, daga tsaye inda yake yana kallon tsakiyar kanta saboda ba ƙaramin tsayine dashi ba, kowa yazo gabansa kallon ƙarami yake masa, Janye hannunsa yayi daga jikin wall ɗin da sehrish take sannan yayi tattaki izuwa inda fridge ɗinsa yake, buɗewa yayi ya ɗauko bottle water mai sanyi sannan ya dawo inda take tsaye, ya buɗe murfin ya yayyafa mata, a wani irin firgice sehrish ta girgiza ta dawo in sense ɗinsa, sai faman zazzare kyawawan idanunta take, bin chest ɗinsa tayi da kallo izuwa face ɗinsa cikin tsoro, hannu tasa ta shafa sumar kanta gabanta ne ya faɗi jin wayam babu yar hularta, hankali tashe ta wurga idonta inda sgr yayi watsi dasu.........nan fa tashiga faɗin "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un dan Allah kayi haƙuri.....nashiga ukuna........' tana kuka tana magana , gaba ɗaya yayi mata rumfa tamkar Zaki haka take ganin sa agabanta 😳😳😳
Idonsa na kumshe yana sauraronta left hands ɗinsa na riƙe da bottle water ɗin, yayin da ɗayan hannun kuma ya mayar dashi jikin bangon ya dafa, sehrish kuma na agabansa suna fuskantar juna, "haɗiye wannan kukan bana so" cikin hanzari sehrish ta dakatar da kukan tashiga taitayinta, bakomai take kallo ba fa ce damtsen hannunsa, tunani kawai take yarda zai kai mata naushi tabbas tasan sai dai Uwarta ta haifi wata (Hafsat bature ana magana) 😂 Cikin natsuwa yasoma magana__________________________________
Abt payment 300 ne, still muna free pages ne wanda suka shirya 08103884440 sumin magana ðŸ‘💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*
*🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
_Sabuwar Marubuciya, mai tafe da sabon salo💫_
*Abban Sojoji part 2*
*EPISODE 2*
*💞LAFAZI WRITTERS ASSOCIATION*💞
Cikin natsuwa ya soma magana "tambaya biyu kawai Wacece ke? Kuma waya turo ki"? Cikin rawar murya sehrish tace "Ni ba kowa bace ba, kuma babu wanda ya turon.......'. Interrupting ɗinta yayi da cewa "ki mun magana a hankali don bana fahimta sosai," Gyara muryarta tayi sannan taci gaba da cewa "Sunana Sehrish, kuma ni babu wanda ya turo ni, banzo da nufin na cutar da kowa ba, aiki kawai nake don nasamu kuɗi........' buga wall ɗin da yayi yasata dakatawa a tsorace "Nace wa ya turo ki!!? Hankali atashe tace "Allah shine shaidata, wlh ni babu wanda ya turoni, banzo da nufin na cutar da kowa ba, ƴan uwana ne Basu lafiya an kwantar dasu asibiti ana buƙatar kuɗin aiki shine na nemi aiki gidan wata hajiya...............sehrish bata 6oye masa komai ba ta faɗa masa tass dalilin zuwanta da dalilin yin shigarta na maza batayi masa ƙarya ba ko kaɗan, ta ƙarasa masa labarin tana faman zubda hawaye tsoranta wane hukunci zaiyi mata don tasan watan Cin Ubanta ya tsaya, shiru su kayi na wani lokaci, kafin daga bisa ni Babban yayan yaja da baya ya juya
bedroom ɗinsa ya shige kafin daga bisa ni, ya fito hannunsa ɗauke da wayarsa wuri yasamu ya zauna saman sofa ɗin sannan yaba sehrish damar ta matso kusa, sai da tafara tattara hularta da mayafin da yayi watsi dasu, ta ruƙesu a hannunta sannan jiki asanyaye ta matsa inda yake kamar wadda tayiwa sarki ƙarya, jikinta sai faman kerma yake, yace "su nan su? da sunan state da sunan hospital da aka kwantar dasu? and the date!? Murya na rawa tace "Hosana Sayyad, da jahad sayyad an kwantar dasu a Fmc katsina........"
duka ta faɗa masa hada date ɗin da aka kwantar dasu duka don bata manta ba, danna wayar yashiga yi kafin daga bisani ya danna calling, ta soma ringing, nan take aka ɗaga wayar suka soma magana, Duk sehrish na tsaye tana kallonsa yadda yake speaking anatse, Bakowa ya kira ba face Babban Likita, dama already sai da yafara tura masa message na sunan yaran da bayanan dayake son sani sannan yakira, kuma anci sa'a On duty yake,' Tabbas yayi mamakin ganin kiran Surgeon general rafayet, kuma yayi mamakin jin sunan yaran da yakeson aduba mishi files ɗinsu, tabbas yasan yaran, waɗanda Omar ya taimaka daga wurin Police, ranshi ne ya bashi cewa may be Omar yasanar mishi game dasu ne that's why yake neman Information akansu , without wasting time Babban likita ya binciko masa files ɗinsu Hosana Da jahad na rashin lafiyarsu duka bayanan ya masa snaping dinsa ya tura masa ta whatsapp ɗinsa, bayan sun kammala phone ɗin, Sgr ya shiga whatsapp ɗinsa ya duba, sai ga Files ɗin yaran na rashin lafiyarsu raɗau da sunansu ajiki Hosana Sayyad Da Jahad Sayyad, Ajiyar zuciya yasaki yanzu ya shaida maganar Yarinyar duba time yayi dare yayi ga wani bacci daya ke ji gashi ko dinner ɗinsa bai cin ba, Ga yarinyar nan dake tsaye duk a tsorace don yana ganin yadda yatsun ƙafarta ke kerma, gyaran murya yayi sannan yace "You're not guilty of anything, the mistake you made shine shiga na maza after knowing that it is forbidden in Islam for a girl to dress like a male,' yayi maganar yana danna wayar hannunsa... Murya na rawa Sehrish tace "bazan ƙara ba........' Jinjina kansa yayi kafin yace"As from now i don't wanna see u wearing this dress again! u can go" ya bata Umarni ta tafi Wayyo Allah sam sehrish ta gaza rufe bakin ta don mamaki, kama hanyar fita tayi tana waiwayansa da kansa ya shiga saving dinner ɗinsa yana ci, Tsantsar farin ciki ne ya cika sehrish sam ta rasa inda zata tsoma ranta, ae tana fita daga part ɗinsa ta buga Wani uban tsalle na murna fuskar nan kamar wacce akayiwa Albishir da gidan Aljanna, watsa wa tayi da gudu gudu sauri sauri tana tattaka Stairs ɗin tana saukowa down a babban falon dama ba kowa nan fa tashiga rawar murna tana zagaye sofas ɗin dake a falon kamar wata yar baby, Duk wannan abun da take yi akan idon Sgr domin kuwa ya biyo bayanta ashe yana daga can Upstairs yana kallonta, don bai cika yarda da mutane ba shiyasa yayi following back ɗinta don yaga reaction ɗin da zata yi bayan da ta fita daga part ɗinsa, abunda yayi tsammani ba shi ya gani ba, zura hannayansa yayi cikin aljhun wandon baccinsa yana kallon Ikon Allah, Sam sehrish bata son babban yaya yana kallonta ba, ita kaɗai tasan farin cikin da take ciki, ta jima tana mamakin yarda Sgr ya kasance mai matuƙar sauƙin kai har haka a tunaninta zai bata horo mai tsanani daga nan akore ta kuma daga gidan, Nace "*Sehrish ba ke kaɗai ba hatta Hafsat bature da sauran makaranta labarin rayuwarki sunyi tsammanin hakan tabbas Surgeon general Rafayet ya bamu mamaki, haƙiƙa shi ɗin na daban ne*"😠Yanzu abunda ya rage wanda take yi ma fargaba shine sauran matasan gidan shin zasu amince a ranar da ta bayyana kanta a matsayin mace !? Uwa uba Abban su,kuma tuna wannan yasa jikinta yin sanyi, dakatawa tayi daga yin wasan da takeyi na zagaye gujerun babban falon, jiki a mace ta kama hanyar bedroom ɗinta, ranta ne ya bata cewa akwai mai kallonta, Cikin sauri ta juya ta kalli upstairs a time ɗin har sgr yabar wurin ya koma part ɗinsa Ganin wayam yasa ta sauke ajiyar zuciya,ba ɗakinta ta wuce ba ɗakin aunty azmee ta wuce don sam tagaza daina murna tafison ta sanar mata abunda yafaru yau ɗin nan da zafi zafinsa, Haryanzu hannunta na ruƙe da hularta da mayafin duka ta ƙanƙame su, tsayawa tayi a ƙopar ɗakin tana bubbugawa ,
Azmee dake zaune saman darduma tasha hijabi ajikinta ga qur'ani agabanta hannunta kuma na riƙe da Cazbaha sai faman gyangyaɗi take yi, jin bugun ƙopa yasata cewa "Wanene" sehrish dake tsaye a bakon ƙopan tace"Nice aunty azmee" Murmushi azmee tayi tare da cewa "Ashe bakiyi bacci ba," tayi maganar tare da tashi daga dardumar ta buɗe mata ƙopa, Shiga ciki sehrish tayi tana faman zabga murmushi, a ɗan ruɗe azmee ke kallonta bayan ta rufe ƙopan tace"Yau wata rana! Sehrish kece da Murmushi haka a fuskarki? Wane albishir ne akayi maki?Cos I forgot when last naga wannan annurin a face ɗinki" cikin mamaki azmee ke wannan maganar kafin ta mayar da idonta kan Hular sehrish dake ruƙe a hannunta ta kuma cewa "Ikon Allah yau kuma hularce da mayafin duka a hannu? Dariya kawai sehrish take yi daker ta tsagaita tace "Aunty azmeee abun mamaki! Abun farin ciki !" Cike da ɗoki azmee tace "menene shi? Nan sehrish ta shiga zayyana mata abunda ya faru tsakaninta da Babban yaya daga farko zuwa ƙarshe Baki washe azmee ta ɗaga hannunta sama tana cewa "Alhamdulillah ! Alhamdulillah godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala naji daɗin wannan lamarin sehrish domin kuwa Babban yaya shine nafi ji dama, gashi kuma cikin sauƙi ya amince wayyo Allah murna bansan inda zan sa kaina ba don daɗi" cike da jin daɗi azmee ke magana fuskarta a washe Sehrish tace "Amma aunty azmee su fa sauran kina ganin zasu amince in suka sani"? Ni ina tsoran ta yarda zan fara fitowa a matsayin mace cikin gidan nan," tayi maganar murya asanyaye tana kallon azmee Ƙarasawa azmee tayi ta dafa kafaɗarta sannan tace "Sehrish matsalarki tazo ƙarshe! tun da har babban yayansu ya amince ba ki da sauran damuwa, Abbansu ne kawai zamu jira muji ta bakinsa, yanzu abunda nake so dake kije kawai ki kwanta kiyi bacci zuwa gobe zamu ga yadda badaƙalar zata kaya idan matasan gidan nan suka ga tukur mai aikinsu a matsayin Mace lallai akwai tashin hankali, " azmee tayi maganar da dariya a fuskarta, sehrish kuwa dafe saitin zuciyarta tayi tana zazzare ido tace "Allah sa su amince suma," "Insha Allah" azmee tabata amasa afterwards suke yi sallama, sehrish ta koma bedroom ɗinta cike da zullumi haye wa tayi saman gadonta, ta janyo pillow ta rungume tana sakin murmushi tunawa da haɗuwarsu ta yau da babban yaya, Allah kenan a daren nan Haroon ya ƙuntata mata, har tayi addu'ar sai Allah ya nuna masa Iyakarsa akanta, to yanzu ga Iyakar tasa nan muddin sauran suka amince da ita kuwa, taci alwashin sai ta Ci mutuncin Haroon 😡👊 A fili tasoma magana " gajan haƙuri kenan Irin na ɗan adam, yanzu da na kashe kaina da shikenan nayiwa kaina, ashe Allah yana dab da kawomin sauƙi arayuwata," ta faɗi tana faman murmushi wani irin nishaɗi take ji ayau , ta kuma cewa "Anya ma zan iya bacci kuwa? gashi ina fargabar mai zai faru gobe? kwara kawai nayi Bacci na goben tayi saurin yi, AYI TA, Ta ƘARE kawai🙅, In jalasa jalasa 😂 in Zahaba Zahaba shine kawai 😅😂😹😹😹
tana gama faÉ—an hakan bacci yayi awon gaba da ita, kai kana ganin yadda reesh ke bacci kasan tana cikin kwanciyar hankali,
murmushi Hafsat Bature tayi tana kallonta wadda ke tsaye shigowarta kenan ta window tabiyo da suffar Farar Tantabara kasancewarta Aljanar sehrish, hannu tasa tajanyo bargo ta lullu6e sehrish dashi sannan ta 6ace 6aaat..............😇 ______________________________________
Kwance suke acikin store ɗin su biyu abunsu, kamar yadda Jahad ta saba yi musu dabara, na jera masu jarkoki su koma kamar single bed sai su kwanta suna facing ɗin junansu sam bacci yagaza ɗaukarsu zullumin su mai zai biyo ba? Wata alƙibla rayuwarsu zata fuskanta yanzu? "Jahad idan Aunty hafsat ta zubar damu ina kuma zamu dosa"? Hosana ta tambaya tana kallon jahad wadda ta zuba mata ido, Cikin sanyin murya tace "Nima kaina bansani ba hosana, ina tsoran hakan," ta faɗi zuciya a karye Hosana tace "Dama Allah ya ɗauke mu yakai mu duniyar sama ko? ko duniyar taurari inda ba mutane muyi rayuwarmu mu kaɗai tare da yaya Omar tunda kowa baison mu shi kaɗae ke son mu ko? Wannan maganar ta hosana tasa jahad fashe wa da dariya daga kwancen da suke ta rinƙa 6a66aka dariya kaman kamar me, Hosana ta ɗan 6ata fuska don ita bada wasa tayi maganar ba, Daker jahad ta jinkirta da dariyar tace "Sorry hosana dole nayi dariya mana, wa kika ta6a ganin an ɗauke daga nan an kaisa sama ? Shiru tayi tana zumbura baki, jahad taci gaba da cewa "sannan kince tare da yaya Omar kaɗai zamu tafi saboda yana son mu, Shin kin manta da Sehrish ne"? Ita kuma fa? akwai wanda yayi mana wahala ne kamarta? sehrish tana son mu fiye da kowa na duniyar nan, saboda mu tashiga duk wani hali da take ciki ayanzu duk da bansan yaya rayuwarta take ba...............wani irin kuka ne yaci ƙarfin jahad har takasa ƙarasa maganar da take yi, Nan take jikin hosana yayi mugun sanyi tunawa da Sehrish ƴar uwarsu mai tsananin son su da ƙaunarsu, tuni itama idonta sun cicciko da hawaye murya na rawa tace "Ya Allah hada sehrish za'a ɗauke mu akai mu duniyar Taurari.....' dakatawa da magana tayi ganin Jahad dake kuka ta fashe da dariya, wato tayi tazarce daga kukan da take Zuwa dariya ba don komai ba sai don jin abunda Hosana ke cewa, share hawayenta tashiga yi tana faɗin "Hosana wasan ya isa haka, muyi magana ta hankali, yanzu yaya za'ayi yaya Omar yasan halin da muke ciki kafin Hafsat da Momynta su sa azubar damu yakamata muyi tunanin hakan in ba haka ba zamu shiga wani mugun hannun ne ko mu ƙare rayuwarmu adaji..............' jinkirtawa tayi da maganar tana sauraron shawara daga wurin hosana, "To ya zamuyi mu sanar mishi jahad? Bayan kullum waccen matar mai kama da samudawa mai kumatun alkubus tana tsare mu da ido duk in yazo tana hanamu kwakkwaran motsi," Shiru jahad tayi tabbas dole su nemi mafita in ba haka ba, zasu fuskanci tashin hankali Can tayi wani dogon tunani tace "Hosana mai zai hana, mu samu paper da biro sai mu rubuta mishi, in yazo sai ki lalla6a kisan yarda zakiyi ki tura masa a aljihunsa? Ko da rungumesa ne sai kiyi kamar yarda kikayi a asibitin nan kin tuna"? Murmushi hosana tasaki anzo inda keyi mata ƙaiƙayi kallon jahad tayi tace "Shawara mai kyau, amma taya zamu rubuta mishi to? Bamu da paper ba biro jahad," Shiru jahad tayi kafin tace "Akwai !!! Na tuna acikin wannan ɗakin da Momyn hafsat takaimu acikin wannan ƴar lokar naga Memo da biro," Cike da farin ciki hosana tace "dama ƙopa a buɗe take, yau ta manta bata rufe mu ba, jahad ki lalla6a ki ɗauko ki rubuta masa," Miƙewa jahad tayi tana faɗin "Zan fita dan Allah hosana karki biyo ni, nasan halin ki, in kika ja asirin mu ya tonu kashin mu ya bushe mu duka," Murmushi hosana tasaki tana cewa "sai dai in baki daɗe ba, kinsan ina jin tsoro fa nikaɗae anan," "Karki damu yanzu zan dawo," "To shikenan," hosana ta bata amsa, Ficewa Jahad tayi cikin sanɗa take tafiya babu kowa wayam sai hasken daya gauraye ko'ina, Wuce wa ɗakin tayi a hankali ta tura ƙopa tashige cikin hanzari ta nufi drawer ta zaro gidan farko ajikinta, anan taga memo ɗin da biron data gani, Fiddo su tayi jiki na rawa ta aza memon asaman drawer ɗin dayake ƙaramace, daga zukunne jahad ta soma bude papers ɗin sannan ta aza biro ta soma rubutu kamar haka _ya Omar naji ma inaso na faɗa maka halin da muke ciki, wlh bamu jin daɗin zama agidan nan, saboda basu son mu, uban aiki suke samu har bugun mu suke yi, dan Allah ya omar in kaga wannan takardar ka taimaki rayuwarmu kamar yarda kayi niya ka tafi damu inda kake rayuwa_ Kamar daga sama Jahad taji ance "Sannu da Ƙoƙari"!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!! Jin wannan maganar a bayanta yasa jahad dakatawa da rubutun da take yi, hankali a matuƙar tashe idonta sun firfirto azare, jikinta ya soma wata irin kerma, Tuni Zufa ta soma gangarowa daga fuskarta da jikinta don bala'e hatta paper ɗin da take rubutun asamanta ta jiƙe sharkaf da gumin da take fitarwa 😳😳😳
*SHIN WACECE WANNAN*‼â‰â“â“â?
🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
*Abban Sojoji part 2*
*EPISODE 3-4*
Sam jahad ta gaza yin kwakkwaran motsi saboda ta riga ta gane muryar wacece....... Idasa shigowa tayi da wannan takun nata, jikinta na sanye da sleeping dress red colour masu zanen flowers ajikinsu, abunka ga fara ta fito 6au acikinsu, kanta ko mayafi babu ba kowa bace wannan face AUNTY BABBA, Lokacin da ta isa inda jahad take, hannu tasa ta fisge takardar da take rubutawa, ta ɗago da ita tana karanta wa, zaro ido tayi hankali tashe tace "Keeeeee! Don ubanki ni zaki tonawa asiri!? Wato Omar kike rubutawa wasiƙa don ki faɗa mashi abunda muke yi maku ! Wlh kin shiga uku, bazan ƙyale ki ba sai kin yabawa aya zaƙinta!!!!
a masifance take magana ƙarshe tayi Wurgi da takardar ƙasa sannan azafafe da wannan hannun nata ƙirar samudawa ta damƙo mayafin dake lullu6e akan Jahad nan take ya sul6e ƙasa hakan ya bata damar damƙar gashin kanta, wani irin zafi ne ya ziyarci jahad saboda ruƙon da aunty babba tayiwa gashin kanta,    Janyo gashin tayi ta ɗago jahad dashi, jikinta sai kerma yakeyi duk ta rurruƙe hannun aunty babba dake ruƙe da gashin kanta tana faɗin "Aunty dan Allah kiyi haƙuri bazan ƙara ba....' bata ƙarasa ba aunty babba takai mata naushi a bakinta, nan take jini ya soma zuba daga bakinta le6enta suka faffashe, saboda tsananin azaba da raɗaɗi yasa jahad fashewa da wani irin matsanancin kuka na tashin hankali,   Wurgi da ita aunty babba tayi jahad ta tafi jiki a mace ta zube ƙasa, tattakawa aunty babbba tayi izuwa inda take don bata gama dukan nata ba,   Tashi zaune jahad tayi tana jan jikinta da baya da baya tana faɗin "dan Allah kiyi haƙuri bazan ƙara ba.....nasan nayi kuskure....   "Ke ƙaramar ƴar iska ce ! bakisan koni wacece ba ! Har ni zakiyi wa iya shege acikin gidana ! Ni zaki tonawa asiri Wurin Omar? idan na so yanzu saina sa wuƙa na yanka ki, shashasha... ta ƙarasa maganar tare da sake damƙo gashin jahad tashiga yi mata azaba dashi, ta ja shi da ƙarfi tamkar zata tsige shi daga kanta, tuni idon jahad yayi jawur wasu irin jijiyoyi suka firfito mata a goshin ta, don rashin imani aunty babba sai ta naɗe gashin a wuyan jahad ta shaƙeta dashi gadan gadan zata kashe ta, murya ashaƙe jahad ke fidda sounds tana faɗin "Ahh...ah..ann...bazan..ƙa..ra..ba' sam aunty babba bata da niyar ƙyale ta sai ma ƙara shaƙeta da take yi   Kamar daga sama Hosana ta faɗo ɗakin saboda tajiyo ihun jahad da farko sai tayi tsammanin kunnanta ne Suke mata gixau,amma rashin kwanciyar hankali da jin bugawar zuciya yasa hosana gaza samun natsuwa ta fito don tazo taga wani hali jahad ke ciki ta rubuta wasiƙar,  Shine ta taras da wannan tashin hankali, ihu tasaki a haukace ta watsa da gudu inda aunty babba ta shaƙe jahad ajikin wardrobe,  "Kada ki kuskura ki ƙaraso in ba haka ba zan haɗa dake kema," aunty babba ce tayi ma hosana wannan maganar batare da ta janye hannunta daga wuyan jahad ba, cikin kuka hosana ke faɗin "ki sake ta...! Ki kyale ta....kada ki kashe mun ƴar uwata.....' amma sam aunty babba taƙiya,   Ganin jahad ta soma kakarin sheƙawa barzahu yasa hosana fita hayyacin ta, aikuwa ta daddage da iya ƙarfinta na ƙarshe tasamu damtsen hannun aunty babba ta Gartsa mata lafiyayyen Cizo da hakoranta 30 cufffff   A firgice aunty babba ta saki jahad tana yarfa hannun ta sai ga jini na ɗigowa, cikin hanxari tasa ɗayan hannunta ta zame hannun rigar jikinta don taga inda hosana ta cije ta, wurin yayi jawur ga sahun haƙoran hosana nan rerass a farar fatar hannunta dama gashi dumurmur na ƴan hutu,   Cike da jin raɗaɗi tace "Innalallahi !ni kika ciza har kika fasa mun fatar jiki na !! Ya salammmm !! Kin mutu wlh !! Kin shiga uku !! tayi maganar idonta jawur saboda taji raɗaɗin cizon hosana wurin har wani Zogin azaba yake yi mata,   Ja da baya hosana tashiga yi a tsorace ganin aunty babba na tunkaro ta Kamar Damusa, gashi jahad tunda aunty babba ta sake ta, ta sulale ta sume a ƙasa balle itama ta taimaki hosana,   Hanyar fita ta nufa da gudu zata fice, cikin rashin sa'a aunty babba tasanya ƙafarta ta taɗiyo ƙafar hosana, aikuwa ba ƙaramin buguwa hosana tayi ba, gaba ɗaya ta kife ƙasan tiles ɗin ɗakin, fuskarta ta dake sa, nan take hancinta ya fashe jini ya soma kwaranyowa, haka goshinta ma ya fashe da La66anta duk sun farfashe ihun azaba kawai hosana ke saki tana faɗin "wayyo Allah na ....! Nashiga uku...na mutu na lalace !!   Aunty babba tace "baki mutu ba, don ubanki, yanzu ne zaki mutun.....tayi maganar tare da kai hannunta kan Gashin hosana wanda ya barbaje ƙasa, kwakkwarar damƙa takai masa, ta ruƙo shi dakyau ta janyo hosana dashi har sai da hosana ta miƙe tsaye tana ihu kamar ranta zai fita, daddagewa aunty babba tayi da iya ƙarfinta na ƙarshe ta buga kan Hosana jikin bangon ɗakin wayyo Allah zoka ga yarda jini ya wanke bangon, Razanan nan Ihu hosana tasaki na azaba tamkar maƙoshinta zai ballo waje nan take ta sulale ƙasa a mace.......
Ihun da hosana tayi na ƙarshe wanda ya karaɗe ko'ina harya sa Hafsat dake kwance ɗakinta saman gadonta farkawa a firgice, ta diro daga saman gadonta jiki na rawa ta fito ta tunkari inda sautin ke fita cikin hanxari ta faɗo ɗakin,  gabanta ne yayi wani irin bugu ganin Momynta a tsaye tana huci kamar wata zakanya, ga kuma twins ɗin da Omar ya kawo a baje ƙasa jina jina musamman hosana an zubda jini   Hankali tashe hafsat tace "Mommy me nake gani haka !! Me kika yi masu ne !! Kashe su Ki kayi da hannun ki !!!   tsawa aunty babba ta daka mata tare da cewa "Eh kashe su nayi,akwai magana ne ! babu ruwanki dani ki koma ɗakinki zai fi miki,"  Cikin rauni hafsat tace "mommy duk rashin imani na bazan iya aikata abunda kika aikata ma yaran nan ba, ashe baki da Imani ko misƙala zarratin ! Kisan kai da hannun ki........'  Bata idasa maganar ba saboda jin saukar wani irin zazzafan mari a kuncinta, tashin hankali da ba'a sama shi rana,    Saboda zafin marin da aunty babba tayi ma hafsat yasata dafe kumatun ta ido jawur take faɗin "Mommy yau ni kika mara da hannun ki"?    "Naje na mara ! duk kece sular da kika 6atamin raina harna aikata abunda na aikata yanzu!!"    shiru hafsat tayi yayin da idonta ke fitar da wasu irin siraran hawaye masu zafin gaske,  Jikin aunty babba ne yayi mugun sanyi ganin hawayen dake fita a idon hafsat ƴarta tilo,    Cikin tashin hankali tace "ba da son raina nayi hakan ba ! Hafsat ke kika 6atamun rai da 6acin ranki na kwanta, cikin daren nan na fito saboda zuciyata batamun daɗi kawai naga yarinyar nan jahad ta nufo ɗakin nan shine na biyota in ga mai zatayi ashe wasiƙa zata rubutama Omar akan abunda muke aikata musu, da nufin inyazo su bashi.......yanzu yaya zanyi hafsat....na kashe su ba'a hayyacina ba...In Omar yazo bansan me zan faɗa masa ba......" tayi maganar tana yarfa hannunta idonta cike tab da hawaye cikin tashin hankali,   Murya na rawa hafsat tace "Mommy kin ja mana masifa da bala'e duka, ni banji xafin marin da kikayi mun ba, domin wannan kaɗanne akan Marin da zamu kar6a ni dake a wurin Yaya Omar wlh bazai ƙyale mu ba !! Yadda kika kashe su ke ma haka zaisa ayi maki hukuncin kisa babu ruwana ......   Cikin shesshekar kuka aunty babba tace "Hafsat yanzu don na kashe waɗan nan tsintattun marasa galihu nima sai Omar yasa akashe ni?   A tsiwace hafsat tace "Eh.!! dama menene alaƙarki da Shi da zai tausaya miki? Kwarama Ni zan tsira ke kuwa Yayansa kawai kike aure !! Wlh mommy kin shiga uku gaki can an garƙame ki a cell ƙarshe a yanke maki hukuncin ɗaurin rai da rai har sau biyu saboda rai biyu kika kashe.......    Hannu aunty babba ta aza akanta tana faɗin "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga Uku Ni LAILA naja ma kaina mutuwa a lokacin da ban shirya ba,      Jiki a mace aunty babba ta zuƙunna inda hosana take kwance a mace tana faɗin "kee!!!kee!!! tashi !! Maza ki tashi don ubanki ! Wlh baxa ku jamin bala'i ba, hafsat ɗauko mun robar ruwa a fridge dan Allah in yayyafa musu ko sun tashi    tayi maganar tana kallon hafsat, fuce wa hafsat tayi da sauri sai gata ta dawo hannun ta ɗauke da bottle water ta miƙa mata, kar6a Aunty babba tayi jiki na rawa ta cizge murfin tashiga yayyafa ma hosana ruwan ajikinta,   Gabansu ne ya faɗi atare ganin hosana ko motsi batayi duk sanyin da ruwan yayi hakan na nufin ta mutu kenann !!!!!!  tuni fuskar aunty babba tayi jawur kamar wadda aka nannausa saboda tashin hankali A ruɗe tace "Hafsat mun shiga uku !! Mun lalace !! Wlh ta mutu wayyo Allah na ni laila......    Hafsat dake tsaye hankali atashe itama aruɗe tace "wlh Mommy laifinki ne, kece saurin fushin tsiya ga zafin zuciya gashi nan kin kashe su, To ni wlh babu ruwana aciki, dama ban da wata alaƙa dake haihuwata kawai kikayi.......   ɗagowa aunty babba tayi ta kalle ta ido jawur cikin disashewar murya tace "Hafsat ni kike ce ma baki da wata alaƙa dani, saboda ƙaddara da tsautsayi sun rutsa dani.....'   Cikin kuka hafsat tace "Ae gaskiya na faɗa mommy ! ina bacci. na kin katse mun shi da wannan tashin hankalin, Allah mommy ba abunda zai hana Omar yasa a garkame ki a cell , har na hango ki cikin kayan gidan yari Allah bazasu yi maki kyau ba yadda kike haka ɗin nan........' tayi maganar tana nuna aunty babba dake zuƙunne agaban hosana kamar buhun masara,  "Yanzu ya zamuyi ? Hafsat kar6i robar ruwan ki yayyafa ma ɗayar muga in ita zata tashi, wataƙil ita In tafarka sai in samu sassauci awurin yanke mun hukuncin......   Cikin sauri hafsat ta kar6i robar ruwan dake hannun aunty babba ta ƙarasa inda jahad take tashiga yayyafa mata shi a fuskarta, Wani irin dogon numfashi jahad taja kafin tace "La'ila ha illallah Muhammad rasulillah....    Ganin jahad tafarka yasa aunty babba tashi tsaye ta tunkare ta tana faɗin " Alhamdulillah saura ɗayar yaya zamuyi hafsat ? Kodai kawai mu binne gawarta a cikin garden ɗin gidan nan ne?   Wani irin kallo hafsat tayi mata tare da cewa "ashe mommy hankalin ɗiyar roba ke gare ki? mu binne gawa acikin gidan nan ? Idan fatalwarta ta tashi fitowa ke zata fara ziyarta Allah,   Hannu aunty babba ta aza akai tana faɗin "Ya salam duk ni naja ma kaina"   daker jahad ta buɗe idonta wanda suka kumbura sukayi jawur, ga le6anta sunyi sutum sutum inda aunty babba takai mata naushi,   Idonta bai sauka akan kowa ba sai kan hosana dake baje ƙasa jini duk ya wanke fuskarta......  Da ƙarfi ta furta "Hosanaaaa !!!!!!!!!,' tamkar bakinta zai tsage yunƙurawa tayi ta tashi a tsananin razane ta ƙarasa inda hosana ke kwance ta zube saman guiwowinta tana faɗin "hosana ki tashi ! mai ya faru dake ne? Wa yayi maki haka !! Innalallahi'wa'inna ilaihirraji'una .....ta ƙarasa maganar tare da kifa kanta jikin hosanar tajima bata ɗago ba sai daga baya ta ɗago da kan nata tana faɗin "Dan Allah ku kaita asibiti kada ta mutu !! Kada narasa ƴar uwata,"  Kallon juna su kayi sai yanzu suka mayi tunanin zuwa asibiti don sam basuyi tunanin hakan ba,   Jiki na rawa hafsat tace "mommy ki ɗauko ta, bari naje room ɗina naɗauko mukullin mota mu tafi,"   Aunty babba tace "Toh,ki tahomun da mayafi dan Allah"  fucewa hafsat tayi tana faɗin "kiyi sauri mommy,"   Cikin hanzari aunty babba ta ƙarasa jiki na rawa, ta cuccu6i hosana ta aza aka faɗarta ta fuce da ita daga ɗakin, itama jahad ta bisu abaya    Fitowa hafsat tayi itama a lokacin har aunty babba ta buɗe back seat na motar ta kwantar da Hosana aciki itama jahad tashiga ciki sannan ta rufe,   Su kuma suka shiga front seat hafsat na a mazaunin driver ita kuma tana a gefenta,   Da gudu hafsat ta tada motar taja ta a tsiyace suka nufi hanyar fita daga gate ɗin gidan   Nan take sojojin dake gadin gidan suka tunkaro su don jin ba'asi  Aikuwa a masifance aunty babbba ta ɗaga murya tana cewa "Nice nan zan fita kar in ga wani shege ya tare mun ƙopa Wlh in bi takansa....'  Jin muryarta yasa su kayi baya baya suka bata hanya ta wuce.......... da gudu suka miƙi titi sai asibiti, kuma duk da haka sai da sojojin nan suka biyo su abaya saboda aikinsu ne basu tsaro musamman acikin daren nan,
Suna isa asibitin gudu gudu sauri sauri Aunty babba ta ɗauki hosana suka shiga ciki,da hanzari reception nurses suka karbe ta aka shiga da ita ciki, anci sa'a an samu likitan dake a bakin aiki, cikin gaggawa suka shiga duba hosana,  Su kuwa su aunty babba da hafsat suna atsaye sai faman zagaye suke kowa cike da zullumin abunda zai biyo baya in yarinyar ta mutu, jahad kuwa tana abakin ɗakin da aka kwantar da hosana ta kwantar da kanta jikin door ɗin idonta na tsiyayar da hawaye masu ɗumi,😠Gaba ɗayansu babu wanda ya samu bacci adaren nan saboda da tashin hankali,   (Na zubda hawaye saboda halin da su Hosana da jahad suke ciki Ya Allah ka kawo masu ɗauki) 😠______________________________________
Ana cikin kiran sallar asuba Sehrish tafarka a hargitse tana faman dafe saitin zuciyarta dake yi mata wani irin raɗaɗi, sai faman ambaton sunan Allah take yi, tabbas ranta na bata cewa wani mummunan abu ya faru dasu Jahad, cikin hanzari ta sauko daga saman gadon tana faman zagaye ɗakim kafin daga bisani ta shiga cikin toilet ta ɗauro alwala,  Fitowa tayi ta nufi wardrobe ɗinta, hijab ta ɗauko da darduma ta shimfiɗa, ta shiga jera sallah, bayan ta kammala ta zauna tare da ɗaga hannayenta sama tana addu'o'i akan su hosana da jahad da sauran al'ummar musulmai, ta jima tana addu'ar kafin ta koma saman gadon nata ta kwanta tana fuskantar sama abubuwa iri iri na zuwa mata aranta daga bisani bacci ya kwashe ta, bata sake farkawa ba sai ƙarfe 10 na safe, Firgit ta farka har time ɗin shiga kitchen ya wuce,  Zumbur ta miƙe shaf shaf ta shirya cikin shigarta ta maza da ta saba, saboda zullumi bazai barta ta fita a matsayin mace ba, a hankali ta tura ƙopa ta fuce izuwa kitchen,  Bin ta da kallo azmee tayi wadda ke gyara kitchen don harta kammala breakfast ɗin already tun ɗazu,  Da mamaki tace"Sehrish ya akai naganki kuma da shigar maza?   Shiga ciki tayi tana cewa "Aunty azmee ni tsoro nake ji Allah,"   "Wani irin tsoro kuma,ba wani tsoro abunda nake so dake bayan mun kammala jera abinci, sai ki koma ɗaki ki cire wannan gashin bakin ki sauko da gashin kanki zan kira ki, sai ki fito a matsayin mace" Shiru tayi tana kallon yatsun hannun ta kafin tace "shikenan Allah yasa komai ya tafi adai dai,
Murmushi azmee tasaki tare da jinjina kai tace"Insha Allah yanzu bari na fara jera miki warmers É—in kina kaiwa dining,"
 Ta amsa mata da "toh", tana jin ɗar axuciyarta
 Cikin ƙanƙanin lokaci suka kammala jerawa, Ayaan da Jahan ne suka fara fitowa sanye cikin kakinsu gwanin kyau, Suka samu wuri suka zauna kusa da Juna, azmee ta soma saving ɗinsu, time ɗin sehrish ta shige bedroom ɗinta don ta kimtsa kamar yadda su kayi da azmee zata fito a matsayin mace, Bayansu sai kanal yusif ya fito shima sanye da Jallabiya launin ruwan toka, wuri yasamu yazauna yana gaishe da aunty azmee, da fara'a take amsa musu, cikin girmamawa su twins suka gaishe shi shima ya amsa musu daga bisa ni kowa ya mayar da hankali kan breakfast ɗinsa, Sehrish na cikin ɗaki cike da zullumin yarda za'ae ta fito a matsayin mace, tana a jikin ƙopar ɗakinta tana ruƙe da handle ɗin kopar cike da fargaba, Gyaran murya azmee tayi ta ɗan ɗaga murya tare da kwaɗawa sehrish kira da sunanta tace "Sehrish ki fito mana," Jin sunan da azmee ta ambata yasa su kallonta da mamaki, sake maimaitawa tayi "Sehrish ki fito nace," Kallon juna Ayaan da jahan su kayi sannan suka kalle ta atare suka haɗa baki wurin cewa "Wanene Sehrish kuma? Kanal yusif shima cike da mamaki yake kallon azmee jin sai faman kwala kira take yi, zuba ido su kayi don suga wanene wannan sehrish ɗin da Azmee ke faman kira, shin baƙo su kayi ne a gidan nasu ko kuwa? buɗe ƙopa sehrish tayi gabanta na faɗuwa ta tunkaro hanyar dining area ɗin, jikinta na kerma a tsorace take tafiya, gaba ɗayansu suka ɗago suna kallon ta tun kafin ta idasa bayyana a area ɗin da suke, bin ƙafafunta su kayi da kallo waɗanda ke sanye da ƴan silifas ɗinta na gado, sai faman kerma yatsun ƙafarta suke yi, Time ɗin da sehrish ta idasa fitowa a raxane jahan ya miƙe tsaye, ayaan kuwa baisan lokacin da ya saki cokalin dake hannunsa ba ya faɗa cikin plate ɗin dake agabansa, kanal yusif kuwa kallon abun yake kamar a mafarki, Bin ta suke da kallo cikin mamaki, kamar a mafarki suke kallon lamarin, ƙarasowa tayi ido a zazzare jiki na kerma, riga da wandon nan ne ajikinta , ta cire gashin bakinta, ta kuma zuba da doguwar sumar kanta har gab da waist ɗinta, ta fito asalin macen ta Tsaleliyar budurwa ƴar matashiyya, A rude jahan yace "Azmee who's she ? daga ina ta faɗo cikin gidan nan? Da iznin wa!? Ayaan kuwa cewa yayi "Ku kuke ganin mu bamu muke ganin ku ba ! Wannan Hurool ainin fa? daga aljanna ta gudo? Kanal yusif sam yagaza magana bayani kawai yake jira daga wurin azmee, ita kanta azmee ta ɗan razana da reaction ɗin da suka bayar, Sehrish kuwa a gefen azmee ta tsaya tana faman zare ido, "Azmeee Explain !!!!' jahan ya faɗi azafafe harda dakar table ɗin gabansa da tafin hannunsa, Murya na rawa azmee tace " Kuyi haƙuri dan Allah...Am wannan da kuke gani ba kowa bane face Tukur mai aikin ku, nasan zakuyi mamakin hakan...... Dakatawa tayi ganin yarda Ayaan da kanal yusif suka miƙe atare, cike da ruɗu Kanal yusif yace "What ! Wai wane tukur ɗin ake magana ! Ba dai wannan yaron mai aikin namu ba, kina nufin dama mace ce ba namiji ba ....? Ya tambaya hankali atashe , Daga sehrish har azmee sun tsorata, Hannu jahan yasa yasake bugun table ɗin abincinsu yace "Impossible bazai ta6a yiyuwa ba ! muddin kuwa hakan ta kasance dole yarinyar nan ta fuskanci hukunci mai tsanani kuma tabar gidan nan ayau ɗin nan, Fashewa da kuka sehrish tayi saboda tsorata da maganar Jahan gashi idonsa na akanta ya zare su, "Dan Allah ku kwantar da hankalin ku, laifi ne nasan ta aikata amma kuyi mata afwa, sam bata da niyar cutar da kowa.....' dakatar da ita Ayaan yayi da cewa "Ba wannan zancen ! Saboda ƙarfin hali irin na Yarinyar nan, tayo shigar maxa ta saje acikin mu tana mana aiki, babu sirrin mu da bata sani ba, babu irin firar da bama yi agabanta, har yawo muke yi da towel a ƙugunmu, muyi yawo da gajerun wanduna duk idonta na akai, kaf ta haddace ashe kallon mu kawai take yi," bil'haƙki ayaan yake kora bani, gaba ɗayansu ba komai suke ji mawa ba face yadda sehrish ta saje A cikinsu matsayin namiji na tsawon lokaci tana masu aiki, duk a tsammaninsu namiji ne ashe maca ce, tagama sanin sirrinsu saboda babu irin firar da basa yi agaban ta, sannan babu irin shigar da basa yi suna yawo duk a idonta, Hannu Jahan yasa yana ƙoƙarin zare belt ɗin wandonsa da nufin ya jibgi sehrish saboda yafi kowa fusata, gashi dama su Mace bata agabansu balle suga kyanta ko wani abu haka don su tausaya mata, A tsorace sehrish ta ƙanƙame kanta ta 6oye abayan aunty azmee tana faɗin "Nashiga uku ! Dan Allah aunty azmee ki basu haƙuri, kada su buge ni...zan tafi nabar musu gidan, ture kujerar gabansa yayi gadan gadan ya tunkari sehrish zai jibge ta, Kamar daga sama suka ji Muryar Abban su yace "Kada ka kuskura ka ta6a ta!' Atare suka ɗago suna kallonsa kowannan su na huci, Ruƙe yake da hannun junaid cikin nasa, yana sanye da jallabiya junaid kuma na sanye cikin riga fara da wando baki, ya tsorata da ganin halin da sehrish ke ciki gashi kuma yayi mamakin ganin ta ta bayyana kanta a matsayin mace, ga kuma jahan tsaye ruƙe da belt wato zai jibge ta, Idasa isowa sukayi inda suke tunkan abbansu yace wani abu Ayaan yace "Daddy dama wannan yaron tukur mai aikin gidan mu mace ne ba namiji baa !! murmushi Abbansu yasaki yana kallon su yadda duk suka zabura, Mayar da idonsa yayi kan Yarinyar dake 6oye abayan azmee yace "Ke zonan," "Sehrish ki fito Abbansu na kira," Azmee ce ke tunasar da ita, fitowa sehrish tayi jiki na kerma ta ƙarasa inda Abbansu yake tsayawa tayi at front of him murya na rawa take faɗin "dan Allah kuyi haƙuri ku yafe mun, nasan nayi laifi wlh ni banzo da niyar na cutar da kowa ba.....' tsawa Jahan ya daka mata da cewa "Rufe ma mutane baki kona zo nan na nakaɗa miki shegen duka," Abbansu yace "Ya isa haka Jahan, bana so kowa yasake magana," shiru su kayi gaba ɗayansu suna sauraron mai abban nasu zai ce,
Shin ina haroon duk wannan abun dake faruwa yana a tsaye fitowarsa kenan, gaba ɗaya ransa ya gama jagulewa mamakinsa yarda akai yarinyar ta bayyana kanta A matsayin mace bayan bai idasa cimma burinsa ba, na tsoratar da ita, Amma ganin yadda su Jahan suka fusata yasa shi jin daɗi aransa burinsa karsu amince su tada 6alli sai anyi mata horo sannan a koreta shi kuma zaiyi amfani da wannan damar wurin ƙuntata mata,
tsayawa yayi da murmushin mugunta a fuskarsa don yaga ya ƙarshen bada'ƙalar zata kaya, Daga shi sai gajeran wando fari ajikinsa tsaye ruƙe da ƙugu, ɗayan hannunsa na ruƙe da Brush da alama ma daga toilet ya fito,
burinsa yaji mai Abban nasu zai ce, gyaran murya Abbansu yayi sannan ya soma cewa "Na riga da nasan komai game da yarinyar! Domin junaid ya jima da sanarmun komai agame da ita, duk abunda junaid ya nuna yana so aduniyar nan koma menene shi zan amince dashi, Junaid ya nuna cewar yana son Zaman yarinyar nan agidan nan, don Haka Na AMINCE masa,!" Cikin mamaki suke kallon abban nasu, Haroon kuwa tuni yayi wata irin raxana har Brush ɗin dake hannunsa ya faɗi ƙasa sbd jin abunda Abbansu yace, Murmushi kawai junaid ke saki, kallonta Abban su yayi tare da cewa "Ya Sunan Ki"? Sehrish dake tsaye agabansa idonta cike tab da kwalla duk ta tsorata murya na rawa tace "SEHRISH" Jinjina kai Abbansu yayi tare da sa hannun shi ya shafa gefen fuskar sehrish yace "Daga yau Ba sunanki Sehrish ba," cikin mamaki suke kallon Abban nasu, itama sehrish ɗin kallonsa take tana jira taji sunan daya canza mata, azmee kuwa Alhamdulillah kawai take faɗi aranta, "Kinsan menene sunan ki daga Yau"? abban nasu ya faɗi yana kallonta, Cikin sanyin murya Reesh tace "a'a". murmushi Abban nasu yayi sannan yace "daga Yau sunanki *SEHRISH SALAHUDDEEN HUSSEIN ABBAN SOJOJI*" 😇😇😇
Sakin baki su kayi suna kallon Abban nasu
Duk wannan Abun dake faruwa akan idon SGR wanda ke saukowa down stairs jikinsa na sanye da t-shirt mai gajen hannu baƙa, sai dogon wando fari, sun bi shape ɗin jikinsa ya fito Handsome stylish ɗinsa, ya ɗaure sumar nan ta baya ba ƙaramin kyau yayi ba, a hankali yake tattaka steps ɗin cikin tafiyar nan tasa ta majiya ƙarfi, duk suka ɗago suna kallon shi................ __________________________________ 🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
*💫LAFAZI WRITERS ASSOCIATION 💫*
*Abban Sojoji part 2*
*EPISODE 5-6*
Ida sa iso wa inda suke sgr yayi idonsa yakai kan Jahan daya zare belt ruƙe a hannunsa, tunkan yayi magana jahan yayi hanxarin mayar da belt ɗinsa, mayar da idonsa yayi kan Abban nasu tare da cewa "Gm dad fatan an tashi lafiya," murmushi Abban su yasaki da cewa "Lafiya Lou son ina fata kaima haka," Sgr yace "Alhamdulillah," sannan ya samu wuri ya zauna saman ɗaya daga cikin dining chairs ɗin, kowa so ya ke yaji mai Babban yayan nasu zai ce, musamman haroon burinsa Sgr yace bai amince da zamanta ba, don yasan in dai yace hakan to Zaman sehrish ya ƙare a gidan, Ita kuwa sehrish hankalinta kwance saboda tasan yarda su kayi jiya dashi haka azmee ma, gyaran murya sgr yayi kafin yace "tsayuwar me kuke yi"? Ya tambaya yana kallon su jahan Ayaan da kanal yusif, koma wa su kayi kowa ya xauna junaid ma yasamu wuri ya zauna, sai Abban nasu dake tsaye sehrish na agabansa yaci gaba da cewa "daga yau kin zama ƙanwarsu kema ƴa' ce acikin gidan nan, duk wani abu da uba keyi ma ƴarsa nima zan miki shi, kuma duk wani abu da junaid zaiyi acikin gidan nan kema zaki iya yin shi, kuma duk wanda yayi yunƙurin 6ata miki acikinsu ki sanar mun zaki ga yarda zanyi dashi,"
Zuru su kayi suna sauraron Abban nasu, sehrish kuwa murmushi kawai take saki koba komai yau tasamu Uba wanda zatayi prouding dashi a faÉ—in duniya, É—ago idansa yayi ya kalli Babban yayan nasu, wanda azmee taci gaba da saving É—inshi breakfst ya kira sunan shi "RAFAYET" amsa wa yayi da "Na'am Abba," batare da ya juyo ba ya kalle su, Abban yace "Ina fata kaji komai ga me da yarinyar nan ? bansan ko kana da abun cewa ba" ya tambaya yana kallonsa,
kowa ya saurara don jin ta bakinsa, haroon Allah Allah yake akan Babban yaya karya amince da zamanta, Boss man ɗin sai da ya gama sipping Coffee ɗin dake hannunsa a natse sannan yace" Umarninka Shine abun bi" amsar da ya bayar kenan, wani irin farin cikine yaci ka Abban nasu saboda shi da yake tunanin zai ƙiya gashi ya amince da duk jawabinsa kai tsaye ma yace Umarninsa shine abun bi, wato duk abunda yace game da yarinyar ya amince, "Kufa kuna da Abin cewa"? Abban nasu ya tambaya yana kallom su, cikin sauri suka haɗa baki wurin cewa "Abba ae magana taƙare kawai tunda Babban yayan mu ya amince mu su wanene da baza mu amince ba"? Wannan maganar tasu tasa Azmee yin ƴar dariya ƙasa ƙasa, Jinjina kai Abban su yayi sannan yace "hakan yayi mun, sannan ko da gigin wasa ban amince wani ya cutar mun da ƴa ta ba," "An gama magana Abba" suka bashi amsa atare yace "Yawwa haka nake son ji, sannan ya mayar da idonsa kan Sehrish wadda ke faman sakin murmushi tayi zuru tana cizar akaifar hannunta da takai bakinta, ba kowa take tunani ba face Haroon yadda zata Zazzaga mashi rashin mutunci, dama taci alwashin hakan Muryar Abban su ce ta katse mata tunanin nata da cewa " daughter ki zauna kiyi breakfast tare da Abban ki da kuma ƴan uwanki," ɗan zaro ido sehrish tayi jin yace zata zauna taci abinci acikinsu cikin mamaki tace "Abba anan," tayi maganar tana nuna dining table ɗinsu, "Eh nan nake nufi" ya bata amsa sannan ya ruƙo hannunta gavan ta na faɗuwa suka samu wuri suka zauna tana gefen Junaid Abbansu kuma na gefenta sun sa ta tsakiya, Babban yayansu kuma Na a side ɗin Abban nasu, ta hannun dama yayin da suke facing Ayaan Jahaan da kanal yusif su da suke hannun haggunsu, "Azmee ke ma ki samu wuri ki zauna A cikin mu," abban su ya faɗi yana kallonta , da fara'a a fuskarta tace "ngde ssae Abba, amma ni nafison a barni a iya matsayi na, nafi jin daɗin kasancewata haka, dama damuwa ta Sehrish ce gashi kuma ta samu Ƴanci ka ƴanta ta, Allah ne kaɗai zai iya saka maka, haƙiƙa kai na musamman ne ka kasance ɗaya daga cikin mutanen da ake Alfahari dasu aduniya kuma ake alfahari da Ƴa'ƴansu kowa burinsa yayi koyi da kyawawan ɗabi'unka da halayanka Abba ba abunda zamu ce sai dai Allah yaci gaba da tsare mana kai, ya tsare zuri'arka, Ya kare ka daga sharrin mahassada da maƙiyan ka, Allah yaci gaba da ɗaukaka darajarka da ta ƴa'ƴanka a faɗin duniya, kamar yadda kake faranta ma wasu Kaima Allah ya faranta maka aranar gobe ƙiyama yasa Aljanna tazama makomarka................azmee bata tsaya ba haka taci gaba da yiwa Abbansu addu'oi' dasu kansu , gaba ɗaya sunji daɗin addu'o'inta kuma dukkansu suke amsa mata da Ameen ameen,
daga bisa ni kowa ya mayar da hankalinsa ga abincin dake agabansa zanso kuka sehrish duk ta gaza samun natsuwa ba wai don bata jin daɗin kasancewarta atare dasu ba, sai don tsoran su ayaan da jahan da take yi, saboda wani irin kallo da suke mata Sam tagaza gane kallon menene wannan, dama fa su ƴa'ƴan Alexandra wuyar sha'ani ke gare su kamar uwarsu haka suke basu cika yarda da mutane ba ko kuma sake musu, junaid ne kawai mai sauƙin kai saboda kaf halayansa shigen na Abbansu ne,
shin wai ina haroon ? Ae tuni ya koma cikin bedroom ɗinsa cikin tsananin ƙunci ransa yayi mugun 6aci sai faman yawo yake a ɗakinsa cike da jin baƙin ciki aransa sai faman huci yake bakowa yafi bashi haushi ba face Abbansu da Babban yayansu saboda sune suka nuna Amincewarsu da ita, a can ƙasan zuciyarshi kuma bakowa yafi ƙuntata masa ba fa ce*JUNAID* Saboda shine silar komai daya fara sanar da Abbansu akan maganar yarinyar, dama junaid ya jima yana ci masa tuwo a ƙwarya don ya lura Yaron Abbansu yafi Son shi fiye da kowa tunda har bai iya 6oye son da yake mashi agaban kowa, Kuma ya Lura cewa Babban yayansu ya mutu akansa hakan na nufin shima Yafi Son*JUNAID* bama su kaɗai ba kowa na gidan in kana so kaga fusatar shi to ka ta6a junaid nan xaka ga tashin hankali, shiru yayi a lokacin ya koma gaban mirror ɗinsa yana kallon fuskar shi ta cikin madubi, a fili yace "saboda*Junaid* Abba da Babban yaya suka mare Ni, a gaban ƙanne na, mutun Uku da suka kasance maƙiya na acikin gidan nan muddin inaso In ƙuntata musu dole saina Cutar da *JUNAID* 😳
ya faɗi tare da sakin wani irin shu'umin murmushi yace "Haroon kenan Mai Fuska biyu ! Wasu suna mun kallon shashasha ɗan giya yayin da ni kuma nake masu kallon garori wannan Alwashi ne na ɗaukarwa kaina saina Tarwatsa farin cikin gidan nan kuma ba da kowa zanyi amfani ba fa ce *JUNAID* 👌💔
"na'am " ya amsa yana Satar kallom sehrish da ta kira sunan shi ta wutsiyar idon shi, "nifa tsoro nake ji junaid nagaza cin abincin dake gaba ba," murmushi junaid yasa ki tare da cewa "CALM DOWN your mind reesh, ke fa ynx ƴar gida ce, ki saki jikinki ki ci Abincin ki a natse," murmushi tasaki yayin da ta sa hannu cikin plate ɗin dake gabanta mai ɗauke da fried chicken taci gaba da ci, ta6e baki Jahaan yayi yana kallonta aransa yace " ƴar shisshigi da kutsu bansan daga ina aka samo wannan yarinyar ba yanzu haka bata Wuce Zariyya dama gata nan kamar Zararrriya sai faman zare ido take,' ya yi maganar yana Hura hanci kamar wanda akayiwa dole yana Cusa bugger abakinsa, Ayaan kuwa cewa yake yi aransa "ƙarfin hali irin na Ifritanyar nan kalli yadda ta wani shige tsakanin Abban mu da junaid tana cin abinci ita ga isasshiya mai walkin sa, ala dole ga ƙanwar Sojoji zaki gane kurenki ! Jibi kunnuwanta don Allah kamar na Zomo falo falo sai faman ƴan ƙefce ƙefcen ido take kamar wadda aka aza A saman kujerar lantarki......,😂
Har cikim ranta sehrish duk ta tsargu da su Twins kamar tasan abunda suke cewa aransu, Azmee ce keyi mata alamar ta kwantar da hankalinta don itama ta lura da abunda su twins ke mata, wani irin Kallon hadarin Kaji 😾😼
Tuni sgr ya bar dining ɗin dama breakfast ɗinsa shaf shaf yake yinsa gyaran murya Abbansu yayi ya kalli azmee yana cewa "idan mun kammala ku shirya ke da sehrish da Junaid saboda yi wa daughter siyayyar kayan sawa da abubuwan amfani na mata, hada ma Saloon da gyaran jiki duka komai nake so ayi mata,' Atare Jahan da Ayaan suka ɗago suna kallon Abban nasu, shima kanal yusif abun ya basa mamaki, Sehrish kuwa murmushi kawai take saki haka Junaid daɗi kamar ya rufe sa, Azmeee tace "To Abba Insha Allah komai za'ayi mata," "Ke ma hada ke, azmee siyayyar duk zakuyi," cike da farin ciki azmee tace "Mun gode sosai Abba Allah yasa ka da alkairi," mayar da idonsa Abban nasu yayi kansu Ayaan da jahan da kanal yusif yace "Bafa ni zan biya kuɗin siyayyar ƙanwarta ku ba, wannan nauyin ku ne, don haka kowa ya tattaro ya bada gudummuwa,
babu wasa a fuskar shi yayi maganar, shiru su kayi don baza suyi mashi musu ba, Abban nasu yaci gaba da cewa "Yusuf kai zaka biya kuɗin siyayyar kayan sawanta, Jahan kuma shi zai ɗauki nauyin kayan ado na mata da za'a siya mata, sannan Ayaan shi kuma zai ɗauki nauyin na gyaran jiki hada takalma da bags ɗin da za'a siya mata ina fata duk kunji," sam takaici ya hana twins yin magana bawai kuɗin bane damuwarsu ba sam basu da matsalar kuɗi saboda bada albashinsu suka dogara ba, Mahaifiyarsu duk ƙarshen wata tana tura masu makudan kuɗi dollars wannan ba tare da sanin Abbansu ba ko Babban yayansu ba, haushin su yarinyar da aka ƙaƙaba musu wadda basu san daga ina aka tsinto ta ba, gashi kuma har ana ɗaura musu responsibilities ɗinta,
"Naji kunyi shiru"? Abbansu ya tambaya yana kallo su, Kanal yusif yace "Atm É—in yana a cikin side drawer É—ina, junaid yaje ya É—auko in zasu tafi," Â Jinjina kai Abbansu yayi tare da cewa "Haka nake son ji ku fa"? Â har suna haÉ—a baki wurin cewa "akwai kuÉ—i cash a É—akin mu junaid yaje ya É—ibi yarda zai ishe su,in kuma Atm suke so shima yana anan saman mirror muka barshi...." suna magana suna yatsina fuska irin an musu dolen nan,
Kanal yusif yace "A'a Abba ba sai sun bada nasu ba, kawai suyi using da Atm ɗina zasu ishe su har ma su rage," acewar kanal yusif,   Abban su yace "a'a ni nafison su sauke nauyin dake akansu na ƙanwarsu yakamata tun yanzu su son yadda zasu ɗauki ɗawainiyar mace kafin Allah yasa lokacin auransu yazo," . atare suka haɗa baki wurin cewa"Aure kuma Abba,"  "Eh mana" ya amsa musu, Kallon Ayaan jahan yayi tare da cewa "tashi mu tafi lokacin aiki yayi " miƙewa Ayaan yayi yana cirar tissue yace "Abba mu mun wuce,"  Murmushi Abbansu ya saki tare da cewa "adawo lafiya, aure dae ba fashi in lokacinsa yayi mutun ko bai so saina ɗaura masa in yaso ya haɗiyi zuciya ya mutu, zan zauna in ta zuba muku ido ne,"   fashewa da dariya junaid yayi bashi kadae bama hada su azmee da sehrish, kanal yusif dae murmushi kawai yayi,
Na wani lokaci kowa yabar dining É—in cikin zumuÉ—i sehrish ta wuce don ta shirya zasu tafi Shopping mall É—oki har ba'ayi, shima junaid bedroom É—insa ya wuce don ya kimtsa yau zasu yi fita ta musamman da sehrish don ya tsara har ice cream sai sunje sha, haka itama azmee kimtsawar take yi don su fice,
Haroon sam yagaza fitowa saboda kunyar haɗuwarsa da sehrish baisan martanin da zata yi mashi ba, dama jiya ta yarda masa magana a cikin toilet ina ga yau da tasamu ƴanci Allah kaɗai yasan Zagin da zaisha, ga yunwa yana ji amma sai faman zarya yake aransa yana faɗin "Ke ma bazan ƙyale ki ba Yarinya saina ƙasƙantar dake kuma bazan fasa abunda nayi niyya ba akan Ki,*YANZU WASAN YA FARA* 🙆
Fitowa azmee tayi jikinta na sanye da doguwar riga ta atampha ta kashe ɗaurin kallabi, sai ƙamshi take cikin hanzari ta wuce kitchen saboda tunawa da Marshal Omar wanda bai fito yin breakfast ba kuma ba'a kai masa ba, shaf shaf ta shirya masa a tray ta wuce part ɗinsa ta shiga da Sallama babu kowa a falonsa hakan na nufin koma bacci bai tashi ba, ajiye masa tayi asaman ƙayataccen table ɗinsa sannan ta fuce,
Tana saukowa down stairs taci karo da haroon wanda ke tafiya cikin sanɗa zai shige kitchen wai don karya ci karo da Sehrish  girgiza kai azmee tayi aranta tace "Shi ko haroon ko lafiya yake faman tafiya cikin sanɗa haka kamar mara gaskiya, Ni wlh nama manta dashi ashe yana nan,'  Gyaran murya tayi tare da cewa "barka da fitowa mlm haroon," firgit yayi tare da juyowa ya kalle ta, ajiyar zuciya yasaki ganin azmee ce "Aunty azmee barka dae fatan an tashi lafiya, shine aka manta dani ina ta fama da yunwa yanzu da ban fito ba da shikenan sai dae yunwa ta kashe ni ko? Ya tambaya hada ruƙe qugu dama ransa a 6ace yake.........  Azmee tace "Kayi haƙuri wlh ni sam na manta ban lura da baka fito ba ba,"  ta6e baki yayi tare da cewa "koda yake dama ae ni ba'a sona na lura, bama kallon mutun ake mun ba acikin gidan nan kowa ya raina ni,"
Murmushi azmee tasaki tana kallonsa tace "kadaina cewa haka bana jin daɗi, koda kowa zai guje ka amma kasan ina tare da kai ko? Ka ta6a ganin inda UWA ta Guji ƊANTA?" tayi maganar ne don ta kwantar masa da hankali ganin ya ɗan fusata,  Sakin fuska haroon yayi sannan yace "Shikenan nadaina aunty azmee tunda baki so, yanzu dai a haɗa mun breakfast ɗina wlh yunwa nake ji har wani jiri nake gani,   Wuce sa azmee tayi tana cewa "a ina za'a kaima abincin anan ko a ɗakin ka," cikin sauri yace "Ki haɗamun kawai natafi da abuna ɗakina naci,Zai fiye mun kwanciyar hankali na"  Kitchen ɗin tashiga ta haɗa masa a tray sannan ta miƙa masa jikinsa na rawa ya kar6a ya wuce ɗakinsa,  Gefen gadonsa ya zuna hannunsa har kerma yake yi yana cusa abincin abakinsa, kamar daga sama yaga sehrish ta bayyana agabansa jikinta sanye da Kayan Sadaukai na Yaƙi, hannunta ruƙe da Zungureriyar wuƙa kanta na ɗauke da Kambun Sarauta, hankali atashe haroon ya fesar da donuts ɗin daya cunkusa abakinsa yana kallonta cike da tashin hankali, fashewa da dariya sehrish tayi tare da cewa "Kai Haroon! Ƙaryarka taƙare ! ka jima kana ƙuntatamun gashi yanzu Allah ya ɗaukakani, babu wata sauran barazana daga gare ka ta ƙare, nazo ne don na ɗauki fansa akan ka, yanzun nan zan fille kanka da wannan wuƙar ta hannu na,  Da ƙarfi sehrish ta ɗaga wuƙar zata fille ma haroon kai, aikuwa a firgice ya miƙe tsaye yana dafe saitin zuciyarshi a tsorace
Lokaci guda Sehrish ta 6ace masa 6aaat hakan na nufin ba ita bace idonsa ne ke masa gizau,amma shi tabbas ita yagani kodai yarinyar Aljana ce ? Ya tambayi kansa,.wannan ba kowa bace face Hafsat Bature Aljanar sehrish 👿 Koma wa yayi ya zauna yana ci gaba da cin breakfast ɗinsa anatse, yayin da ransa ke saƙa mashi abubuwa da dama game da mummunan ƙudirinsa
__________   💪   ______________
OMAR a hankali ya soma buɗe idanunsa bakinsa na ambaton addu'ar tashi daga bacci, yayin da zuciyarsa ke cike fal da son ganin Tagwayensa, tun da asuba daya sha maganin mura bacci mai nauyi yayi awon gaba dashi sai yanzu Allah yayi mashi ikon Farkawa daga bacci, a hankali yasa hannun sa ya janye blanket ɗin daya lullu6a dashi jikinsa na sanye da Night dress riga ce dai dai guiwa mara nauyi, fararen idanuwansa yafara kaiwa ya kalli agogon dake manne jikin bango ƙarfe 12 na safe yayi mamakin yadda lokaci ke gudu har haka, ko don yayi overdose na maganin muran daya sha ne yasa shi yin dogon bacci har haka,  Cikin sauri ya yunƙura ya miƙe direct toilet ya wuce , brush yafara yi yana tsaye agaban wash basin amma idonsa Fuskar Jahad da Hosana take hasko masa ta cikin mirro ɗin gabansa, shaf shaf yayo wanka ya fito jikinsa sanye da Bathrobe(rigar wanka) fara, wadda ta tsaya masa adai-dai guiwarsa, Marshal Omar kenan Son kowa ƙin wadda tarasa 😉  kai tsaye wuce wa yayi ya ɗauki wayarsa dake a saman gadonsa, sak irin ta sgr ce, Company ɗaya ce waya ce ta musamman domin Manyan jami'an sojoji irinsu kirar Companyn Iphone Ce, hamshaƙiyar waya haɗaɗɗiyar gaske wadda kuɗinta sun haura 30millions, ba kuɗinta bane abun mamaki ba a'a amfaninta shine abun dubawa, ƴar bala'en wayace bakowa ma zai iya Controlling ɗinta ba sai mamallakinta.  dannata ya soma yi Contact ɗinsa ya shiga kai tsaye numbar aunty BABBA ya laluba, ya buga mata Calling ta shiga ringing, burinsa tayi picking yasanar da ita cewa Zai shigo kaduna don ya duba su Hosana da Jahad, almost 3 times ba'a ɗaga kiran ba, domin kuwa wayar tabar ta agida, canza ra'ayi yayi ya dannawa Wayar Hafsat kira,
Suna a asibitin nan zaune saman waiting seats, bacci duk ya kwashe su daga zaune don daren jiya ba wanda ya runtsa sai da sassafe wurin ƙarfe 10 suka samu baccin wahala shima saboda likita yasanar dasu cewa Yarinyar da ranta bata mutu ba, farkawa ne kawai batayi ba doguwar suma tayi, shine suka ɗan samu natsuwa suka baje suna bacci kamar wasu shanaye ga uwar yunwa na cinsu, kiran Omar ne yashigo da ƙarfin gaske a wayr hafsat dake acikin purse ɗinta data aza saman cinyarta, a firgice suka farka su duka wuri wuri da ido, cikin hanzari hafsat ta zura hannunta cikin purse ɗinta ta duba me kira sunan MARSHAL OMAR ne ya bayyana, dafe ƙirjin tayi hankali atashe tace "MUNSHI GA UKU ! MOMMY YA OMAR NE KE KIRA"😳
  Mu haÉ—u ranar monday Insha AllahðŸ™
Kar amanta da paymemt wanda suka shirya sumin magana 08103884440, 300 ne VIP kuma 700 ga wanda basa ra'ayi a grp*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*
*🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
*Abban Sojoji part 2*
*EPISODE 7-8*
*AYAAN* arab name ne for boys means God's Gift (kyautar Allah) â¤ï¸
Waro ido waje aunty babba tayi tana faɗin "Shikenan komai ya ƙare, Hafsat kada ki ɗaga kiran nan, katse shi kwai , a rude take magana, Hafsat tace "Mommy how can i reject his calls ! Idan zuwa zai fa ? ba kwara na ɗaga naji mai zai ce ba, don mu son yadda za'ae mu dakatar dashi ba.....' ta ƙare maganar tare da ɗaga kiran ta ƙara a kunnanta tana Zabga sallama, Hankali atashe aunty babba ke cewa "Kisa wayar handsfree," cikin hanzari hafsat ta mayar da kiran handsfree don aunty babba tasamu damar jin abunda Marshal Omar ɗin zai ce,  Bayan ya amsa mata sallama yace "Zan Shigo kd yau insha Allah ki sanarwa Mommynki," yana faɗin hakan ya katse kiran since bfr hafsat tace wani abu, Cikin tashin hankali Hafsat ta janye wayar daga kunnanta,a wani slow tana kallon mommynta wadda itama kallon nata take yi ido azare,  Murya tamkar zatayi kuka tace "Mommy duk ke kika ja mana wannan bala'en da muke ciki, gashi nan daga ni har ke ba wanda ya runtsa daren jiya rabon mu da abinci ma tun jiyan, yanzu kuma gashi Ya Omar zaizo, Ina fata kin tanadi bayanin da zakiyi masa game da Twins ɗinsa da kika Faffasa ma fuska, ki ka canza musu kamanni, nayi imanin kema Ya omar bazai barki ba, sai ya Canza miki kamanni, don Allah naushi ɗaya zai ma kumatun nan naki Mommy sai an neme su an rasa a fuskarki,' Tuni ido ya raina fata, aunty babba tace "hafsat ki daina mun waɗan nan suratan naki ki barni inji dakaina, yakamata musan abun yi before Omar ya diro garin nan,'
Zama su kayi zugum kowa zuciyarsa na bugawa daram daram, kowa da irin idea dake zuwa masa akai,  Jahad kuwa na a ɗakin da aka kwantar da hosana dama gado biyu ne aciki, itama doctor sai da ya duba ta, baccin wahala kawai take yi saboda allurar da dr yayi mata don tasamu bacci, duk inta farka sai ta ambaci sunan Hosana saboda itace aranta, so take tama fi ƙarfin allurar da dr yayi mata, don ƙoƙori take ta tashi da ƙarfin gaske don taje ma hosana wadda ke kwance magashiyyan rai hannun Allah 😥
______________________________________
Bayan Omar ya kammala wayar fitowa yayi daga bedroom ɗinsa ya zauna a palor saman sofa yana yin breakfast ɗinsa anatse, wayarsa ce ta shiga ringing wadda ya ajiye agefensa, kai idonsa yayi ya duba Gwaggon katsina ce ke kiransa, murmushi yasaki don kusan kullum saita kira layinsa ta tambayesa ina Ƴa'ƴan Abusufyan ɗinta ya basu su gaisa, hannu yakai ya ɗauki wayar ya kara a kunnansa yana faɗin "Gwaggona kenan fatan kin tashi lafiya," Daga can 6angaren gwaggon katsina tace "Allah sarki Omar jiya ko isasshen bacci ban samu ba saboda tunanin ƴa'ƴan abusufyan ɗina, Jiya zuciyata tayi ta bugawa inaji kamar wani abu ya same su, dan Allah Omar karka bari a cutar dasu, Sai faman zuba take masa a waya sam taƙi bari yace wani abu har sai da ta gaji ta dakata da maganar sannan Omar yace "Ki kwantar da Hankalin ki goggo na, Ƴa'ƴan abusufyan ɗinki suna nan cikin ƙoshin lafiya,"  Ajiyar zuciya tasaki kafin tace "Suna tambayata ko? Suna atare da kai Omar? Ka basu dan Allah muyi waya mana,"  omar yace "Goggo kin manta suna a kaduna,ae gidan Yaya ishaq nakai su..." Kamar tana agabansa ta zabga salati tana cewa "La'ila ha illallah Mahammadar rasulillah Omar ! dama gidan Ishaq ka kaisu? Gidan wannan matar Shuwa mai ƙirar samudawa sam matar nan bata da Imani, zuciyarta irin ta kafuran farkon ce wlh, shikenan ni Allah kaɗae yasan wane hali ƴa'ƴan abusufyan ɗina suke ciki . ......fashe masa da kuka goggon katsina tayi,
Sam omar ya gaza gane ma goggon tasu, a tunaninsa haukan nata ne ya tashi, in ba haka ba ina matar ishaq keda aibu har haka, gashi kuma ta fashe mashi da kuka, cikin rarrashi yace "Calm down your mind Goggona, ƴa'ƴan abusufyan ɗinki suna cikin ƙoshin lafiya, yau ma nake shirin zuwa in dubo su,'   Cikin shessheƙar kuka tace "To shikenan amma dan Allah Omar nidai nafison su bar gidan matar nan, adawo mun dasu nan in basu kulawa kamar yadda na kula da mahaifinsu tun yana yaro," Murmushi Omar yasaki sannan yace "Insha Allah my aunt don't worry ur self abt them, suna Lou and insha Allah in naje zan basu waya ku gaisa kiji muryarsa may be u will be calm,"
 "Shikenan Omar kada ka manta sai na jika,"   Ya amsa mata da cewa "Insha Allah"
daga bisa ni su kayi sallama ya ajiye wayar yaci gaba da Cin breakfast É—insa,
Acan ciki kuwa tuni Sehrish ta shirya kayan mazan ne ajikinta tunda su ke gare ta, hijab kawai tasanya ajikinta brown colour, azmee kuwa dama atampa ce ajikinta, Mayafi kawai ta lullu6a a jikinta ba ƙaramin kyau tayi ba, suna a babban falon sai ga junaid shima ya sauko, bin shi da kallo sehrish tayi jikinsa na sanye da suits baƙaƙe kamar ma'aikacin banki, yayi kyau sosai acikinsu abun sai wanda yagani, sai faman murmushi yake saki da white teeth ɗin nan nasa kamar gonar auduga, "Gsky junaid bazan iya jerawa dakai ba, Irin wannan kyan haka," sehrish ta faɗi tana nuna shi da hannu,  Ƴar dariya junaid yasaki kafin yace "duk kyan da zanyi bazan fi ki ba, ke fa maca ce, ni kishi ma nakeyi don nasan yanzu zaki fara ɗaukar wanka da zarar munyi Siyayyar nan,"  Murmushi sehrish tasaki ita kanta har ta hango ta cikin Gown ta gayu wow, azmee ma murmushin take saki, atare suka jera suka fuce, a cikin Motar Junaid haɗaɗɗiyar gaske, Shi ke driving yayin da sehrish ke a gefensa sai faman fira suke suna zuba, azmee na a back seat tana sauraron su wani lokacin ma tana sa musu baki suna firar atare, suna ta tiƙar dariya abinsu gwanin burgewa, har suka isa katafaren shopping mall ɗin mai matuƙar girman gaske, sehrish taga haɗuwa yau dae karo na farko data fito kuma karo na farkon data fara ziyartar wuri irin wannan, atare suka fito suka shiga wurin, Mutane gasu nan kowa ya ɗau wanka ana ta siyayya ba kowa ya tsone mata ido ba face ƴan mata da samarin dake a wurin, duk sai taji kunya ta kamata ganin yarda Matasan matan dake a wurin siyayyar suka ɗau wanka iya wanka, ita kuwa kallo ɗaya za'ae mata ansan bazata wuce ƴar aiki ba,  6oyewa ta rinƙa yi abayan junaid da Azmeee, dariya kawai junaid keyi don ya gano dalilin dayasa sehrish jin kunya tana la6ewa abayansu,
Sam ruwan ido ya hana sehrish Sa hannu ta ɗauki wani abu, junaid ne kawai da azmee ke faman ɗebar mata kayayyakin sawa iri iri masu kyan gaske na mata, yawanci arab gowns ne, turkish dress, night dress, Pakistan, english wears komai jidar sa kawai suke yi, laces ne atampa ce, materials, shadda, Everything,  Duk tana tsaye tana kallonsu kowanne ya cike shopping basket dake hannunsa, sai dai in sun matsa nan tabisu, in kuma anzo abunda zata gwada tasanya su bata taje dressing room ɗin dake a wurin ta sanya, lokacin da suka zo wurin jerin panties da bra, hannu junaid yasa ya ɗauko brazier ya ɗago da ita yana cewa "Sehrish Ga wannan gwada mu gani," Sam bata lura ba tana ta faman kalle kalle, ganin hakan yasa shi ta6o hannunta yana nuna mata bra ɗin dake hannunsa yana cewa "Ina magana," aikuwa cikin jin kunya ta zaro ido tare da sa hannu ta rufe fuska tana faɗin "junaid dan Allah kadaina menene haka agaban mutane," fashewa da dariya yayi cikin mamaki yace "menene aciki? Kunya kuma ni bansan wannan zancen ba, ni dae ki amsa kawai kije ki gwada in tayi maki, in batayi ba acanza wata shine kawai,"  Hannunta na kerma ta karba tana ɗan kallon shi, har time ɗin dariyarsa yake Don shi mamaki ta bashi wai kunya,  Shiga dressing room ɗin tayi hada datso kopa, faskekan madubi ne aciki ya cike bangon, cikin hanzari ta tu6e hijab ɗinta da rigarta, ta shiga kiciniyar zira bra ɗin daker hada su sakin nishi,  Tsayawa tayi tana kallon kanta acikin mirrow ɗin wow, ta fito ɗas abunta dama tubarkallah masha Allah full ɗinsu suke, bra ɗin ta hau raɗau launin ta maroon colour ce, abunda sehrish take ma mamaki yarda akai junaid ya nemo bra dai-dai size ɗinta,duk jerin braziers ɗin dake a wurin, Cikin hanzari ta cire ta, ta mayar da rigarta da Hijab ɗinta, sannan ta fito, karaf suka ci karo dashi abakin ƙopan ɗakin,  a ɗan razane tace"junaid yaushe kazo nan," hannu yasa ya ɗan sosa sumar kansa yana cewa "Naji kin jima ne, shine nazo in ga ko kin gaza sawa ne, sai in taimaka miki.....," ganin yarda ta waro ido waje yasa shi dakatawa, muryarta har wani shaƙewa take yi wurin cewa "Junaid kana nufi brazier ɗin zaka taimaka mun nasa !!" ta tambaya a rikice,  Kai tsaye yace "eh mana," Jinjina kai sehrish tayi tare da wuce shi aranta tana mamakin hali irin na junaid shidae ba ruwansa komai normal ne a wurinsa,  tsayawa ta ɗanyi da tafiya ta ɗago ta kallesa Cike da tuhuma tace "Ya akai kasan size ɗina?  Da buɗar bakinsa sai cewa yayi "Ni dana ga Zahiri," Cikin sauri yasa hannu ya rufe bakinsa saboda su6ul da bakan da yayi, kamar zatayi kuka take kallonsa tana cewa "Junaid hakan na nufin ka ta6a gani na babu kaya ko"?  Girgiza kai yayi yana faɗin "No ba haka bane reeesh, baki fahimce ni bane, Ina nufin....," sam ya gaza samun amsar da zai bata gashi ta tsare shi da ido tana jiran amsar shi,   Muryar azmee ce ta katse su da cewa "tsayuwar me kuke yi ne? Ku hanzarta mana muyi mu kammala, yaushe har muka wuce wurin Saloon ɗin,"   cikin sauri junaid yace "Hakane aunty azmee muje kawai yanzu saura me ya rage," Ya tambaya yana kallonta
yayi hakan ne don ya gusarma sehrish da tuhumarsa da take yi, cikin sauri suka wuce tabi bayansu itama,
A ranar yini su kayi siyayya Kamar zasu kwashe kayan Mall ɗin,komai sai da suka siyar mata shoes & bags ne Cosmetics komai wannan ba abunda suka bari,  Daga nan suka wuce wurin haɗaɗɗen Saloon ɗin duk acikin Mall ɗin yake, a lokacin junaid ya koma cikin mota yana jiran su, Already sun kammala purchasing ɗinsu an jera Manyan akwatinan guda uku biyu sunfi girma a boot aka zuba su, Wasu kayan kuma na acikin Manyan Shopping bags an zuba su har a cikin back seat na motar,
Murmushi kawai junaid ke saki ya langwa6ar da kansa jikin seat É—in motar, babban burinsa shine yaga yarda sehrish É—insa zata fito amatsayin mace a fili ya furta "Can't wait to seee" tabbas yanzu ne yasan yasamu abokiyar rayuwa wadda zasu kasance atare na har iya tsawon rayuwarsu, shigowar sehrish rayuwarsa ta canza mishi wasu abubuwan da dama da yake kewarsu,daga ciki harda kewar Mommynsu da tatafi tabarsa tun yana jinjiri wannan abun ya ta6a mishi zuciya sosai raÉ—aÉ—in na'a ransa yana jin cewa duk cikinsu shike bata so, hakan yasa shima baya sonta duk in ta kira waya tana so abashi tayi magana dashi baya kar6a, har ila yau junaid bai ta6a ganin Mommynsu ba ido da ido sai dae a hoto, babu yarda batayi ba akan akawo mata shi Sydney amma abbansu yace muddin tana son ganin shi ta tako tazo da kanta in ba haka ba ita dashi har abada, saboda batayi mashi adalci ba,' wannan kenan
Ya jima yana tunane tunane shi kaɗae abunsa yana ta faman sakin murmushi, adai dai time ɗin Sehrish ta fito tare da Aunty azmee, Ƙaraso wa su kayi ta bude gaban motar ta shiga aunty azmee kuma ta shige baya sannan junaid ya tayar da motar yana faɗin "Har an kammala saloon ɗin"?  ya tambaya yana ɗan kallonta tace mashi "Eh,'.  "In munje gida za'a nuna min," ya faɗi da ɗan murmushi a fuskar shi, kai tsaye yabar bakin Mall ɗin yaja Motar kai tsaye ya nufi hanyar gida dasu duk da yaso su biya wurin shan ice cream amma shi kanshi a gajiye yake yafi buƙatar gidan don ya huta, Dama jikinsa sam ba irin na ƴan wahala bane,  Motarsu na shiga babban entry ɗin gidan adai-dai time ɗin kuma Motarsu Marshal Omar ta fuce daga gidan, Tasu na shigowa tashi na Fice wa, 🙅   Bayan yayi parking ɗin motar, wani sergeant ya ƙaraso ya kwashe akwatinan da junaid ya fito a boot ɗin motarsa, , Hada jakunku nan siyayyar na cikin back seat ɗin duk ya fiddo su, yayin da sojan ke kwashe su izuwa cikin gidan, Agajiye azmee da sehrish suka shiga cikin Babban falon bakowa alamar duk sun fita, azmee ta taimaka mata suka shigar da kayan ɗakin suka jibge su da nufin in sun huta an jera su a wardrobe ɗinta,  Cike da zumuɗi sehrish ta cire hijabinta don taga gyaran gyashin da akayi mata, Gaban mirror ta tsaya tana kallon gashinta, haɗaɗɗen gyaran gashi akayi mata mai haɗe da Twist,  Sai ta rinƙa jinta tamkar Queen saboda haɗuwa, ta jima tana kallon kanta a mirror kafin ta wuce toilet don yin wanka da alwala,  Shaf shaf ta fito jikinta ɗaure da toilet, wardrobe ta wuce ta samu riga da wandonta ta zura ajikinta sannan ta ɗauki hijab da dardumar salla ta shimfiɗa, ta kabbara sallah A natse ta Gabatar da sallar,
Bayan ta kammala Jiki na rawa ta cire hijab ɗinta ta ninke tare da abun sallar asaman gado ta ajiye su,   Zama tayi tana bubbude kayayyakin da aka siya mata na cikin jakun kunan, sam bakinta yaƙi rufuwa, wani haɗaɗɗen takalmi ta ɗauko high heels ta ciro shi daga kwalinsa tana gwadawa a ƙafarta ita kanta ta razana daganin yarda ƙafarta ta fito ɗass acikinsa gashi ash colour jikinsa duk kyalli yake ga wasu igiyoyi na ɗaure sa ya haɗu, Shigowa azmee tayi tana faɗin "Kai!kai! Irin wannan zallar kyau haka gaskiya naji tsoran haɗuwar da zakiyi anan," .   Dariya sehrish tayi tana cewa "dama yanzu nake so in jera kayan acikin wardrobe bansan ma ta inda zan fara ba,"  Azmee tace "kada ki damu ae shiyasa nazo saboda nata Ya ki jera su Muyi mu gama, akwai sauran aiki agabanmu ga gyaran cikin gida ga kuma aikin Kitchen,'  Miƙewa sehrish tayi ta janyo akwati nan biyu da hannunta izuwa wurin wardrobe ɗinta ta jingi ne su,itama azmee ta janyo ɗayan akwatin tana cewa "Ki barmun jeran kawai, kije ki gyara cikin gidan kafin na kammala Canza ma ɗakin nan naki kamanni," . Murmushi sehrish tasaki tare da cewa "Toh aunty azmee," Sai da tafara ɗaukar mayafinta a cikin wardrobe ɗin sannan ta fuce tana murmushi,
Babban falon tafara gyarawa duk da babu wani datti a tsaftacensa yake, shaf shaf tagama, cikin hanzari ta wuce upstairs don gyara ɗakin babban yayansu, tana cikin taka steps ɗin taji motsin mutun a down, juyowa tayi don taga kowane ne, Karaf idonta suka sauka akan na HAR0ON, sam yagaza ɗauke idonsa akanta kallon kallo suka shiga yiwa juna, duk a tunaninsa sehrish zata mayar masa da martani amma abun mamaki sai yaga tasakar mashi wani irin ƙayataccen murmurshin kashe zuciya tamkar ta soke shi da kibiya a ƙahon zuciyarshi haka yaji, don har saida yasa hannu ya tarbe saitin zuciyarshi, wani irin sabon kyau yaga yarinyar tayi mishi (nace ba kabari sai ta fara ɗaukar wanka tukunna munyi wannan maganar,"  Juyawa sehrish tayi cikin hanzari ta wuce apartment ɗin SGR, tabbas taso ta mayarwa Haroon martani amma daga baya tagane cewa ba buƙatar yin hakan, yanzu fa ita tamkar Princess take ƴa ɗaya tak ga Shugaban sojoji kuma ƙanwar sojoji, dole ne taja class muƙami iya muƙami, wannan kaɗae ya isa ya kashe haroon saboda ƙululun baƙin ciki,  Zuru haroon yayi sam yagaza motsi daker ya iya ɗaga ƙafarsa ya soma tafiya jiki a mace, Har time ɗin tafin hannunsa na a dafe da saitin zuciyarshi  Bin shi da kallo junaid yayi wanda fitowar shi kenan daga sashen abbansu, Ƙarasawa yayi cikin sauri ya nufi haroon yana faɗin "Yaya Haroon lafiya meke faruwa ne, naga ka dafe zuciyarka, ince dai ba wani abu ya same ka ba,'   ɗagowa da ido haroon yayi yana kallonsa yace "Jini Junaid," Jin wannan yasa junaid tallabo shoulders ɗinsa yana faɗin "Subhanallahi jini kuma a ina yaya haroon,"   da wannan muryar tasa ta ƴan giya yace "Yanzu duk jinin dake kwaranyowa daga zuciyata ba ka gani ba? Kibiyar da aka soka mun fa? Ko shima baka gani ba"? Ya faɗi a susuce yana kallon junaid, Baki asake junaid ke kallon ikon Allah shidai baiga komai ba a ƙirjin haroon hannunsa ne kawai daya tallabe wurin, Cikin ruɗi yace"yaya haroon babu komai fa a wurin hannunka ne kawai daka sa ka dafe,  Muryar tamkar zaiyi kuka yace"Manxon Allah yayi gaskiya Junaid, shikenan bakomai jeka kawai Allah yayi maka albarka, ya kare ka daga sharrin Maƙiya,  Ya faɗi tare da janye hannun junaid daga kafaɗarsa ya wuce sa yana cigaba da sambatu   Girgiza kai junaid yayi tare da cewa "Allah ya baka lafiya yaya haroon ya yaye maka wannan shaye-shayen da kake fama dashi,"
Yana gama faɗan hakan ya wuce direct ɗakin sehrish don yagaza runtsawa burinsa kawai yaganta ta zura kayan mata ajikinta, yana shiga ya samu azmee tana faman jejjera mata kayan a cikin wardrobe ɗinta, ko ina da abunda aka zuba aciki, gasu nan komai ajere, gwanin kyau,  Jin sallamar junaid yasa ta juya da fara'a tana amsa mashi,  Yace "Aunty azmee ina Sehrish ne i thought zanzo na same ta anan ne,"  Azmee tace "ae tuni ta fita don gyara cikin gidan kasan munbar aiki dayawa shiyasa bamu samu hutu ba,"  ɗan zumbura baki yayi tare da cewa "Aunty azmee wane aiki kuma? Mu dawo agajiyen sai kuma ta kama wani aikin, gaskiya bai yiyuwa zanje na dakatar da ita,' ya faɗi tare da juya ya fuce Murmushi azmee tasaki aranta tana fadin "Romea kenan, Allah dae yasa sehrish tazama mallakin ka, duk da nasan abune mai wuya ayi mashi aure at his age, bansani ba shi da ita waye zai raini wani shi shagwa6a ita kuma shiririta, amma kuma raina na bani cewa akwai wanda sehrish ke so ga dukkan alamu...............   ta ƙare maganar zucin nata ayayin da ta koma gaban dressing mirror ɗin sehrish dayake wayaam babu kayan kwalliya kona shafawa illa kwalba ɗaya tak na turaren junaid da tata6a satar mashi wanda har yau bata ta6a amfani dashi ba,    Janyo trolley ɗin dake ɗauke da cosmetic tayi ta shiga jera mata su, da turarurruka da mayukan jiki masu kyau da ƙamshi da sauransu, sai gashi mirror ɗin yafito sosai na ƴar budurwa,
Cikin ƙanƙani lokaci rishi ta kammala gyara masa part ɗinsa, da wata irin yunwa ta fito ga bacci tana ji tana saukowa down suka ci karo da junaid dake tunkaro stairs ɗin,  da murmushi a fuskarta tace "Junaid dama idonka biyu ae nayi tunanin kana can kana sharar bacci,'
yatsina fuska yayi tare da cewa "taya zan iya bacci bayan banga gyaran gashinki ba, zuwa nayi ki nuna min in gani," ya faɗi hada ruƙe ƙugu,
Dama tana kallon fuskarshi tasan rigimar ta motsa ga Idonshi sai faman lumshewa suke yi alamar bacci yake ji over,  Saukowa ta yi tana cewa "Shikenan zan nuna maka ammma kabari nafara samun natsuwa tukunna, yanzu kitchen zanje na gyara kuma yunwa ma nake ji,"    Shiru yayi baice komai Ba dayaso hannu kawai zaisa ya tu6e mayafin data yafa, abunda ya hanasa yin hakan baiso wani yagani cikin Yayyensa balle ya ƙyasa, don kishinta yake ji ayanzu kamar kamar me,  Shiga gaba sehrish tayi ta nufi hanyar kitchen, cikin hanzari yabi ta yana faɗin "Nima yunwar nake ji, zan tayaki mu gyara kitchen in mun kammala cin abincin atare,    "Shikenan bita zaizai," ta bashi amsa tana dariya, shima dariyar yayi jin sunan da tasa mashi,   "Idan baki so zan daina bin ki,' ya faɗi ayayin da suke shiga kitchen ɗin,   Sehrish tace"Nafison hakan ae, saboda kana ɗebe min kewa sosai,"  Jin hakan yasa junaid sakin murmushin murna,   Wuce wa yayi yazauna saman ɗaya daga cikin dining chairs ɗin dake kewaye da dinner table yana cewa "Ki haɗa mana corn flakes kawai mu sha, in akwai snacks ki haɗo mana dashi,  Ta amsa mashi da "Toh,"
A cup biyu ta haÉ—a musu sannan ta haÉ—o masu da snacks suka zauna suna sha suna fira, â? ________________AUNTY BABBA______________________
Suna cikin wannan fargabar wayar hafsat ta sake yin ringing, cikin hanzari tunkan tasa hannunta ta ɗauka aunty babba ta riga ta ɗaukar wayar asaman cinyarta, a tunaninta Omar ne amma tana dubawa taga Sunan My Dad ya bayyana, ɗagowa tayi ta kalli hafsat hankali atashe tace "Abbanki ne ke kira, Allah yasa dae ba dawowa zaiyi ba, ya salammm ni bansan meke faruwa dani yau Ba Hannu hafsat tasa ta kar6i wayar, ta amsa kiran sannan takara a kunnanta tana zabga Sallama, Janar ishaq ya amasa mata da cewa "Wa'alaikum salam my daughter, ina mommynki take ne, i ave been trying her phone number tana ringing ba'a ɗagawa why"? Ya tambaya yana jiran amsa, Murya na rawa hafsat tace "am..dama...umm...tabar wayar a ɗaki ne ina ji, saboda ta shiga kitchen,  tayi maganar tana kallon mommyn nata data ke faman dafe zuciya,tana sauraron mai zai ce saboda wayar na a handsfree,.   Genar ishaq yace "shikenan ki sanar da ita cewa cikin week ɗin nan zan dawo insha Allah,".    "Shikenan daddy Allah ya dawo daku lafiya," sukayi sallama ta ajiye wayar tana faɗin "Tabɗijan Can akwai matsala fa,"  Aunty babba kuwa miƙewa tayi tana faɗin "Nashiga uku ishaq zai dawo ga zuwan Omar yau, bansan me zan fuskanta ba a wurin kowannan su... '. Muryar hafsat ce ta katse ta da cewa "Amsar fa abayyane take mommy, ke ma kin sani Allah,saki ukun nan sun Wajaba Akan ki muddin Abba yaji abunda kika aikata, saboda wancan karan Ladi mai aikin mu da kika ma bugun mutuwa sai da ya aika ki maiduguri bayan marukan da kika sha awurinsa ina ga waɗan nan bayin Allahn da kika naƙasa har Su biyu, gasky mommy kin shiga Uku, ga kuma ƴa Omar zaizo ni addu'ata Allah yasa Abba kada ya sake ki yabarki kawai da hukuncin Omar na zuwa prison kowa ma ya huta.....  Hankali tashe aunty babba tace"Hafsat prison fa kika ce? So kike akaini can kin gaji dani kenan"? Rai a6ace hafsat tace "dole nagaji dake mommy, duk ke kika ja mana wannan masifar da muke ciki muna zaman lafiyar mu,' ta faɗi a ƙuke hada buga tsoki kamar bada uwarta take magana ba,
Jinjina kai aunty babba tayi batare da tace komai ba, adai dai time ɗin dr ya fito daga ɗakin da aka kwantar dasu hosana, jiki na rawa tabishi tana faɗin "dr ya jikin nata ta farfaɗo,"?  dr yace "Alhamdulillah tafarka yanzu haka bacci take yi itama saboda allurar da nayi mata,"  ɗaga hannu tayi tana cewa "Alhamdulillah har naji ɗan sauki, amma dr babu yarda za'ae ciwon fuskarsu ya warke nan take? kumburin ya sa6e, ni dr kodai surgery za'ae musu ne acanza fuskar,' tayi maganar in serious matter tana kallon shi,   Wani irin kallo dr ɗin ke yi mata yama rasa amsar da zai bata,   wuce wa gaba yayi ya tunkari Office ɗinsa yana cewa "sam Bazaiyiyu ba gsky,ba muyin irin wannan aikin anan, kuma fuskarsu batayi komai ba da za'a canza musu Ba,da alama madam kema kina buƙatar Aduba ki,' sarai taji abunda dr ɗin yace amma bata ji zafin maganarsa ba, saboda bata cikin natsuwarta a yanzu,
Yini su kayi cikin fargaba ba salla ba salati dama ba ita bace agabansu ba, an saba haÉ—a salloli ayisu a lokaci guda,Saboda duniya aka sa agaba Ba lahira ba,
gajiya su kayi gaba ɗayansu da zaman asibitin ga uwar yunwa kamar suyi hauka, ga zullimi da fargabar zuwan Omar, ganin har Magrib tayi babu kiran Omar yasa suka fidda tsammani da zuwan shi,  Ƙarshe basu jira dr yayi discharge ɗinsu ba, aunty babba ta ɗauko hosana dake kwance saman gado agalabaice ta sa6o ta a kafaɗarta ta fito da ita, sai cikin mota ta kwantar da ita, Jahad ma tashiga motar baiwar Allah ga zazza6i tana ji, gashi dr yace suna buƙatar jini su duka biyun amma babu yarda zasu yi, rayuwarsu a tagayyare sai yarda akayi dasu,  Shiga motar hafsat tayi mazaunin driver aunty babba na gefenta suka ja motar suka bar asibitin, a time ɗin har dr ya biyo su da sauri sauri don ya dakatar dasu amma ina tuni har sun bar arean asibitin.............  A tsiyace ta shiga da motar cikin gidan tayi parking ɗinta, tana fito wa ta wuce ciki saboda jirin da take ji na yunwa, fitowa itama aunty babba tayi sam bata tsaya taɗauki hosana ba ta shige ciki itama,  Hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba ganin sun tafi sunbar hosana kwance sai faman nishi take saki numfashinta na fita daker-daker,   bata son yaya zatayi ba ta ɗauke ta saboda itama babu sauran ƙarfi ajikinta, fitowa tayi daga cikin motar tana faman zubda hawaye, Iya cuta dae an cuci rayuwarsu,  Ganin yarinya tsaye abakin mota yasa wani soja ƙaraso wa yana faɗin "Lafiya dai ƴan mata meke faruwa ne,"   Cikin shessheƙar kuka jahad tace "ƴar uwata ce ciki kwance bata lafiya bansan yarda zan shiga da ita ciki ba,"   Sojan yace "Can I help"? Jahad tace masa "eh" saboda bata da wata mafita da ta wuce hakan,  Buɗe motar yayi ya zura hannunsa ya sungumo hosana dake kwance magashiyyan ya ɗaurata a kafaɗarta ya shige da ita ciki jahad ta bi bayansa,   A saman 3 seater ya kwantar da hosana, jahad tayi masa godiya sannan tasamu wuri daga ƙasa ta zuƙunna fuskarta na dai-dai saitin ta hosana, Hawayen fuskarta har ɗiɗɗiga suke yi a fuskar hosana, addu'o'i tashiga karantowa tana tofa mata,.  Duk hosana na jinta tana so ta buɗe idonta amma ta kasa saboda kumburar da su kayi, tana so ta buɗe bakinta tayi ma Jahad magana amma tagaza saboda haƙoranta kansu sun raunata sosai don ba'a rasa mai girgiɗi acikinsu, ga la66anta da sukayi suntum sam bata iya motsa su, Cikin kuka jahad tace"Hosana na sani nasan akwai abunda kike son faɗa mun amma kin kasa, kada ki damu ina jin duk wani raɗaɗi da kike ji azuciyarki, inaji inama ace zan iya ɗauke maki zafin ciwon da kike ji da tuni nayi wlh.......taƙarasa mgnr tare da kifa kanta ajikin hosanna,sun jima a haka wulaƙance babu wanda ya leƙo su, sai daga bisa ni hafsat tafito har tayi wanka da alama ta canza kayan jikinta, doguwar riga ce tasanya har ƙasa, ta ɗaure gashin kanta,  Binsu da kallo tayi gwanin ban tausayi ita kanta duk rashin imaninta yau ta tausaya ma twins ɗin,girgiza kai tayi tare da wuce wa ta nufi kitchen,  Jim kaɗan sai gata ta fito hannunta ɗauke da tray mai girma, Tea set ne ɗauke asaman shi, sai French toast ɗin da ta hado masu dashi da sauran snacks, duk da tasan ma daker zasu iya ci   Bedroom ɗinta ta shigar masu da shi ta ajiye Tray ɗin asaman table ɗin dake a dab da gadonta, Sannan ta fito ta nufe su jin takun tafiyar hafsat yasa jahad ɗagowa daga kwancen da take tana kallonta da rinannun idanuwanta da suka jigata,      Hafsat batayi mata magana ba hannu kawai tasanya ta cicci6i hosana ta ɗaura a kafaɗarta sannan ta wuce izuwa bedroom ɗinta tana cewa jahad "Ki biyo ni,"  Cikin sauri jahad ta tashi tabi su cikin ɗakin, kwantar da hosana tayi asaman shimfiɗeɗen gadonta, sannan ta juyo ta kalli jahad tace "Ga tea nan da snacks nasan kina jin yunwa ki ɗaure ki sha,'   Girgiza kai jahad tayi tana cewa "Bazan iya cin komai ba, "Soboda me"? Hafsat ta tambaya tana kallonta,  Jahad tace "Sabodo ƴar uwata, bata ci komai ba,idan naci ita kuma fa"?   Shiru hafsat tayi jikinta yaɗanyi sanyi aranta har tana mamakin dama har yanzu akwai ƴan uwa masu ƙaunar junansu haka aduniya? Jinjina kai tayi kafin tace " kada ki damu, zan ƙara dubata yanzu insha Allah,zata ji sauƙi,"  Shiru kawai jahad tayi,amma fa ba zancen Cin abinci agare ta muddin hosana bata ji sauƙi taci ba itama, sai dae yunwa takashe ta,
 "Ave a seat," hafsat ta faÉ—i tana nuna mata saman gadonta, Jahad tace "Ina so nayi sallah tukunna," ta6e baki hafsat tayi tana cewa "okey ga toilet nan ki shiga,"  wuce wa Jahad tayi ta shige toilet É—in tana rufe Æ™opa tafashe da kuka mai cin rai tunaninta yanzu shine yarda zasu gudu daga gidan gaba É—aya, don yanzu ta kwammace Su Æ™are rayuwarsu a titi akan su faÉ—a hannun wani, tunda abun nasu ba sa'a kowa baisan taimakonsu don Allah batare daya cutar dasu ba,mutun huÉ—u kawai tasan suna da kyakkyawan niyya akansu, tsohuwa wadda Allah yayiwa rasu sai Goggon katsina da aunty saude da Yaya Omar É—insu.....   hafsat na jiyo kukan jahad dake acikin toilet, jikinta duk ya Æ™ara mace wa, karo na farko da ta fara jin tausayin wani aduniyar nan,  Â
   gaban mirror ɗinta taje wata roba ta ɗauko ta magani na shafawa a ciwo mai kashe raɗadi,  Dawowa tayi ta zauna saman gadon ta buɗe murfin tasoma lakuto shi tana shafa ma hosana a fuskarta, cikin lokaci ƙankani wurin yayi mata wani irin sanyi tamkar an ɗebe ciwon,  "Sannu ya jikin naki," hafsat ta tambaya tana kallon hosana wadda ke ɗan buɗe ido a hankali, sam ta kasa magana,   pillow hafsat ta janyo ta sanya mata kan gadon,sannan ta taimaka wurin tada hosana zaune ta jingine ta ajikinsa,  jikinta sai faman kerma yake yi, cup hafsat ta ɗauka ta shiga haɗa mata tea,bayan ta kammala ta sheƙa mata dashi da wani kofin donya rage zafi daga bisani taimaka wurin bata abakinta, la66anta har rawa suke yi wurin buɗesu saboda wata irin mahaukaciyar yunwa da take ji, sosai tasha tea ɗin kaf tashanye har dae hafsat ta ƙara haɗa mata wani ta bata,   Jahad ba ƙaramin sanyi taji aranta ba ganin yadda hafsat ke kula da hosana tayi mamakin yarda take bata tea abakinta, tsayawa tayi tana kallon su har sai da hafsat ta juyo ta kalle ta tace "ki buɗe closet ɗina akwai hijab ki ɗauko tare da Sallaya," Bude wa jahad tayi ta ɗauko hijab tasanya sannan ta shimfiɗa carpet ɗin tashiga yin sallah Hada isha'e tayi wadda ake cikin kira,  Daker hafsat tasamu hosana taci kaɗan daga cikin snacks ɗin data kawo mata saboda ciwon da bakinta ke yi mata, tea ɗin dae ne tasha sosai,   Gyara mata kwanciya tayi, sannan ta sanya bargo ta lullu6e ta,   tashi tayi ta koma saman doguwar sofa ɗin dake facing gadonta ta haye sama ta kwanta itama,.    Bayan jahad ta kammala sallar ta ninke mata abun sallar da hijab ɗin ta mayar dasu inda ta ɗauko su,   Sannan ta koma saman gadon ta haye, ta soma haɗa tea ɗinta tasha tana ci tare da french toast ɗin da hafsat ta haɗo masu, sosai taci don bata rage komai ba duka ta lamushe,
Bayan ta kammala ta shiga cikin bargon da hosana take ta kwanta itama, janyo ta tayi jikinta ta rungume ta tana kiran sunanta "hosanna ya jikin ki"? Har yanzu akwai raɗaɗi ko"?  daker tace "Eh," Jahad tace "kiyi haƙuri kinji, insha Allah bazamu ƙara shan wahala ba,inaji araina komai ya kusa zuwa ƙarshe bansani ba ko mutuwa zamuyi ba shine sauƙin mu Allah kaɗai yasani,   saurarawa tayi don jin mai hosana take cewa, saboda fuskarta na'a kwance achest ɗin jahad,sam sautin bai fita sosai   "Bana jinki hosana, kibar magana kawai kada ciwonki ya ƙara raunana,"   Shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, bakomai take son faɗama jahad ba face sunan YA OMAR da take kira.....................................*💋💋🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
*EPISODE 9-10*
https://youtu.be/rnmDunstSN4
Abun da ya faru MARSHAL OMAR bai samu zuwa kaduna ba sakamakon Emmergency Call din daya samu daga wurin Abbansu cewa yana bukatar shi A headquater dinsu, a lokacin Motarsu har ta fita daga garin Abuja amma suka juyo da hanzari saboda Omar baya wasa da Omarnin mahaifinsa ko musu baya iyayi mashi, duk da yadda ya matsu akan son ganin su hosana da jahad amma haka ya haƙura😔
Tun bayan da suka kammala shan corn flakes junaid ya wuce bedroom dinsa saboda dama agajiye yake, sehrish kuwa sai da ta tsaya a kitchen din har azmee tazo suka fara aiki, cikin kankanin lokaci suka kammala dinner, sannan ta wuce bedroom É—inta ta kwanta tasha bacci har wurin magrib sannan ta tashi donyin sallah, bayan ta kammala jiki na rawa ta bude wardrobe dinta, tsayawa tayi saboda ruwan ido ta ma rasa me zata sanya acikin kayan, hannu tasanya ta janyo wata haÉ—aÉ—É—iyar Gown black colour mai kyalkyali masu daukar ido, jinjina kai tayi tare da cewa "Wannan zan sanya," tayi maganar tare da hanging dinta asaman murfin wardrobe din, shaf shaf ta tube riga da wandon dake jikinta ta tura su, cikin laundry basket dinta, sannan ta dauki rigar ta shiga kiciniyar zira ta ajikinta, bayan ta kammala ta koma gaban mirror tana kallon kanta ta cikinsa, fuskarta dauke da murmushi tana tuna yaushe rabon da taji ta acikin kayan mata, kayan ma irin wannan sabbi masu kyau, rigar tabi shape din jikinta,hannunta mai dan tsayi ne wanda ya tsaya dai-dai elbow dinta,Jujjuyawa tayi tana Æ™arewa kanta kallo, kafin tasa hannu cikin jerin Perfumes dinta ta dauko kwalbar turaren TOUCH ta feffesa ma jikinta har wani lumshe ido take yi saboda yarda fragrance dinsa ke dakar hancinta, bayan ta mayar da turaren ta koma cikin wardrobe din ta É—auko mayafi white colour tayi rolling dinsa irin lagen da larabawa suke yi masha Allah ðŸ˜
Kama hanyar fita tayi tana bude kopan azmee na sanyo kai dama dakin nata ta nufo itama, ganin yarda azmee tasaki baki yasa sehrish sa hannu ta rufe fuska don tasan kallon na menene,  "Nama rasa mai zance irin wannan kyau haka? Yarinya kamar ƴar larabawa ashe dama haka kike da Kyau ga ki dirarra,'?  Cikin jin kunya sehrish tace "Aunty azmee ko fa makeup banyi ba, i know u are just teasing me,  Azmee tace "Reesh ae ko ba kiyi kwalliya ba kyau kike, ae ni ban ma so kiyi kwalliyar yanzu, don banson ki rikita samarin gidan nan, mu rasa wa zamu ba acikin su,'  "BABBAN YAYA' ta faɗi acikin zuciyarta a fili kuma tace "Mai rabo," dariya azmee tayi tana cewa "Toh Allah yaba mai rabo sa'a time kawai zamu jira muga wanene wannan in da rai da lafiya,'  Murmushi kawai sehrish ke saki, suna cikin wannan tsayuwar motocin su suka shigo atare mai ɗauke da jiniya, azmee tace "Alhamdulillah shikenan ma, tun da kin shirya in suka shigo ki tabbatar kin kaima Babban yayansu dinner dinsa tare da Omar, yanzu ma na kammala jera na dining din basu kai ga saukowa sunci ba, dama Twins ne da suka dawo bada jimawa ba sai Junaid da HAROON, just zanji da sauran kawai,'  ta ƙare bayanin tare da kama hanyar fita daga ɗakin tana nanata mata,  Sehrish ta amsa mata da "toh insha Allah,"    cikin sauri ta koma wurin window dinta ta janye labulan ta zuge glass din tana hangensu,   kowannansu agajiye ya fito daga cikin Motar, Abbansu ne tare da marshal Omar sai SGR, Abbansu na sanye cikin kaki, haka SGR army trouser ne ajikinsa sai shirt light green mai gajeran hannu sun ɗame jikinsa, Omar kuma Shigar dazu ce ajikinsa wadda yayi shirin Zuwa Kaduna dazu,
tunda Armstrong ya buɗe masa mota ya fito yake faman lumshe ido hannunsa ɗaya na acikin sumar kanshi yana yamutsa ta, kallon shi Abban su yayi tare da cewa "Ko dae saina taimaka na goyaka ne? Naga alamar baka iya tafiya," ɗago da eye balls dinsa yayi ya kalli Abban nasu sannan anatse yace "Dad kenan, ni da kai wa zai goya wani? kai ma ka sani,"   Yayi maganr tare da soma tafiya abban nasu kam dariya yayi yana cewa "Oh kana jin kanka Tamkar giwa ko? Ae ba abun mamaki bane kaga na sa6eka abayana, in banda ma yanzu daka zama jibgege haka ga tsayi nan nan nake ɗaukarka kana yaro har goya ka nake yi," duk Omar na jinsu yana murmushi kawai saboda atare suka jera suka nufi cikin gidan,  ɗan gyaran murya yayi tare da cewa "Abba yanzu ae sai dai ka goya grandchild dinka masu zuwa," Omar ya faɗi,  Abban su yace "hmmmm taya hakan zata faru bayan ƴan bukulu sun hana ruwa gudu, burina kenan kullum kamar yadda na haifa nima nawa su haifa amma abun takaici duka ya'yan nawa babu wanda ya ajiye ko budurwa bayan ni tun ina 20 years aka sanƙamamun aure muka sha soyayya gaba ɗaya,'  Omar yace "Kada ka damu Abba, Insha Allah burin ka zai cika, in har hakan zaisa ka farin ciki, kawai acigaba da yi mana addu'a,'   Jinjina kai abbansu yayi yana ɗan kallon SGR dake gefensa shiru tamkar baya jin me suke cewa,   Ruko hannunsa yayi cikin nasa sannan yace "kai fa Son, Naji baka ce komai ba ? Ko baka son farin ciki na ne?  yatsina fuska yayi tare da cewa "In dai yaron da zaka goya ne zan kawo maka shi,'  "Uwar fa"? Abban ya tambaya adai dai lokacin da suke shiga babban falon SGR yace "Babu," dariya omar kawai yake yi.abbansu kuwa baki sake yace "Shege zaka kawo min,'?  "Ko baka so ne"? Sgr ya tambaya shima da zolaya,  Abbansu yace "Ae da babu gwara ba daɗi, akawomin inaso,"   Omar yace "So funny wlh, abba son jikokin harya kai haka, to. Insha Allah ba shege acikinsu, Original zaka samu daga gurin kowan nan mun, ' cike da nishaɗi suke fira kamar bazasu iya rabu ba, wuce wa Abbansu yayi part dinsa, shima SGR tare da OMAR suka wuce Uptairs nasu parts din, 💪   Tun da Omar ya shiga bedroom dinsa ya rage kayan jikinsa toilet yashiga ya yi wanka, yafito ya zura kayan baccinsa, har cikin ransa yaso ya kira Aunty babba don abasu Hosana yaji Muryarsu amma ransa yana bashi cewa yanzu sun isa suyi bacci, wannan dalilin ya hana shi calling ɗinsu,
Fitowa parlor dinsa yayi yasamu wuri saman sofa yazauna hannunsa ruƙe da wayarsa, sai lokacin yake dana sanin rashin daukar su hosana da jahad hoto ya ajiye acikin wayar shi koya samu na rage kewarsu, yana cikin wannan tunanin wayarsa ta soma ruri karatun kur'ani Ne ringin tone dinsa duba sunan daya bayyana a screen dinsa yayi nan take sunan*ABUSUFYAN*ya bayyana muraran,  Cikin hanzari ya ɗaga ya kara a kunnansa "Assalamu Alaikum Uncle Sufyan yau an tuna dani ne"?  On ther other hand ABUSUFYAN yace "Ko da yaushe cikin tunawa nake yi dakai Omar, nayi trying number dinka dazu baya shiga, kuma na jaraba ta RAFAYET tana ringing amma bai ɗaga ba,'  Omar yace " Kash ! rashin sani ɗazu ne na kashe wayar muna aiki ne shiyasa,"   Abusufyan yace "Dama inaso na maka magana ne About wannan yaran da goggon katsina ta ƙaƙabamun a matsayin ya'ya na"?  Murmushi Omar yasaki kamar yana agabansa yace "Ae ko ɗazu da safe ta kira ni awaya, kusan kullum ne sai ta mun Complain akan ƴa'ƴan abusufyan ɗinta,'   Abusufyan yace"Allah sarki, Nima tana kira na tana mun complain akan nasa ka mayar mata da ya'yana wuri ta, ynx ina yaran suke ne? Ya tambaya yana jiran amsa Omar yace "A gidan general ishaq suke da zama, can na kaisu,"   "Ina iyayen su suke ne"? Ko yan uwan matar ishaq din ne? Ya tambaya  Omar yace "A'a Uncle yaran fa basu da kowa kamar yadda suka sanar mun, na haɗu dasu ne a asibiti cikin mawuyacin hali tagwaye ne baza su wuce 17years ba Suna buƙatar taimako,   Ajiyar zuciya abusufyan yasaki kafin yace "Meyasa ba zaka dawo dasu nan ba cikin abuja kusa da kai ba"?  "Uncle kaima ka sani, zaman su anan bazaiyi yu ba, maza ne mu duka duk ba wannan ba AMMI bazata ta6a lamuntar wani bare ya zauna acikin jinin ta ba,especially su da suka kasance basu da asali,' bayani yake masa tamkar yana agabansa  ɗan gyaran murya abusufyan yayi kafin yace "Listenin to me OMAR! kana da kyakkyawar niyya akansu, inaso ka kaddara aranka cewa waɗannan yaran jinin ka ne, kasanya wa ranka cewa Ƴa'Ƴa na ne, ya'yan ƙanin mahaifin kane *ABUSUFYAN* ina so ka basu kulawa Omar ! Dan Allah kada ka bari su wulaƙanta kayi mun wannan alƙawarin.......  Jikin Omar ne yayi mugun sanyi jin abun da Uncle Abusufyan ke faɗamasa, yanayin sautinsa da yadda yake yin kalamansa haƙiƙa ya ta6a Zuciyar Omar sosai, tunani omar yashiga yi aransa har sai da Abusufyan yace"Naji kayi shiru OMAR,"  Cikin sauri yace "Insha Allah Uncle i wll take care of them more than u think, nima inajin su araina sosai Uncle, ina ƙaunar yaran har cikin raina,  yana iya jiyo sauke ajiyar zuciyar Abusufyan alamar hankalinsa ya kwanta kuma yasamu natsuwa da bayanin Omar,  ABUSUFYAN yaci gaba da cewa "OMAR! INA SO KA DAWO DA YARAN NAN GIDA NA DAKE ANAN SU CI GABA DA RAYUWA, KA SANYA MUSU SECURITY TARE DA MAI AIKIN DA ZATA KULA DASU, INA SO SU RAYU ACIKIN GIDA NA, KAYI MUN WANNAN ALƘAWARIN!!!"   runtse ido Omar ya ɗanyi yana jinjina kalaman Uncle din nasa daga bisa ni yace "Insha Allah Uncle zanyi komai kake so, zan dawo dasu nan acikin gidan ka kamar yarda kake so,"   Sun jima suna waya kafin daga bisa ni su kayi sallama, ya ajiye wayar yana mai tunani iri-iri aransa, yana ji aransa in ya ɗauke su hosana daga gidan aunty babba tamkar baiyi mata adalci ba don ya Lura tana son yaran kuma sun saba dasu anya kuwa zai iya cika alƙawarin Uncle Abusufyan Na dawo dasu hosana cikin Abuja da zama!!? 😟
  Yana cikin wannan tunanin Sehrish ta shigo da sallama, batare da ya ɗago ya kalle ta ba ya amsa mata sallamar, sam ransa ajagule yake uncle dinsa ya ɗan ruɗa masa brain ɗinsa  Tray na a hannunta ƙarasawa tayi tare da gaishe shi "ina yini ya Omar," ƙiris ya rage omar ya ɗago ya kalle ta saboda Voice dinta tayi mashi kama da ta JAHAD, amma yabar Abun a matsayin muryar mai aikinsu ne ya koma masa ta Jahad Saboda kewarsu da yayi sosai Amsa mata yayi da cewa "Lafiya lou"
  Ajiye masa tray din tayi mai dauke da food stuffs dinsa asaman table Din dake a front dinsa sannan ta juya takama hanyar fita tana jiyo shi yana furta "ngde,"   Sauƙin kan MARSHAL OMAR yana matuƙar burgeta, babu ruwan shi ba kamar SGR ba, yana da IZZA ta wani bangaren kamar abinci muddin takai masa sai tayi saving ɗinshi, amma Omar sam baya buƙatar wannan kawai daga an kaimasa shi yake zuba abunshi yaci,  Saukowa tayi down a lokacin har su Twins da kanal yusuf Sun hallara suna cin dinner dinsu, tayi mamakin ganin babu Abbansu da junaid may be yana a part dinsa azmee takai masu acan  Gaishe su tayi gaba ɗaya suka ɗan dago suna kallonta, Kanal yusif ya amsa mata da sakin fuska amma Ayaan da jahan kuwa sai dai suka bita da ido,😡
 Har bugun zuciya take ji in ta gansu cikin hanzari ta shige kitchen ta shirya ma SGR dinner ɗinsa ta fito ɗauke da tray ahannu ta nufi hanyar upstairs dinsa,
  Da sallama ta shiga palor dinsa baya aciki, Æ™arasawa tayi ta ajiye masa kayan abincin saman table dinsa, sannan ta É—an dakata ko zai fito amma shiru babu alama, . yanke shawarar zuwa bedroom dinsa tayi a bakin Æ™opar shiga ta tsaya sannan tayi sallama, daga ciki taji ya amsa mata Æ™asa Æ™asa kafin ya bata permission É—in shiga ciki,   A hankali ta zura Æ™afa ta shiga ciki jikinta na É—an kerma Hango shi tayi daga shi sai bathrobe ajikinsa kwance abaje saman gadonsa, alamu sun nuna cewa baiji ma da fitowa daga wanka ba, ya kwanta gajiya ce tayi masa yawa, idonsa na'a lumshe yace "Wanene ne," sehrish tace "mai aiki ce dama dinner ne na kawo maka yana a palor naga baka fito ba, Jim yaÉ—anyi kafin yace "Tea kawai nake buÆ™ata,akawo mun nan,' Amsa mashi tayi da toh, sannan ta fuce ta koma palor dinsa ta É—auko kayan tea din dake acikin tray din da ta ajiye anan sannan ta shigar masa dashi, har gab da gadonsa ta ajiye masa saman madai-dai cin table din dake a wurin ta matsa masa dashi jikin gadonsa, bin shi tayi da kallo saboda bai buÉ—e idonshi ba kuma baiyi yunÆ™urin tashi ba, yayi wani fresh dashi, Ganin alamun fa zai iya zarcewa da bacci yasa tace "Na kawo maka Tea É—in," "I knew," ya bata amsa, jinjina kai tayi ashe yasan ta kawo É—in, wahalar tashin ce kawai yake ji, kusan 15 mins sannan ya Æ´unkura ya miÆ™e tare da sauko da Æ™afafunsa Æ™asa, rigar iya guiwar Æ™afarsa ta tsaya, saukin yasa shorts daga ciki amma chest É—in shi a buÉ—e yake fari kal, Zuba mishi ido tayi tana kallon ikon Allah wani irin bacci ne ke fusgar shi, ga uwar yunwa yana ji, ji take tamkar ta bashi tea É—in abaki yasha, cikin sauri ta haÉ—a masa tea É—in a cup ta É—an tura masa agabansa tace "gashi nan,' buÉ—e blue eyes É—insa yayi a hankali sannan yakai hannu daker ya É—auki cup É—in yakai bakinsa yana É—an kurba da zafinsa, ya sha ba laifi kusan sau biyu tana Æ™ara masa yana shanye wa, Bayan ya kammala tace "kayan dinner É—in fa na mayar dasu"? Ta tambaya cike da jin tsoran amsar da zai bata, "In akwai fruits ki haÉ—o mun," ya faÉ—i tare da mayar da jikinsa ya kwantar akan pillow, Tattara kayan tea É—in tayi sannan ta fuce dasu ta ajiye su a tray din dake É—auke da warmers na abincin sannan ta É—auke shi ta fita dashi kitchen ta shiga ta ajiye su, sannan ta É—ebo mashi fresh fruits acikin fridge, A plate ta zuba mashi su sai da tafara yayyanka mashi su sannan, tana Æ™oÆ™arin fita suka ci karo da Haroon tsaye abakin Æ™opar kamar aljani, Da Æ™arfi ta furta "A'uzu billahi minashshaiÉ—anin rajim,' Haroon ya fashe da dariya tare da cewa "Ni ne shaiÉ—an É—in, ko kin ga Æ™aho akaina ne? "Eh," ta bashi amsa, Yatsina fuska yayi yana bin jikinta da kallon frm up to down kafin yace "HaÉ—aÉ—É—iyar Sura," tace "Tubarkallah masha Allah," Murmushi yaÉ—anyi kafin ya kuma cewa "ki dai bi ahankali naga kamar zakiyi rawar kai Kada kici ka zaÆ™ewa mana domin kuwa har yanzu fa baki da wani matsayi acikin gidan nan, duk inda za'aje adawo bakya wuce Æ´ar aiki, sannan na lura kina shisshige ma wancan ifritun ko? to inaso ki sani wancan dashi da dutse duk É—aya suke indai agame da feelings ne, mace bata gabansa koda zai kula matan ma bana tunanin irin ki, ae ma zaren ba kalar yadin bane iska ce kawai zata wahalar da mai kayan kara......... tun da yasoma magana idon sehrish suka soma ciccikowa da kwalla amma bata bari hawayen sun zuba ba, ganin zai bata mata lokaci yasa ta bi ta gefensa ta fuce da sauri, tana jiyo dariyarsa sam tarasa gane ma haroon, batasan mai ta tsone masa ba, time É—in da tashiga bedroom É—in SGR samun shi tayi yana ta faman sharar baccinsa alamu sun nuna cewa ma tunda tasa Æ™afa ta fuce ya fara baccin, tsayawa tayi akansa tana kallonshi hannunta na riÆ™e da fruits É—insa, Yayin da idonta Suke cike da hawaye saboda kalaman haroon ita kanta tasani tabbas SGR ba tsaran yinta bane kwata-kwata bama haÉ—i, jinjina kanta tayi aranta tace "nasani kafi Æ™arfina nesa ba kusa ba, kuma nasan cewa kafin ni akwai wanda suka ruga ni faÉ—awa wannan tarkon bila adadin, Amma inaji araina babu wadda zata soka dan Allah kamar yadda nake sonka, tun bansan ya kamannin fukarka suke Ba, da sunanka kawai nakamu da tsananin Æ™aunarka kuma zan cigaba da addu'a akan hakan koda bazan ci nasara ba aÆ™arshe...Ana ahabbuk kasiran BABBAN YAYA.........â¤ðŸ’? Wani irin juyi SGR yayi har sai da Sehrish ta É—an tsorata gudun karya farka ya ganta, gyara kwanciyar shi yayi, yadda yake sakin numfashi anatse yana bacci ba Æ™aramin tafiya yayi da ita ba, Ajiye fruits É—in tayi saman table sannan ta matsa a hankali cike da fargaba ta janyo lallausan blanket É—insa jikinta na É—an kerma ta samu ta hayo dashi jikinsa ta lullu6a masa har zuwa neck É—insa, Murmushi ta É—an saki ganin ta kammala batare da ya farka ba, juyawa tayi ta tattaka izuwa inda makunnin hasken É—akin yake ta kashe mashi shi, nan take É—akin ya soma kyalli yana bada wani irin haske har sai da ta É—an razana, ashe furnitures É—in dakine masu wannan sparkling light É—in launi daban daban suke badawa, aduk time É—in da aka kashe hasken É—akin Yayi dark gaba É—aya su kuma sai su soma bada nasu hasken mai launuka, fuska É—auke da murmushi sehrish ke kallon wannan ikon Allan Bin su take yi da kallo tun daga Bed É—insa da bedside table É—insa, drawer É—in da ke É—auke da mirrow jerin wurin Closet É—insa gaba É—aya sun É—au hasken nan, sai taga ya Æ™ara yi mata kyau sosai, Lalla6awa tayi ta koma inda yake kwance tana kallon fukarshi yadda eye lashes dinsa suka fito radau zira zira dogaye kasancewar idon na'a rufe, sun kwanta luf, Addu'ar bacci tashiga yi mashi saboda tasan cewa bai samu damar yi ba ayarda ya kwanta É—in nan agajiye ta jima sannan ta É—an tattofa masa ajikin bargonsa, kamar karta bar É—akin haka take ji (Nace ba mai zai hana kawai ki kwana anan Ehen 😂) hannu tasa ta É—auki Kayan marmarin dake acikin plate É—in sannan ta fuce dashi bakowa a babban falon Dama tun fitowar farko da tayi duk sun kammala dinner É—insu sun shige cike aranta tace "Allah sarki su fawan hada rashin su yasa yanzu basu cika haÉ—uwa atare suna cin abinci ba ko zama a palor suna fira, ko yaushe zasu dawo? Duk da ina tsoran abunda zasu ce in suka ganni a Matsayin mace, Especially fawan nasan halinsa sosai baijin magana shine ya ta6a bani horo harna galabaita," ta Æ™arasa zancen zucin nata , bedroom É—inta ta wuce da fruits É—in saboda dama itama bata ci komai ba, asaman gadonta ta zauna tsakiyar gadon ta lankwashe Æ™afa tana shan fruits É—in tass ta shanye su sannan ta ajiye plate É—in asaman side drawer É—inta, dama empty yake tunda ta rotsa ma haroon fitilar saman shi akai, bata sake ajiye komai asaman wurin ba, sauko wa tayi tashiga toilet saboda bata yi sallar isha'e ba, alwala tayi sannan ta dauko hijab ta zura bayan ta shimfiÉ—a carpet ta gabatar da salla, Tana gama wa ta naÉ—e carpet É—in ko addu'a bata tsaya yi ba, ta tura su cikin wardrobe sannan ta haye saman gadonta taja bargo ta kwanta daker tayi addu'a kafin bacci 6arawo yayi awon gaba da ita.................(Shin ko kun lura cewa Sehrish ta manta dasu hosana da jahad bakamar da ba? hmmmmm rayuwa kenan baka ta6a sanin asalin ya mutun yake sai yasamu wurin zama koya samu abun duniya nan zaka ga zahirinsa😥)
_____________________🌹🌹🌹____________________
In midnight Hosana tafarka da matsanancin Ciwo, wani sabon raÉ—aÉ—in ciwon ne ya taso mata agigice tafarka tana kuka tana zabga Uban ihu tana faÉ—in "Innalallahi wa'inna ilaihiraji'un , La'ila ha illallah muharammadur rasulillah Wayyo Allah na, mutuwa xanyi, gaba É—ayansu suka farka hankali atashe tun daga jahad har hafsat dake kwance saman Sofa sai da tafarka a tsorace, taruwa su kayi akanta jahad na faman yi mata addu'a tana tofa mata cikin kuka take faÉ—in "Hosana ki daina magana ciwon bakin ki zai Æ™ara raunata, dan Allah kiyi haÆ™uri innalallahi bansan ya zanyi ba,'tafaÉ—i tare da fashewa da wani sabon kukan itama, dama sai da ranta yabata cewa raÉ—aÉ—in ciwon hosana zai iya dawo wa sai gashi ya dawo, fuskar tayi suntum la66an sun kumburo hancinta ma yayi girma, idanunta ma sun kumbura duk kwantsa ko buÉ—e su bata iyayi saboda sun datse sosai, ita kaÉ—ae tasan azabar da take sha ga haÆ™oranta suma nasu Zogin daban, ko'ina ciwo hakanne yasa ta haukace taita faman zabga salati tana kiran Sunan Allah da manzon sa ðŸ˜*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*
*🔥The Father Of Soldiers🔥*
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖâ¤â€ðŸ”¥ðŸ’žðŸ’˜ðŸ’?
*Story & Written by* *Hafsat Bature Muhammad*
~💋BOSSLADY💋~
*EPISODE 11-12* Ita kan ta Hafsat ba ƙaramin tashin hankali tashi ga ba ganin halin da yarinyar ta shiga, da alama ma raunukan nata sun ɗuri ruwa dole sai an fitar da ruwan Ya Salam, Yarfa hannu kawai take yi tana zabga uban kuka, hankali atashe JAHAD ta kalli hafsat tare da cewa "Aunty dan Allah ki taimaka mu mayar da ita asibiti aduba ta.....' ta ƙare maganar tana faman zubda hawaye, Ita kanta hafsat tunanin da take yi kenan can ne kawai mafi ta, ta shi tayi jiki na rawa ta ɗauko hijab ta zura sannan ta ɗauki mukullin motarta da ta bari a saman mirror, da kanta ta cuccu6i hosana daker ta ɗauko ta a kafaɗarta, ta fuce da ita cikin sauri itama jahad tabi bayanta a babban falon suka samu aunty babba saman Sofa hannunta ɗauke da plate ta dafa taliya sai faman ci take a tsiya ce saboda yunwar da ta taso ta, duk ihun da hosana take yi a kunnanta amma batayi yunƙurin tashi ba, balle taje ta dubo meke faruwa, Ganinsu afujajen yasa ta miƙewa tana cewa "Hafsat ina zuwa cikin daren nan? Ina zaki kai ta? Batare da hafsat ta kalle ta ba tace "Zan mayar da ita asibiti ne," hankali atashe aunty babba tace "Saboda me !! Acikin daren nan ! Ki barta kawai inyaso gobe dr yazo ya duba ta har gida," tsoki hafsat taja dama a ƙule take da Mommyn nata saboda duk ita taja mata halin da suke ciki,.
Wuce ta tayi tana cewa "da yake ba jikin ki bane ae dole ki ce haka,'
Bin su kawai aunty babba tayi da kallo har suka fuce, abayan mota hafsat ta kwantar da hosana, sannan suka shiga gaba ita da jahad, taja motar da gudu ta fuce da ita a wani privet hospital takai ta, cikin sa'a suka karbi hosana kuma nan take suka shiga bata taimakon gaggawa,
Yayin da hafsat da jahad suka samu wuri suka zauna nan waje suna jira saman waiting chairs, runtse ido kawai jahad ke yi tana faman karanto addu'a, tsigar jikinta har tashi take yi saboda jin yarda ihun hosana ya cika asibitin gaba É—aya baiwar Allah, ita kaÉ—ai tasan azabar da take sha,
Ita kanta hafsat dake gefenta jikinta duk ya gama mutuwa haƙiƙa taji tausayin Yarinyar fiye da tunanin mai tunani,
Jim kaɗan suka ji tsit babu kukan hosana babu alamar shi, jin hakan yasa jahad yin zumbur ta miƙe ta tunkari ƙopan ɗakin da suka kwantar da ita, tsoranta kar ace hosana ta mutu ne shiyasa suka ji shiru, turo ƙopar Nurse tayi ta fito cikin sauri jahad ta tare ta tana cewa"dan Allah sister ya jikin nata yake? ta tambaya a ɗan ruɗe Nurse ɗin tace "Alhamdulillah, kada ki sa damuwa aranki, jikinta da sauƙi sosae anyi mata dressing na raunukan nata sannan Mun taimaka mata da pain relievers yanzu haka allurar bacci mu kayi mata, addu'a kawai zaku ci gaba da yi mata,' tana faɗin hakan ta wuce gaba, Ajiyar zuciya jahad tasaki har hankalin ta ya kwanta sosai, komawa tayi ta zauna gefen hafsat wadda ke ta faman yin gyangyaɗin bacci, Rufe idonta kawai tayi tana faman ci gaba da yiwa hosana addu'a, bata jin zata iya runtsawa a daren nan, tsawon awanni suna anan jugum time ɗin hafsat ta jima da yin nisa a baccin ta, jahad kuwa na nan ido buɗe, kamar daga sama taji hosana na kiran sunan ta ƙasa ƙasa da farko tayi tunanin gizau muryarta keyi mata amma daga baya ta tabbatar da cewa ita ɗin ce ke kiranta, Cikin hanzari ta miƙe ta shiga ɗakin samun ta tayi ta tashi zaune saman gadon, ba ƙaramin farin ciki bane ya cika jahad, ganin yadda fuskar hosana ta sa6e an matse mata ruwan anyi dressing ɗin wurin ga bandage nan a forehead ɗinta da saman hancinta, duk da fuskar ta canza sosai kamar ba ita ba, idanuwanta sun buɗe sosai tana ganin jahad takama Murmurshi 😥
Faɗawa saman gadon jahad tayi ta rungumo ta sosai ajikinta tana faɗin "Allah sarki hosana ashe kin farka ban sani ba kina ta kiran suna na, ya jikin naki? Akwai inda ke miki ciwo yanzu"? Tayi tambayar tana janye jikinta daga na hosanar, Daker ta iya cewa "Naji sauƙi sosai jahad ba inda ke mun ciwo yanzu, amma magana tana mun wahala,Kuma ina jin jikina kamar ba nawa ba" hannu jahad tasa tana shafa gefen fuskarta tace "Insha Alah zaki dawo dai-dai hosana, yanzu hankali na ya kwanta tun da naga kina murmushi nasan cewa sauƙi ya samu, yanzu ki faɗamun wanene yayi maki wannan bugun mutuwar?' turo baki hosana tayi tana cewa "Wannan mara imanin, saboda nazo na same ta, ta shaƙe maki wuya kamar zata kashe ki, na bata haƙuri ta ƙyale ki ta ƙiya shine na gartsa mata Cizo a hannun, wannan ne fa kawai yasa ta kamani ta jibga ta faffasa mun fuska..........," shessheƙar kukan da take yi ne ya hana ta cigaba da maganar Cikin sanyin Murya jahad tace "ashe duk don saboda ni ne tayi maki wannan bugun, babu komai akwai ALLAH ! , Zai bi mana haƙƙin mu duk wanda ya zalunce mu Allah zai saka mana insha Allah! Jinjina kai hosana tayi tana share hawayen ta tace "Yaya Omar bazai ƙyale su ba, duk sai sun gane kurensu..... ta faɗi wit angry face can kuma ta sake cewa "Jahad komai yasa yaya Omar har yau baizo ya duba mu ba"? Jahad tace "muyi mashi Uziri hosana, ni nasan cewa yana sane damu kuma zaizo nan very soon,' Sun jima suna yin fira atsakanin su, ita kanta jahad tasan cewa hosana juriya kawai take yi tana yin surutu, daker tasamu hosana ta koma ta kwanta, itama a gefenta ta ra6a ta kwanta, lokaci guda bacci ya kwashe su su duka,
Ba ƙaramin bacci suka sha ba, don kuwa har sai da gari ya waye rana ta fito sannan jahad tafarka, hosana kuwa nata faman sharar baccin ta, ganin yadda hosana ke bacci anatse ya ƙara tabbatarwa da jahad cewa tasamu sauƙi sosai, tashi tayi ta cire hijab ɗin dake jikinta, ta shige toilet ɗin dakin Alwala tayi sannan ta fito ta ɗauki hajiabin ta zura, tana faman tunanin in da zata samu tayi sallah don babu carpet,  Fitowa tayi don ta duba hafsat samu tayi bata anan inda tabar ta jiya babu ita ba alamarta a wurin, sai taji hankalin ta ya ɗan tashi tsoranta kar ace guduwa tayi tabarsu a asibitin,  Hankali atashe ta fito harabar asibitin ga mutane nan nata wuce wa wasu na shigowa wasu na fuce wa, sai faman waige waige take yi tana neman hafsat, har wurin ajiye motoci taje taga ko zata ga motarta amma babu ita, hakan na nufin tabar asibitin kenan, da alama ma tun asubahi tabar asibitin, tuni jikin JAHAD yayi mugun sanyi,  Koma wa tayi tasamu wurin inda taga wasu mata zazzaune suna fira, tayi musu sallama suka amsa mata da fara'a   Tambayarsu tashiga yi idan suna da abun sallah su ara mata, nan wata daga cikin su ta miƙa mata sallaya ɗinsu da suka zo da ita, anan harabar jahad tayi sallah bayan ta kammala ta mayar masu da dardumar sannan ta koma ciki a kasalance, bakowa tafi ji ba face HOSANNA, yanzu in da gaske hafsat tafiya tayi tabarsu yaya zasu yi? Ina zasu dosa? bakomai ma yafi damunta ba face Hosana in tafarka ta son dole akwai yunwa atattare da ita, gashi ita ba ta da ko sisi balle ta siya musu abunda zasu samu su Ci,   Gefen hosana tasamu ta zauna wadda ke kwance tana faman sharar bacci, tagumi ta zabga tare da zuba mata Ido tana kallonta, in taƙaice muku tsawon lokaci ba hafsat ba alamarta 😧😳 Gashi in sunce zasu kai kansu gidan duka ba wanda yasan hanyar da zai bi, saboda da daddare ne kawai suka fito daga gidan baza su iya shaida kwatancen gidan ba, gashi ko Sunan unguwar basu Sani ba, ajiyar zuciya jahad tasaki aranta tana jin cewa hutu ne yazo musu, zasu ci gaba da rayuwarsu ne kawai akan titi,
_____________________SEHRISH__________________
Around 8 Ta farka kai tsaye kitchen ta wuce har time ɗin rigar jiya ce ajikinta da rolling ɗinta, a kitchen ta samu Azmee harta kusan kammala breakfast din gaba ɗaya, bayan tayi sallama ta shiga suka gaisa da junan su, Daga bisa ni azmee tace "Ina fata jiya kin kai ma SGR dinner ɗinsa ko? don na shigo na taras da kayan abinci a warmers ko ta6a su ba ayi ba,'   Sehrish tace "Na babban yaya ne, Jiya bai samu yaci ba dana kai masa, Tea kawai yasha daga baya yace mun yana buƙatar fruits, shine kafin naje na kawo masa har bacci ya ɗauke sa,'  Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "Allah sarki da alama jiya sun sha aiki ne that's why harya gaza cin abinci, Yanzu bari na shirya miki breakfast ɗinsa ki kai masa da sauri saboda nasan dole ya tashi da yunwa,'   Sehrish ta amsa mata da Toh, ta tsaya tana jiran ta shirya mata kayan breakfast ɗin nasa, Shiru tayi tana tunano maganar da HAROON ya faɗa mata jiya, akwai abunda ya tsaya mata arai take son fitar dashi "Aunty azmee dan Allah me ake nufi da ZAREN BA KALAR YADIN bane? ta tambaya tana kallom azmee dake shirya abinci cikin warmers asaman kitchen drawers din dake jere,  Ba tare da ta juyo ta kalle ta ba tace "idan aka ce Zaren ba kalar yadin bane, a tunani na ana nufin kamar abunda bai dace da wani ba, a misali kamar ace kina son wani wanda yafi ƙarfin ki nesa ba kusa ba, bari na baki wani misali ma kamar yanzu ace mace tana Son Namiji wanda ya kasance hamshaƙin mai kuɗi ne ko mai mulki ga ilmi ga kyau gashi prominent dae, ke kuma ace kin kasance ƴar talakawa ce koma kina aiki a ƙasan shi baki da duk wani abu daya mallaka da zaku zo ɗaya dashi kin ga kuwa ba sa'an yin ki bane,wannan shi ake nufi da Zaren ba kalar yadin bane......'   Jinjina kai sehrish tayi aranta tana cewa "Wato abunda haroon yake nufi kenan hmmm," Sannan a fili tace "To Aunty azmee me ake nufi da cewa ISKA NA WAHALAR DA MAI KAYAN KARA,!"?  Har sai da azmee ta ɗanyi dariya jin wannan, ɗan gyaran murya tayi kafin tace "Kamar mutun ya yi ta wahalar da kansa akan abunda bazai ta6a samu ba, yanzu in mutun ya sanya kayan kara ana iska shin kayan zasu zauna ne batare da sun tarwatse ba?  Sehrish tace "Eh hakane kuwa,"  "Yawwa ma'anar kenan, mutun yasanya wa ransa abunda bazai ta6a samu ba, kin ga zai tashan wahala ne,"  ta ƙarasa maganar tare da cewa "Zo ki ɗauki breakfast ɗin ki kai masa na kammala," ƙarasawa sehrish tayi ta ɗauki tray ɗin duk jikinta yayi sanyi ga me da abunda Azmee ta fassara mata yanzu, amma taci alwashin duk runtsi duk wuya zata jaraba Soyayyarta Agare shi ba fashi 💔
   Fuce wa tayi ta miƙi hanya kamar daga sama taji muryar haroon a kunnanta yana cewa "ƴar Shila barka da safiya fatan kin kwana cikin ƙoshin lpy,   Shiru tayi bata bashi amsa ba, yana tsaye ruƙe da ƙugu daga shi sai gajeran wando ajikinsa, Ci gaba da magana yayi "Dole kisha ƙamshi baby, an fa samu Freedom dole a hura hanci, hallau dae bari na ƙara tunasar miki, shisshigi da kutsi ba zai kai ki ga cin nasara ba akan wancan Babban kayan da ki ke hari, ke bama shi ba ko junaid dana ga kina shisshige mawa wlh yafi ƙarfin ajin ki, kwara ma ni zan iya yin maneji na lalla6a ki mu rufa wa juna asiri, ke ƴar aiki ni kuma ɗan masu gida Fantsararre,,,  takaici ya hana ta cewa komai wuce wa kawai tayi upstairs,   Tun da ta nufi part ɗinsa take jin tashin ƙamshi ya gauraye ko'ina Har cikin hancin ta direct masu daɗin ƙamshi,
  Bayan tayi sallama tashi ga, babu kowa a palor ɗinsa ƙarasawa tayi ta ajiye masa tray ɗin asaman table ɗinsa, tsayawa ta ɗanyi don ta jira fitowarsa,
 Tana cikin tsayuwar nan wayarsa da ya bari asaman hannun Sofa ta soma ringing da ƙarfi har sai da sehrish ta ɗan yi firgit da ido, kai idonta tayi a inda wayar take hada sa hannu tana dafe kirjinta, matsawa tayi a ƙoƙarinta na ta ɗauki wayar takai masa,  Adai-dai time ɗin yafito cikin sauri Don ya ɗauki wayar saboda Kira ne mai mahimmanci agare Sa yasan dashi   Jin motsin mutun yasa sehrish ɗagowa takai ido a kansa, aikuwa a tsananin firgice ta ɗanyi wani sauti tare da yin Hanzarin juyawa cikin tsananin farga ba,   Sam baisan da mutun ba, fitowa yayi daga shi sai ɗan pant a jikinsa gaba ɗaya halittar jikinsa ta bayyana,   bin bayan ta yayi da kallo mamakin sa ganin yarda ta razana kamar taga wani dodo, wuce wa yayi yasa hannu ya ɗauki wayarsa sannan ya shige ciki yana amsa kiran a kunnansa,  Juyo wa sehrish Tayi jin alamar ya koma ciki sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, gaba ɗaya duk ta firgice ta gigice ta tsorata da yanayin da tagansa,*💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋*
_🔥The Father Of Soldiers🔥_
Story & Written By *BOSS BATURE*
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••�*Episode 13-14*•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•�
*_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* âœï¸ ─────────────────────── ```{Kyakkyawan lafazi a cikin rubutu yana É—amfare da bin Æ™a'idar Adabin Hausa.```
```Lafazi gidan karamci da mutuntaka, Harshenmu abin alfaharinmu.}``` âœï¸âœï¸âœï¸ ____________(âœ?)______________
Tsawa tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, after some minutes sai gashi ya fito jikinsa sanye da jeans da t-shirt, hannunsa ruƙe da wayarsa ya samu wuri ya zauna saman Sofa, cikin sauri sehrish ta gaishe shi "Barka da safiya, fatan ka tashi lafiya," a tunaninta bazai amsa ba amma sai ji tayi yace "Alhamdulillah Am well," murmushi ta ɗan saki, kafin ta shiga haɗa masa Tea a cup mai ɗan xafi ta tura masa agabansa, hannu yasa ya ɗauka yakai bakinsa yana kur6arsa a hankali, ci gaba da saving ɗinsa sehrish tayi, kamar daga sama taji yace "Meyasa jiya ba'a kawo min fruits dana buƙata ba"!? Murya na rawa sehrish tace "na same ka kana bacci ne lokacin dana kawo maka," ta ƙarasa maganar tana kallon fine face ɗinsa, Bayan wasu mintina ya kuma cewa "daga yanzu inaso a rinƙa kawo min Coffee or Tea wit fruits around 12 pm,"  Cikin hanzari ta amsa mashi da cewa "Insha Allah," jinjina kansa ya ɗanyi yayin da yake ci gaba da cin pancakes ɗin data haɗa masa da Zuma,   tsayawa sehrish tayi tana jiran ya kammala ta zuba mashi wani abun,  Wayarsa dake ajiye a gefensa ta soma ringing cikin sauri takai hannu zata cirar mashi tissue ya goge hannunsa adai-dai lokacin shima ya miƙa hannunsa zai cira karaf suka haɗa hannunsu cikin na juna 😌 zaro ido sehrish tayi cikin tsananin jin tsoro tana ɗan kallonsa,  Shi kuwa bin hannun Yarinyar yayi da kallo sam ba'a yi masa irin haka amma yayi mata Uziri ne saboda da alama batasan ko shi wanene ba, gata kuma ƙaramar yarinya,  "Am sorry,...' sehrish ta furta aɗan tsora ce yayin da ta janye hannunta, shi kuma ya ciri tissue ɗin a natse yace "Don't repeat that mistake again,"  Cikin sauri tace "Insha Allah," goge hannunsa yayi sannan ya ɗauki wayar ya ɗaga kiran tare da karawa a kunnansa, taso taji mai zai ce acikin wayar amma sai dai kash cikin wannan harshen taji yana magana wato Espanol da alama yafi jin yaren sosai ko kuma shi ya taso yana ji,  Zuba mashi ido tayi tana kallon shi tun daga shafaffen cikinsa har zuwa saman wide Chest ɗinsa haɗaɗɗiyar ƙira, maganar haroon ta tuna dayake cewa Zaren ba Kalar yadin bane Iska ce kawai zata wahalar da mai Kayan kara, tabbas kuwa yayi gaskiya amma in ta tuna wannan karin maganar da ake Cewa *DUK KYAN TAKALMI ƘAFA CE ZATA TAKA SHI* sai taji wata irin natsuwa tazo mata, tana tunani tana ci gaba da kallon fuskarsa yadda yake Moving pink lips ɗinsa yana magana tamkar baison yi, da kuma yarda yake faman lumshe sexy blue eyes ɗinsa ba ƙaramin Yanayi yake jefa ta ba, "Allah yasa bada budurwarsa yake waya, koda yake aunty azmee tace baya soyayya, To Allah yasa dai bada mace yake waya ba," ta faɗi acikin zuciyarta saboda ganin yarda yake ta faman lumshe idonsa kamar wanda ke waya da mace cikin shauƙi,  tana cikin yi mashi wannan kallon ƙurullan nata ya kamata, adai dai time ɗin ya ɗan ware idonsa direct suka sauka kan na sehrish dake faman Zuba masa ido tana kallonsa abunda ya tsana arayuwarsa ba, sam bata lura daya kamata ba saboda idonta na akan Sumar kansa, har sai da ya ɗanyi gyaran Murya cikin sauri ta wurga kwayar idonta kan tashi aikuwa har sai da ta ɗan Razana ganin ya aza idonsa acikin nata Unexcepted,   ƴar harara ya wurga mata sannan yace "Stop looking at me, i don't like,' ya faɗi tare da cigaba da yin wayarsa,   Sunnar da kai sehrish tayi cikin jin kunyar Kamatan da yayi tana masa kallon kurulla, amma wannan hararar daya sakar mata ba ƙaramin kashe mata zuciya yayi ba, ya jima yana wayar kafin ya kammala ya ture ta gefensa, sehrish ta cigaba da saving ɗinshi harya kammala cin breakfast ɗin nasa sannan ta tattare komai ta fuce dasu kitchen ta ajiye agefen Kitchen sink yadda in tadawo wankewa kawai zatayi, Daker ta iya fitowa daga kitchen ɗin saboda taga duk sun Hallara suna yin breakfast, tunkarar su tayi gabanta na faɗuwa saboda ganin hada HAROON zaune ga kuma Twins duk suna zazzaune, tunkan ta isa junaid na ganinta yasoma sakin murmushi kamar gonar Auduga, sallama tayi masu suka amsa sannan ta kalli Abbansu wanda keta faman sakar mata murmushi tace "Ina kwana Abba, fatan kun tashi lafiya," Abban nasu yace "Alhamdulillah My Only daughter, yanzu nake tambayar azmee take cemun kin shiga kaiwa Babban yayanku Abinci," "Eh hakane," ta bashi amsa sannan ta juya ta kalli sauran ta gaishe dasu duk suka yi tsit sai kanal Yusif daya ce "Ae nayi tunanin bazaki gaishe da yayyen naki ba, yanzun nan nayi fushi dake,"   Murmushi sehrish tasaki tana mai mamankin hali irin na kanal Yusuf sam bakamar na sauran ba,  "Samu wuri ki zauna mana," Abbansu ya umarce ta kujera taja ta zauna zuciyarta na ɗar ɗar, tana a jerin inda Abbansu yake gefensa junaid daga shi sai ita, a ɗayan side ɗinta kuwa haroon ne tabbas tasan dole ya hantare ta, ga kuma AYAAN Da JAHAN da take facing ɗinsu duk ta tsargu saboda tasan halinsu suna jere tare da kanal yusif,  azmee da kanta tayi saving ɗinta acikin plate ta buɗe saving dish ta zuba mata Chicken pper soup Sannan ta haɗa mata da Cofee acikin Cup� Sehrish ta kalli azmee tare da cewa "nagode aunty amzee"
hararar ta amzee tayi alamar cewa bata son godiyar, ..a hankali take kurbar coffee É—inta duk da kermar da hannunta ke yi, muryar haroon taji a Æ™unnanta yayi Æ™asa Æ™asa da Voice É—insa don kada wani yaji yace"Su acici mala'ikun tauna, an fa samu wurin zama, to adai ci ahankali kar a shaÆ™e," banza tayi dashi batace komai ba, amma sam tarasa cin chicken É—in dake agabanta shaÆ™e cikin plate,  Sanyayyiyar muryar junaid ce ta ratsa kunnanta da cewa "Sehrish ya akai naga yanayin ki ya canza? ko breakfast É—inki baki fara ci ba,"   tace "bakomai junaid kawai bana jin daÉ—i ne, inaji kamar na tashi na tafi É—aki kawai,"  cikin sauri junaid yace "a'a reesh pls kada kiyi haka ki daure kawai ki ci, kinji My sister," murmushi tasaki jin sunan da junaid ya kira ta dashi, É—an É—agowa tayi da idonta karaf suka sauka kan na Jahaan da Ayaan da suka É—ago atare, shiru tayi tana É—an kallonsu, atare suka yatsina fuska suna yi mata wani irin kallon Tara saura kwata, Æ™asa da murya Jahan yayi tare da cewa "Ayaan kalli yarda junaid ke fira da wancan yarinyar, shi junaid kowa nasa ne, baya tsoran mutane sai sunyi masa Illah," yayi maganar cikin nuna damuwa   Ayaan yace "ba kai kaÉ—ai ba jahaan, ni ma abun na damuna wlh, shiru kawai nayi amma na lura da yadda suke shiri, bazan Æ™yalesa ba dole na buga masa warning Allah,   Jahan yace "gasky kam, janyo shi yakamata muyi a É—akin mu, muja masa kunne tunda shi shashasha ne kowacce baÆ™uwar fuska shige mata yake yi, sai kace ba Jinin mu ba," Ayaan yace "kwarai kuwa, ae shi junaid da kake ganinsa half cast ne, ruwan Abba ne dana Mommyn mu ya É—auko, mu kuma ruwan mommy ne kawai ajikin mu, banda na daddy," Wannan maganar ta Ayaan tasa kanal yusuf fashe wa da dariya ashe duk yana jin firar tasu saboda shine kusa dasu a jere, É—agowa su kayi suna kallonsa dukansu hada Abban nasu da junaid da sehrish da azmeee, Abban nasu yace "in ce dai ko lafiya? Kanal yusif yace "babu komai Abba, gasu nan su Ayaan da jahan ne suke fira su faÉ—a maka abunda suke cewa ka ji,"   tunkan Abbansu ya tambayesu suka haÉ—a baki wurin cewa "Babu komai Abba, firar wani film muke yi,'  girgiza kai kawai Abbansu yayi, Haroon kuwa cewa yayi "Allah yayi wa É—an iska uwa koda ta kara ce," ya faÉ—i yana kallonsu salon jan faÉ—a kawai, Babu wanda ya tanka masa miÆ™ewa Ayaan da jahan su kayi tare da yiwa Abban su sallama suka fuce,Â
💪 Fito wa marshal Omar yayi daga upstairs yana saukowa down jikinsa sanye da jallabiya ash colour sai faman ƙamshi yake yi, tunkaro su yayi Abbansu na ganinsa yafara fara'a yana cewa "Omar sai yanzu ka tashi? tun ɗazu nake ta faman waige-waige naga ta ina zaka 6ullo,   Ɗan ƙayataccen murmushi yasaki tare da cewa "Gm Abba ina fatan ka tashi cikin ƙoshin lafiya,"  "Alhamdulillah Son, Samu wuri ka zauna na baka abinci a baki," cikin zolaya yayi maganar su kuwa sauran dariya su kayi, ɗagowa OMAR yayi tare da gaishe da Azmee ta amsa mashi, sannan su kuma Su kanl yusif da junaid suka shiga gaishe shi, Haroon yace "Barka da fitowa Damusa mai maganin ƙananun ƴan iska," ɗan harararsa Omar yayi tare da cewa "Zaka fara wannan tsokanar taka ko? To ka shiga taitayin ka ko yanzun nan na saita maka waɗannan haƙoran naka, don naga ba'a jere suke ba,' shima da zolaya yayi maganar ayayin da yake zama azmee kuma ta soma zuba masa breakfast ɗinsa,   Mayar da idonsa yayi kan JUNAID dake ta faman sakar masa murmushi yace "My shagwa6a boy, irin wannan kallon haka da kake mun ko kana buƙatar wani abu ne?  Cikin jin kunya junaid yace "Babu komai ya Omar kawai inaso inta kallon ka ne, aduk lokacin danayi kewarka,"  Murmushi Omar yayi kafin yace "Ae da ka sani jiya ka shigo bedroom ɗina mun kwana tare,"  Junaid yace "ae Abba bazai bari ba, Kishi yake yi," gaba ɗayansu suka fashe da dariya jin abunda junaid yace,   Abban nasu kuwa murmushi kawai yayi tare da ɗan jinjina kai yana kallon junaid ɗin, Haroon yace "Ae na Lura da yadda Abban mu ke ji dakai, kamar kai kaɗai ya haifa bayason komai ya same ka,'   Junaid yace "Yaya haroon ka ta6a ganin inda mutun ke wasa da bugun zuciyarsa? to aeni zuciyar Abban tamu ce gaba ɗaya shiyasa Yafi sona," yayi maganar wit proud,  ta6e baki Haroon yayi yana kallonsa, MARSHAL OMAR yace "Ae bama Abban mu kaɗai ba Haroon, Junaid farin cikin kowan nan mune acikin gidan nan, bamu son wani abu ya same shi domin tamkar mu yasha fa, JUNAID BUGUN ZUCIYAR FAMILY ɗin mune gaba ɗaya,"  Kanal yusif ya ƙara da cewa"Maganarka gaskiya Ce Yaya OMAR, Ni kaina aduk lokacin dana aza idona akan na baby junaid wlh farin ciki ne ke ziyarta ta, kuma aduk lokacin da wani ya 6ata mun rai junaid ne ke lallashi na da kalaman sa masu kwantar da hankali, tabbas shi Yaro ne amma yana da baiwar iya sarrafa harshe wurin farantawa mutane," Har cikin zuciyarsa yake wannan bayanin, junaid kuwa farin ciki ya hanasa idasa shan cornflakes ɗin dake agabansa, haka zalika Abbansu murmushi ne a fuskarsa saboda bai da Burin daya wuce yaga ana yabon Jininsa, kuma ma Junaid,  Haroon kuwa tuni zuciyarsa tayi baƙiƙƙirin ji yayi bazai iya ci gaba da zama ba, don haka da hanzari ya miƙe tare da fuce wa daga babban falon gaba ɗaya, sam ba wanda ya damu dashi bare su son halin dayake ciki,  Duk fa wannan abun dake faruwa a kunnan Sehrish tana sauraron su, sam tagaza gaishe da Marshal Omar tsoran ta kada ya ƙi amincewa da ita duk da ta lura bazaiyi Tsauri ba,  Sai da tabari duk sun natsu wuri ya ɗanyi tsit sannan ta ɗanyi gyaran Murya tare da cewa "YAYA OMAR ina kwana,"    Jin Muryar mace yasa shi saurin ɗagowa yaga wacece karaf fararen idanuwansa suka sauka akan na SEHRISH, ae baisan lokacin da ya fesar da Tea ɗin daya kur6a abakinsa ba, hankali atashe yake kallonta, Ajiye cup ɗin dake hannunsa yayi tare da miƙewa tsaye idonsa akan na sehrish wadda ta gama tsorata dashi ganin yadda ya firgita da ganinta kamar yaga wata ALJANA, tuni jikin sehrish ya soma kerma, ita kanta azmee ta tsorata da ganin reaction ɗin Omar akan Sehrish haka zalika Abbansu kanal yusif da junaid duk mama ki ya ɗaure musu kai  Nuna ta da hannu Marshal Omar yayai tare da cewa "Keeeee !!!!!!!!!! " gaba ɗaya ya razana da ganin yarinyar, ganin haka yasa kowannan su ya tashi tsaye suna kallonsa, Abbansu yace "Omar meya faru ne? Na manta ban faɗa maka ba game da yarinyar nan ba, ƴa Ce Allah yabani daga sama.... .kallonsa Omar yayi a ruɗe kafin ya mayar da idonsa kan Sehrish wadda tuni idonta sun cuccuko da kwalla saboda tashin hankali,   da hanzari OMAR ya bar dining ɗin yayi saurin haye wa upstairs part ɗinsa, zuciyarsa a cunkushe sam yagaza gane ma Idonsa dayake yi masa Gizan Fuskar Hosana da Jahad a fuskar wannan yarinyar daya gani a yanzu,   Bedroom ɗinsa ya shiga hannu yasa ya ɗauki wayarsa daya ajiye asaman pillow, cikin hanzari ya daddana layin aunty babba ya buga mata Call, kusan 3 times yana kira bata shiga, numbar Hafsat ya kira itama tana ringing ba'a ɗagawa,
Wurgi yayi da wayar saman gadonsa, tsayawa yayi yana faman sauke ajiyar zuciya, hannu yasa ya dafe kansa tamkar wanda ke fama da ciwon kai, tabbas ransa na basa cewa Ba fuskarsu hosana bace a fuskar yarinyar, ya sawa ransa cewa tsananin Son da yake yi ma yaran ce da ƙaunar da yake yi musu da kuma kewarsu da yayi ya sanya Fuskarsu keyi mashi gizau afuskar yarinyar daya gani ayanzu, tabbas Omar yayi Confusion ɗin kansa, ya rikita tunaninsa bazai ta6a yarda da abunda idonsa ke nuna masa ba akan Waccan Yarinyar................   Ajiyar zuciya yasaki aransa yana ƙara jin cewa bai kyauta musu ba da baije ya dubo su, amma ya shirya zuwa gobe domin ya duba su,  Yana gama wannan tunanin ya dawo Downstairs da sauri ya sauko a lokacin Sehrish harta gudu zuwa ɗakinta saboda ta tsorata,  Abbansu na ganinsa yace "Omar wai lafiya meya faru ne? Naga duk ka rikice lokaci ɗaya ko don saboda wannan yarinyar ne da ka gani yanzu,"  Zama Omar yayi yana cewa "No ba haka bane Abba just there's something that confused me but am ok now,"  Ajiyar zuciya Azmee tasaki jin yace babu komai, ci gaba da yin breakfast ɗinsa yayi anatse but still his brain was confused,
Zuwa wani lokaci kowa ya Kammala breakfast ɗinsa sai daga bisani Sehrish ta fito suka shiga gyara gidan ita da azmee,     ______________________________________________Farkawa hosana tayi da wata irin matsananciyar yunwa don hada kukan ta dama ita bata da jumurin yunwa ko kaɗan, hankalin jahad ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yarda hosana ke ta faman rusa kuka gashi sai faman lallashinta takeyi amma sam taƙi yin shiru sai ta runƙa cewa "baki ji yadda nake ji bane, babu komai acikina kamar zan mutu," runtse ido jahad tayi sam tarasa abunyi, yanke shawara tayi kawai tafita waje taga ko zata samo mata abinci, tun da taga akwai visitors dake zuwa wurin marasa lafiya wata'kil ko Allah ya haɗa ta dana gari su sam mata abinci taba Hosana, tashi tayi cikin sauri tana cewa "Hosana ki jira dan Allah ki daina kukan nan, yanzun nan zan dawo," shiru hosana tayi tana faman sauke ajiyar zuciya, fita jahad tayi tana faman zarya a asibitin wurin nema musu abincin da zasu ci, taimako yayi ƙaranci a arayuwar nan domin kuwa duk wanda jahad ta tunkara da niyar ya taimaka musu sai suce suma bazai ishe su ba, ga abinci nan tana gani haje-haje agaban wasu sun baje suna ci amma tarasa wanda zai taimaka musu koda da rabin plate ɗaya ne,   A ƙarshe da ta gaji da yawon neman taimakon abinci sai ta samu wuri abakin wata bishiya ta zuƙunna tare da kifa kanta tana faman shesshekar kuka, babban tashin hankalinta yarda zata tunkari hosana tace mata bata samo masu komai ba, 😥
tana cikin wannan zuÆ™unnan Motar hafsat tashigo asibitin da gudu tayi parking É—inta a harabar ajiye motocinsu, fito wa tayi fess da ita tayi wanka ta canza kayan jikinta yanzu tsadaddiyar atampha ce riga da skirt ajikinta sun bi shape É—in jikinta very tight, ta É—aure kanta da É—an kwalin sannan ta yafa veil a shoulder É—inta, Æ™arasawa tayi ta buÉ—e back seat É—in Motar hannu takai ciki ta É—auko kwando mai É—auke da kayan abincin da tazo masu dashi, bayan ta rufe motar ta wuce ciki sam bata lura da Jahad ba, haka itama jahad bata É—ago ba balle taganta,.   tana Æ™okarin shiga cikin É—akin da aka kwantar da hosana dr yafito suka ci karo, ganin ta yasa ya saki fara'a yana cewa" ke ce mai kula da wannan patient É—in ko"?  Hafsat tace "Yeah its me,"  Dr yace "yawwa tun dazu take faman kukan yunwa gashi naga ba kowa tare da ita, amma tun da kin zo yakamata ki kula da ita, sannan idan ta kammala cin abincin akwai magungunanta dana ajiye wanda za'a bata,"   hafsat ta amsa mashi da cewa "Shikenan dr ngde ssae," tana faÉ—in hakan ta wuce ciki shi kuma ya nufi cikin asibitin,   Samun hosana tayi tayi kukan tayi mai isarta har ta gaji, tana zaune saman gadon ta kife kanta saman guiwowinta, jin muryar hafsat yasa ta É—agowa cikin sauri,  Ae tana ganinta É—auke da food stuffs a basket nan take jikinta ya soma rawa kaf-kaf kamar kura taga nama,   Da murmushi hafsat ta isa ta zauna gefen gadon kusa da Hosana tana cewa "Ya jikin naki"? Murya na rawa Hosana tace"da sauÆ™i sosai" ita burinta tafara zuba ma cikin ta abinci,  Ajiye basket É—in hafsat tayi Æ™asa, sannan tasanya hannunta ta curo flask mai É—auke da haÉ—aÉ—É—en ruwan tea ta ajiye sa, Cup ta curo guda biyu ne a haÉ—e, É—aya ta É—auka ta bude flask É—in ta tsiyaya mata shi sannan ta zuzzuba mata madara da bornvita aciki har sai da yayi kauri, sannan ta miÆ™a ma hosana, kar6a tayi takai bakinta tana sha da hanzari har wani sauti maÆ™oshinta keyi kwat-kwat , kusan sau 3 tana shanye wa hafsat na Æ™ara mata, bayan ta kammala ta ciro kula mai É—auke da Chips haÉ—i na musamman, ta zuba mata a plate, miÆ™a mata tayi tana cewa "ki ci a hankali saboda ciwon ki," hosana ta amsa da "toh" Turawa kawai take yi abaki kamar zata haÉ—a da plate É—in duka, bayan tagama dashi hafsat ta zuba mata fruits a plate ta bata, shima tashiga sha kamar kamar me,   "Ina Ƴar uwarki take ne ban ganta ba"? Hafsat ta tambaya yayin da take kallon hosana,.   Hosana tace "tun É—azu ta fita tace na daina kukan yunwa na jira ta, har yanzu bata dawo ba,"  Murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Nasan bai wuci taje nema muku abunda zaku ci bane, May be tayi tunanin na tafi nabarku ne,"  suna cikin magana jahad ta turo Æ™opar a galabaice take tafiya saboda tsabagen yunwa, Æ™afafunta har harÉ—ewa suke yi tana tafiya kamar wadda tasha Codine,    shigowa tayi tana faÉ—in"hosana sai dai kiyi haÆ™uri wlh bansamu komai .........' ganin hafsat yasa ta dakatawa da maganar cikin mamaki take kallon su, hannu tasanya tana murza idonta don ta tabbatar wa kanta cewa ba mafarki take yi ba, sakin hannunta tayi tana Æ™are masu kallo, Expecially hosana data gani sai faman cusa fruits takeyi abakinta wanda hafsat ta zuba mata, Wani irin farin ciki ne ya cika jahad har batasan lokacin da ta fashe da kuka ba Don tsabar murna,  tashi hafsat tayi ta ruÆ™o hannunta tana cewa "Kukan ya isa haka, tun da gani na zo ko? Halan kinyi tunanin na gudu ne nabarku shiyasa kika fita nema muku abinci"? ta tambaya tana kallon jahad dake faman shesshekar kuka tace"Nayi tunanin kin tafi kin barmu ne shiyasa na fita, ashe zaki dawo,".   ɗan murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Am so sorry nayi laifi ban sanar muku ba, da asuba na tafi gida, nayi sallah bacci ya kwashe ni without my knowing bayan na tashi ne kuma na wuce kitchen na shirya muku breakfast dana kammala shine nayi wanka na fito,"  bayani take yi jahad na kallonta tsananin mamaki ne yakamata ganin yadda lokaci guda Hafsat ta canza musu gaba É—aya tamkar ba ita ba, tazama wata mutuniyar kirki lokaci guda ANYA?  jan hannunta hafsat tayi ta zaunar da ita gefen hosana sannan tashiga saving É—inta abincin tare da miÆ™a mata, sannan ta haÉ—a mata tea itama, bayan ta kammala ta samu wuri saman plastic chair É—in dake facing gadon da suke tana kallonsu,  A hankali Jahad ke kurbar tea É—in tana É—an kallonta, bakomai take jin tsoro ba fa ce kada ace Hafsat tasanya musu POISON acikin abincin da takawo su,tun da dama tasan sarai neman hanyar da zasu kawar dasu suke yi, kuma wannan ce hanya mafi sauÆ™i, yadda hafsat É—in ke kallonta ido cikin Ido yasa Jahad Æ™ara jin wani irin Tsoro aranta nan take hannunta ya shiga yin kerma kaf!kaf!kaf! 😳😳😳 Wani shu'umin Murmushi Hafsat tasa ki tana cewa "nasan mai ki ke tunani JAHAD, tabbas abunda kike tunani gaskiya ne, POISON nasanya muku a abincin saboda wannan ce hanya mafi sauÆ™i da zamu kawar da ku acikin arayuwarmu, kuma zaku huta da wahalar zaman duniya,"   Hankali atashe Jahad ta Zazzare ido waje jikinta na kerma tace "POISON!!!!!!!!!!!!!! "*🪩🪩🪩🪩🪩ABBAN SOJOJI🪩🪩🪩* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·â€? *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·â€? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* âœï¸ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•Â?15-16•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•Â? ____________(âœ?)____________
Story & Written by *BOSS BATURE*
Firgit jahad tayi daga zurfin tunanun da ta shiga tana faman sauke ajiyar zuciya, ɗagowa ta ɗanyi ta kalli hafsat samunta tayi fuskarta ɗauke da murmushi tace "Tun ɗazu na lura da kallon da kike yi mun Jahad, na menene? ɗan sunnar dakai jahad tayi tace "Babu komai kawai ina mamakin yarda kika canza mana ne ba kamar da ba, kin nuna tausayi agare mu, ba muyi tunanin haka ba, Hafsat tace "Nima kaina nayi mamakin yarda na canza wurin nuna muku tausayi, bayan ba hali na bane gaskiya, tun ina yarinya bani da tausayi ko kaɗan kuma bana son mutun mai tausayi, ban sani ba ko kunayin addu'a ne shiyasa Allah ya kawo muku sauƙi ta 6angare na.....' ta ƙare maganar tana kallonsu, Jinjina kai Jahad tayi jin abunda hafsat tace, Lallai ne Allah ne ya amshi addu'arsu ya kawo musu sauƙi ta wurin hafsat, Ajiyar zuciya Jahad tasa ki tare da juyawa ta kalli hosana wadda ke zaune wuri da ido, taci ta ƙoshi tayi hani'an, Hafsat tace "Ga maganin da dr yace abaki, tun da kin kammala cin abincin bari na baki ki sha, sannan zuwa anjima insha Allah zamu koma gida," jahad tace "Allah ya kaimu lafiya," "Ameen," ta amsa mata sannan tasanya hannu ta ɗauki ledar maganin,
ta shi ga fiddo su tana duba su, kafin tasanya hannu cikin basket ɗin da tazo dashi ta ɗauko robar ruwa, ta buɗe ta bayan ta ciro maganin ta miƙa ma hosana tare da ruwan tana kar6a tana sha, haƙiƙi su Hosana da jahad ba ƙaramin kwanciyar hankali suka samu ba, saboda sun ga tausayinsu ƙarara a fuskar Hafsat kuma da alamun zasu samu sauƙi ta 6angarenta, *Shin Ya maganar matar da ta ba Hafsat miliyan shidda don ta zubar mata dasu Jahad? Kuna ganin zata fasa wannan aikin ko kuwa*? 😳
*AUNTY BABBA* 😈
Sam ta gaza samun natsuwa hankalin ta ba ƙaramin tashi yayi ba ganin yarda hafsat ta fara damuwa da twins ɗin da OMAR ya kawo, tabbas dole ta ɗauki mataki akan hakan, kuma haryanzu tana akan bakanta na sai tasa an zubar mata dasu Hosana da Jahad, *Tabbas dole na ɗauki mataki akan hakan* tayi maganar tare da dakatawa daga zirga zirgar da takeyi acikin ɗakin nata, fitowarta kenan daga wanka, ta zumbula doguwar rigar Buba ta Material, hannu takai ta ɗauki wayarta dake ajiye saman stool dake agaban mirror, cikin hanzari ta shiga contact ta dannawa wata number kira wadda tayi saving ɗinta da *BABA ALAMU* Nan da nan kiran yashiga wayar ta soma ringing zuwa wani lokaci mai numbar data kira ya amsa wayar, Cikin sauri tace "Assalamu Alaikum," daga can 6angare wata murya kakkausa ta gawurtattun ƴan iska ta amsa mata da cewa,"Hajiya Laila manyan gari, ashe kuna neman mutane? Ae nayi tunanin daga in da amfanin mutun ya ƙare a wurinki yazama shara......' dakatar dashi Aunty Babba tayi da cewa "Baba Alamu ! mu aje wannan gefe, wlh ina cikin tsananin damuwa ne, tunawa dakai yasanya na kira ka domin nasan kai kaɗai ne zaka iya yi mun wannan aikin.....' ta ɗan dakata tana jiran amsar da zai bata , Baba Alamu yace "Ae dama ke ba'ki ta6a neman mutun sai in buƙatarki ta taso, tun da ansan muna da amfani ae a rinƙa ɗan kiran mu ana bamu hasafi don tafiya tayi kyau ko?, yanzu dai faɗa mun me kike so in aiwatar kawai ! Wa kike so akashe miki har lahira? Ko wa kike so In Naƙasa Miki kasusuwansa ajefar bayan Duniya?😳
Dariya aunty babba tayi cikin jin daɗi tace "Yawwa Mutumina, dama nasan kaine kawai zaka iya share mun hawaye na, abunda ke faruwa wani ƙanin Mijina ne wlh ya tsinto wasu ƴan mata tagwaye ya kawomin a gida na, na tsani yaran nan ko ganin su bana son yi, saboda zasu tarwatsamun target ɗina abunda nakeso kawai so nake kazo ka ɗauke su Ka fitar mun dasu daga gidan nan ka kai su can bayan gari ka jefar mun dasu Can cikin ƙurmin daji wanda zasu rikice su gaza gane hanyar da zasu fita daga cikin shi,"😳 tamkar tana agabansa haka take masa bayani tana faman cizon la66a, 😠fashe wa da dariya baba Alamu yayi daga bisani ya tsagaita yace "Ƙaramin aiki kenan, ni nama yi tunanin wani za'a kashe maki ne yanzun nan mu kai shege lahira, amma tun da wannan ne kada ki samu damuwa, yanzun dai bana nan kinsan naje lagos ƙarƙashin gada amma maƙo mai zuwa bi iznil lahi, aikin ki zai kammalu, ƴan Canji kawai zaki tanada " Aunty Babba tace "in dai wannan ne an gama, zanyi maka biya na musamman babban kaso mai tsoka, Baba Alamu yace "Shikenan sai kin jini, da zarar na dira kaduna zan zo da rugwagwar mota ta na kwashe Maki Sharar azubar abayan gari,'😂
Jinjina kai aunty babba tayi har wani sauke ajiyar zuciya take yi jin burinta zai cika na kawar da su Jahad, Sun jima suna waya da baba Alamu kafin daga bisa sukayi sallama, ta ajiye wayar saman mirror tana cewa "Yanzu abunda ya rage mun shine, na dakatar da Omar don nasan zai iya zuwa yace zai tafi dasu na lura da hakan I ave to do something â—â€? .........!👷wani irin shu'umin murmushi tasa ki, saboda plan É—in da ta tsara,
*********
Sai wuraren bayan Sallar La'asar sannan dr yayi discharge É—insu daga asibitin kamar yadda hafsat ta buÆ™ata don bata son zaman su a asibitin gudun kada Omar yayi musu Dirar Mikiya, duk da dr yaso ya Æ™ara ma hosana Jini amma ta hana hakan sai dai tayi alÆ™awarin cewa zata mai do ta asibitin Next time, A hankali take driving É—insu acikin motar, hosana na'a a back seat kwance sai faman sharar bacci take yi, yayin da jahad ke agefen hafsat dake driving, adai-dai wani Store ta tsaya da motar, sannan ta kalli jahad tace "Ki kula yanzu zan dawo," Jahad ta amsa da cewa "Toh Aunty" Shiga cikin wurin tayi bayan wasu mintuna tafito hannunta ruÆ™e da leda, ta buÉ—e motar ta shiga miÆ™a ma jahad ledar tayi tace "RuÆ™e wannan a wurin ki," Amsa jahad tayi ta Æ™anÆ™ame ledar a hannunta, sannan hafsat taja motar suka tafi gida kai tsaye, Bayan tayi parking suka fito daga motar daker jahad tasamu hosana tafarka ta ruÆ™e hannunta suka nufi ciki hafsat na biye dasu, sai faman jin fargabar haÉ—uwa da Aunty babba suke yi, Aikuwa suna shiga suka same ta zaune a babban falon saman sofa tana faman danna wayarta, tana ganinsu ta miÆ™e tsaye tare da cewa "Sannun ku da dawowa, Allah sarki hosana da jahad kuyi haÆ™uri ban samu damar zuwa asibiti ba na dubo ku, Ya jikin naku"? ta faÉ—i cikin nuna tausayin su, ai ba su jahad da hosana ba hatta hafsat tayi mamakin jin abunda Momyn nata tace lokaci guda ta canza tamkar ba ita ba, tsayawa sukayi suna kallonta baki asake, Ganin hakan yasa aunty babba Æ™arasawa ta ruÆ™o hannun kowannan su , sannan cikin sanyin murya ta wanda yayi nadama tace "HaÆ™iÆ™a nasan na cutar daku sosai, Allah ma ba zai yafe mun ba, tabbas jiki na yayi sanyi, nayi danasanin abun da na aikata muku dan Allah kuyi haÆ™uri ku yafe mun........' Hawaye ne suka soma saukowa daga idon aunty babba fuskarta duk a yamutse tana kallonsu, cikin mamaki hafsat tace "Shin mafarki nake ko gaske!? Mom are u serious about what are u sanying? Ko dai kin sha wani abu ne bayan na fita? kece dakan ki kike danasani hada neman gafara a wurinsa? É—ago ido aunty babba tayi tare da kallon hafsat tace "Shin ni ba mutun bace kamar kowa daba zanyi laifi na nemi gafara ba"? na zauna nayi wani tunani menene riba ta idan na cuci waÉ—annan bayin Allan? Allah fa dakansa ya haramta ma kansa zalunci kuma ya haramta shi atsakanin mu, kuma yace kada muyi zalunci, amma ni na kansance mai son zuciya..........' Sam ta kasa Æ™arasa maganar saboda shessheÆ™ar kukan da tafara, juyawa hafsat tayi ta kalli jahad yayin da ita kuma jahad idonta na akan Hosana wadda ke kallonta, gaba É—ayansu mamaki ne ke É—awainiya dasu, shin taya zasu gasgata tuban da Mommyn hafsat tayi? Anya ba wata Æ™ullalliya bace? "Naji kunyi shiru baza ku yafe mun bane? In har baku yafe mun ba bana ji zan iya bacci adaren nan," Cikin sauri Jahad da hosana suka haÉ—a baki wurin cewa "Aunty mun yafe miki, Allah ya yafe mana gaba É—aya," Murmushi Aunty babba ta saki tare da sa hannu ta haÉ—a su duka ta rungumesu ajikinta, tana faman ci gaba da basu haÆ™uri akan kuskuren da tayi masu na jibgarsu da tayi, Jikinsu duk yayi mugun sanyi, gaba É—aya kwalwarsu ta rikice sun rasa gane dawa zasu YARDA? SHIN HAFSAT ko MOMMYNSU? Taya hakan zaiyiyu ace lokaci guda sun canza musu izuwa mutanen kirki masu tausayin su? Bayan aunty babba ta janye su daga jikinta ta mayar da idonta kan na hafsat tace "daughter daga yau inaso ki É—auke su tamkar Æ™annen ki, ni kuma insha Allah zan É—auke su tamkar nice na haife su, zan basu duk wata kula daya dace uwa tabawa ya'yanta, " Murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Insha Allah mommy as from now hosana da jahad sun zama Æ´an gida, zasuyi rayuwar Æ´anci acikin gidan nan, babu wanda zai sake cutar dasu acikin mu," Jinjina kai aunty babba tayi sannan tace "ina so daga yanzu su koma É—akin Ladi mai aikin mu da kwana," Hafsat tace "a'a Mommy, mattress ce kawai acikin É—akin, gaskiya ni nafison su dawo bedroom É—ina da kwana yadda zanfi basu kulawa," Aunty babba tace "hakan ma yayi, yanzu yakamata ku shiga ciki ku huta, sannan hafsat ki taimaka ma hosana tayi wanka da ruwa mai É—umi ko taji daÉ—in jikinta, Hafsat tace "insha Allah mommy," sannan ta mayar da idonta kansu hosana tace "mu shiga ciki," hannun su cikin na juna suka bi bayan hafsat har izuwa cikin bedroom É—inta, Da taimakon hafsat hosana tayi wanka ta canza kayan jikinta izuwa doguwar riga mara nauyi, bayan ta kammala hayewa kawai tayi saman gadon hafsat, tana jiran zuwan jahad wadda ta shiga toilet yin wanka itama, Ajiyar zuciya kawai hosana ke saki amma tana jin fargabar canjin da su ka gani wurin hafsat da Mommynta, sam bata amince dasu ba, kuma taci Alwashin muddin YA OMAR yazo Æ™afarta Æ™afarshi sai ta bishi, ðŸ˜
**********SEHRISH**************
A gajiye ta shiga cikin bedroom ɗinta bayan sun kammala gyare-gyaren gidan, sai lokacin tasamu damar yin wanka tare da alwala tafito ɗaure da towel, agaban dressing mirror ta zauna saman kujera tana Shafa mai ajikinta, bayan ta kammala ta feshe jikinta da turare, sannan ta koma ta buɗe wardrobe ɗin kayanta, ta ɗauko dogon skirt brown color ta zura sannan ta sanya t-shirt fara, daga nan ta zura hijab tare da shimfiɗa carpet tayi sallah anatse, tun kafin ta kammala azmee ta turo ƙopar ɗakin ta shigo, wuri ta samu gefen gadonta ta xauna, bayan sehrish ta kammala sallar ta naɗe dardumar ta mayar da ita cikin wardrobe tare da hijabin, sannan ta juya da fara'a tana gaishe da azmee "Ina yini aunty azmee," Azmee tace "lafiya lou sehrish, zo ki zauna," Ƙarasawa tayi ta samu wuri kusa da ita ta zauna, azmeee tace "sehrish wai ina wayarki take ne? Na lura tun ranar dana baki ita, ban sake ganinta a hannunki ba, kodai baki so ne? zuru sehrish tayi don ita tuni ta manta da zancen wata waya, kuma ba kowa bane yaja mata hakan ba face haroon, shine silar damuwar da tashiga harta manta in da ta jefe wayar "Ina sauraron ki ina wayar"? Azmee ta ƙara nanata mata, cikin en ina sehrish tace "Aunty azmee tun....ranar...da...kika...ban...ita..na manta inda na ajiye...ta,' ta ƙarasa maganar tana ɗan kallonta azmee tace "Sehrish kenan kin cika shiririta yanzu wayar mai tsada ita kika 6atar? To ina so ki nemo ta yau ɗin nan duk inda take, in ma saman ceilling kika turata ki hau saman ki fiddo ta, Ki kawo min ɗaki na ina jiranki,!" tana faɗin hakan ta tashi ta fuce........ tafa hannu sehrish ta shiga yi tana tunanin ta ina zata fara neman wayar, ita kanta abuƙace take da wayar ko don ta rinƙa ɗebe kewar zama ita kaɗai aɗaki, Tashi tayi cikin ƙanƙanin lokaci ta hargitsa ɗakin wurin neman wayarta, duk ta zabure har ƙarƙashin gado ta leƙa, ta bincika cikin laundry basket ɗinta, gaba ɗaya ta zazzago kayan wankinta dake cikinsa babu komai, agajiye ta mayar da kayan, zarya tashiga yi tana tunanin ina ta wurgar da ita, ci gaba da neman wayar tayi, a ƙarshe tayi deciding zuwa ɗakin junaid ta roƙesa ya kira layin wayar ko tayi ringing, cikin hanzari ta ɗauki mayafinta dake ajiye saman bed ɗinta, ta yarfa shi a head ɗinsa, sannan ta fita cikin sauri babu kowa a babban falon direct upstairs ta wuce da ƙarfi take tattaka stairs ɗin ko kallon gabanta batayi burinta kawai ta isa bedroom ɗin junaid,. Kamar daga sama taji ta bugi wani abu da ƙarfi nan take wani irin jiri ya kwashe ta, agigice tasaki wata irin ƙara ganin yarda ta tafi gaba ɗaya zata faɗi amma ina tuni yayi mata wani irin kwakkwaran ruƙo da hannu guda ya tallabo waist ɗinta, Zazzare ido sehrish tayi cikin Jin tsananin tsoro yayin da take faman sauke ajiyar zuciya, gabanta ne ya soma faɗuwa saboda tuna hannun wa take a ruƙe, sam tagaza ɗago ido ta kalle sa, ae tun daga ƙamshin turaren nan nasa ta shaida kowane ne, ɗago da ita yayi ta tsaya da ƙafafunta sannan ya wuce abunshi, juyawa sehrish tayi cikin sauri tana kallonsa ba ƙaramin wanka ya ɗauka, har sai da ya fice daga babban falon sannan ta kawar da idonta sannan ta ƙarasa haye wa upstair ɗin, har time ɗin jikinta wata irin kerma yake yi hannunta na dafe da ƙirjinta, A hankali tayi knocing ƙopar ɗakin junaid tana buga ƙopar a slow saboda zuciyarta dake tariyo mata abunda yafaru yanzun nan, kusan 3 times tana knocking sai daga bisa tajiyo muryar junaid yace "Come in," Ashe door ɗin a buɗe take, tana zura ƙafarta ciki karaf taci ido dashi gaban mirror daga shi sai short towel a waist ɗinsa sam baisan cewa sehrish bace, ta cikin mirror ya hangota, aikuwa cikin sauri yace "dakata !! Kada ki shigo! Ja baya," dariya sehrish tayi sannan taja da baya ta tsaya jikin ƙopar tana cewa "Junaid yaushe ka fara jin kunyata har haka"? daga cikin ɗakin tajiyo muryarsa yana cewa "tun ranar dana gane cewa ke maca ce.....,' Murmushi ta saki tana faman sauke ajiyar zuciya har time ɗin temperature ɗin jikinta yayi mugun zafi ba don komai ba sai don abunda yafaru da ita yanzun nan, "Come in Sehrish," junaid ya faɗi, Shiga ciki tayi a lokacin harya zura jallabiya ash colour ajikinsa yana gyara hannun rigar, wuri tasamu agefen gadonsa ta zauna tana cewa "Junaid dama wannan wayr tawa nake nema narasa inda na jefar da ita, shine nazo ka taimaka ka kiramin layin dake cikinta, may be in tayi ringing in gano ta, Murmushi junaid yasaki kafin yace "shikenan zan kira maki ita, amma under one condition? Ya faɗi ayayin da ya tsaya agabanta ya ruƙe qugu, sehrish tace "Menene sharaɗin? Junaid yace "Tun ran nan nake ta fama dake ki nunamin gyaran gashin ki kin ƙiya, to yau indai kina So na kira layin wayarki sai kin cire mun nagani" ya faɗi yana murguɗa mata baki, Yamutsa fuska tayi tare da cewa "look junaid yanzu ba lokacin wannan bane, am not in mood Just ka kiramun wayar,' ta faɗi tana tsuke baki, Bin shi tayi da kallo ganin ya ɗan ɗaure fuskar shi alamar baiji daɗi ba, Cikin lallashi tace "junaid are u angry with me? Am sorry pls ni bazan so naga king of smile ya koma king of Angry ba,' tayi maganar da ɗan zolaya, Ɗan sakin fuskarshi yayi sannan yace "its ok, go back to ur bedroom i wanna call u righ now," Murmushi sehrish tasaki tare da cewa "yawwa mutumi na, Allah yabar mun kai," ta faɗi tare da miƙewa ta wuce bedroom ɗinta cikin sauri, Junaid kuwa acikin ransa yace "Ameen sehrish Allah yabarmun ke till the end of my life,' sannan yasa hannu ya ɗauki wayarsa dake ajiye saman mirror, contact yashi ga tare da lalubar nombar sehrish da yayi mata Saving da*FUTURE DREAM* sa'an nan ya danna mata kira, tunkan sehrish tashiga ɗakinta ta rinƙa jin ringing ɗin wayar da ƙarfin gaske, tura ƙopar ɗakin tayi ta shiga ciki tana bin inda sautin ke fitowa, ashe tana cikin bedside drawer ɗinta, duk wannan uwar wahalar da tasha, cikin hanzari ta janyo drawer chest ɗin gida na farko, sai ga wayar ajiye sabuwarta kusan 1 month kenan tana ajiye bata mutu ba, saboda ruƙon chargyn ta, ajiyar zuciya sehrish tasaki tana shasshafa screen ɗin wayar da hannunta, . .........................tuna da azmee dake jiranta yasanya ta fice da wayar cikin sauri ta isa ƙopar ɗakin azmee knocking tayi daga ciki taji azmee tace "in kin son bada wayar kika zo ba ki koma," wato har ta gane ce sehrish ce ta kwankwasa mata, Gyaran murya sehrish tayi tare da cewa "Tare da wayar nazo aunty azmee," Azmee tace "shigo ciki," Tura kopar sehrish tayi ta shiga, samun ta tayi kishingiɗe saman gadonta, ganin sehrish yasa ta tashi zaune tana cewa "yanzu naji magana," Murmushi sehrish tasaki tare da samun wuri gefen azmeen ta zauna sannan Ta miƙa mata wayar tace "Gata," Azmee ta kalli wayar tare da cewa "dama ba wani abu zanyi da ita ba, ke nake so ki runƙa amfani da ita akai-akai takasance tare dake, saboda daga yanzu duk wani mai buƙatar wani abu ke zai kira kai tsaye a waya yasanar miki," jinjina kai sehrish tayi alamar gamsuwa da bayaninta, Sannan azmee taci gaba da cewa "nikam inaso na tambaye ki, shin kin ta6a yin makaranta ne before? ɗagowa sehrish tayi ta kalle ta a wani irin yanayi kamar wani abu yaɗan sosa mata zuciya, shiru tayi na wani lokaci kafin tace "eh nayi primary bayan nan nafara secondry karatun duk ashiriri ce ƙarshe ma muna gab da zamu shiga ss3 nadaina zuwa gaba ɗaya......' ta ƙarasa maganar asanyaye Azmee tace "yanzu kina da burin ci gaba da karatun ne ko kuwa a'a? Ta tambaya tana kallonta, Sehrish tace "ina so mana sosai, ina so nayi Ilmi saboda wata rana nima nazama abun alfahari, kuma wannan burin mahaifiyarmu ne, tun lokacin da ta haife mu takance Sehrish zata zama Achitecture, Hosana kuma Doctor, Jahad kuma Nurse haƙiƙa inaso nacika mata wannan burin nata.......................' idonta ne suka cuko tab da kwalla sunnar da kanta tayi ƙasa tana kallon wayar dake hannunta, Cikin mamaki azmee ke kallonta ita kanta sehrish batasan me take cewa ba, ci gaba da magana tayi kawai tana cewa "Allah sarki a lokacin ni nafi kwarewa wurin yin zane, hosana ce mai ƙoƙari acikin mu amma yanzu bata da cikakken hankali tun lokacin da ta duro daga saman window mai tsayin gaske ..........ban......ban....... Kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan da yazo mata nan take ta fashe da matsanancin kuka, Gaba ɗaya hankalin azmee ya tashi sam tarasa gane ma sambatun da sehrish ke yi, cikin ruɗu tace "sehrish wai meke faruwa ne? Su wanene waɗannan kike magana akansu ne? ƴan uwanki ne? ɗaga mata kai tayi alamar "Eh" jinjina kai azmee tayi tare da cewa "share hawayenki daina kuka ya isa haka, duk da bansan Labarin ki ba amma ina da tabbacin cewa wani mummunan abu yafaru acikinsa wanda ke yawan saki cikin damuwa, don haka zanso naji labarinki sehrish amma ba yanzu ba aduk lokacin da muka samu free time sosai zamu zauna ki bani shi tun daga farko har ƙarshensa,' "Insha allah aunty azmee na yarda dake sosai baxan 6oye maki komai ba," ta faɗi ayayin da take share hawayen ta, Bayan sun samu natsuwa su duka azmee taci gaba da cewa "Zaki fara zuwa school insha Allah....' Cikin mamaki sehrish ta ɗago ta kalle ta tare da cewa "Makaranta? Ni kuma? Aunty azmee taya za'a ɗauke ni a school bayan ko takardun kammala primary ɗin bani dasu na rasa su,' "Kada ki damu sehrish wannan ba wata damuwa bace, komai za'a iya yi maki shi insha Allah, kuɗi ne kawai ke magana, kuma ni zan tsaya maki harki samu don nasan muddin na tuntu6i koda kanal yusif ne da maganar zai iya sama maki hanya, bama shi ba junaid zai iya yi maki wannan hanyar cikin sauƙi ki fara daga ss1 daga baya kin zana Jsce in time ɗinta yayi,' Wani irin farin ciki ne ya lullu6e sehrish har tagaza rufe bakinta, aranta tana cewa nan bada jimawa ba nima zan fara zuwa makaranta kamar kowa ?Alhamdulillah 😇 Hannu azmee tasanya ta kar6i wayar hannun sehrish tana cewa "ina fata junaid ya nuna miki komai ko? "Eh harma ya tura mun wasu apps ɗin da zanyi amfani dasu," Azmee tace "okey, idan kina so kiyi amfani da data ko wurin yin browsing da sauransu just Wi-fi kawai zaki kunna, ' Jinjina kai sehrish tayi alamar gamsuwa, sun ɗan jima suna fira kafin daga bisani ta sallame ta, komawa bedroom ɗinta tayi cike da murna koba komai in tafara zuwa school zata haɗu da friends irinsu Hafsat Bature Domin ɗebe kewa 😇 Sehrish first day at school 😮 Can't wait to see 💃💃💃💃
Ga wanda ba suyi payment ba su hanzarta su biya before end of this week👠Yanzu littafi Zai fara 🔥🔥🔥 (08103884440) LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* âœï¸ ──────────────EPISODE 17-18
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖ💋â¤ï¸?
*Mallakin Hafsat Bature Moh'd* ~BossBature~ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·� bayan Jahad ta kammala wankan ta canza kaya ixuwa doguwar riga, hawa tayi itama saman gadon kusa da hosana suna daf da juna tace "hosana me kike tunani game da hafsat da mommynsu? Anya ba wani abu suka shirya mana ba? Kada fa ace so suke yi su kashe mu ko su zubar damu shiyasa suka tsara mana hakan,' tayi maganar cikin nuna damuwa a fuskarta, Hosanna tace "jahad ni nasan abunda mommynsu hafsat ta shirya mana, fuska biyu tayi mana wlh, so take ta nuna mana kulawa sosai don mu saba da ita yadda in yaya Omar yazo yace zai tafi damu muƙi binsa saboda sun nuna mana kulawa.........' dakatawa tayi da maganar jin alamun tunkarowar mutun ɗakin da suke ciki, Hafsat ce ta shigo ciki fuskarta ɗauke da murmushi tace "sannunku My sisters ya jikin naku"? Ta tambaya ayayin da take samun wuri saman room sofa ɗin tazauna, "Alhamdulillah da sauƙi" suka bata amsa atare, mayar da idonta tayi gefen kujerar da take zaune leda ce ajiye wadda taba Jahad ta ruƙe mata bayan ta fito daga store, hannu tasa ta ɗauki ledar tana cewa "Lahh Jahad wannan ae naku ne na siya maku, Chocolate ne da sweet ko bakwa so ne"? ta tambaya tana kallonsu, Suka haɗa baki wurin cewa "muna so," sannan jahad ta sauko daga saman gadon tasanya hannu biyu takar6a tana fadin "mungode Aunty hafsat," Murmushi hafsat tasaki tare da cewa "Naji daɗin sunan nan da kuka kira ni dashi, amma nafison ku kira ni da Sister Hafsat akan aunty hafsat zanfi jin daɗin hakan," Murmushi su kayi su dukan su, kafin daga bisani Jahad ta curo musu chocolate cookies ɗin data siya musu, guda biyu ta curo ta ɗauki ɗaya sannan ta miƙa ma hosana suka 6are suna sha, Har lokacin idon hafsat na akansu kallonsu takeyi gwanin burgewa, dama tun ranar farko data fara cin karo dasu sun burgeta kawai baƙin hali ne irin nata yasa bata nuna ba, Ɗagowa su kayi jin alamar shigowar mutun, AUNTY BABBA ce ta shigo fuskarta ɗauke da murmushi tana kallonsu tace "Ya jikin naku My daughters? haɗa baki su kayi wurin cewa "da Sauƙi Alhamdulillah," Jinjina kanta tayi kafin daga bisa ni ta kuma cewa "Yakamata ku fito mana kuzauna a palour ko kallo ne kuyi zai ɗebe muku kewa kuma zaku samu nishaɗi," Amsa mata sukayi da "Toh" sannan suka sauko daga saman gadon hannun jahad ruƙe da ledar choculate ɗinsu, A falon suka samu wuri saman gujera mai mazaunin mutun biyu su ka zauna tare da mayar da hankalin su Wurin kallon shirin da akeyi a tashar Bollywood, tuni kallon ya ɗauke musu hankali saboda daɗin dramar da suke yi ta india, dama kuma ga chocolate ɗinsu suna sha sai abun yaƙara nutsar dasu gaba ɗaya, AUNTY BABBA kuwa wuri tasamu ta zauna agefen gadon tana fuskantar hafsat tace "Sannu Madam," tashi hafsat tayi zaune tana cewa "Mommy dama ina son magana dake! Wannan canjin dana gani a tattare dake shin dagaske ne? Ko duk shiri ne? ta tambaya tana kallonta don jin amsar da zata bata, ɗan ƙayataccen murmushi AUNTY BABA tasaki tare da cewa "Hafsat kenan ! Ke naso ki fara faɗamun gaskiyar lamarin nan shin dagaske ne yanzu kin fara jin tausayin yaran nan? "Mommy da gaske ne, natausaya musu sosai saboda bugun rashin imanin da kika yi musu, kuma ayanzu bana son wani yaƙara ƴunƙurin cutar dasu daga ni har KE ! Ajiyar zuciya aunty babba tasaki tana mai jinjina kai tace "Shin ya maganar matar da kika amsar ma kuɗi kusan miliyan shidda? Mayar mata su zakiyi kenan.....? Hafsat tace "wannan ni tashafa mommy, zan san yarda zanyi da ita, in ma bazaiyiyu ba just zan mayar mata da kuɗinta ne,"
ɗan ta6e baki AUNTY BABBA tayi daga bisani tace "Shikenan Daughter but lemme remind u something, kin manta da uban bashin da Ake bin ki kenan u ave to think about it, how can u pay all ur debt? Dole ki buƙaci kuɗi ....................tana kai ƙarshen maganarta, ta tashi ta fuce tana faman sakin shu'umin murmushi aranta tana cewa "Yarinya kenan! Naki wasa ne," **********💪💪💪***************
misalin ƙarfe 5 da rabi na marece a lokacin suna dab da kammala aikace-aikacen su na girki, sai ga OMAR ya shigo cikin gidan kai tsaye kitcen ya nufa in da suke, Hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba ganin OMAR don atsorace take dashi, bai shiga kitchen ɗin ba tsayawa yayi daga waje ba tare da yace komai ba, Sehrish ce tace "Aunty Azmee ga yaya Omar nan," azmee na jin haka cikin sauri ta fito izuwa inda yake tsaye da murmushi a fuskarta tace "Omar ashe kaine ina fata lafiya dai ko," Jinjina kansa ya ɗanyi ayayin da idonsa ke kallon sehrish wadda ke acikin kitchen taƙi ɗagowa su haɗa ido dashi, har time ɗin ya gaza gasgata abunda idonsa ke nuna masa, ɗan gyaran Murya yayi tare da mayar da idonsa kan na Azmee yace "Sannuku da ƙoƙari, ina fata dai ban katse maku aikin ku ba" Azmee tace "A'a wlh Ae ma mun kammala girkin gyaran kitchen ɗin ne kawai ya rage mana yanzu," OMAR Yace "Okey, dama aiki ne nake son kuyi mun ke da waccen Yarinyar ta cikin kitchen,' Jin hakan yasa sehrish ɗan ɗagowa suka haɗa ido dashi cikin sauri ta sunnar da kai ƙasa, Azmee tace "Wane kalar aiki kenan Omar? "Zan baku makullin gidan Uncle ABUSUFYAN so nake Kuje can ku duddubamun gidan duk wani abu da ake buƙata kawai inaso ku rubuta mun shi," Murmushi azmee ta saki tare da yin ƙasa² da murya tana cewa "To fa, kodai Abusufyan ne zai dawo nigeria da zama ne? Kamar daga sama taji muryar Omar yace "Bashi bane zai dawo, wasu marayu ne nake son zubawa aciki, so inaso agyara mun gidan da duk wani abu na more rayuwa da mace zata buƙata acikin Sa, sannan bayan kun kammala wannan aikin inaso ku shirya zuwa Yi masu siyayyar kayan sawa da sauran abubuwan buƙata na mata,' Azmee tace "wannan ai aikin lada ne, insha Allah Omar zamu yi komai yadda kake so," "Hakan yayi mun, bari na ɗauko maki key ɗin gidan ku tabbatar kunje yau, zansa Junaid ya kai ku a motarsa," ya yi maganar yayin da yake wuce wa izuwa sashen Abbansu, Hannu yasa ya ciro wayarsa daga cikin aljuhun wandonsa, contact ya shiga tare da dannawa Abban nasu kira, kamar jira yake omar ya kira sa awaya sai gashi ya ɗauka, Ƙara wayar Omar yayi a kunnansa yana cewa "Abba gani nashigo bedroom ɗin naka, wurin ina key ɗin yake"? "Ka duba cikin side drawer ɗita gida na tsakiya suna anan ciki makullan na zuba su," "Ok to ngde Sosai Abbana, take care of your self for me," yana jiyo sautin muryar Abban nasu Mai haɗe da Murmushi yana cewa "Nima haka ka kulamun da kan ka," "Insha Allah," Omar ya faɗi tare da rejecting kiran, ya mayar da wayar tasa cikin aljihunsa, Kai tsaye inda Bedside drawer ɗin Abban nasu take ya ƙarasa tare da zuƙunnawa ya janyo gida na tsakiya acikinta, Sai ga makullan sun bayyana hannu yasanya ya ɗauka sannan ya fito daga ɗakin nasa, Kitchen ya nufa azmee na ganinsa ta fito, ƙarasawa yayi tare da miƙa mata key ɗin yana cewa "Ga shi nan ku tabbatar kunyi aiki mai kyau, yanzun nan zan ma junaid magana yazo yakai ku can gidan," Azmee ta amsa masa da cewa "Toh insha Allah," sannan Omar ya fuce daga main palour izuwa filin buga ball ɗinsu tunkan ya isa yake faman kwalawa junaid kira wanda ke acikin filin kwallon sai faman buga ball suke yi su uku shi da wasu daga cikin security ɗin gidan, Jin kiran Omar yasanya shi dakatawa da yin kwallon ya wurgar masu da ita sannan ya fice daga cikin ragar izuwa inda Omar yake, tsayawa yayi agabansa tare da zuƙunnawa ya dafe guiwarsa sai faman haƙi yake yi daker ya iya cewa "Yaya Omar gani," Hannu omar yasa tare da bugun bayan junaid yace "Bana hana ka buga ball dayawa har haka ba? Tun fa ɗazu dana shigo nasame ka, cikin waɗancan gardawan sai faman wahalar mun dakai suke yi," Murmushi junaid yasaki tare da ɗagowa tsaye yana cewa "Yaya Omar zandaina ne, amma yanzu tana sanya ni nishaɗi sosai," Jinjina kai Omar yayi tare da dafa kafaɗarsa yace "ko don saboda lafiyarka junaid, yakamata kadaina yawan buga kwallon ɗin nan da kuma yawan yin guje-guje,' Cikin girmamawa junaid yace "insha Allah yaya Omar zandaina," dafa kafaɗarsa omar yayi sannan yaci gaba da cewa "ka shiga ciki ka shirya zaku fita tare da Azmee da wannan Yarinyar inaso ka kaisu Gidan Uncle Abusufyan, zasu yi mun aiki ne kaima sai ka taya su," Cike da zumuɗi junaid yace "To shikenan yaya Omar, bari naje yanzun nan nashirya nakaisu," "Yawwa My boy," Omar ya faɗi tare da wuce wa gaba, Shige wa junaid yayi da gudu cikin babban falon kamar ba wanda aka gama ja ma kunne akan yin gudu ba, A lokacin azmee da sehrish sun kammala gyara kitchen ɗin, kowan nan su ya wuce ɗakinsa domin kimtsawa, Da gudu yake tattaka Matattakalar benen adai-dai lokacin SGR ya fito shima yana ƙoƙarin saukowa down, jikinsa na sanye da jallabiya fara mai gajeran hannu abun ba'a magana, tsayawa yayi yana jiran isowar junaid Domin yayi masa kyakkyawan ruƙo, sai da junaid yakai ƙarshe sannan ya lura dashi, ɗan zaro ido yayi tare da dakatawa da tafiyar gabansa na faɗuwa, sarai yasan cewa sun hana shi gudu shi kuma abun ajinin sa yake yadda kasan wanda aka sanya Ma battery haka junaid yake, Tun kafin Babban yayan nasu yace wani abu junaid yayi saurin cewa "Bazan ƙara ba wlh, na daina" ya faɗi yana ɗan raku6e fuska yana kallonsa wuri da ido, Sgr yace "Junaid na ta6a sa hannu na ajikinka, da sunan zan buge ka ga? Girgiza kai yayi tare da cewa "a'a babban yaya, baka ta6a ba kuma bana fata, ai nasan ma bazaka ta6a buguna ba," ya faɗi da murmushin nan nasa, Sgr yace "meyasa kake tunanin cewa bazan iya bugunka ba,"? ɗan cizon red lips ɗinsa tare da cewa "Because.......You love me so much......' ya ƙarasa maganar tare da wuce wa cikin sauri yana dariya, bin shi da kallo kawai Sgr yayi, tunawa yayi da wata magana da aka ta6a faɗa masa cewa *Kowa ne ɗan adam yana da lagwansa, kaima haka ga lagwagonka nan, wato ƙanin ka JUNAID, Yakamata ka kula dashi sosai, Saboda duk wanda zai kawo maka hari acikin maƙiyanka, to ina da tabbacin cewa zasu 6ullo maka ne ta wurin JUNAID, So you've to be very careful,"! Jikinsa ne ya ɗanyi Sanyi amma ta wani 6angaren yana jin cewa bazai ta6a barin hakan ta faru ba A matsayinsa na SURGEON GENERAL RAFAYET, A babban falon ya zauna saman doguwar kujera mai mazaunin mutun uku, ya kishingiɗa tare da ciro wayarsa yana daddanawa, Shigowa Omar yayi cikin babban falon ganin SGR yasa shi sakin fara'a yana cewa "Ashe kana ciki yaushe ka shigo," tashi zaune Rafayet yayi jin muryar omar, Kallonsa yayi tare da cewa "ban jima da dawowa ba, what of u ,"? ya tambaya yana kallonsa, Zama Omar yayi saman Sofa ɗin da sgr yake suna ɗan fuskantar juna yace"Nima yanzun nan nashigo, bansan kana aciki ba ae dana shigo, dama inaso nace kunyi waya da EVA? tana so tayi magana dakai sosai tayi mun magana ɗazu, its better ka kira ta if not kasan halinta ƙaramin aikinta ne kaganta a Nigeria," ɗan ta6e baki sgr yayi tare da cewa "naga missed Calls ɗinta, na manta nabi kiran nata that's why," Jinjina kai Omar yayi kafin ya kuma cewa "Har yanzu baka yanke shawara bane game da ita? Pls bro kodan saboda Uncle Donald yakamata ka sassauta mana....' Wani irin kallo Sgr yake binsa dashi kafin yace "Uncle ya riga da yasan tsarina, ko shi kansa ya tsawatar mata akaina amma taƙi ji so ni banson ya zanyi na fahimtar da ita ba," Omar yace "matsalar kenan, ni abunda yafi damuna taurin kanta, in banda ƙarfin hali irin nata taya zata ce dole sai kai zata aura? a ƙalla EVA ta baka kusan 10years aduniya, har yaushe ne zata daina wannan mafarkin? ya tambaya yana kallonsa, Sgr yace "Omar da ace zan iya canza ra'ayi na akan mace ,to ina mai tabbatar maka da cewa ita ce mace tafarko da ta cancanta ta mallake ni, saboda kusancin dake a tsakani na da ita..................." Karaf!! Maganar Sgr ta sauka a kunnan Sehrish wadda fitowarta kenan ta nufo cikin babban falon, har ta kammala shiryawa tsaf, ta zumbula jalbaba ajikinta har ƙasa maroon colour, hannunta na ruƙe da hand bag, ƙafarta kuma na sanye da flat shoes launin hijab ɗinta, fuskarta sam babu makeup ƴar hoda ce kawai ta shafa sai ta murza man baki a la66anta, amma ba ƙaramin kyau tayi ba, tsayawa tayi jiki amace tana sauraron firar tasu sam tagaza motsi, har sai da Marshal Omar ya ɗago da idonsa ya kalle ta, gabansa ne yaji yayi mugun bugu sam yagaza ganewa wannan ruɗanin dake a fuskar yarinyar nan, Sehrish bata lura da kallon da Omar keyi mata ba, juyawa Sgr yayi don yaga me Omar yake kallo ne karaf idonsa suka sauka ana sehrish wadda itama idon nata na akanshi, from up to down ya kelle ta kafin yace "Ke zonan," gabanta ne taji ya faɗi rass tayi firgit tana kallonsu, hankali atashe ta tunkare su gabanta na ɗarr!ɗaarr ta ƙarasa inda suke dab da Babban yayan nasu daya kira ta, Hannu yasa tare da ruƙo jalbabar dake ajikinta, saboda tsananin tsoro sai da sehrish ta kusa sakin fitsari tuni jikinta yasoma kerma kaf!kaf !!kaff! cikin sanyayyiyar muryar nan tasa ta natsastsu yace "Menene wannan haka ajikin ki,"? Ya tambaya in serious matter batare da ya aza idonsa akanta ba, Murya na rawa sehrish tace"hi..hij..hijabi ceeee...' "Masallaci zaki je ne"? Ya tambaya yana jiran amsa, "A'a fita zamu tare da aunty azmee," Cire hannunsa yayi tare da nuna mata hanya yace"maza ki koma, ki cire wannan abun, bana son sake ganin shi," cike da mamaki Omar ke kallon sgr har dai yagaza yin shiru yace "Rafayet nan fa ba Us bane Nigeria ce, kuma wannan shine best outfits da yace mace musulma tayi, Domin rufe surar jikinta daga jan hankalin mutane akanta saboda tsaro,' girgiza kai sgr yayi tare da cewa "ban yarda da wannan shigar ba, shin Omar taya mutun zai iya motsi acikin wannan abun"? Ya tambaya yana nuna hijabin jikin sehrish,😂 Fashewa da dariya Omar yayi kamar kamar me, ganin yarda Sgr ya haƙiƙance akan hijabin dake ajikin yarinyar, shi a ganinsa takurace kuma mutun bazai iya motsi acikinta ba, daƙer ya dakatar da dariyar tasa ya kalli sehrish tare da cewa "Ki faɗa masa yarda kike motsi acikinta may be ya fahimta," ɗan murmushi sehrish ta saki ita kanta abun ya gama ɗaure mata kai, ɗagowa da hannayenta tayi tare da cewa "Ga hannun hijabin nan, tun da na fiddo da hannun acikinsa lafiya lau nake motsi acikinta," ta ƙarasa bayanin tana kallonsa Jingina bayansa yayi ajikin sofa ɗin tare da cewa "Its Okey, u can go,' har ta juya zata tafi Omar yace "Ya Sunan ki ne? Juyo wa tayi ta kallesa da murmushi a fuskarta tace"SEHRISH" Omar yace "masha Allah suna mai daɗi, amma menene ma'anarsa? ya tambaya yana kallonta, *kyawawan halayyu na mutun," ta bashi amsa, *ina fata zaki nuna mana waɗannan kyawawan ɗabi'un acikin gidan nan, har ma ki zama alkhairi agare mu," omar ya faɗi da ɗan murmushi a fuskarsa, duk Sgr na sauraronsu duk da ya ci gaba da dannar wayarsa, Sehrish ta amsa masa da cewa "Insha Allah," sannan ta wuce Sai lokacin Sgr yace "Ashe kana surutu har haka Omar? Kallonsa Omar yayi tare da cewa"Yarinyar ce tana tattare da wani abun al'ajabi a fuskarta shiya sanya Na sake mata," "Ba kowace baƙuwar fuska yakamata ace kana sakemawa ba irin haka ba, Mata Basu da tabbas they're trouble makers," acewar Babban yaya, ƴar dariya Omar yayi batare da cewa komai ba, Sehrish kuwa kitchen ta wuce ta zubo musu coffee tare da snacks a plate Cikin tray sannan tadawo inda suke tare da ajiye masu saman Table, Omar yace "thank u miss Sehrish," Murmushi tayi masa sannan ta juya ta nufi ɗakin azmee tunkan ta ƙarasa ɗakin nata sai ga Azmee ta fito itama ta kammala shiryawa cikin atampha ja, ta aza babban mayafi milk colour launin takalminta ƙafarta, atare suka fuce suna jiran isowar junaid, Ba da jimawa ba sai ga junaid ya fito daga upstairs yana saukowa down sai faman zabga murmushi yake yi, jikinsa na sanye da haɗaɗɗiyar shadda gezner blue colour mai maiƙo sai faman ɗaukar ido yakeyi kai kace wani sabon ango ne, shaddar tasha aiki a wuyanta tsantsararre, hannunsa na ruƙe da wayarsa haɗe da key ɗin motarsa, Lokacin daya ƙarasa saukowa daga saman stairs ɗin, gaba ɗaya Marshal Omar da Sgr suka bishi da kallo, Zagayawa yayi inda babban yayan nasu yake yana isa ya manna mashi kiss agefen fuskarsa sannan yace "Zan fita, saina dawo," ko amsa bai jira ba cikin sauri ya lalla6a ya fuce yana cewa "yaya Omar kayi masa bayani, mu mun wuce ," Girgixa kai kawai SGR yayi sam ya kasa magana, wato junaid yasan cewa zai iya dakatar dashi daga fita shine yayi dabarar tserewa, Murmushi Omar yasaki tare da cewa "Junaid kenan ! komai nasa na burgewa, ya cika ƙiriniya ga shegen wayon tsiya, saboda kada ka hana shi fita shiyasa ya gudu bai jira amsarka ba," yayi maganar yana kur6ar coffee ɗin da sehrish ta kawo masu a cup, "Ina zasu je ne"? Sgr ya tambaya yana kallonsa, Omar yace "Gidan Uncle Abusufyan na aikesu, inaso zanyi amfani da gidan ne akwai wasu marayune da zan zuba acikinsa kwanan nan," Sgr yace "Omar kenan, meyasa baka sanarmun ba? ko ni ba'a buƙatar gudummuwata ne? ya faɗi yana kallonsa, Murmushi Omar yasaki dama sun saba indai irin haka ne, muddin akace aikin lada yasamu, to har rububi suke yi wurin bada taimakonsu, kowa burinsa ace da dukiyarsa za'ayi amfani wurin bada tallafi sam basa gajiya da irin wannan (Kaji masuyi don Allah) Shiyasa dukiyar tasu kullum hau hawa takeyi kamar kamar me, a ƙalla su kansu basu son adadin gidajen marayun da suka buɗe ba a kasashe daban daban kuma suke ɗaukar ɗawainiyarsu da komai, Manyan asibitoci kuwa da suka buɗe ba iyaka, wanda suma duk kyauta ne ake duba marasa lafiya acikinsu, ga makarantu na marayu da marasa hali da suke dasu ba adadi, wannan ba komai bane ba, kaɗan ne daga cikin abubuwan da suke yi na taimako, Ya Allah ka bamu arziƙi mai albarka wanda zamu amfana dashi kuma ƴan uwanmu musulmai suma su amfana dashi, ba irin arziƙin da mutun zai mallaƙe ba, ka ga ko cikin gidansa fama ake dashi basa ciyuwa balle na waje su samu😧
*****GIDAN ABUSUFYAN*******
Haɗaɗɗiyar daula, Aljannar duniya tun daga kan Tanƙameman gate ɗin gidan Golden colour & brown sehrish ta saki baki tana kallo Ikon Allah, Ba don daga gidan Abban sojoji ta fito ba da sai tace wannan gidan a dubai yake, tsayar da motar junaid yayi abakin gate ɗin sannan ya fito daga cikin Motar, ya nufi jikin gate ɗin, tunkan ya isa ya danna madannin da ke ajikin key ɗin gidan a hankali gate ɗin ya soma zugewa da kansa daker daker yake tafiya saboda gidan ya jima ba'ayi amfani dashi ba tunda Abusufyan yabar Nigeria a fusace gidan yake ahaka garƙame, ganin zai 6ata musu lokaci yasa junaid sanya hannunsa yana ƙoƙarin turasa da ƙarfinsa don yayi saurin f Buɗewa, aikuwa nan take zufa tasoma wanko masa kamar wanda aka watsa ma ruwa a fuska dama jiki bana wahala ba, muryarsa kamar zaiyi kuka yace "Aunty Azmee wai bazaku fito ba mu tura, Wlh ban iyawa ni kaɗai," Jin hakan yasa su fitowa daga cikin motar suna faman tikar dariya, azmee tace"Haba junaid wannan fa ƙaramin aiki ne, sai kace ba Namiji ba haba karka ban kunya mana, Be a Man,' Kallon azmee yayi yana faman sauke haƙi yace"In dai saina tura wannan jibgegen gate ɗin zan zama namiji, to Allah abarni a jinsin mace yafi mun," Fashewa da dariya sehrish tayi har tana dafe ciki jin abunda junaid yace, harara ya watsa mata yana hura hanci, Azmee na isa jikin gate ɗin tace"Matsa ka gani junaid, ni bari in zama Namijin, ni kaɗai zan tura sa," Jin haka yasa junaid matsawa suka bata wuri don ta jaraba, gefen Sehrish ya tsaya suka zuba ido suna kallon azmee, Hannu tasanya sannan ta soma tura gate ɗin nan take ya tafi da gudun gaske ya ƙarasa zuge kansa, Zaro ido Junaid da sehrish su kayi cikin tsananin mamakin ƙarfi irin na AZMEE, A ruɗe junaid yace"Aunty azmee taya hakan ta faru? Ni nakasa turasa amma ke kina aza hannu gate ɗin ya buɗe," Murmushi azmee ta saki tare da nuna masa damtsen hannunta tace "Tsohon ƙashi kenan! ba irin naku ba na ƴan shila," Fashewa su kayi da dariya su duka kafin daga bisani suka koma cikin Motar, junaid ya shigar da ita cikin gate ɗin kai tsaye yayi parking ɗinta a harabar gidan
*Shin Kuna tunanin Cewa Omar zai samu damar ɗauko su hosanna da Jahad daga gidan Aunty babba*?😟
Ku hanzarta yin payment 300 ne ga acct 3196407426 Bature Hafsat Muhammad first bank, sai aturomin shaidar biya ta numberta 08103884440, idan kuma recharge sai ayimun magana ta numberta,ðŸ‘👠[9/9, 4:03 PM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·â€? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* âœï¸ ──────────────EPISODE 19-20
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖ💋â¤ï¸?
*Mallakin Hafsat Bature Moh'd* ~BossBature~ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·�
bayan sun fito daga motar kai tsaye suka nufi hanyar da zata sadaka da babban falon gidan, Sehrish sai faman bin ko'ina take da kallo aranta tana cewa"tab ! Mace ta samu wannan amatsayin gidan aurenta, ae kawai ta bi mijinta sau da Æ™afa, tabi da addu'a don ni gaskiya na mallaki wannan hamshaÆ™in gidan amatsayin gidana, ko Æ™ofar gida bana leÆ™awa sai in ta kama,' sai faman zancan zuci take yi har suka Æ™araso wurin wani bene mai kanannaÉ—a, hawa junaid yayi sannan azmee tabi shi, itama sehrish tabi bayansu, sai faman jinjina kai take yi tana cewa"lallaine Aljanna ta mai rabo ce," daker take tattaka matattakalar benen saboda gajiya don yana da É—an tsayi, bayan sun kai Æ™arshensa, wata haÉ—aÉ—É—iyar Æ™opa ce wadda kai tsaye in ka bi ta zata sauke ka upstairs inda main falo É—in gidan yake, key junaid yasanya yabude Æ™opar sannan suka shiga cikinsa,wurin ya haÉ—u an Æ™awata shi ahaka ma wai ba furnitures acikinsa, to inaga ansanya mashi kujeru da sauran abubuwan Æ™ayatarwa, Batare da 6ata lokaci ba, sehrish ta buÉ—e handbag É—inta, memo ta ciro tare da biro, junaid da azmee suka dunga dudduba falon suna karanto mata abunda za'a buÆ™ata acikinsa, ita kuma tana rubutawa acikin memo É—in hannunta, bayan sun gama da falon kaf sun lissafa duk wani abu da za'a sanya mashi, Sannan acikin babban falon akwai bedrooms guda biyar Æ™ofofinsu na acikin falon, ciki suka shiga suna dudduba É—akunan masu girman gaske, nan ma azmee ta faÉ—a ma sehrish duk abunda za'a buÆ™ata na furnitures ta rubuta, daga nan kuma suka sauko downstairs stairs shima bene ne zai biyo dakai Æ™asan, Agajiye sehrish ta kalli junaid tare da cewa "dan Allah wannan wane irin gidane haka junaid? Nafa rikice wlh, mun shigo ta Upstairs yanzu kuma ga mu a downstairs yanzu ta ina zamu bi mu fita? Ba dai sai mun koma upstairs É—in ba don wlh Æ™afafuna a sanÆ™are suke hawa stairs ko wahala, Junaid da fuskarsa tayi jawur ya gama cika ya 6atse saboda uwar yunwar da yake ji, ga gajiya duk ta baibaye shi, daker ya iya cewa "wannan ne damuwarki, Ni ta cikina nake yi yaushe har muka kammala muka koma gida ni daga nan ma, ba abunda zan Æ™ara yi Allah, ku je ku Æ™arasa sauran aikin in kun kammala kuyimun magana," Wuri yasamu a sitting room É—in dake a downstairs saman wani benci ya zauna, da alama tun lokacin da akayi ginin gidan aka barsa, don akwai tarkacen kayan aikin da aka bari acikinsa, Acikin sitting room É—in akwai Æ™ofofin bedrooms guda biyu, sai kitchen mai girman gaske, sunsha aiki kaf sai da suka zagaye gidan bayan sun tabbatar sun bincika ko'ina sun dudduba abunda ya dace duka kaf sehrish ta rubuta a memo É—inta, Ana cikin kiran Sallar magrib suka bar gidan kowa agajiye, Suna Æ™arasawa gida daga babban falon kowa ya wuce É—akinsa, shaf shaf junaid ya tu6e kayan jikinsa ya faÉ—a toilet donyi wanka, haka itama sehrish tana shiga É—akin nata bayan tayi wurgi da handbag É—inta saman gado tare da memo da biron duka, kai tsaye ta tu6e Jalbab É—in dake ajikinta, ta cire rigar jikinta, cikin sauri ta faÉ—a toilet wanka tayo tare da Alwala, tana fito ta É—aure da towel ta bude wardrobe ta ciro wata doguwar rigar mara nauyi ta zura, daker tasamu tayi sallah bayan ta kammala ta baje saman gadonta, bata Æ™ara sanin meke faruwa ba sam ta manta da batun jera abinci adining, gana babban yaya da zata kai mashi bacci kawai take kwasa, Azmee ce kawai tayi Æ™oÆ™arin fitowa bayan ta canza kayan jikinta, tunda ta leÆ™a tasamu sehrish na jan minsharin wahala, bata tashe ta ba kitchen kawai ta wuce ta shirya masu abincin dinner É—insu ta dunga kaiwa a dining tana jerawa harta kammala, Daker junaid yasamu ya fito sai da yaci ka cikinshi sannan ya wuce masallaci yin sallah, Sai bayan sallar isha'i sannan sehrish tafarka tana faman zazzare ido, agogon bangon É—akinta ta duba kusan Æ™arfe goma da rabi cuf, arazane ta miÆ™e tana faman dafe Æ™irji tuna cewa bata kaima SGR dinner É—insa ba, cikin sauri ta É—auko mayafi a wardrobe tayi lagensa a kanta, sannan tafito dakin azmee tafara wuce wa don taji ko takaimasa, kwankwasawa tayi sannan ta jira ta buÉ—e mata, A lokacin azmee bacci takeyi jin bugun Æ™ofar sehrish yasanya ta, farkawa daga baccin nata, tasowa tayi ta buÉ—e mata Æ™ofa, Ganin sehrish yasa ta cewa "ashe kin tashi daga baccin? Lafiya naganki ko akwai wani abune? Sehrish tace "dama babban yaya na manta bacci yaÉ—auke ni ne, bankai masa É—ina É—insa ba, shine nazo na tambaya naji ko ankai masa," Azmee tace "Ae basu kai ga dawo cikin gidan ba Shi da Omar, pls kada ki koma bacci ko kuma ki sanya alerm na wayarki in sun dawo ki tabbatar kin kai masu abincinsu, sannan kada ki manta ki bama Omar list din da mukayi masa acikin memo dinki,' Sehrish ta amsa mata da cewa "to shikena insha Allah zan bashi, mu kwana lafiya," Tayi ma azmee sallama sannan ta fito ta wuce nata É—akin, gefen gado tasamu ta zauna sannan ta miÆ™a hannu ta É—auko handbag É—inta, wayarta ta ciro daga ciki sannan ta shiga dannata, Tunawa tayi da maganar Azmee da tace mata in zatayi amfani da data, wi-fi kawai zata kunna, Cikin sauri tasanya yatsanta ta janyo top of the screen din wayar ta, danna wi-fi É—in ya kunnu, tsayawa tayi tana tunanin me zata fara yi da wayar yanzu, tana cikin tunanin nan taji Æ™arar shigowar motocinsu cikin gidan kusan Æ™arfe 11-30 na dare, mayar da wayar tayi saman bedside drawer É—inta ta ajiye asamanta, miÆ™ewa tayi tana jiran su kammala shigowa sai taje ta kai masu, sai da tabari 12 tayi dai-dai a lokacin tasan sun kimtsa kowannansu na a bedroom É—insa, Sannan ta fito ta wuce kitchen ba Æ™aramin daÉ—i taji ba ganin azmee ta kammala zuzzuba musu komai na dinner É—insu, a cikin tray guda biyu ta jera masu asaman table na kitchen É—in, Hannu kawai tasanya ta É—auki tray É—aya ta wuce dashi sashen marshal Omar sallama da Æ™arfi tayi saboda yaji ta da kyau, kasancewar yana acikin bedroom É—insa bayan tajiyo Muryarsa yana amsa mata sallamarta ta, sai ta shiga cikin falon nasa ta ajiye masa tray É—in asaman table, sannan ta fita cikin sauri tunawa da Memo É—in da azmee tace ta bashi, bedroom É—inta ta shiga ta dauko memon data bari asaman gadonta, sannan ta koma part É—in nasa a lokacin har ya fito jikinsa sanye da jallabiya ash, wuri yasamu yazauna saman sofa fuskarsa É—auke da É—an murmushi ganin Sehrish, Ƙarasawa tayi inda yake tare da gaishe shi "Yaya Omar barka da dare, ya gajiyar aiki," ? "Alhamdulillah miss Sehrish, ya maganar aikin dana saku? Ina fata komai ya tafi dai-dai, sannan ya gajiya nasan kun kwaso ta ko? Murmushi tasaki tare da miÆ™a masa memo É—in hannunta tace"Gashi nan, mun dudduba gidan duka kuma mun rubuta duk wani abu na furnitures da za'a buÆ™ata acikinsa," Jinjina kai Omar yayi bayan yasanya hannu ya kar6a yana duddubawa yace "Very good, naji daÉ—i sosai gaskiya kunyi Æ™oÆ™ari, insha Allah zuwa gobe zanyi oder na duk wannan abubuwan da kuka lissafa ana buÆ™ata acikin gidan, zuwa dai next week zan sake tuntu6arku," Sehrish tace "toh Allah ya kaimu lafiya," Har ta juya zata tafi ya kuma cewa "kina zuwa school ne? Ko baki fara ba? Sehrish tace"a'a ban fara ba, amma aunty azmee tace zan fara cikin kwanan nan," Omar yace "Owk, inaso ne suma yaran da nakeson kawo wa cikin gidan can, su fara zuwa school amma zan jira naga wadda zaki fara zuwa, in yaso suma saina sanya su amakaranta É—aya dake," Murmushi sehrish tasaki tare da cewa "mata ne suma? ta tambaya tana kallonsa a lokacin harya fara cin abincinsa yace "Eh Æ´an mata ne, kyawawan gaske inason yaran sosai tun dana ganki sai na ga fuskarki tana koma mun irin tasu, nasan saboda son da nake masu ne da kuma kewarsu da nake yi,......' ya Æ™arasa maganar asanyaye, Hakanan sehrish taji gabanta ya É—an faÉ—i raaasss! amma batasan dalilin faÉ—uwar gaban nata ba, taso ta tambaye shi sunayen su amma tunawa da cewa ba ta kaima babban yaya abincinsa ba yasa ta saurin cewa "Allah sarki yaya Omar Allah yabaka ikon Kula dasu, yasa su zama alkhairi agare ka,' Ya amsa mata da "Amin," Sannan cikin sauri ta fuce ta koma kitchen sai da tafara haÉ—a masa yankakkun fruits acikin madai-daicin plate ta azashi asaman tray É—in sannan ta fuce hannunta dauke da tray É—in acikin babban falon suka ci karo da haroon wanda fitowarsa kenan daga part dinsu, night dress ne ajikinsa riga dai-dai guiwa, kawar da kanta tayi tare da miÆ™ar hanya tana jiyo shi yana cewa "a rinÆ™a haÉ—awa da sallar dare ko an samu adace asamu shiga," Murmushi sehrish tasaki batare da tace komai ba bayan ta isa part É—insa da sallama tashiga, baya acikin falon nasa Æ™arasawa tayi ta ajiye masa asaman table dinsa, sannan ta tattaka izuwa bedroom É—insa tsayawa tayi abakin Æ™opar É—akin nasa, sallama tayi masa amma shiru babu amsa hakan na nufin yana cikin toilet ko kuma bacci ya É—auke sa ne, aranta tace "Allah yasa baiyi bacci ba," É—an sa Æ™afarta tayi cikin É—akin nasa ta shiga ciki sai uban Æ™amshi ke daker hancinta kamar wadda tashiga gonar turare, samun shi tayi baje a saman gadonsa daga shi sai Short ajikinsa, ji tayi gabanta ya faÉ—i rass saboda yadda surar shi ke É—aukar idonta, sam tarasa me zatayi ta tashe shi don tasan dole akwai yunwa atattare dashi, kuma in ya tashi da safe yaga ba'akai masa abinci ba zai iya tuhumarta, Shawara ta rage ma mai shiga Rijiya, tana cikin wannan tsayuwar abakin Æ™opan É—aki nasa Æ™afarta har ta soma rawa saboda gajiya da tsayuwa, Wani irin Juyi taga yayi daga saman gadon nasa gaba É—aya ya tafi dukansa zai faÉ—o daga saman gadon, agigice sehrish ta watsa ciki da gudun gaske ta Æ™arasa tare da kai hannu zata tarbesa sai gashi ya buÉ—e blue eyes É—insa kuma nan take yasanya hannusa É—aya ya dafe Æ™asan yarda bazai faÉ—i ba, Tsayawa tayi tana faman sauke haki tare da sauke ajiyar zuciya, matsawa yayi tare da cire hannunsa ya gyara kwanciyarsa saman bedmattress É—in sannan ya É—an ware idonsa akan Sehrish dake atsaye, mamaki ne ya kamasa ganin ta tsaye dab da gadonsa me hakan ke nufi badai tazo bane don ta hanasa faÉ—uwa ba, Æ™arfin halin ta yabashi mamaki shin ko ta ina zata iya ruÆ™oso daga faÉ—uwar da ya kusan yi? tabbas da ace sehrish takai hannunta da nufin ta dakatar dashi daga faÉ—owa daga saman gadon,Æ™arshenta ya faÉ—a mata ajikinta ya danneta tagaza tashi don kuwa ko kusa sehrish bata da Æ™arfin da zata iya taimakonsa daga faÉ—uwa,' Sunnar da kai Æ™asa sehrish tayi cikin jin kunya sam tarasa gane ma kanta, ita dai kawai burinta karya faÉ—o Æ™asa yaji mummunan rauni shiyasa tayi yunÆ™urin tarbosa, Kasalalliyar muryarsa ce ta ratsa ta da cewa"Sannu da Æ™oÆ™ari, amma kada kiyi attempting cewa zaki ruÆ™oni next time, if not jikinkin ki nei zai gaya maki," Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"kayi hakuri bazan Æ™ara ba," Shiru yayi tare da mayar da idonsa ya lumshe su, yana faman sauke ajiyar zuciya, É—agowa ta danyi tare da kallonsa tace "dama......na kawo maka dinner É—inka ne, yana a falo na ajiye," Kusan minti 5 da yin maganarta ta sannan yace"Shigomin da fruits tare da Coffee, su kawai nake buÆ™ata," Juyawa tayi cikin sauri ta koma cikin falon hannu tasa ta É—auki plate É—in dake dauke da fruits É—in ta shigar masa dashi saman front table É—im gadonsa ta ajiye masa, sannan ta koma ta dauko masa hadaÉ—É—en Coffee din dake acikin Cup ta dawo É—akin nasa a lokacin har ya tashi zaune ya sauko da Æ™afafunsa Æ™asa, a gefen plate É—in ta ajiye masa sam yagaza buÉ—e idanunsa da alama ba Æ™aramin bacci yake ji ba, sai faman cizon pink lips É—insa yake yi, Ita dai burinta ya buÉ—e idonsa yafara shan fruits É—in kafin ta tafi, don batason ya kwanta bai ci komai ba acikinsa 😒 Muryarsa taji yace"What are u waiting for? Ko zaki ban abaki ne? ya faÉ—i a time din yaÉ—an ware idanunsa masu É—auke da bacci, Cikin sauri sehrish tace "a'a sai Allah yakaimu, mu kwana lafiya," ta fadi tare da juyawa cikin sauri ta fuce daga É—akin nasa sai da tafara tsayawa ta dauki food stuffs din dake acikin tray É—in da ta ajiye masa sannan ta fuce dasu, a kitchen tasamu wurin ta zauna saman dining table É—in ciki, buÉ—e kayan abincin tayi tazauna ta shaÆ™e plate tana ci, bayan ta kammala ta koma bedroom É—inta sai da tafara yin sallar isha'e sannan tayi addu'ar yin bacci taja bargo ta lullube jikinta cikin wani irin yanayi na abunda yafaru tsakanin ta da SGR, ***************AUNTY BABBA********** Da kanta ta girka masu hosana da jahad lafiyayyen abinci ta kuma jera masu shi adining, su duka suka halarta suna ci jahad na kusa da uosana polyayin da Hafsat ke kusa da mommynta dama mai 4 seats ne, Duk sun kasa sakewa suci Abincin saboda fargabar da suke ji aransu, kwarama hussana tasamu tana shan kakkauran tea É—in data haÉ—a mata tare da bread wanda yaji butter ajikinsa, É—agowa Aunty babba tayi ta kalli jahad tare da cewa "My daughter me yake faruwa ne? Naga tun É—azu sai fama juya cokali kike yi acikin plate, yakamata ki fara cin abincin ko saiya huce"? ta tambaya cikin nuna kulawa, murya na rawa jahad tace "babu komai Aunty zanci ne yanxu," Jinjina kai aunty babba tayi tare da cewa "kwara dai kici ta da zafin ta, saboda in ta huce baza tayi maki daÉ—in ci ba," Jahad ta amsa da toh sannan ta soma cin taiyar pasta din dake agabanta, Mayar da idonta tayi kan na hussana tace "Yawwa my daughter, ae ke na lura bakya wasa da abinci da alama, kamar ni kike, shiyasa gani nan kamar buhun masara sai uban auki," Jin abunda tace yasamu fashe wa da dariya su duka banda hafsat dake satar kallon mommyn nata, abun É—aure mata kai yake ganin yadda lokaci guda Mommynta ta sakewa yaran aranta tana cewa "gaskiya Mommy ba Æ™aramar Æ™uruwa bace wurin iya tsara tuggu, ta iya shu'umanci Allah kaÉ—ai yasan me take shirya wa, koma dai menene nidai ina nan ina zuba ido in gani......👀 Murmushi Aunty babba tasaki tana kallonsu ganin yarda tasanya su nishaÉ—i aranta tace "haka nake so don kutmar ubanku a hankali zan canza muku tunani har na cimma burina," a fili kuma ta washe baki tana cewa "ku hanzarta ku kammala ci dare yayi sosai yakamata ace yanzu kun kamma yi nisa a bacci, sannan jahad kada ki manta kafin ku kwanta ki tabbatar kin ba Hussana maganinta, Jahad ta amsa mata da "toh," Bayan sun kammala yin dinner É—in nasu suka wuce bedroom din hafsat bayan hussana tasha maganinta sannan suka kwanta, bacci mai nauyi ya É—auke su............. Kallon Hafsat aunty babba tayi a lokacin itama idonta nakan Mommyn nata, "tun É—azu na lura da satar kallona da kike yi shiru kawai nayi," aunty babba ta fadi tana kallonta Hafsat tace "hmmmm mommy kenan ni so nake ki faÉ—amun abunda kike shiryawa game da twins É—in nan yakamata na sani," Dariya aunty babba tayi kafin tace "bai da amfani koda kin sani hafsat ! ki ma daina tambayata domin kuwa bazaki ta6ajin mutuwar sarki abakina,!" Jinjina hafsat tayi tare da miÆ™ewa daga kan dining É—in tace "Shikenan Mommy kwarama ki ruÆ™e sirrinki, yarda in asiri ya tashi tonuwa ke kaÉ—ai zakiji jiki ban dani, ni dae nayi nan," tana faÉ—in hakan ta wuce cikin bedroom É—inta, Saman Sofa ta kwanta tare da jan bargo ta lullu6e jikinta, Shu'umin murmushi Aunty babba tasaki tare da cewa "Yanzu wasan ya soma, " 😳 Nikuma nace Allah yaba mai rabo SA'A ***********AFTER 1 WEEK********* BAYAN SATI ÆŠAYA Acikin waÉ—annan kwanakin Jahad da hussana ba Æ™aramin kwanciyar hankali suka samu ba, sun samu Æ´anci sosai acikin gidan jikinsu yayi kyau ba laifi sun É—an murmure, gashi hafsat bata gajiya da É—awainiya dasu har fita takeyi dasu yawan shaÆ™atawa, su fita shan ice cream ko kuma ziyarta gidan friends É—inta, Aunty babba dae ta zuba ma sarautar Allah Ido burinta kawai Baba alamu ya diro Garin kaduna kafin Zuwan Omar, don tuni Baba Alamu yasanar da ita cewa suna kan hanya yau Litinin zasu sauka kaduna, 😳 A 6angaren Sehrish kuwa tana cikin farin ciki matuÆ™a saboda makaranta da zata fara zuwa, an riga da an kammala yi mata komai hatta Uniform É—inta an kawo mata su kusan kala 3, ga sandals É—inta masu kyan gaske, ga jibgegiyar school bag É—inta da aka siya mata tare da textbooks na amfani da sauransu, abunda ya rage mata yanzu shine fara zuwa makarantar acikin satin nan, 😇 Tuni Marshal Omar yayi oder na haÉ—aÉ—dun furnitures made in dubai, kamfanin da yayi siyayyar kayan su da kansu, suka tsara mashi gidan wa'iyazubilla wurin kyau ba'a magana, komai sabo fal acikin gidan, kayan kitchen ne kayan É—aki kayan falo komai fa wannan an zuba acikinsa ba abunda ya bari, bari in taÆ™aice muku zance hatta wannan kayan store na abinci yasa an jibge masu shi, duka freezer É—in dake acikin gidan yasa an cike masu shi da Kayan marmari dana sha, komai fa Omar ya tanadar musu na jin daÉ—in Rayuwa, dama abunda ya hana shi zuwa kaduna kenan saboda yafi son saiya fara gyara masu gidan ya sanya musu komai na more rayuwa acikinsa sannan ya je yaÉ—auko su, kuÉ—i sosai Omar yaba Sehrish da azmee don suje yi musu siyayya, koda suka tambaye shi size dinsu na kayan da zasu siya masu gudun kar ayi kuskure, sai yace musu komi zasu siya irin na Sehrish saboda yana da tabbacin cewa tsayinsu da komai na jikinsu bazai wuce na SEHRISH É—in ba, da sukayi masu siyayyar kaya masu yawan gaske kamar irin na sehrish amma nasu yafi yawa saboda su biyu ne, Æ™arshe sai dai motar kamfanin da su kayi siyayar ta kawo musu kayan har gidan Abusufyan saboda motar junaid bazata iya kwashe su duka ba, saboda shine ke É—awainiya dasu duk in da zasu fita, finally dae komai ya kammalu,ðŸ‘
Ga masu karantawa a facebook indai kuna son Cigaba da kawo muku littafin Abban sojoji to ku hanzarta yin payment recharge card zaku tura ta wannan numbar 08103884440, 200 ne saura 3 pages free ya qare, Ga masu acct gashi nan 3196407426 first bank, Bature hafsat Muhammad, wanda sukayi payment ina sane dasu kuma kuÉ—insu bazai tafi abanza ba🙌 [9/12, 8:44 AM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·â€? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* âœï¸ ──────────────EPISODE 21-22
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖ💋â¤ï¸? ~Story & Written~ *BossBature* •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·â€? Ringing É—in da wayarta ke faman yi ne ya tashe ta daga guntun baccin daya É—auke ta, farkawa tayi tana faman yin Hamma, hannu ta miÆ™a tare da É—aukar wayarta dake ajiye saman side drawer, duba screen É—in wayar tayi don taga wanene ke kiranta, lokaci guda gabanta ya faÉ—i rass ba arziÆ™i ta miÆ™e zaune saman gadon tana duban sunan mai kiram nata, sam tagaza sa hannu ta É—aga kiran saboda tasan mai zai biyo baya,  Kusan sau uku kiran nashigowa cikin wayar ta ta, amma taÆ™i É—agawa daga bisa ni mai kiran nata yadaina kira,  Can sai ga Æ™arar shigowar Message cikin sauri tasa hannu ta buÉ—e sakon ta soma karantawa kamar haka _Babu buÆ™atar yin Sallama! Malama hafsat kin ban mamaki,Na kwashi uban kuÉ—i nabaki donki gudanar mun da aiki na, amma sai gashi Labari ya risÆ™eni cewa Anganki kina yawo dasu agari,Don haka ina so ki mayar mun da kuÉ—ina yau É—in nan in ba haka ba kotu ce zata raba ni dake_!!!!!!!!   Wata Irin nannauyar Ajiyar zuciya Hafsat tasaki afili take furta "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un, ni sam na manta da maganar wannan matar ashe tana sane da kuÉ—inta, gashi har na fasa su, yanzu dole ne na biya ta kuÉ—inta ko na samu salama, tabbas zata iya ja mun bala'e Ya zanyi ni! Gashi Yau Daddy zai dawo in yaji wannan abun tabbas Nashiga Ukuna!  YunÆ™urawa tayi cikin sauri daga saman gadon jikinta na sanye da dogon wando baÆ™i sai Æ´ar Riga fara mai dogon hannu ajikin rigar an rubuta *I Love Paris*   Hannu tasa ta É—auki ribbom É—inta da ke ajiye saman mirror, ta É—aure sumar kanta dashi sannan ta fito cikin hanzari, a babban falon tasamu Jahad da hussana zaune saman 3 seater suna kallo a plasman dake facing É—insu, jin alamar tafiyar hafsat yasa su É—agowa tare da haÉ—a baki wurin cewa "Barka da fitowa Aunty hafsat," daker ta iya yi masu murmushin yaÆ™e tace "Yawwa My Twins," sannan cikin sauri ta wuce upstairs direct izuwa bedroom É—in aunty babba,
tun kafin ta shiga ɗakin nata take faman kwala mata kira Mommy!mommy!!Mom!!" Aunty babba da fitowarta kenan daga bathroom waist dinta daure da farin towel tana faman tsane gashin kanta da karamin towel tace"daughter lafiya kike mun irin wannan kiran na tashin hankali !!!," Shiga ciki hafsat tayi tana cewa "Mommy akwai matsala wlh! Dakatawa da tsane gashin kanta tayi sannan ta juyo ta kalli hafsat tare da cewa "Matsala kuma ta me kenan"?Cikin tashin hankali hafsat tace "Mommy wannan matar data ban kuɗi don na zubar mata dasu hussana da jahad, wlh itace ta kira ni yanzu, ban ɗaga kiran ba shine ta turo mun saƙon cewa na biya ta kuɗinta ko kuma ta haɗa ni da hukuma!!Ta ƙarasa maganar tana jira taji mai Aunty babba zata ce, abun mamaki sai taga ta fashe da dariya mai sautin gaske....... Cikin ruɗu hafsat tace "Mommy na faɗa maki tashin hankalin da nake ciki maimakon ki tayani jimami amma sai naga kina dariya saboda me!? tsagaitawa da dariyar Aunty babba tayi sannan tace"Hafsat kenan to ni menene ruwa na aciki? Ki mayar mata da kuɗinta mana shine kwanciyar hankalin ki," Muryarta tamkar xatayi kuka tace "Amma mommy sarai kinsan cewa nariga da na ta6a kuɗin nan kusan dubu ɗari takwas nayi amfani dasu aciki, Bani da kuma hanyar da zan biya su shiyasa nazo wurin ki saboda nasan akwai kuɗinsu Jahad wanda yaya Omar ya bayar ayi masu hidima, Inaso ki bani su don na biyata kuɗinta," Turusss ! aunty babba tayi kafin tayi Uwar shewa tace "Ahayyeeeee ! Anzo wurin dana fi so !! tabbas don kuɗi akwaisu kuwa suna kwance cikin bank account ɗina suna bacci, Ko sisi wlh baxan baki ba !! Har ni zaki watsa ma ƙasa a ido saboda waɗancan tsintattun yaran da ke da kan ki kika ce zasu iya zama nakiyar da zata tarwatsa mun plan ɗina, amma sai gashi akan idona kike nuna masu soyayya don ki 6atamun rai Ko?, don haka kije kiji da matsalar ki ! Ni babu ruwana acikin lamarin ki!!! Ido cike taf da kwalla hafsat ke kallonta cikin tsananin 6acin rai da ƙuna har ta nufi hanyar fita daga ɗakin ta tsaya tare da juyowa ta kalle ta tace "Mommy naji duk abunda kika ce ! Nayi mamakin yarda kike tada jijiyoyin wuya akan kuɗin da bada gumin ki kika same su ba! Kuɗin nan Mallakin Su hussana ne! saboda su Omar yabada ayi masu hidima, ke kuma kika kwamashe su Saboda son zuciyarki, don haka muddin kika ce zaki hanani kuɗin nan, zan kira yaya Omar ne na tona maki asiri game da duk irin cin Zalin da kika yima Twins ɗinsa.............' dakatawa tayi da maganar tana faman haƙi, Aunty babba kuwa wani irin shu'umin murmushi tasaki kafin tace "and then So What Hafsat! Go ahead ki faɗa masa wlh ko ajiki na! Ni nasan yarda zan fidda kaina wlh, kece a ruwa bani ba, Ni dan Allah fuce mun daga ɗaki............ tayi maganar tare da nuna ma hafsat hanya alamar ta fuce mata daga ɗakinta, murmushin takaici kawai hafsat tasaki kafin tasa kai ta fuce daga ɗakin, cikin tsananin jin 6acin rai Fuuuuu ta wuce izuwa downstairs ta wuce bedroom ɗinta, wuri ta samu gefen gadonta ta zauna cikin tashin hankali tana cikin wannan tunanin message ya sake shigowa cikin wayarta data bari saman gadon,Hannu tasa ta ɗauki wayar tare da buɗe saƙon ta karanta kamar haka "ina tsammanin jin alert ɗin kuɗina, a yau ɗin nan in ba haka ba, nasamu labarin cewa yau general ishaq zai dawo wato Abbanki, kai tsaye zanzo har gidan ku, adai-adai lokacin dana tabbatar cewa ya iso gari zan shigo na tada maki 6alli" Shiru hafsat tayi gabanta na wani irin faɗuwa tuni idonta sun canza launi, bata da wata mafita daya wuce ta koma ma mommyn nata, ta lalla6a ta tasamu tabata kuɗin ta mayar ma jarababbiyar matar nan, ko sun rabu lafiya, Zumbur ta miƙe tashi ga yin sintiri acikin ɗakin nata cikin tsananin damuwa, Sallamar Jahad ce ta katse mata dogon tunanin da ta shiga, "Jahad har kun gama kallon"? ta tambaya yayin da take ƙaƙaro murmushi a fuskarta, Jahad tace "A'a aunty an fara kiran sallar la'asar ne shine nashigo nayi sallah," Hafsat tace"Allah sarki, na lura bakya wasa da sallah Jahad, da zarar lokacinta yayi komai kike saina ga kin dakatar dashi don yin ibadah,"Murmushi jahad tasaki tare da shige wa ciki tana cewa "aunty babu abunda yakai sallah muhimmanci acikin dukkan aiyuka, babu wani jin daɗi na duniya da zai sanya na manta da yin ibadata abisa lokacinta..........' Wayar Hafsat da tayi ringing ya hana jahad ƙarasa jawabin nata, cikin sauri hafsat taƙarasa ta ɗauki wayar tare da dubawa, ganin numbar matarnan ce tsanya ta, yin wurgi da wayar, hankali tashe ta fuce daga ɗakin......... Shiru jahad tayi cikin mamamki ganin yarda hafsat tayi wurgi da wayarta ga fuskarta da alamun damuwa hakan na nufin wani abu na damunta, "Ya Allah ka yaye ma aunty hafsat damuwar dake damunta, ka kawo mata mafita Alfarmar Annabi Muhammad (S.A.W)," ta faɗi acikin ranta sannan tashige cikin toilet donyin alwala,kai tsaye Hafsat ta koma ɗakin Aunty babba, lokacin da ta shiga har ta kammala shirya kanta cikin atampha Embellished mai tsadar gaske da kyau, tana zaune saman stool agaban mirror tana shafa jan baki abakin ta, Hafsat ta shigo, wuri tasamu gefen gadonta tazauna tana kallonta,Juyowa Aunty babba tayi ta kallota tare da sakin Murmushi tace "My daughter, Look at my face how do i look? Kinsan yau Abban ki zai dawo, Shiyasa na taƙarƙare ina masa kwalliya, yau inajin kaina tamkar sabuwar amarya," Fuska a ɗaure hafsat tace"Kinyi kyau,"Aunty babba tace "Ae ko baki faɗa ba, nasan cewa ni kyakkyawa ce, tun da gashi nan ke ma albarkacin kyau na kin samu har kinyi ɗan haske da dogon hanci ga gashi har kina taƙama," Hafsat tace "hmmm mommy kenan, amma dai kinsan cewa Hanci na ba irin naki bane ko? kuma da kike maganar kyau kar ki manta Abbana fa kyakkyawa ne hausa fulani," Tsoki aunty babba tasa ki tana cewa "Menene wani hausa fulani, Jinin Larabawa ake magana, kowa yasan mu da kyau babu jinsin da suka kai mu kyau aduniya kaf," ɗan guntun murmushi hafsat tasaki kafin tace"Ae shi kyau mommy ba'a fuska yake ba, ko a Surar jiki, a zuciya yake!! Duk kyan mutun muddin zuciyarsa baƙa ce, to ya tashi abanza mummuna ne shi,'Jin abunda hafsat tace ne yasa ta ajiye jan bakin dake hannunta tace "Tashi ki fuce mun daga ɗakina ! Bansan ma uban me yakawo ki ba," Shiru hafsat tayi batare da ta motsa daga inda take ba, illa kawai ta zuba mata ido,"baxaki fuce mun daga ɗaki na ba"? ta faɗi fuska aɗaure, Sassauta murya hafsat tayi tare da cewa "Kiyi haƙuri mommy in na 6ata maki rai, zuciyata ce bata mun daɗi........' Aunty babba ta katse ta da cewa "don zuciyarki bata maki daɗi shine kika zo na wanke maki ita? Ko me? girgiza kai hafsat tayi tare da cewa "kusan hakane mommy, ni yanzu zuwa nayi ki taimaka mun na mayar ma matar nan kuɗinta, ta addabe ni da kira, narasa ya zanyi," Murmushi aunty babba tasaki tare da juyowa sosai tana fuskantar hafsat tace,"Na Amince zan baki kuɗin ki mayar mata, amma bisa wasu sharuɗɗa! In kin bi muzauna lafiya daga ni har ke!? jinjina kai hafsat tayi tace "ina sauraronki, wasu sharuɗɗa ne? aunty babba tace "Inaso ki amince da maganar Fitar da yaran nan daga cikin rayuwarmu !!!!!! ɗagowa hafsat tayi aɗan razane tana kallonta..............Murmushi Aunty babba ta saki kafin taci gaba da cewa "Abun da nake son ki fahimta hafsat, ko da mun bar Omar ya ɗauki yaran nan ya tafi dasu can gidansu, wlh baza su ta6a samun kwanciyar hankali ba, domin kuwa Ke kinsan wacece Ammi ta tsani mutumin da bai da asali ya ra6i jinin ta, koda Omar yakai su can wlh ba zasu tsira ba!domin kuwa Ammi na zuwa zatasa a Kore su daga gidan! don haka yakamata kiyi tunani akan hakan kwarama cikin ruwan sanyi mu rabu dasu Lafiya, Shiru Hafsat ta ɗanyi na wani lokaci kafin tace,"Yanzu mommy Idan na Amince, su kuma yaran Yaya rayuwarsu zata kasance?ina za akaisu? Ina tsoran Rayuwarsu ta salwanta ! Aunty babba tace "Hafsat don me zaki damu akan haka? ni in dai kin Amince zan sa akai yaran gidan marayu acan zasu samu kulawa, kuma dama can yafi dacewa dasu, in yaso sai mu runƙa zuwa muna kai musu Ziyara tare da tallafi koya kika ce? shiru hafsat tayi na wani lokacin sannan tace"Shikenan Mommy na yarda da hakan, Amma yaya Omar fa? In yazo yaya zamu ce mashi in ya tambayi twins ɗinsa? ɗan murmushi aunty babba ta saki ba ƙaramin daɗi taji ba jin yarda hafsat ta amince yanzu komai zai fi zuwa mata da sauƙi, taci gaba da cewa "Hafsat duk yarda zamuyi kada mu bari Abban ki yasan da yaran nan har izuwa gobe, Akwai wanda nayi ma magana zai zo gobe insha Allah, Shi zai kai su gidan marayun, Sannan maganar Omar tunda har yakai yanzu bai zo ba, inajin cewa tabbas akwai abunda ya tsaida shi wannan ba matsala bace kibar mun komai a hannuna ni nasan yarda zance mashi ya yarda.................. Jinjina kai hafsat tayi jikinta a matuƙar mace saboda sabon da tayi da Su hussana da jahad sam batason rabuwa dasu amma kuma babu yarda zatayi this is the Only solution !!! Ajiyar zuciya ta saki tare da kallon Mommyn nata tace "Shikenan Mommy, ni zan wuce ɗaki sai naji ki ............ Muryarta na rawa take magana cikin sauri ta ƴunƙura tare da miƙewa ta nufi hanyar fita ɗakin tana jin Muryar Aunty babba tana cewa "Yanzu zan tura maki da kuɗin ki mayar mata abunta, kar taja mana bala'e Hafsat bata ce komai ba saboda yanayin da ta shiga, cikin sauri ta fuce kai tsaye ta shiga bedroom ɗinta, Lokacin da ta shiga ta samu su hussana da jahad zaune saman darduma suna karatun Al'qur'ani da kansu, sai taji zuciyarta ta ƙara karaya, cikin sauri ta faɗa toilet tare da rufo ƙopa tana faman shessheƙar kukan rabuwa dasu.........................................
__________________SEHRISH__________
Sam bakin ta yaƙi rufuwa don Murya, tun ɗazu ta shimafiɗa uniform ɗinta saman gadonta tare da sandal ɗinta da kuma school bag ɗin duka, ta tasa su gaba sai kallonsu take yi,bakomai take tunani ba face yarda zata fara shiga school gobe Talata, irin wankan da zata ɗauka,tana daga zuƙunne saman gadon nata sae faman sakin murmushi takeyi, hannu tasa tare da shafa uniform ɗin data jera tana cewa "daga gani zasuyi mun kyau,oh ni reeshi yanzu zanyi new friends a makaranta, da na banza da na kirki, Allah dae ya haɗa ni dana gari, ba wanda zasu canza min tunani na ba, ina ƴar talaka dani," ta faɗi da ƴar dariya, Turo ƙopar Azmee tayi tare da shigowa tana cewa "Da alama yau sehrish kin manta da shiga kitchen ko? kin barni da aiki narasa dalilin dayasa kika zubama kayan makarantar nan naki ido,sai kace ba mallakin ki ba"?   tayi maganar yayin da take ƙarasawa ciki, ɗagowa sehrish tayi ta kalle ta fuskarta washe tace "Am sorry aunty azmee, Yanzun nan nake shirin fitowa wlh, na kammala salla ne shine nake ɗan ƙara binsu da kallo,   girgiza kai Azmee ta ɗan yi kafin tace "maza ki tattara kayan nan, ki mayar dasu cikin wardrobe, Kizo maza mu kama aiki,'   Sehrish ta amsa mata da Toh sannan ta miƙe cikin sauri ta sauko daga saman gadon, Tattara kayan Uniform ɗin tayi takai su cikin wardrobe, bayan ta kammala ta ɗauki mayafinta saman gadonta, tayarfa shi akanta dama riga da skirt ne ajikinta,   Cikin sauri tabi bayan Azmee suka fuce izuwa kitchen,  Cikin hanzari suka soma shirye shiryen fara girkin dare, suna cikin aiki Azmee nagaban gas tana tafasa nama, yayin da sehrish ke ta faman fere kayan lambu asaman Chopping board,   Faɗowa junaid yayi cikin kitchen ɗin jikinsa na sanye da Kayan ball yellow sai faman zufa yake yi da alama shigowarsa kenan daga wurin ball, sam yagaza rufe bakinsa sai faman murmushi yake yi,  "Wlh harka ban tsoro junaid, yarda ka faɗo suddenly,jibi jikin ka sai faman zufa kake yi," Sehrish ta faɗi tana nuna sa da wuƙar dake hannunta,  Juyowa azmee tayi tana kallonsa batare da tace komai ba,  "Zuwa nayi in tunasar maki cewa, gobe ni zan kai ki school da mota ta," ya faɗi yana faman sauke ajiyar zuciya,. Sai lokacin azmee tace "Salon wahalar da kai junaid, ka bari tahau school Bus mana,ƙwara tasa ba da bin motar makaranta tun yanzu, amma in kace zaka runƙa kai ta ɗawainiyar zatayi yawa, kuma kasan sarai Babban yayan ku baya so kana fita ko?.ta faɗi tana kallonsa,.  turo baki junaid yayi tare da ɗan buga ƙafarsa yace "Nidai Aunty azmee zan kaita, just for tomorrow cos this is the first time da zata fara zuwa school ɗin yakamata tasan wasu abubuwan inaso zan nuna mata ne, tun da ni nasan school ɗin sosai...."  gaba ɗaya kallon shi suke yi yarda yake magana cikin shagwa6a, yana faman bubbuga ƙafa Dariya azmee tayi don ta Lura rigimarsa ce ta tashi, dama aduk lokacin daya buga ball sosai yagaji alokacin rigimarsa tafi tashi,  Sehrish tace "Shikenan junaid gobe kai zaka kaini school, amma yanzu kana buƙatar yin wanka ka ɗan huta,,"   ɗan murmushi yayi jin abunda tace "Amma ina jin yunwa fa sosai," ya faɗi yana kallonta  "Shikenan kada kadamu yanzun nan zan kawo maka abinci,"  "Yawwa My lovely sis," ya faɗi tare da kama hanya ya wuce upstairs room ɗinsa,   A tray ta shirya masa coffee tare da snacks, sannan ta fito ta wuce upstair domin takai masa, tana hawa saman stairs ɗin sai ga SGR shi da Marshal Omar suna nufo stair ɗin, ganin su zo dab da benen yasa ta saukowa gaba ɗaya don tabasu wuri su wuce, dukansu suna sanye da jean da t-shirt, sai faman sauri suke alamar akwai wani Uzuri dake gare su, suna ƙarasowa inda take tsaye tayi saurin cewa "ina yinin ku," Omar ne kawai yasamu damar Amsa mata, amma shi SGR sam ko kallo ma hasalima baisan da mutun a wurin ba, gabanta ne ya faɗi don alamu sun nuna cewa ba ƙaramin abubane ganin yanayin fuskar kowannansu Especially Omar da ta sani, Kullum cikin sakar mata fuska yake duk in suka haɗu amma yau dakyar ya amsa mata gaisuwarta,  Bin su tayi da kallo, yayin da suka wuce kai tsaye hanyar fita falon suka nufa, har sun kusa fita Omar ya juyo ya kalle ta, bakomai yasa Shi juyowa ba fa ce tuna Hussana da jahad yau tsawon wata kenan baije ya dubo su, saboda busy ɗin daya shiga, yana da burin zuwa ɗaukosu amma aiyuka sun hana shi, Ajiyar zuciya yasaki tare da mayar da kansa suka sa kai suka fuce,   sam sehrish tagaza yin motsi da ƙafafunta, hakanan ta dunga jin gabanta na faɗuwa, bata kai ga hawa benen ba, taji dirar motoci cikin gidan nan take ta sake jin faɗuwar gaba, cikin sauri ta haye upstairs ɗin da hanzari ta shiga bedroom ɗin junaid a lokacin yana cikin toilet yana wanka, ajiye masa tray ɗin tayi saman table, sannan tafito da sauri-sauri ta fito daga babban falon ta tsaya abakin ƙofar shigarsa, .  Kamar dai ranar da SGR da Omar suka zo Nigeria tare da uban security guards na sojoji haka yau ma, tsoro ne yakama sehrish gudun kar ace US zasu koma,   Tana ganin lokacin da suka shiga cikin motocinsu kuma nan take motocin ajere suka nufi dogon titin da zai fidda ka daga cikin gidan,   Komawa ciki tayi da gudun gaske ta faɗa kitchen tana faman kwalama aunty azmee kira, a ɗan razane azmee ta juyo ta kalle ta tare da cewa "Sehrish lafiya kuwa kike ta faman kwalamun kira haka!?  Cikin tsananin tashin hankali tace "Aunty azmee meke faruwa ne? Yanzun nan naga Babban yaya tare da Yaya Omar, sun fito fuskokinsu ba annuri kuma ga tarin motoci can sun fita dasu,"   tsayawa azmee taɗan yi jimmmmmmm tana ɗan tunani kafin tace "Tabbas ina hasashen cewa Us zasu tafi Saboda ɗazu da safe naji ƙishin-ƙishin ɗin cewa Momynsu matar Uncle ɗinsu donald tana fama da blood cancer, To ina da tabbacin cewa kodae ta rasu ne...........'   Zaro ido sehrish tayi cikin tsananin tashin hankali take furta "Innalallahi wa'inna ilairaji'un Allah yasa bata mutu ba, Yanzu shikenan in suka koma ko yaushe zasu dawo.....'   Murmushi Azmee tayi kafin tace "naga kin tayar da hankalin ki, nasan saboda Tafiyarsu Rafayet ne bawai don jin mutuwar ba,    Hannu sehrish tasa tare da rufe fuska saboda hawaye da taji sun tafo mata,   bin ta da kallo kawai azmee tayi cike da mamakin ganin tana shessheƙar kuka,   Matsawa tayi kusa da ita tare da dafa ta tace"Sehrish !! Wannan kukan na menene? Ba dai don tafiyarsu bane?   shiru kawai tayi batare da tace komai ba, ita kaɗai tasan me take ji aranta, gaba ɗaya fuskarta ta damuje da hawaye,    Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "Ki koma ɗaki ki kwanta kawai,"  Cikin kuka sehrish tace "a'a aunty azmee zanyi aikin,"   Azmee tace "a'a banaso ki tafi kawai zan ƙarasa abuna,"   Juyawa sehrish tayi tare da fuce wa daga kitchen ɗin ta koma bedroom ɗinta, saman gado tafaɗa tare da cigaba da kukan, To fa sehrish komai yasata yin kuka? Allah wa'alamu,  Azmee kuwa ta jima tana mamakin dalilin kukan Sehrish tarasa gane mata, aranta tana cewa "Badai saboda tafiyar SGR take kuka ba? Don ta lura da yadda sehrish ke matuƙar ƙaunarsa, sam bata iya fira batare da ta, Amabaci sunan shi ba ita dae kawai tafison jin Ana maganarsa,nan zakaga sakewarta,   "Lallai ne akwai Babbar Matsala, muddin abunda nake zargi ya tabbata,ya zama dole in ja ma Sehrish burki, don gujema kamuwa da CIWON ZUCIYA,"!! Azmee ta faɗi acikin ranta,  _______________________
Sehrish kuwa Tuni wani Irin zazza6i taji ya rufe ta lokaci guda, jikinta har kerma yake yi wurin janyo bargonta dake asaman gadonta ta lullu6e jikinta dashi, tana faman fidda numfashi mai zafin gaske, sam tarasa ina zata tsoma ranta ita kaÉ—ai tasan irin raÉ—aÉ—in da take ji acikin zuciyarta
Har wuraren Sallar Magrib sehrish bata motsa ba, tana nan yarda take ƙudundune cikin barko,tamkar mai bacci alhalin nan Idonta biyu jikinta ne kawai da bayayi mata daɗi, Acan ciki kuwa fitowa junaid yayi bayan yasha baccin sa, ya sauya kayan jikinsa izuwa riga da wando, lokacin daya sakko down yayi mamakin ganin Azmee ita kaɗai tana faman jera masu dinner a dining, ƙarasawa yayi cikin sauri yana cewa"Aunty Azmee ina sehrish ɗin ne? Ita bazata fito ta tayaki ba? Azmee ta ɗan ɗago ta kallesa tare da cewa "Junaid ni kaina bansan meke damun Sehrish ba, Lafiya lou fa muke aiki da Ita, amma tunda tazo ta tambaye ni game da babban yayanku da Omar da taga sun fito fuskarsu cikin wani irin yanayi, kuma taga Sun fita tare da motoci dayawa, shine nake ce mata may be Us zasu je, tunda ɗazu da safe naji ƙishin ƙishin ɗin cewa Matar Uncle ɗinku donald tana fama da blood cancer may be ta rasu ne.....shine fa kawai sehrish takama kuka har nace mata ta koma ɗakinta kawai ni zanyi aikin," ta ƙarasa maganar cikin damuwa, Junaid kuwa shiru yayi hankalinsa ya rabu gida biyu, sam ya rasa gane inda maganar Azmee ta dosa, cikin mamaki yace "Us kuma? Taya babban yayan mu zaibar ƙasar nan batare da sani na ba? Anya kuwa aunty Azmee am just doubting about it bana tunani Us zasu je, kuma Matar uncle donald bana tunanin ta rasu gaskiya, tunda da naji ko a wurin Abban mu ne, Ni dai Allah yasa ba wani abu bane ya faru mummuna," ya faɗi cikin tashin hankali kafin ya wuce yana cewa "Bari naje wurin Sehrish ɗin naji meke damunta," Azmee tace "to shikenan,"
A hankali ya tura Æ™opar É—akin yashiga da sallama, tsayawa yayi yana kallonta yarda take Æ™udundune cikin bargo, A hankali ya kira sunanta "Sehrish..........' shiru bata amsa masa ba, Æ™arasawa yayi izuwa gab da gadon nata yaÉ—an zauna gefe tare da sa hannu ya yaye mata bargon dake jikinta, dogon numfashi taja tare da cewa "Junaid ka mayar mun da bargona, Sanyi nake ji," Junaid yace "Reesh wai meke damunki ne? Aunty azmee ta faÉ—amun cewa kinbar kitchen kina faman kuka? Cikin kuka tace "Junaid wai dagaske ne cewa Babban yaya da Yaya Omar us zasu koma yau? Sakin baki junaid yayi yana kallonta cikin tsananin mamaki amma bai kawo ma ransa komai ba sai cewa yayi "Sehrish dama akan wannan kika shiga damuwa? to ki kwantar da hankalin ki, Yaya Omar da yaya Rafayet bana tunanin sun bar Æ™asar nan ne, Aunty azmee ce kawai tace maki hakan a hasashen ta, just calm down ur mind My lovely sis... . ...........jin abunda junaid yace yasa ta sauke ajiyar zuciya tare da miÆ™ewa zaune daga saman gadon tana cewa "ngde da jin hakan junaid, naji ma anata kiran sallar magrib bari naje nayi alwala," junaid yace "to shikenan nima bari naje nayi salla,pls reesh karki Æ™ara sa damuwa irin haka, kuma in kin kammala sallar, ki fito muyi dinner atare," Murmushi ta sakar masa tare da cewa "Ok my lovely bro, da zarar nayi sallah zan fito nima," lumshe ido junaid yayi tare da buÉ—e su akanta fuskar nan É—auke da Murmushi, sai da yaga sehrish tashiga toilet sannan yafuce hankalinsa a kwance..........................â? remain 2 pages free su Æ™are, wanda baiyi payment ba ya hanxarta Yi, Abban Sojoji 300 ne, discount da nayi na Abbban sojoji fans group ne kawai 200, Vip kuma 700, bank details É—in da za'a tura,3196407426 First bank, Bature Hafsat Muhammd Evidence of payment 08103884440 [9/13, 11:08 AM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* •·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·â€? *_LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ®_* âœï¸ ──────────────EPISODE 23-24
ﻗﺼïº? ïº£ïº ïºï»ï»£ïºŽï»§ïº´ï»´ïº” ﺑﻴï»? ﺳﺤﺮﻳïº? ï»ïºï»Ÿïº ﺮïºïº? ïºï»Ÿï»ŒïºŽï»? ïºïºï»“ﻴﺖ💋â¤ï¸?
*Mallakin Hafsat Bature Moh'd* ~BossBature~ •·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·� Fitowa tayi tana faman yarfar da ruwan alwalar dake hannunta,hijab da sallaya ta ɗauka a wardrobe, ta shimfiɗasu tare da kabbara sallah,bayan ta kammala tabar darduman anan saboda in an kira isha'e, hijab ɗin ta cire tare da ajiye shi saman gadon sai ta ɗauki Mayafinta, ta yafa shi akanta, Fitowa tayi kai tsaye ta wuce dining, a lokacin junaid ma yana a wurin tare da Haroon sai kanal Yusif duk suna zaune, yayin da Azmee ke faman ɗawainiyar Zuba masu abinci,   Ƙarasawa tayi tare da cewa "Sannu da aiki Aunty Azmee," Juyowa azmee tayi tare da kallonta tace"Yawwa mutuniyar sarkin kuka, Lamarinki naban mamaki kamar me iska,"   Sunnar da kai Sehrish tayi tana ɗan Murmushi kafin daga bisani ta gaishe da Kanal yusif da fara'arsa yace "Our Princess,duk yau ban saki a idona ba, Yakamata ace kina sakewa da ƴan uwanki sosai,"   Murmushi kawai Sehrish tayi tare da zama kusa da junaid suna facing ɗin kanal yusif da haroon ta hannun dama,   Zuba mata abinci azmee ta soma yi a plate, junaid dake a gefenta yace"Da ace baki fito ba ko, da bazanci komai ba Allah,"   Kafin sehrish tace wani abu haroon yayi saurin cewa "Saboda ciki ɗaya kuka fito ko? murmushi junaid yayi tare da cewa "Yaya Haroon yadda na ɗauƙi Sehrish ta wuce haka a wurina," ta6e baki Haroon yayi yana kallonta, Harara Sehrish taɗan wurga masa tare da murguɗa masa baki, jinjina kansa yayi tare da cewa "An fa samu freedom of sitting the same table da Ƴa'ƴan masu gida dole ayi iya shege,   Jin wannan maganar ta Haroon ta sanya junaid ɗaure fuska lokaci guda yace "Yaya haroon me kake nufi da hakan?   Haroon yace "Abunda ranka yabaka"  Dakatawa kanal yusif yayi daga cin abincin da yakeyi ya ɗan bubbuga plate ɗin dake gabansa da cokalin hannunsa ya bada sauti sannan ya aza idonsa akan na Haroon, Ganin irin kallon da kanal yusif ya jefa masa ne yasa shi, yin tsit ya shiga taitayinsa,   Mayar da idonsa yayi kan Sehrish yace"Sister Yaushe ne zaki fara zuwa school ɗin? yayi hakan ne donya mantar da ita maganar haroon, ganin yarda tayi sanyi lokaci guda,  daƙyar ta ƙaƙaro murmushi tare da cewa "Gobe ne insha Allah,"  Kanal yusif yace "Masha Allah,A matsayina na yayan ki, akwai wani jan hankali da nakeso nayi maki, kin ga gobe zaki fara zuwa, kuma zaki fara haɗuwa da sababbin ƙawaye iri-iri,akwai good friends waɗanda zasu dunga ƙarfafa maki guiwa akan karatu ta hanyar baki shawarwari masu kyau,bayan su kuma akwai bad friends gur6atattu waɗanda majority ɗinsu ba karatu ya kaisu ba,Asarar kuɗin iyayensu kawai suke yi, basa karatu ƴan abi yarima asha kiɗane,babban ma tashin hankalin yanzu majority na irin waɗannan ƙawayen ƴan Lesbian ne,fitsararru marasa kunya waɗanda suka gagari iyayensu da malamansu, burinsu kawai su 6ata tarbiyyar wasu, bana so ki kasance ɗaya daga cikin irin waɗannan ko kusa, dayawa wasu suna kuskuren yin abota da irin waɗannan bad friends ɗin, sai suce ae basu suke aikatawa ba,sun manta cewa zama da maɗaukin kanwa shi ke kawo farin kai,to koda gigin wasa bana so ko fira ta haɗaki da irin waɗan gur6atattun balle harku ƙulla Abota, Ina gargaɗin ki akan hakan ! And i want u to know that Ke yanzu kina ɗaya daga cikin Mutuncin gidan nan!! Kuma kinsan yarda sunan family ɗinmu ya karaɗe ko'ina, ba inda ba'asan Jinin SALAHUDDEEN HUSSEIN ba, don haka yazama dole ki kiyaye mutuncin family ɗinmu da kuma ƙimarsa, ina fata kina fahimtar abunda nake cewa"? Ya tambaya yana kallon sehrish wadda ta natsu tana sauraronsa cikin sauri tace "Ina fahimtar duk wani abu da kace yaya yusif, kuma insha Allah zan kiyaye faruwar hakan,kuma naji daɗi sosai harma baxan iya misaltawa ba,saboda na samu ɗan uwa nagari wanda yake mun nasiha akan na tsira da mutunci,babu wanda ya tunasar dani akan hakan sai kai, kuma insha Allah bazan ta6a baku kunya ba, zan kasance ɗaya daga cikin abun Alfaharin gidan nan,"  taƙarasa maganar yayin da idonta suka ciko da kwalla, gaba ɗaya Azmee da Junaid sun kasa kunne suna sauraron maganar tasu, dukansu babu wanda baiji daɗin maganar Kanal yusif ba, Illa mutun ɗaya Wato Haroon wanda ke ta faman tur6une fuska yana faman hura hanci aransa yana cewa "Insha Allah ni kuma bazan taba barin ki ki xama abun alfaharin gidan nan ba, balle har ki samu matsayi acikinsa, saina san yarda zanyi in tarwatsa komai har inyi sanadiyar korarki acikin gidan nan," ya faɗi yana kallon sehrish rai a6ace yana faman tura dambun nama abakinsa har yana shaƙewa,   Kanal yusif kuwa murmushi ya saki sannan yaci gaba da cewa "Allah ya yarda Sehrish,Nima inason ki zama Abun alfaharin mu gaba ɗaya," ya ƙarasa maganar tare da sanya hannu ya ɗauki glass cup dake ɗauke da Lemu mai sanyi yakai bakinsa yana kur6a,  ƙasa-ƙasa da murya junaid yayi tare da cewa "sehrish nima fa naso nayi maki nasiha akan zuwanki makaranta, amma kash sai gashi Yaya yousouf ya riga ni, amma duk da haka ban makara ba, don Allah sehrish karki canzamun koda kin fara zuwa school don nasan zaki ƙara wayewa sosai..........'  Murmushi sehrish ta saki jin abunda junaid yace, kafin tace "Insha Allah junaid hakan baxata ta6a faruwa ba,mu aminnan juna ne zamu kasance atare ako wane hali na rayuwa, kaine abokin shawara na,"  ajiyar zuciya junaid ya saki aransa yana ƙara samun kwanciyar hankali jin bayanan da sehrish tayi masa,  wayar haroon ce dake acikin aljihunsa ta soma ringing taken waƙar nan da ake cewa "ɗan duniya hayaƙin taba," jin ringing ɗin wayar yasa kanal yusif girgiza kai tare da cewa "Allah ya shirya ka,"  Haroon yace "Ameen don son Annabi," sannan yayi saurin tashi daga dining ɗin yakama hanyar fita daga falon yana zaro wayar daga aljihun wandonsa, ɗaga kiran yayi tare da karawa a kunnansa yana cewa "Shegen bisa ashe har ka isa hotel ɗin, ae ko gani nan zuwa Yanzun nan Allah yasa ka taho mana da harkar nan..........' ya yi maganar da dariya a fuskarsa kafin yasa kai ya fuce,  Bayan sun kammala dinner ɗin junaid suka wuce masallaci tare da kanal yousouf jin ana kiran isha'e,.   Itama Sehrish bayan ta kammala dinner ɗin tare da azmee suka kwashe kayan da sukayi amfani dasu izuwa kitchen, Sehrish ce ta wawwanke su tare da jerasu a ma'ajiyarsu,  Bayan ta fito suka ci karo da azmee tace " Inaso naje na kwanta,pls kada ki bari bacci ya kwashe ki, idan Twins sun dawo ki tabbatar kin kai masu dinner ɗinsu, Shima Abbansu pls ki kaimasa nasan ƙila sai wurin 12 zasu shigo,.  Sehrish tace "To aunty azmee insha Allah baxanyi bacci ba, zan kai masu in sun dawo,"   daga nan azmee ta wuce ɗakinta, itama sehrish bedroom ɗinta tashiga, sai da tafara shiga toilet ta kuskure bakinta, dama da alwalarta,   Fitowa tayi ta ɗauki hijab ɗinta da ta ajiye saman gadonta, ta kabbara sallah
_________________________________________________
Tuni General ishaq ya iso gidan ya cika tab da mutane tare da jami'an sojoji da suka rakosa, su Aunty babba sai faman rawar kai akeyi miji ya iso gari, a lokacin hafsat har ta shirya kanta itama tsaf ta kimtsa cikin haɗaɗɗen cord lace Ash colour mai adon duwatsu,rigar mai dogon hannu sai skirt ba ƙaramin kyau kayan su kayi mata ba, gashi dama takware wurin iya kashe kallabi, tare da Mommyn nata da wasu daga cikin abokanan aunty babba da suka zo dana hafsat suke taimakawa wurin tarbar baƙi da abunsha dana ci,   "Jahad ya Omar shiru kodai ya manta damu ne"? Hussana ta faɗi fuska tamkar zatayi kuka tana kallon jahad suna zaune dab da juna daga gefen gadon hafsat,   "Hussana bana tunanin hakan, Ya Omar yana son mu sosai ni ina da tabbacin yana sane damu,kuma zaizo ne insha Allah," acewar jahad Hussana tace "Ni inajin tsoron a rabamu da ya Omar, wlh banso banso....'  Kamar daga sama suka ji Muryar Aunty babba tace "Saboda ƙanin ubanki ne ko? ta faɗi ayayin da take shigowa, arazane suka miƙe tsaye su duka suna kallonta, su biyu suka shigo cikin ɗakin ita da wata hajiya, amma ita ta tsaya daga baya   Kusa dasu taje sannan tasoma magana "Ko da gigin wasa bana so wata daga cikin ta leƙo da kanta daga cikin ɗakin nan ! Saboda Mijina ya dawo kuma banaso ya gan ku, ina fata kun gane?  Cikin sauri suka haɗa baki wurin cewa "Insha Allah aunty bazamu fito ba,"   ta6e baki tayi sannan ta juya bayanta ta kalli matar da suka shigo tare tace "Hajjaju gafa yaran nan da nake faɗa baki, Omar yakawo min cikin gidana,"   ƙarasa shigo wa ciki matar tayi jikinta na sanye da shadda gezna green colour tasha uban aiki a wuyan rigar, tayi ɗaurin ɗan kwalin ture kaga tsiya sannan ta yarfa gyalenta a kafaɗarta,   Alokacin da matar ta ƙaraso Jahad taganta nan take gabanta yayi wani irin bugu zaro ido tayi tana kallonta saboda son tuna inda tasan fuskarta,  Hajjaju kuwa tana ganin su hussana da jahad farat ɗaya ta gane su, a ɗan razane ta dafe ƙirji tare da cewa "Kaiii !!!" taja maganar da ƙarfin tana kallonsu cikin mamaki da al'ajabin wannan Ikon Allahn,  tuni aunty babba tagama ruɗewa ganin yadda hajjaju ta razana da ganinsu, da kuma yarda jahad ta firgita itama wannan alama ce dake nuni da sun san juna kenan ko yaya,  Cike da mamaki Aunty babba tace "Wai meke faruwa ne hajiya rabi? kinsan su ne?  Cikin sauri hajjaju tace "A'a bansan su ba, Kamar dae nata6a ganin mai kama dasu ne,"   tayi maganar tare da ruƙe hannun Aunty babba taja ta, suka fuce daga ɗakin,   Kallon jahad hussana tayi tare da cewa "Jahad wacece wannan matar? Naga kin razana da ganinta,"   "Nima so nake na tuna inda nasanta," Jahad ta faɗi tana faman cizon akaifar hannunta da takai abakinta,  Hajjaju kuwa da taja Aunty babba suka fuce can suka nufa wurin kitchen suka tsaya, ga mutane sai faman shige da fuce suke,.  "Dan Allah ki faɗamun gaskiya hajjaju raina na bani cewa kinsan yaran can ko? Aunty babba ta tambaya tana kallonta cike da son jin ƙarin bayani daga wurinta,  Jinjina kai Hajjaju tayi tare da cewa "Yau naga ikon Allah, Lallai ne duk zakaran da Allah ya nufa da cara,to fa sai yayi ta, haƙiƙa nayi matuƙar mamakin yarda akai har Allah ya haɗa Omar da waɗannan yaran , kai kaga wani ikon Allah nan ! mai matuƙar ban mamaki da Al'ajabi?  Hajjaju tayi maganar cikin nuna mamakinta, Aunty babba kuwa cewa take yi "Hajjaju kin barni acikin duhu, wlh har kinsa hantar cikina ta kaɗa dan Allah kisanar dani me kika sani agame dasu?  dariya hajjaJu tayi tare da tafa hannayenta tace "Ana bura'uba a lagos! yo ke laila da kike cewa zaki sa a zubar maki da waɗannan yaran don ki nisanta su da Omar, idan Kin toshe wannan hanyar to ita waccen ɗayar hanyar da ta ruga isa inda bakya so ya zakiyi da ita?   gaba ɗaya fa Aunty babba ta gama rikicewa da bayanin hajjaju, cikin tashin hankali tace "wai me kike nufi ne hajjau, kiyimun bayani mana yadda zan fahimta !!!   ta faɗi tare da ɗan jan guntun tsoki, Murmushi hajjaju tasaki sannan tace "Ni baza kiji mutuwar sarki abakina ba!kawai abunda nakeso ki sani shine babu wanda ya isa ya hana ruwa gudu sai Allah! Bakin alƙalami dai ya ruga daya bushe, Amma fa waɗannan yaran da kike gani wlh ikon Allah ne su, tunda har Allah ya haɗasu da Omar aikuwa magana ta ƙare, Yakamata kisan abunyi,'  Hajjaju tayi maganar tare da wuce wa ciki tabar Aunty babba tsaye abakin kitchen baki asake, lokaci guda taji ta ƙara tsanarsu hussana da jahad tabbas suna tattare da wani abu yaran, duk da bata fahimci inda maganar hajjaju ta dosa ba,  ranta ya gama 6aci tsoki ta buga tare da cewa "ta tsaya tayimun bayani amma ta tsaya yimun wasu sambatun banza dana wofi,ni duk tasa hankalina ya ƙara tashi, kuma wlh goben nan zansa a Kwashe mun su aje can azubar dasu tsakar daji, sai dae abunda bangane ba acikin maganar hajjaju wacece ɗayar hanyar da take nufi wadda ta isa inda banaso!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!? ta tambayi kanta sai dae kash babu amsa hakanan ta koma ciki tana faman sambatu aranta,    Zumbur !! Jahad tayi tare da kallon husana tace "Wlh nasanta!! Nagane ta !! Itace matar da ta taimaka mana a asibiti har ta biya kuɗin gadon Ki husana, wlh itace matar da tasama ma SEHRISH aiki, hakan na nufin ta son inda sehrish take.....!!  Cikin tsananin farin ciki jahad tayi maganar, hussana ma aɗan raxane tace "dagaske jahad itace tasama ma sehrish aiki? Ke nan itace kawai zata iya faɗa mana inda ƴar uwarmu take kenan,.   jahad tace "eh itace, nagane ta yanzu ya za'ayi muyi magana da ita, gashi aunty ta hanamu fita, amma ni dae inason magana da ita kodan saboda ta faɗa mana inda sehrish take,' jahad tayi maganar fuskarta tamkar zatayi kuka,   Cikin sanyin murya hussana tace "Jahad kada ma musa rai don nasan bazata faɗa mana ba, ita fa ƙawar Aunty ce, kuma kinsan muguwace idan halinsu ɗaya fa? Bazata ta6a faɗa mana ba, Ni tsorona ma kada ta faɗa ma wannan muguwar auntyn inda sehrish take, suna iya zuwa su cutar da ita, Allah yasa sehrish tana lafiya banaso wani abu yasame ta.........'" tayi maganar cikin shessheƙar kuka,   "Da gaskiyar hosana,Nima ina tunanin hakan Allah yasa karta faɗama auntyncan inda ƴar uwarmu take, amma dai ni inason naga matar na roƙeta akan ta faɗa mana inda sehrish take,yakamata musan inda take, wane hali take ciki, gashi yanzu sai mutuwa akeyi Ya Allah kasa sehrish tana araye har mu haɗu," tayi maganar idonta cike tab da hawaye,  daga bisani ta kalli hosana tace "ki zauna hosana kada ki fito bari ni naje nayi magana da matar na roƙe ta, ta faɗamun inda rishi take,"  Hosana tace "toh," sannan tasamu wuri ta zauna gefen gadon tana faman sauke ajiyar zuciya,   Cikin sanɗa jahad ta futo daga kopar ɗakin ta tsaya tana ɗan leƙa kanta, mutane tagani gasu nan sai faman zarya sukeyi acikin babban falon,   A hankali ta miƙi hanya ta soma tafiya tana faman waige-waigen neman hajjaju, ta ɗanyi nisa a tafiyar ta ta, tajiyo magana daga bayanta ana cewa "Nasan cewa ni kike nema ko"? Cikin sauri jahad ta juyo bayanta, hajjaju ce tsaye tana kallonta fuska ɗauke da murmushi, Ajiyar zuciya jahad ta saki sannan itama ta mayar mata martanin murmushin tare da gaishe ta, hajjaju ta amsa mata da cewa "Nayi mamakin ganin ku, anan gidan ko ba'a faɗamun ba nasan cewa kunsha wahalar rayuwa don nasan Laila sarai muguwace bata da Imani,kuma tana sanar dani game daku a waya sai dai bansan cewa ku bane," Jinjina kai Jahad tayi tare da cewa "Munsha Wahala sosai tamkar ba zamu rayuwa ba,dan Allah ki faɗa mana ina Sehrish take? Munyi kewarta sosai, rabon mu da ita, tun da ta tafi aikin nan da kika sama mata,bayan wasu kwanaki hosana ta 6atar mana da wayar da muke amfani da ita wurin kiranta, shikenan rabuwarmu da ita......' jahad ta ƙarasa maganar idonta cike tab da kwalla,   ɗan shuru hajjaju tayi tana kallonta gwanin ban tausayi kafin tace "Kiyi haƙuri, amma bazan iya shaida a ina sehrish take ba nikaina,saboda nasaba hulɗa da yara ina sama musu aiki, bazan iya tuna a wane gari nakai sehrish ba, bazan iya tunawa ba......'  Jin hakan yasa Jahad fashe wa da kuka mai cin rai, matsawa hajjaju ta ƙara yi gab da jahad tasanya hannunta tare da dafa kafaɗunta tace"kiyi haƙuri Jahad, ina mai matuƙar jin takaicin gaza taimaka maku akan halin da kuke ciki, haƙika kun ga rayuwa, amma ni abunda nakeson sani taya akai kuka haɗu da Omar? bayan naji labarin rasuwar tsohuwa ya gigita ni matuƙa, sannan naji labarin cewa ana zargin cewa kune kuka bata poison amma bansan ya ƙarshen labarin yake ba,'.  Cikin shessheƙar kuka jahad tace "bayan tsohuwa ta rasu, mutane suka ce mune muka kashe ta alhalin mu bamu da masaniya akan mutuwarta, shine aka kaimu police station, munsha Wahala sosai saboda bamu da sheda, ana shirye shiryen za'a miƙa case ɗinmu kotu, hussana tayi rashin lafiya shine dalilin dayasa ƴan sanda suka tafi da ita asibiti tare dani, Acan ne Allah ya haɗamu da yaya Omar shine ya kwace mu daga hannun police ɗin kuma ya kashe case ɗin gaba ɗaya......' ta ƙarasa maganar tana faman sauke ajiyar zuciya,  Murmushi hajjaju tasa ki tare da cewa "Allah sarki Omar mutumin kirki ne sosai, yana da tausayi inama ace tunfarko ba nan ya kawo ku ba, wlh da kun more rayuwarku,amma sai dai kash yayi kuskuren jefa rayuwarku cikin haɗari batare da sanin shi ba, Amma insha Allah Laila bazata ta6a cin nasara akanku ba,'  Jinjina kai kawai Jahad ke yi, bayan sun ɗanyi shiru hajjaju tace "Muje ɗakin da kuke,ina son ganin ƴar uwarki danaji kin kirata da hussana, bazan manta ba itace a lokacin kwance saman medical bed ansa mata oxygen tana shaƙar numfashi cikin mawuyacin hali, Amma yanzu naganta taji sauƙi sosai jiki yayi kyau,' hajjaju ta faɗi da ɗan murmushi a fuskarta yayin da suke nufar ɗakin hafsat atare,   Suna shiga suka samu hussana atsaye sai faman zirga-zirga take yi burinta kawai jahad tadawo kusa da ita,   Tsayawa tayi ganin sun shigo tare da matar, Murmushi hajjaju ta sakar ma hussana tare da ƙarasawa inda take ta rungumo ajikinta, tana ɗan bubbuga bayanta tace "nasan ke baki sanni ba,sabosa lokacin kina kwance rai hannun Allah, amma ni nasan ki saboda naganki a lokacin, naji daɗi sosai dana ganki cikin ƙoshin lafiya,   Hajjaju ta ƙarasa maganar tare da janye hussana daga jikinta, ita dai hosana kallonta kawai take yi don batasan ta ba, mayar da idonta tayi kan jahad tace "ta faɗa maki inda sehrish take?  Jahad tace "a'a hosana, tace itama ta manta inda takaita aiki saboda ta saba kai yara aiki bazata iya tuna inda takai su ba,"   Jin haka yasa Hosana fashewa da kuka tana cewa "..yanzu shikenan bazamu ƙara ganin sehrish ba....  Hajjaju tace "Ki daina kuka hosana,wayace maki bazaku sake ganin sehrish ba? Ki daina wannan tunanin Insha Allah zaku haɗu da ƴar uwarku, abunda nakeso daku kawai ku cigaba da addu'a insha Allah zaku dace,"  Jahad tace "kullum muna cikin yin addu'a,Kuma zamu cigaba da yi har illa masha Allah"    Murmushi hajjaju ta kuma yi sannan tace "Ni zan wuce,Ku kula da kan ku,Allah ya Albarkanci rayuwarku, yaci gaba da tsare ku aduk inda zaku kasance arayuwar nan,"  Suka amsa mata da "Amin," sannan tasa kai ta fuce tana mai jin rashin daɗin gaza taimaka masu da tayi na ƙin faɗa masu inda ƴar uwarsu take, bayan ta son inda take,  Komawa sukayi atare suka zauna jikinsu amace, Shin mai zai biyo baya?😥
Bayan wasu lokutta, duka baƙin da suka zo suka tafi gidan yayi tsit ba hayani, suna cikin wannan zaman na jimamin Ga samu ga rashi, na hajjaju da suka haɗu da ita yau, sun son itace kaɗai zata faɗa masu inda Sehrish take gashi itama tace bata sani ba, hakan ba ƙaramin kashe musu zuciya yayi ba, daker suka samu bacci ya ɗauke su, _______________________
Fitowa daga wanka general ishaq yayi jikinsa sanye da gajeran wando, Closet ɗinsa ya nufa tare da sa hannu ya buɗe ya ɗauko jallabiya ya zumbula ajikin shi, Sarai yasan cewa tana ɗakin Amma sai yayi tamkar bai ganta ba, sai da ya kammala kimtsa kansa sannan yace "Ya Rashin Ji"? Ya tambaya yana kallon kansa acikin Mirror, mamaki ne ya kama aunty babba jin abunda yace, tana zaune daga gefen gadonsa tace "Nifa ce ba hafsat ba," ta faɗi tana kallonsa Ishaq yace"Nasani ae, dake nake magana, duk rashin jin hafsat ae bata kai ki ba, kefa tamkar 6eran gida kike wurin 6arna da rashin ji," ɗaure fuska tayi jin abunda yace rai a6ace tace "Alamu sun nuna cewa ba kayi kewata ba ko? shiyasa kake gayamin magana, ko da yake dama kai ae ba ka iya soyayya ba, Iya ruƙe bindiga kaɗae ka sani," ......juyowa Ishaq yayi yaɗan kalle ta tare da ta6e bakinsa yace "ban iya soyayya ba, amma gashi nan har kin haifi hafsat dani ko? Naga wannan ma ae wani sashe ne na soyayya," ya ƙarasa maganar tare da wuto wa ya haye saman gadonsa ya kwanta yana cewa "Idan kin tashi fita daga ɗakin kada ki manta, ki kashe mun hasken inaso nayi bacci," a ƙule aunty babba ke kallon shi, can kuma ta miƙe fuuuuu ta nufi hanyar fita har takai bakin ƙopar ɗakin ta kuma tsaya tare da juyowa tana kallonsa, abun mamaki sai ta same shi yana ta faman tiƙar dariya, Bakomai yasa ta tsayawa ba face tsananin son kasancewa dashi da take yi, dakatawa da dariyar yayi sannan yace "nifa ba korarki nayi ba, zaki iya dawowa kiyi zaman ki," murguɗa masa baki tayi aranta tace "shashasha dama nasani ae dole ka buƙace ni," shi kuma aransa yace "Mayya, Jibi yarda take ta hau hawa kamar buhun harawa, duk an cinye mun abincin gidana," 😂 Kamar taji mi yace ta ɗan kallesa tare da jinjina kanta tace "bari na kawo maka Tea," "Ok i wll be waiting for u," ya faɗi yana faman yin dariya ƙasa-ƙasa, general ishaq kenan tamkar Abbansu haka yake indai wurin iya zolaya ne,
****************************** A 6angaren sehrish kuwa, sam taƙi bari bacci ya ɗauke ta sai faman gyangyaɗi take yi tana zaune asaman kujerar dake gaban mirror burinta kawai su twins su dawo ko tasamu ta kai masu abincinsu, sune kawai suka rage mata takai mawa, domin kuwa ta jima da kaima Abbansu nashi tunda ya dawo,
Basu tashi dawo wa cikin gidan ba sai wuraren ƙarfe Sha biyu da rabi suka shigo suka shigo cikin falon kai tsaye ɗakinsu suka wuce, shaf shaf suka shiga rage kayan jikinsu, sai da ya rage daga su sai shorts ajikinsu, sannan suka shige toilet donyin wanka, sun jima aciki kafin daga bisa ni suka fito kowannansu ɗaure da towel a waist ɗinsa, closet ɗinsu suka buɗe jerin kayansu ne ajere komai iri ɗaya, kamar yadda suke tagwaye haka komai nasu yake iri ɗaya, kimtsawa su kayi cikin sleeping dress riga da wando milk colour,
faɗawa su kayi saman gadon Su tare da rungume junansu suka ci gaba da abunda suka saba, kamar injina haka suke sam basa gajiya,abun ya zamar masu jangwangwam, Kwankwasa ƙopar bedroom ɗinsu akayi, kusan sau uku basu ji ba, sai ana huɗun Jahan yace "Wai Uban wanene yake buga ma mutane ƙopa? Atunaninsa Sehrish ce tazo kawo masu dinner ɗinsu, Amma sai yaji akasin hakan Muryar haroon yaji yace "Ubanka ne shege, zoka buɗe mun ƙopa in shigo," Uban tsoki Jahan yasaki tare da ƙara ƙanƙame Ayaan ajikinsa yana cewa "wlh bazan buɗe masa ƙopar ba, bansan uban me yakawo shi bedroom ɗinmu ba," Ayaan yace "Amma sweet heart baka tunanin wani abu mai mahimmanci ya kawo shi"? ya faɗi yana faman lumshe idonsa akan Jahan, guntun tsoki jahan yaja tare da cewa "Wlh bazan buɗe masa ba, yazo yayi disturbing ɗinmu ne kawai," duk abunda suke cewa a kunnan haroon dake tsaye abakin ƙopar ɗakin nasu, Jinjina kansa yayi yace "Yara kenan dani kuke magana," hannunsa ya tura cikin aljihunsa tare da zaro wayarsa yaci gaba da daddanata na wani lokaci, daga bisani ya mayar da wayar cikin aljihunsa sannan ya ɗaga murya tare da cewa "tunda bazaku buɗe mun ƙopar ba, ku duba wayoyin ku acikin whatsapp ɗinku na turo maku wani saƙo mai mahimmanci," Jin hakan yasa su dakatawa gaba ɗayansu cikin sauri jahan ya zura hannunsa asaman side drawer ya ɗauko wayarsa da hanzari ya miƙe zaune, whatsapp ɗinsa yashiga mamaki ne yakamasa ganin Numbar da yayi saving da yaya Haroon ya turo masa Video, cikin sauri yashiga chat ɗin tare da danna video ɗin ya buɗe...........lokaci guda jahan yayi wata irin Zabura sai gashi tsaye saman gadon hannunsa na kerma gaba ɗayama jikinsa, nan take kuma wata irin Zufa ta shiga wanko masa duk da sanyin A.c in dake ɗakin, Zazzaro idonsa yayi hankali a matuƙar tashe yace "AYAAN MUN SHIGA UKU!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!! jin hakan yasa Ayaan tasowa shima ya miƙe tsaye yana cewa "jahan menene ya faru na ga duk ka razana," Miƙa masa wayar yayi batare da yace komai ba, amsa Ayaan yayi yana duba video ɗin, porn video ɗinsu ne shida Jahad, gasunan kwance saman gado a ɗakin hotel ɗin da suka kama, tsantsar mamaki ne a fuskar Ayaaan a ruɗe yace"Jahan taya yaya haroon ya samu wannan video ɗin? "Nima shine abunda ban sani ba," Jahan ya faɗi cikin tashin hankali, Muryar haroon ce ta dakatar dasu da cewa "Oya, azo abuɗe mun ƙopar," A hanzare suka diro daga saman gadon tare da nufar ƙopar suka buɗe masa, shigowa yayi yana faman sakin shu'umin murmushi yace"Ƴan duniya, fararen Balbelu tun yaushe kuka fara wannan harkar bansani, ahhh gaskiya wannan anyi mun nisa har suna haɗa baki wurin cewa "yaya Haroon ba yin kan mu bane, dan Allah ka rufa mana asiri," atsiyace yabi su da wani irin kallo kafin yace "taya kuke tunanin zan iya rufa muku asiri hakanan siddin ragadan ku ci banza!!? nifa dama nasani duk kaf zuri'armu babu fasiƙai irin ƴa'ƴan mommynku, masu jaza mana bala'e acikin zuri'armu,' yayi maganar fuska aɗaure yana kallonsu Jin wannan magana ta haroon ya sanya su jin wani irin ɗaci aransu, Ci gaba da magana haroon yayi "kai nifa tunda Mommynku ta nuna ta tsane ni bataso na, Nima naji cewa bana ƙaunarku! bama wannan ba adalilin ku yasa abba yadaina so na kwata-kwata nazama abun ƙyara acikin gidan nan, don hak wannan babbar dama ce agare ni, Idan har na ɗaura wannan videon a Social media, Abban mu ya gani to tabbas nan take zuciyarsa zata buga ya mutu! idan kuma babban yayan ku ya gani hohohoho ku kunsan mai zai faru, Idan Ammi tagani shikenan zata rabaku da mahaifinku ne na har Abada dama ba sonku take ba, tabbas wannan babbar dama ce agare ni !!! Ya faɗi da dariya a fuskarshi tuni Ayaan da Jahan sun zube agabansa saman guiwowinsu idonsu cike tab da hawaye, tabbas sunyi mamakin Kalaman haroon yadda ya nuna irin tsanar da yayi masu tamkar ba jininsu ba, cikin tsananin ƙunci suke cewa "Yaya Haroon pls ka rufa mana asiri dan Allah, kada kace za kayi amfani da wannan damar wurin tarwatsa farin cikin gidan nan, kaifa ɗan uwan mu na jinin mu dan Allah yaya haroon ka dubi girman Allah kada kayi mana haka," Fashewa da dariya haroon yayi yana binsu da wani irin kallo na ƙasƙanci yace "Au haba? Ashe nifa jinin ku ne? Amma taya akai bamu kama? Ikon Allah sai yau kukasan da hakan? kaiiiii ! Ni saima yanzu na lura wai yau ƴa'ƴan Alexandra ne durkushe saman guiwowinsu agabana suna neman afwa hada matsar kwalla kodai mafarki nake yi ne? Yayi maganar tare da sa hannunsa yana murza idanunsa wai donya tabbatar ba mafarki yake yi ba, shiru su kayi gaba ɗaya jikinsu ya mutu sai uwar zufa dake wanko masu, ga jikinsu dake ta faman kerma yayin da idanunsu suka ciko tab da kwalla, gwanin ban tausayi Murya na Rawa Ayaan yace "Ka faɗi komai kake so za muyi maka donka rufa mana asiri," Haroon yace"yanzu naji magana, Anzo dai-dai wurin dana fi so," ya faɗi tare da ƙara gyara tsayuwarsa yace "Abu biyu nake buƙata muddin kukayi mun hakan to shikenan zamu raba jaha daku,". Cikin sauri suka amsa masa da cewa "muna sauraronka," wani irin bazawarin murmushi ya saki kafin yace "Nima fa kwararrene a irin wannan harkar taku! gashi kuma dama na jima ina sha'awarku musamman junaid, Kai yaron akwai sirrin kyau atattare dashi kuma daga gani zaiyi ni'ima sosai........' a firgice jahan ya daka masa tsawa tare da cewa "Ya isa haka!! Komai za kayi ka tsaya a iya kan mu kawai, amma koda gigin wasa kada ka ƙara kiran Sunan junaid da waɗannan munanan kalaman naka! saboda ba zaka ta6a samun abunda kake so agame dashi...........' cikin sauri Ayaan ya rufe ma jahan baki muryarsa cikin kuka yace "Jahan dan Allah kayi shiru, kada ka ƙara ja mana wani bala'en, ka bari muji da wanda muke ciki," shiru jahan yayi yana faman sakin Huci ji yake tamkar ya tashi ya shaƙe wuyan Haroon, Hannu haroon yasa abaki irin mamakin nan yace "Wow wai meyasa kowa yake ma junaid irin wannan zazzafar soyayyar har haka? Gaskiya anyi mun nisa kaina na cikin duhu, farin jinin junaid yayi yawa ina kishi da hakan," ya faɗi yana dafe saitin zuciyarshi . Ayaan yace "Ba son junaid muke ba, Ƙaunarsa muke yi saboda shi ɗin jinin mu ne," ta6e baki haroon yayi tare da ɗan jinjina kai yace "hmmmm ni wannan ba damuwata bace ba, abu biyu nake buƙata daga gare ku, inaso ku gamsar dani acikin daren nan, saboda inji irin naku salon, Sannan abu na biyu kuɗi nake so kimanin naira miliyan 50, in kun mun hakan zaku zauna lafiya, Wani irin kallo suke bin shi dashi, Jahan yace "50m fa kace? Ina zamu same su? ka ruga da kasan iya salary ɗin mu, kuma ba tarawa muke yi ba, kashewa muke yi," haroon yace "Wannan ba damuwa ta bace, in kun so there's many way da zaku samu waɗannan kuɗin ! Yayan ku fa billionare ne! Mahaifiyarku ma billionaire ce, yadda take son ku ɗin nan, da zarar kun mata waya kunce kuna son Ƴan silalla zata turo maku," Murya a sanyaye Ayaan yace "mun ji zamu samu kuɗin mu baka amma dan Allah kada kace zaka aikata wannan abun damu, wlh bazamu iya ba, iya mu biyu ne kawai ba kowa muke bi ba, ka faɗi mashi jahan kada ya cutar da rayuwarmu bazamu iya jurewa ba........................" bugun ƙopar da akayi ne ya hana Ayaan ƙarasa maganarsa, Cikin sauri Haroon yayi tsalle yashige bayan labule ya 6oye, tashi su kayi atare suna faman sa hannu suna goge hawayen dake fuskarsu, sannan jahan yayi ƙoƙarin cewa "Wanene? Sehrish dake tsaye ruƙe da tray a hannunta tace "Ni ce sehrish," Ayaan yace "Shigo ciki," Tura ƙopar tayi da tray ɗin hannunta mai ɗauke da food wermers tare da kayan tea ta shiga ciki, tsayawa tayi tana kallonsu cikin mamaki ganin yadda fuskokinsu sukayi Jawur, idanunsu sun Canza launi alamar sunsha kuka, Muryarta na rawa tace "Dama.............' bata ƙarasa ba Jahan ya katse ta da cewa "Ki barshi kawai, bazamu iya cin komai ba, ki koma da kayan," Shiru tayi aranta tana mai mamakin jin yadda Jahan ke mata magana cikin sanyin Murya, shi da kullum atsiwace yake mata magana, Jinjina kai tayi tare da yin juyi zata futa karaf idonta suka sauka kan ƙafafun haroon dake 6oye bayan labule, tana ganinsu tagane cewa ƙafafunsa ne kamar na shebur haka suke, tsananin tsoro da mamaki ne suka kamata daker ta iya fuce wa daga ɗakin, Kai har ta futa tana waiwayen ɗakin nasu, cikin mamaki take cewa "Meke faruwa ne? Naga fuskar Ayaan da jahan jawur alaman sunsha kuka, kuma menene yakai ƙafafun haroon ɗakin, hakan na nufin shine 6oye bayan labule? ko uban me yakaisa ɗakin hada su 6oyewa abayan labule, gaskiya akwai wani mummunan abu dake faruwa, Nashiga ukuna Allah yasa dae Haroon kada ya cutar dasu don nasan halinsa ba ƙaramin shaiɗani bane...........' ta ƙarasa zancan Zucin nata ayayin da take saukowa down daga saman stairs ɗin, Kitchen ta shiga ta ajiye tray ɗin, sannan ta wuce bedroom ɗinta cike da zullumin abunda tagani,
A daren ranar haroon sai da ya tabbatar ya wulaƙantar da rayuwar Ayaan da jahan domin kuwa har sai da Ayaan Ya sume sannan ya ƙyalesu ya fuce yana ƙara jaddada masu maganar kuɗinsa, bayan ya fita jahan ya fashe da wani irin matsanancin kuka na tashin hankali yana jijjiga jikin Ayaan dake sume aƙasa 😠[9/15, 9:20 AM] 💋BOSS LADY💋: *💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋* ~🔥The father Of Soldiers🔥~ *Episode 25-26* *Story & Written by*💫 *Hafsat Bature Moh'd* *BOSS LADY*
cikin sauri Jahan ya miƙe fitowa daga ɗakin yayi ya sauko down kai tsaye freezer ɗin dake a babban falon nasu ya tunkara, buɗewa yayi tare da zura hannu ya ɗauki robar ruwa mai sanyi, sannan ya juya ya koma ɗakin nasu, bayan ya buɗe robar ruwan ya ɗebo ya yayyafa masa a fuskarsa, wata irin doguwar ajiyar zuciya Ayaan ya saki tare da buɗe idonsa da sukayi jawur dasu yana kallon jahan dake zuƙunne agabansa, ganin Ayaan ya farka yasa jahan faman sauke ajiyar zuciya, yayin da hawaye ke sintiri a fuskarsa yana kallon ɗan uwan nasa, Buɗe baki Ayaan yayi zaiyi magana, nan take wani irin yunƙurin amai yazo masa, a hanzarce ya zabura ya miƙe duk jikinsa ba ƙwari da gudun gaske ya faɗa toilet agaban basin ya tsaya yana faman kwarara aman, biyo sa jahan yayi cikin toilet ɗin tsayawa yayi kusa dashi ya sanya hannunsa yana ɗan bubbuga bayan Ayaan cikin muryar kuka yake cewa "Ayaan kayi haƙuri ina mai takaicin wannan ranar, naji natsani kaina Ayaan saboda nagaza ceton ka a hannun wancan fasiƙin, tabbas Haroon bai da Imani ko misƙala Zarratin kashe mu kawai yake son yi, ni ina kokwantan cewa Anya haroon JININ MU NE !!!!!!!!!! dakyar Ayaan yasamu ya dakata da Aman hannunsa yasanya yana tarbo ruwan dake kwararowa daga jikin fanfon yana kuskure bakinsa, bayan ya kammala ya kashe Tap ɗin, Sannan ya ɗago da shanyayyun idanuwansa ya kalli jahan yace "Haroon bai da Imani, Ƙazamin banza mugu macuci kuma Azzalumi wlh Allah bazai ta6a ƙyalesa ba sai ya bi mana haƙƙin mu, Jahan ni sam bana jin kunyar videon tsiraicin mu ya fita, babban abunda nake jimawa shine Mutuncin mahaifin mu da kuma na Babban yayanmu, jahan dole mu nemi mafita akan wannan Baƙin Shaiɗanin...........' ya ƙarasa maganar yana faman sakin Numfashi mai zafi, don tuni zazza6i yakama jikinsa, Jahan yace "yanzu dare yayi Ayaan,Gobe sai musan Abunyi amma gaskiya bazan ƙara bari haroon ya ƙara kusantar ɗaya daga cikin mu ba, ko nawa yakeso muyi ƙoƙari mu biyasa shine kawai !!! Sun jima suna jimamin abunda yafaru dasu kafin daga bisani suka sake sabon wanka don tsarkake jikinsu, bayan sun fito suka zura jallabiya ajikinsu, sai da Jahan ya canza musu bedsheet sannan suka kwanta, sun juma idonsu a buɗe kafin daga bisani bacci ya ɗauke su 😥 (Arayuwa kowa da irin tashi jarabtar, babu wanda Allah baya jarabta, kuma bawai don baya son mu bane a'a face don ya jaraba imanin mu) **************Morning*********************** tun da sassafe sehrish ta farka daga baccin da ta koma na asuba, fuskar nan awashe yau zata fara shiga school, jiki na rawa ta faɗa toilet shaf-shaf tayi wanka ta fito jikinta ɗaure da farin towel, Uniform ɗinta ta curo daga cikin wardrobe duka ukun, ta jera su saman gadonta tana tunanin wanne zata sanya, duk kala ɗaya ne amma na farkon riga ce da mini skirt ɗan dai-dai guiwa shafa su tayi tare da girgiza kai tace "Ba wannan zansa, basu son cewa ni musulma bace, taya zansa wannan gajeran skirt ɗin cinyoyi awaje kamar ƴar christiana," tayi maganar tana yatsina fuska, buɗe na biyun tayi riga ce tare da skirt pencil ba ƙaramin ɗame jikin mutun zaiyi ba, "Kamar dae wadda zata club," ta faɗi tana ƴar dariya, na ƙarshen ta buɗe riga ce tare da dogon wando, duka uniform ɗin suna da Top wadda ake sanyawa daga sama bayan an zura rigar sai kuma guntun hijab wanda daƙyar ya dire kafaɗa, "Kwarama wannan zasu fi dacewa dani," ta faɗi tare da hanzarin komawa gaban mirror sai da ta kammala shafe jikinta da body oil tabi ta feshe shi da turare ko'ina yakama ƙamshi sannan ta koma gaban gadon tana zura uniform ɗinta, lokacin da ta kammala zura kayan duka ta kalli kanta a mirror sai da taji gabanta ya faɗi saboda yadda kayan suka hau jikinta su kayi mata wani irin kyau, Rigar white colour ce wandon kuma Maroon colour launi ɗaya da Top ɗinta, jujjuyawa tayi agaban mirror ɗin sannan ta sakarwa kanta murmushi, sai da tagama shiriritar sannan ta ɗauko takalmanta, tsayawa tayi tana ƙoƙarin zura safa a ƙafarta, ta aza ƙafar asaman kujerar gaban mirror tana gyaggyara safar, Azmee ta shigo ɗakin da sallama tana yin arba da sehrish ta soma washe baki tana cewa La!la! Irin wannan kyan haka, Masha Allah gaskiya uniform ɗin nan ba ƙaramin kyau su kayi maki ba Sehrish sai kace donke akayi su," Murmushi kawai Sehrish ke saki tana ɗan kallonta a lokacin ta kammala sa safar da takalmin a ƙafar daman ta, saura ta hagun zata sanya mawa, "aunty azmee ina kwana fatan kun tashi lafiya," ta faɗi tana aza ɗayar ƙafar saman kujerar , Azmee tace "Lafiya lou Alhamdulillah, naga sai faman shiri kike yi, maganar breakfast ba? "Aunty azmee lokaci zai ƙure ne, idan nadawo zanci," ta faɗi tana zura safa a ƙafar hagunta, Azmee tace "Kin ta6a ganin inda akaje ɗaukar karatu da yunwa? gaskiya bazaiyiyu ba, akwai sauran miyar jiya na ɗumamata saina haɗa maki da dankalin dana soya kici, bari na kawo maki" ta fadi tare da juyawa ta fuce cikin sauri bayan wasu mintina sai gata ta dawo hannunta ɗauke da plate, soyayyan dankalin ne aciki tare da jar miya, ajiye mata tayi asaman side drawer ɗinta, sannan ta koma ta ɗauko mata kayan tea don ta haɗa tasha, "Nagade sosai Aunty azmee da kulawarki," sehrish ta faɗi a lokacin ta baro gaban mirror ɗin, wuri ta samu gefen gadon ta zauna tana cin breakfast ɗinta, yayin da azmee ta fuce tana cewa "ki hanzarta ki shirya kafin Junaid ya fito," ta amsa mata da "Toh," A can ciki kuwa tuni junaid ya farka saboda ya tashi da wuri ya sanya alerm a wayarsa, shaf shaf yayi wanka ya fito ya kimtsa cikin pakistani riga da wando farare amma anyi masu ado da stone launi daban daban ajikinsu, ba ƙaramin kyau yayi ba, bin jikinsa yayi ya feshe shi da Spice bomb, sannan ya gyara sumar kanshi, gaban mirror ya tsaya yana kallon kansa yace "Nima kaina nasan cewa Ni kyakkyawa ne, Son kowa ƙin wadda ta rasa, Allah kaɗai yasan ƴan matan da suke crushing akaina," ya faɗi yana tsumbula yatsansa na tsakiya a dimple ɗin fuskarsa daya Lotsa, daga bisani ya ɗauki key ɗin motar shi tare da wayarsa ya fito daga ɗakin, cikin hanzari ya sauko down babu kowa saboda duk basu tashi daga bacci ba, wuri ya samu asaman Royal sofa ɗin dake a falon mai mazaunin mutun 3 ya zauna yana jiran fitowar sehrish, wayarsa ya shiga daddanawa, message ya tura mata cikin wayarta, na cewa yana jiranta ta fito, a lokacin ta kammala kur6ar tea ɗin data haɗa, message ɗin junaid ya shigo mata karantawa tayi "Am waiting for u reesh,' murmushi ta saki cikin sauri ta miƙe tare da ɗaukar guntun hijabin ta zura ajikinta, sannan ta ɗauki School bag ɗinta ta ɗan sagala hannun jakar a kafaɗarta, sai da ta ɗauki wayarta sannan ta fito daga ɗakin, kai tsaye ta nufi falon tunkan ta ƙarasa junaid ke kallonta baki asake, Ganin hakan yasa ta sakin dariya, ƙarasa wa tayi wurinsa tare da tsaya agabansa ta ruƙe waist ɗinta tace "Nayi kyau,"? Cikin mamaki yace "Reesh irin wannan kyau haka? Anya karfa malaman makarantar su rikice? innalallahi," ya faɗi tare da aza hannunsa akansa, ɗan bubbuga ƙafarta tayi tare da cewa "ka tashi mu tafi junaid har 8:30 fa tayi," Mamaki tayi ganin yarda yake kallonta hannunsa yakai tare da cafko wutsiyar gashinta da ta sauko har tsakiyar bayanta yace "Sehrish jibi fa? Babu wani dogon hijabin ne sai wannan? Taya zaki bar gashin nan haka bainan nasi? Kowa ya kalla? Sai lokacin ma ta ankara sam ta manta bata sanya ribom ba ta ɗaure gashin, dafe kanta tayi tare da cewa "kash ! Wlh mantawa nayi ban ɗaure gashin ba, kuma fa in na sanya ribbom gyaran gashin da akayimun zai 6ace," tashi junaid yayi tare da ruƙo hannunta yace "Mu shiga cikin ɗakin na ɗaure maki shi, nasan yarda zanyi batare dana 6ata maki gyaran gashin ba," bin shi tayi suka wuce ɗakin nata, duk wannan abun dake faruwa akan Idon haroon sam basu ankara dashi ba, tun fitowar sehrish yake tsaye ruƙe da qugu daga shi sai gajeran wando fuskar nan a murtuke kamar ta shanu, jinjina kansa yayi tare da cewa "Wato ni waccen ƴar shilan zata raina ma wayau, in na ta6a jikinta taita ƙyamata amma gashi junaid har wani ruƙe hannunta yake yi, hada su shiga ɗaki ko uban mi zasu yi aciki,"? Ya tambayi kansa can kuma ya saki wani irin shu'umin murmushi yace "Wannan babbar dama ce agare ni ! Zanyi amfani da ita wurin gur6ata sunanta acikin gidan nan, Zan ƙala mata sharrin cewa ta koyama junaid lalata, kuma na kama su hannu dumu-dumu, " fashe wa yayi da wannan mahaukaciyar dariyar tasa kafin ya juya ya nufi hanyar komawa dakinsa yana cewa "Yarinya kin gama yawo acikin gidan nan, sai kin gane baki da wayau !," yana tafiya yana sambatu har ya shiga ɗakinsa, Junaid kuwa bayan sun shiga ɗakin sehrish ta cire hijabin nata agaban mirror suka tsaya, ribbom ɗinta dake ajiye saman mirror ta ɗauko tare da miƙa masa, hannu yasa ya kar6a sannan yashiga kiciniyar tattara gashin kanta donya ɗaure mata, Murmushi ta dunga saki saboda jinsa yadda junaid ke faman nishi aranta tace"junaid ba ƙaramin rago bane, yanzu gashin kan nawa ma yagaza ɗaure wa, shi dai sai kace ba namiji ba, sam babu wannan karsashin na maza atattare dashi...... Muryarshi ce ta katse ta da cewa "Gulma ta kike ko"? Cikin sauri tace "a'a ni na isa," Murmushi kawai yayi, daƙyar yasa mu ya tattara sumar kan sehrish ya ruba ta biyu ya haɗa ya ɗaure," sannan ta mayar da hijabin nata, "Gaskiya junaid ka iya dabara, gashi nan yanzu babu gashin bai leƙo ba," ruƙo hannunta yayi tare da cewa "Mu tafi ko," cikin sauri ta bishi suka fito da hanzari suka fuce, Buɗe mata motar yayi ta shige sannan shima ya zagaya yashiga ciki, yana a driver seat ita kuma tana a gefensa, tayar da motar yayi sannan suka fuce daga gidan, A natse yake yin driving ɗin sehrish na satar kallon shi tace acikin ranta "koya akai ya iya driving yanzu yadda yake shagwa6a66an nan karfa wata rana ya tunkari babban mota damu kwatsam ta rotse damu duk mu mutu.....' "Matsalar ɗan nigeria kenan, duk wani bala'e shike fara kira ma kansa, yanzu ko menene na wannan tunanin"? Cikin mamaki tace "Acikin Zuciya fa nayi maganar" ta faɗi tana kallonsa Junaid yace "Eh nasani, ae muddin zaki yi gulmata acikin zuciyarki to fa saina ji don haka ki kiyaye," ya faɗi yayin da yake shan kwana dasu, Shiru tayi tun daga lokacin bata sake maganarsa ba acikin zuciyarta amma fa tayi mamaki don ita tasan cewa acikin zuciyarta tayi maganar amma gashi yaji," Tunkan su ƙarasa sehrish ke hangen katafariyar makarantar motoci sai shiga suke yi ciki suna sauke ɗalibai, tsayawa zayyana kyawun makarantar 6ata baki ne, gashi bani da isasshen lokacin yin wannan bayanin 😆 A parking space dinsu junaid ya sauke sehrish tare da cewa mun iso, atare suka fito gaban sehrish ne ya faɗi ganin tsala-tsalan ƴan mata young ladies irinta sun ɗau wanka, ƴa'ƴan masu kuɗi wayayyun gaske tun daga shigarsu zai tabbatar maka da cewa An sangarta su da yawa, saboda majority ɗin matan Mini skirt ne ajikinsa sai santala santalan cinyoyi awaye, kuma mafi yawancinsu babu hijab ajikinsu gyaran gashi ne kawai iri-iri, wasu kuma skirt ɗin nan ne ajikinsu waton pencil yabi shafe ɗin jikinsu, iya guiwar ƙafarsu ya tsaya, waro ido waje sehrish tayi tana cewa "kai!kai!!kai!!! Junaid mu koma gida, gaskiya bazan iya zama a school ɗin nan ba, wannan sunfi ƙarfi na Allah," Fashewa da dariya junaid yayi ganin yarda sehrish duk ta dabarbar ce, hannunta na kerma ta ruƙo rigarsa tana 6oyewa abayansa tana faman yi masa sambatun su koma gida, abu kamar wasa har hankalin wasu students ɗin suka dawo kansu ganin yadda Yarinyar ta ƙanƙame jikin dan uwan nata hada su hawaye a fuskarta, Shima kansa junaid sehrish ta rikita shi hankali atashe yake cewa "dan Allah sehrish ki daina, karki bani kunya mana kalli yarda hankalinsu yafara dawowa kan mu innalallahi, yanzu da ace school bus ce ta kawo ki bansan ya zaki ƙare ba," "Junaid nidai mu tafi gida, Allah bazan zauna anan ba" ta faɗi tana shesshekar kuka 😆 dariya kamar zata kashe junaid ba shi kaɗae ba hada wasu daga cikin ɗaliban dake a wajen, Wasu gungun ƴan mata ne suka ƙaraso kusa dasu, ɗaya daga cikinsu tana cewa " Wow friends kalli wani handsome guy nan ya burgeni sosai," Jin hakan yasa sehrish dakatawa da kukan tana ɗan kallonsu kai kana ganinsu kaga jarababbu, Murmushi ta gefenta ta saki tare da cewa "Kamar nasan shi a tiktok fa, zanso ko na tuna sunan shi daga gani cele ne shi sosai," Sai faman surutu suke yi suna yaba kyan junaid, "Kai nifa bazan iya jure ba, sai nayi ma shi magana," ɗaya daga cikinsu ta faɗi atare suka iso dab da su junaid da sehrish, su uku ne matan junaid yace "Sannun ku fa," suka amsa mashi da "Yawwa," sannan ɗaya daga cikinsu tace "Kamar na sanka,"ta faɗi cikin rangwaɗa Junaid yace " Sunanki Parveena," zaro ido su kayi jin yadda junaid ya faɗi sunan ɗaya daga cikinsu kai tsaye, Nuna ɗayar yayi ta tsakiyarsu yace "ke kuma Sunanki Amrish ta ƙarshen kuma sunanki Naja'at," ya faɗi da murmushi a fuskarshi, su kuwa sai faman yarfa hannu suke yi suna kallon shi cikin mamaki jin yadda ya zayyana sunayen su gaba ɗaya, Cikin mamaki wadda ya kira da Amrish tace "Dan Allah ya akai kasan sunayen mu"? Ta tambaya cike da zumuɗin son jin amsa, Duk wannan abun dake faruwa akan kunnan sehrish wadda ke ruƙe da rigar junaid taɗan la6e abayansa, Junaid yaci gaba da cewa "Ban son ku ba nima kawai abunda nasa ni ke Amrish kece kullum kike isarmu da surutu a group, ke kuma parveena baki da aikin yi sai turo hotunan Chacolate iri-iri, Sannan ke kuma Naja'at kinfi kowa iya turo hoton abinci duk in zaki ci sai kin turo mana hotansa," Gaba ɗayansu suka saka ihu da sowa har suna haɗa baki wurin cewa "Wai dama kaine ! junaid romeo ko? Murmushi junaid ya saki tare da cewa "Ni ne, bamu ta6a haduwa ba amma muna yin chat sosai ta whatsapp a group, na ruƙe fuskar kowannan ku da sunayen ku,". Ba ƙaramin farin ciki su kayi ba, Amrish ta nuna sehrish tare da cewa "wannan fa? sister ɗinka ce"? Junaid yace "Eh, younger sis ɗina ce, new comer ce yau tafara zuwa," Parveena tace "No wonder, that's why naga tana hiding kanta abayanka, amma kamar batason mutane ko? Naga ko son kallon mu bata yi," Junaid yace "No just kin gane shagwa6a6iya ce, Last born ɗin mu ce bata saba shiga cikin mutane ba kullum tana a gida, so aduk lokacin da aka fito da ita cikin mutane tana ɗan razana," tunda ya soma jawabi sehrish ke kallon shi baki asake, jin irin ƙaryar daya zuƙa mata nafarko yace ƙanwarsa ce ita, kuma ya laƙwafa mata sharrin cewa tana shagwa6a bayan shine shagwa6a66e, jinjina kanta kawai takeyi, Amrish tace "Ayyah na tausaya mata but she's so cute kuma ta fito daga babban gida yakama ace tana shiga mutane," ta6e baki sehrish tayi tana ɗan kallonsu, 6an6aro hannunta junaid yayi daga jikin rigar shi, sannan ya miƙa ma Amrish yace "Gata nan dan Allah amana na baki ita, ki tafi da ita ba ta son komai ba da yake ita ɗin rainon kakarmu ce, sai ahankali," 😆 Murmushi Amrish ta saki tare da kar6ar hannun Sehrish tace"aikuwa na gode sosai da wannan kyautar, kuma zan ruƙe amana," Cikin raha sukayi sallama da Junaid yayin da suka shiga ciki da Sehrish duk ta zama tamkar mutun-mutumi , suna tafiya tana waiwayon junaid shima kansa sam yagaza tafiya kallonta kawai yake yi, sai yaji duk kewarta ta kama shi daker ya ɗaga mata hannu tare da yi mata bye-bye,' Sannan ya buɗe motarsa ya shige, yayi mata key sannan yaja ta da gudu yabar makarantar, sai da yayi nisa da driving ɗin sannan yayi parking ɗin motar agefen titi yana shesshekar kuka yana cewa "ko na minti ɗaya bana son rabuwa dake sehrish kewarki nake yi," yayi maganar tare da curo handkerchief ɗinsa daga front pocker ɗin rigarsa yana faman share hawayensa, ya jima acikin motar duk kasala ta dabaibaye shi daker ya iya tayar da motar yaci gaba da driving ya miƙi hanyar komawa gida 😥 Parveena da Naja'at Class ɗinsu suka wuce, Amrish ce tayi ɗawainiya da Sehrish ta raka ta har Admin ɗinsu wurin principal ɗin makarantar, maca ce hamshakiyar gaske tun da taji sunan sehrish tagane cewa daga Family ɗin Salahuddeen Hussein take, hakan yasa ta sake mata sosai har tana jan ta da fira, daga bisa ni taba ma Sehrish Sunan Class ɗin da zata zauna, Science department ne kuma an ci sa'a Class ɗinsu ɗaya da Amrish SS1 science C, Madaddalar ƴan iska ba 😂 (Nima Science C nayi a school ɗinmu wlh basa jin magana, dama anyi ittiƙafi babu wanda yakai ƴan C rashin jin magana) Hannunta na ruƙe dana Sehrish suka tunkari benen da zai sadaka da Upstairs ɗin makarantar, anan Classes ɗin suke akwai kuma na down, sehrish dae sai bin ko'ina take da kallo makarantar ta haɗu kamar ba wurin ɗaukar karatu ba saboda tsaruwarta ga wuraren shaqatawa, shiga Class ɗin sukayi mutun goma ne a cikinsa a ƙa'ida kowane class mutun 12 ne kacal acikinsa maza 6 mata 6, idan aka haɗa da Sehrish da Amrish 12 kenan student ɗin cikin sa, gaba ɗaya Ido yadawo kan Sehrish kowa da irin kallon da yake yi mata, Mazan class din kuwa tuni sun soma sakin baki suna cewa "Wow so beautiful, so hot, She looks so sexy," Gabanta ne ya faɗi kowa da irin abunda yake cewa, Matan kuwa wani irin kallo suke binta dashi irin kallon hadarin kajin nan,' ƙara ƙanƙame school bag ɗinta tayi daga tsayen da take, Amrish ce ta soma magana" Hello Class we ave a new comer today, She's from awesome family, i hope zaku bata hankalin ku domin tayi mana Introducing kanta," ta ƙarasa maganar tare da kallon Sehrish tace "Pls introduce ur self," ɗan gyaran murya Sehrish tayi sannan ta soma cewa "am....Sehrish Salahuddeen Hussein by name, 17years old.... Alhamdulillah I love the Way i am," Wannan bayanin na sehrish yasa su gaba ɗayansu Clapping hands ɗinsu suna tafa mata, musamman ƙarshen maganarta ta ƙayatar dasu, Sun mata kyakkyawar tarba duk da akwai waɗanda tunda ta shigo ma basu ɗago da kansu ba daga saman desk sun kife shi kamar masu bacci, Kowane seat mutun ɗaya ne, Amrish ta sama ma Sehrish gurbi a Middle Roll na Class ɗin 0a Second seat Amrish kuma na'a First seat, sai da tafara neman alfarma wurin asalin mai seat ɗin na sehrish akan tabar mata, kuma cikin sa'a ta amince shine har tasamu gurbi abayanta, komai yazo mata cikin sauƙi kuma ba ƙaramin daɗi taji ba na haɗuwarta da AMRISH 💃 ******************AUNTY BABBA*********************** tun da sassafe suna kwance wayarta ta soma ringing a firgice ta farka jikinta na sanye da kayan bacci brown colour, leƙa fuskar Ishaq tayi taga koya buɗe ido samun shi tayi sai faman Sharar baccin sa yake, don haka a hankali ta lalla6a ta sauko daga saman gadon cikin sanɗa, Bayan ta sauko ta ɗauki wayarta data ajiye saman side drawer ɗin shi, sannan ta lalla6a ta shige cikin toilet ta duba mai kiran nata mutumin da tayi tsammani shi ta gani wato*BABA ALAMU* murmushi ta saki cikin sauri ta ɗaga kiran ta kara a kunnanta tun kafin tayi magana baba alamu yace "Na faso gari fa, tun jiya da daddare inata kiran layin ki baya shiga," Aunty babba tace "wlh bansan ka kira ba, dayake nabar wayar acikin ɗakina sai da asuba na ɗauko ta, tun jiya nima nake jiran kiran naka mutumina," Dariya baba Alamu yayi sannan yace "Ae ke baki sani ba, jiya muna dira gari na kwaso rugwagwar motata na shigo unguwarku don in sanar maki kawai sai naga waɗannan Masu fuskar shanayen tsaitsaye ruƙe da bindiga ae ba arziƙi naja motata na koma," Fashewa da dariya aunty babba tayi tace"Ae mijina ne yadawo jiya shiyasa kaga sojoji nan," Baba Alamu yace "Oh to ashe angon ne yadawo, yanzu dae ya za'ayi wurin fitar da yaran kinsan fa wlh shegen tsoran Soja nake, don kwanaki sun ta6a tarar mu a hanya suka sanya mu tsallen kwaɗi a tsakiyar titi da rana tsaka," Aunty babba tace "Ae basu da Imani, musamman in suka ji su acikin kakin nan sai su dunga ɗaukar kansu tamkar wasu dodonni, yanzu abunda za'ayi kana ina ne? Baba alamu yace "yanzu haka na fito da mota ta ina kan hanyar zuwa unguwarku amma fa bazan shigo ciki ba sai dai ki san yarda zakiyi a fito da yaran, Aunty babba tace "Shikenan ka jira ni, zaka ga kirana yanzun nan bada jimawa ba,". bayan ta kammala maganar ta kashe wayar sannan ta fito daga cikin toilet ɗin cikin sanɗa ta lalla6a ta fuce daga ɗakin, Kai tsaye ta nufi ɗakin hafsat ta shiga, tsayawa tayi tana kallonsu hussana da jahad dake ta faman sharar bacci baje saman gadon hafsat, yayin da ita kuma hafsat ɗin ke kwance saman doguwar kujerar ɗakin tana bacci, da alama dukansu daga tashin asuba suka koma bacci, jinjina kanta tayi sannan ta ƙarasa dab da hafsat ta ɗansa hannu ta bubbuga ƙafarta, a dan firgice hafsat tafarka tana cewa "wanene," Murya ƙasa ƙasa aunty babba tace "ke ki taso inason magana dake," Bin ta da kallo hafsat tayi tana yamutsa fuska Alamar bacci bai ishe ta ba, daker tasa hannunta ta janye bargon data lullu6e rabin jikinta da tashi sannan ta miƙe tsaye tabi bayan aunty babba, suka fito daga ƙopar ɗakin suna fuskarta junansu hafsat tace "Meya faru mommy naga kin tashe ni ina tsaka da bacci na? Aunty babba tace "Mutumin fa wanda zai kai su hussana da jahad gidan marayu ya ƙaraso....," jin hakan yasa hafsat canza fuska tuni tace "Mommy yanzu dole sai kin raba ni da yaran nan? Wai me suka tsare maki ne? Dan Allah mommy kibarsu suyi rayuwarsu cikin salama, sun sha wahala fa baki tausayin su? tsoki Aunty babba ta buga tuni ta tamke fuska tace "Tausayin Uban me? menene alaƙata dasu? ke bana son zancen banza mun riga da mun gama magana dake don haka ! Ke nake so ki fidda yaran nan daga cikin gidan nan!! In yaso zan baki numbarsa in kin fitar dasu acikin motarki sai ki kira shi ki bashi su ya tafi dasu can Orphanage home ɗin," Murya asanyaye hafsat tace"shikenan mommy amma ina so ki sani haƙƙinsu ba zai ta6a barin mu ba! Sai Allah ya saka musu duk wani cin zalinsu da mu kayi,!!!!!!!!!!!!!!!! tana faɗin hakan ta juya tare da shigewa cikin ɗakin, wani irin matashin murmushi aunty babba tasa ki tare da cewa "Komai zaki ce ki ce, nidae in dae burina zai cika ba abunda bazan iya aikatawa ba ehen," acan ciki kuwa bayan hafsat ta shiga wuri tasamu gefen gadon ta zauna maimakon ta tashe su sai kawai tafashe da kuka mai cin rai Sautin kukanta ne ya farkar da jahad a firgice ta tashi zaune hankali atashe take cewa "Subhanallahi Aunty hafsat meya faru naga kina kuka? Meya same ki? jahad ta tambaya fuskarta cike da nuna alamun damuwa, Ci gaba da kukan hafsat tayi sam ta gaza cewa komai jikinta har wani jijjiga yake yi, jahad ta kuma cewa "dan Allah sister hafsat ki daina kuka, ban ta6a tunanin zanga wannan ranar ba, idan wani abu ke damunki, zan taya ki addu'a Allah ya yaye maki jin wannan maganar ta jahad yasa hafsat ƙara sautin kukan nata, ɗagowa tayi ta kalli jahad idanunta jawur suna fitar da zafafan hawaye tace"Jahad ba saboda kaina nake wannan kukan ba, face saboda ku ! Ina tausayinku, Nasaba daku zan iya cewa akanku nafara jin tausayin wani ɗan adam aduniyar nan !! tun da jahad taji hakan gabanta ya faɗi Rasssss !! Duk da hafsat bata fito fili ta faɗa mata kai tsaye abunda yasa ta kuka ba, miƙewa hafsat tayi tana faman sharar hawaye tace "Ki tashi hussana ku shirya inaso zan fita daku," Jiki a mace jahad tace "Toh," cikin sauri hafsat ta fuce daga ɗakin, Jahad kuwa jikinta har kerma yakeyi saboda tsoran inda hafsat zata kaisu, daker tasamu hussana ta farka daga bacci sannan ta sanar da ita cewa ta tashi su shirya Sister hafsat zata fita dasu, Batare da sunyi wanka ba, tsaka tsami kawai su kayi acikin toilet sannan suka fito suka shirya, jahad ta zumbula doguwar riga Orange colour ta yafa mayafi launin fari akanta, ita kuma Hussana riga ce Square neck green colour, sai Skirt Ethnic maxi ta sanya ajikinta yana da dan faɗi ya bude da ƴar bazarsa, ba ƙaramin kyau su kayi mata ba, Mayafi tasamu launin skirt ɗin black colour mai ɗigon fari² ajikinsa, tayi rolling ɗinsa tamkar yadda Jahad tayi, Kallon hussana kawai jahad keyi kallon tausayi don ita ranta yana bata cewa lokacin barinsu gidan ne yayi, yanzu kuma zasu fuskanci wata ƙaddarar !!! lokacin da suka fito daga ɗakin hannunsu ruƙe dana juna, Aunty babba na'a falon sai faman zagaye zagaye take yi, tana ganinsu ta nufo su cikin sauri gudun kada ishaq ya farka daga bacci ya fito yagansu, Tana ƙaraso wa inda suke tace "Ku biyo ni," sannan ta juya ta miƙi hanyar fita daga falon, bin bayanta su jahad su kayi gabansu na faɗuwa, suna fitowa daga falon a harabar gidan tuni hafsat ta fito da motarta, buɗe musu motar aunty babba tayi tana cewa "Maza ku shiga ciki, ku jira hafsat yanzu zata zo, Allah ya kiyaye hanya," ta faɗi tana faman tiƙar dariya sannan ta rufe musu motar, Kusan minti goma sha biyar suna zaune jigum cikin motar gaba ɗayansu babu mai magana duk jikinsu yayi mugun sanyi ganin yarda Aunty babba ke faman yi musu dariya, tun daga haka suka gane cewa ba lafiya," 😳😳😳
_wannan na jiya ne da banyi ba, da Anjima zan saki next page insha Allah kuma shine, Ga masu son cigaba da karanta Littafin Abban Sojoji su tuntu6e ni ta wannan numbar (08103884440) [9/16, 2:19 PM] 💋BOSS LADY💋: 💋💋💋ABBAN SOJOJI💋💋💋
The father Of Soldiers Story & Written by_*Boss Bature* page 27 Fitowa hafsat tayi hannunta janye da trolley ba komai bane aciki ba fa ce kayansu jahad, ɗayan hannun nata kuma na ruƙe da basket na breakfast dinsu data haɗo masu, 😥😥😥 Tana isowa ta buɗe boot ɗin motar ta saka trolley ɗin sannan ta rufe, duk aunty babba na tsaye ruƙe da qugu tana sakin murmushi, Bude back seat ɗin hafsat tayi inda su jahad ke zaune ta miƙa musu basket ɗin, hannu na kerma jahad ta kar6a, Sannan ta rufe musu murfin motar, har tasa hannu zata buɗe gaban motar ta shiga ta juyo ta kalli aunty babba idonta jawur tace "Baki bani numbar mutumin ba, wanda kika ce zai kaisu Orphanage home ɗin," cikin sauri aunty babba ta ɗago wayarta dake hannunta, tashiga contact numbar baba alamu ta lalubo, sannan ta shiga karanto ma hafsat ita kuma tana rubutawa a wayarta, bayan ta kammala sa numbar tashige cikin motar kafin ta rufo ƙopar ta aza idonta akan aunty babba tace "Ina fata kin ji daɗi mommy, yau hussana da jahad zasu bar miki gidanki, sai ki zuba ruwa a ƙasa kisha don murna," tana faɗin hakan ta datse motar tare dayi mata key, ta juya sitiyarin motar tayi baya² da ita sannan ta karya kwana ta juyar da ita direct ta nufi gate ɗin gidan ta fuce da motar aguje, Lumshe ido Aunty babba tayi afili tace "Alhamdulillah na kawar da wannan matsalar, yanzu abunda ya rage mun shine zuwa wurin boka domin gudanar da target ɗina na gaba," tana faɗin hakan ta nufi cikin gidan fuskarta washe yau ta rabu da alaƙaƙai,
sai da ta ɗan yi nisa da motar ta fito bakin titi sannan ta dakatar da driving ɗin, wayarta ta ɗauko dake ajiye agefe, Lambar baba alamu ta danna ma kira, bayan ya ɗaga ta sanar dashi kwatancen inda motarta take, bayan ta katse kiran ta ambaci sunan Jahad da Hussana, atare suka amsa mata da "Na'am," juyo taɗanyi ta kallesu da idanunta waɗanda suka canza launi, cikin sanyin Murya tace"kun san inda za'a kai ku"? Har suna haɗa baki wurin cewa "A'a," Shiru taɗanyi kafin taci gaba da cewa "Gidan marayu !!!!!!!' Zaro ido su kayi gaba ɗayansu hankali atashe suna kallonta, hussana da tagaza jurewa tuni ta soma kuka tana cewa "Yaya Omar fa? dan Allah kar akaimu can ku bari yaya Omar yazo ya ɗauke mu mana, ni bana son mu rabu dashi," Murmushin takaici jahad ta saki tare da cewa "Aunty hafsat ba wai gidan marayun ke bama so ba, kawai ni so nake naji da sanin yaya Omar za'a kaimu can"? girgixa kai hafsat tayi tare da cewa "Jahad bada sanin shi ba, kuma nima ba da son raina ba na amince da hakan, amma ina so ku sani can shine zaifi muku zama cikin salama, saboda shi kan shi ya Omar ya manta daku tun da gashi ko kira a waya yadaina yi, babu tabbacin cewa ma yana ƙasar tunda dama banan yake zaune ba, don haka ku Cire tsammani da shi, kawai ku rungumi ƙaddara, kuyi haƙuri³," har kusan sau uku tana maimaita masu kalmar suyi haƙuri,. Hussana dae bata dakata da kukan da takeyi ba sai ma sautin da ta ƙara, jahad ta jinjina kai idonta acikin na hafsat tace "Shikenan Aunty hafsat, kada ki sa damuwa aranki, mu kan mu bamu ta6a tunanin zamu kawo wannan lokacin araye ba, amma gashi mun kawo da ran mu da lafiyar mu, wannan alama ce dake nuni da cewa Allah yana sane damu !!! Kuma shine zai kare mu aduk inda muka kasance a faɗin duniyar nan! mun gode sosai da kulawar da kika nuna mana," daga haka jahad tayi shiru idonta na zubar da hawaye hussana kawai take kallo wadda ke ta faman shessheƙar kuka,
Jikin hafsat ya gama yin sanyi sam tagaza yin kwakkwaran motsi, suna cikin wannan Yanayin Motar baba Alamu ta ƙaraso dab da tasu, wata tsohuwar jeep ce ta ragwaggwa6e ta fita hayyacinta, kai wannan motar ko kyauta aka bani ita wlh na kwammace in ƙaraci yawona da ƙafafuwana saboda muninta, gaba ɗaya fa glass ɗin motar ya faffashe kana hangen cikin motar, babban abunda zai ɗaure maka kai shine yadda yakeyi wurin tayar da motar domin kuwa babu wurin zura mukulli atada mota, sai dae wasu wayoyi gasunan birjik su yake haɗawa sannan ya tashi motar, hankaɗa murfin motar yayi sannan ya fito, wani irin Matsolan mutun ne ramamme sai uban ƙasusuwa gashi baƙi wulik kana ganinsa kaga cikakken ɗan duniya, fuskarsa yana da wasu irin tsaguna waɗanda zasu tabbatar maka da cewa Magobiri ne, yadda kasan kwarya haka tsagunan fuskarsa suke, yana da kwalakwalan idanuwa kuma jawur dasu, ga wani irin fankacecan hanci harya so yafi ƙarfin fuskarshi, haƙoran bakinsa kuwa sunyi jawur dasu saboda Cin goro, a shekaru zai iya zarce shekara hamsin, jikinsa na sanye da wani tsohon yadi wanda yausha rabon da yaji dutsen guga tun 1960 😔
fitowa hafsat tayi ita kanta da ta ga mutumin sai da gabanta ya faɗi saboda muninsa, shi kuwa washe baki ya shiga yi yana cewa "Yarinya ta girma ! komai yaji dai² nasan baki sanni ba, amma ita jatumarki kullum tana bani labarinki,"
ɗaure fuska hafsat tayi zuciyarta har wani tashi take yi, hannunta na kerma ta buɗe masu hussana motar, fito wa Su kayi atare da jahad duk jikinsu ya gama mutuwa, musamman da su kayi arba da baba alamu, sai duk suka firgita jiki na kerma Hussana ta ƙanƙame jahad saboda tsoro, Buɗe boot ɗin motar hafsat tayi tare da curo masu trolley ɗin kayansu ta miƙa ma jahad ta kar6a, sannan ta ɗauko masu food basket ɗinsu da suka manta, ta miƙa ma hussana daker ta kar6a, Cikin kuka Hussana ke cewa "Aunty hafsat dan Allah kada ki tafi kibarmu a hannun wannan mutumin !!" rigima sosai hussana ta sanya, hafsat kuwa tsananin tausayinsu duk ya kamata, purse ɗinta ta ɗauko cikin motar, sannan ta ƙirgo kuɗi kusan dubu 30 ta miƙa ma Jahad tace "Ki ruƙe wannan a wurinki nasan za suyi maki amfani, ni zan wuce," Bin ta da kallo kawai jahad ke yi idonta na zubar da hawaye duk yadda hussana ke faman rusa kuka tana rurruƙe mayafin jikin hafsat amma hakan bai hanata tafiya ba, cikin sauri ta shige motarta, taja ta da gudun gaske tabar wurin,
Mayar da idonsu su kayi kan Baba alamu wanda ke ta faman bin jikinsu da kallo yana sakin wani irin shu'umin murmushi, hannu yasa ya buɗe masu motar yace "Maza ku shiga ciki," Amsar trolley ɗin yayi ya bude boot ɗin motar ya wurgar dashi ciki sannan ya datse shi, shiga ciki su kayi gabansu na faɗuwa zuciyarsu nayin wani irin bugu mai sauti, dawowa yayi ya shige gidan gaba sannan ya jona wayoyin nan take motar tayi wata irin ƙara ƙirrrrrrrr bakin hayaƙi ya soma fita ta baya, sannan yaja motar da gudun gaske ya miƙi hanya dasu,
****************** tun jahad tana ganin gine-gine da gifcin mutane har ta soma ganin dajijjika, hakan yasa hankalin jahad ya tashi ganin ya fidda su cikin gari bayan cewa Hafsat tayi zai kai su gidan marayu, zazzare ido jahad ta soma yi gabanta na wani irin bugu, juyawa tayi don taga wane hali hussana ke ciki, abun mamaki saita samu hussana sai bacci take shara hannunta Æ™anÆ™ame da kwandon abincin su, Kai tsaye baba alamu ya kutsa dasu cikin dajin mai uban bishiyoyi da ciyayi ba gifcin mutun acikinsa sai dabbobi dake shawagi, Murya na rawa jahad tace "Bawan Allah ina zaka kaimu ne !? Ba gidan marayu akace zaka kaimu ba,"? Ta tambaya idonta cike taf da hawaye cikin tsananin tsoro, fashewa da dariya baba alamu yayi sannan yace "A sanin ku ba, amma ni ba gidan marayu nayi da ita hajiyar zan kaiku ba, ce mun tayi in zubar mata daku acikin daji," Cikin kuka jahad tace "Dan Allah kada ka cutar damu , ka sauke mu kawai anan," Baba alamu yace "Yarinya kenan ki daina wannan tunanin, ae tunda idanuwa na suka yi arba da surar jikinku na kwaÉ—aitu da son kasancewa tare daku, don haka zan kai ku gidan gonata dake acikin dajin nan don na runÆ™a rage zafi daku," ya Æ™arasa maganar da wata irin shaÆ™iyar dariya, Jahad kuwa neman hanyar fita take yi daga cikin motar amma ta gaza buÉ—e murfin motar saboda ya datse shi sosai, duk wannan tashin hankalin da ake ciki hussana bata sani ba, saboda baccin da takeyi, jahad bata haÆ™ura da Æ´unÆ™urin buÉ—e motar ba sai da ta sanya iya Æ™arfinta na Æ™arshe ta tunkuÉ—e murfin motar ya buÉ—e aikuwa nan take baba alamu ya girgiza motar da mugunta, hakan yasa jahad ta faÉ—o Æ™asa timmmmm ! ta gangara Ta bugi wani dutsi nan take goshinta ya fashe, Shi kuma yaja motar da gudu ya tafi da hussana acikinta, hankali a matuÆ™ar tashe jahad ta É—ago daga jikin dutsen jini na zuba a goshinta, miÆ™ewa tayi da gudun gaske tabi motar tana kuka tana ambaton sunan HUSSANA, muryarta har wani shaÆ™ewa take yi saboda yadda take kwala mata kira ga uban gudun da takeyi don ta taddo motar, amma ina tuni yayi mata nisa ga tafin Æ™afarta da Æ™ayoyi suka sossoke ta duk Æ™afar ta fashe, jini nata faman gangarowa a Æ™arshe data gaji da bin motar jiri na kwasarta nan take ta yanke jiki ta faÉ—i sumammiya acikin korayen ciyayin dake a wurin, ðŸ˜
Kiran ƙarshe da jahad ta kwalama hussana kafin ta sume har cikin zuciyarta taji shi tuni ta soma ƙoƙarin buɗe idanunta wanda ke cike da bacci, a lokacin har baba alamu yashiga da ita gidan gonarsa ƙopar katako ce ke gare sa tamkar ɗan gate, bayan ya shigar da motar ya fito ya rufe ƙopar gidan gonar da kwaɗon dake ajiki, Sannan ya koma tare da buɗe murfin motar inda hussana ke zaune tana faman lullumshe ido alamar bacci bai isheta, so take ta buɗe Idonta taga ina jahad take amma sam bacci ya hana Ta, hannu baba alamu ya zura tare da ɗauko hussana ya sa6ata a ƙafaɗarsa ya miki hanyar wata ƙopa inda ya dosa ya buɗe ta ya shige da ita ciki sannan ya sauke ta ƙasa har tana yin tangyaɗi zata faɗi, sai da baba alamu ya datse ƙopar ɗakin gam yadda bamai shigowa sannan ya juyo yana kallon hussana tare da washe waɗannan haƙoran nasa marasa saiti, A lokacin Hosana ta dawo cikin hayyacinta baccin yabar jikinta, bin wurin tayi da kallo ɗakine mai faɗin gaske babu komai aciki sai jarkokin ruwa da bulo bulo, da wani ajiyayen genarator tsoho, sai sauran tarkace, wurga idonta tayi akan baba alamu dake tsaye agabanta yana washe mata baki, nan take ta buga uban tsalle taja da baya tana faɗin "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga uku, Ina jahad take! Wayyo Allah na Me zaka yi mun meyasa ka kawo ni nan ! tayi maganar tana ja dabaya a tsorace Baba alamu ya kashe mata ido ɗaya tare da cewa "daɗi zan baki, kiyi shiru da bakin ki kada wani yaji mu, indai kina son ganin ƴar uwarki to ki bani haɗin kai muyi mu gama cikin salama,' Yayi maganar tare da kai hannu zai shafa fuskarta a firgice taja baya tana girgiza masa kai atsorace take cewa "Dan Allah kada ka cutar dani, ka ƙyale ni bani da lafiya, idan ka ta6ani mutuwa zanyi," ta faɗi tana faman zazzare ido, ga wata irin zufa dake wanko mata dakyar take haɗiyar numfashi, "Ba zaki mutu ba, bada zafi zan miki ba kaɗan kaɗan, in dai baki bani haɗin kai ba zan ƙwata ta ƙarfi kuma naƙi nuna miki inda ƴar uwarki take," Cikin kuka hussana tace "a'a nidai kada ka cutar dani bana so, kadaina matsowa kusa dani, wlh Allah bazai barka ba kuma yaya Omar ma bazai ƙyale ka ba sai ya kashe ka," fashewa da dariya Baba alamu yayi tare da gwalo ido yana mata gwalo yace "Wanene wani Omar kuma? babu kowa anan daga ni sai ke ! Kuma yanzun nan zan kawar da sha'awata tare dake," yayi maganar tare da yin kwakkwaran taku ya fusgo mayafin jikin husana nan take ya zame ƙasa, watsa wa tayi da gudu ciki tana kuka cikin rashin sa'a tayi tuntu6e da bulo ƙafarta ta harɗe ta kife ƙasa gaba ɗaya.........................
dariyar mugunta baba alamu ya saki ganin abun yazo mashi cikin sauƙi, nan take ya shiga kwance zariyar wandonsa, daker hussana take jan numfashi saboda buguwar da tayi wani irin ciwon kai yafar mata lokaci guda, jin motsinsa dab da ƙafafunta yasa ta dumbuzar ƙasa a hannunta, ta daddage ta tashi zaune tare da watsa mashi ita a fuska, nan take yashiga yin tsalle yana faɗin "kai ! Kai!! Kai !! Don ubanki ni kika watsa ma ƙasa a ido! aiko bazan ƙyale ki ba, saina wulaƙanta rayuwarki, Jin hakan yasa hussana zabura tare da miƙewa tsaye zata gudu batayi wani aune ba taji yaja rigar jikinta nan take ta soma yage wa, juyowa tayi tare dasa hakoranta ta gartsa mashi Cizo, azaba da raɗaɗi suka sa shi sakin ihu, kuma hakan ya ƙara fusata shi, a fusace yabi ta tare da damƙo gashin kanta ya janyo shi da ƙarfi ta dinga sakin ihu tana kuka tana kiran Sunan Jahad,
Matse ta yayi ajikinsa tare da sa hannun shi biyu ya ƙarasa yage rigar jikin hussana gaba ɗaya, hankali a matuƙar tashe husana ta watsa mashi miyau afuskarsa biji-bijin daya daya fara gani ne yasa shi ɗan dakatawa, hannunta ta sanya tare da ingije shi da ƙarfin gaske gaba ɗaya baba alamu yayi taga² zai faɗi ƙasa, Cikin sauri hussana ta tattare rigarta ta kare kirjinta da ita, hanyar fita daga ɗakin ta nufa da gudun gaske tana kuka burinta kawai ta isa kopar ta buɗe ta fuce tana cikin gudun nan baba alamu ya taso a matuƙar zuciye ya nufe ta da sauri yakai hannunsa tare da jan rigarta data rufe jikinta da ita, gaba ɗaya ya 6an6are rigar daga jikinta ya cire ta gaba ɗaya ya ruƙe a hannunsa, Wani irin kuka hussana ta saki mai matuƙar cin rai ganin yarda ya cire mata rigarta, gashi ko brazier bata sanya ba, ƙirjinta gaba ɗaya sun fito, hannunta ta sanya ta tarbesu tana kuka kuma hakan baisa ta daina tunkarar ƙopar ba,
Bin ta baba alamu yayi da gudun gaske saboda ya ruÆ™o ta jikinsa don ya idasa nufinsa, Sai dae ina kafin yayi wani kwakkwan yunÆ™uri tuni anyi ma Æ™opar É—akin wani irin kwakkwaran Naushi nan take katakon jikinta ya farfashe gaba É—aya ta buÉ—e, A tsorace baba alamu ya dakata yana faman zazzare ido don son ganin wanene wannan ya faÉ—o masa cikin gidan gonarsa !!!!!!!!!!!! Ita kanta hussana ta firgita tsayawa tayi jikinta na wani irin kerma ga zazza6i daya lullu6e ta, har lokacin hannunta na tarbe da Æ™irjinta, Duro Æ™afarsa yayi cikin É—akin tamkar damusa wani irin kakkarfa ne mai ban tsoro, jikinsa na sanye da Jacket baÆ™a daga ciki kuma farar t*shirt ce wadda ta bayyana Æ™irar Æ™arfinsa, Sai dogon wando baÆ™i, bai bamu damar muga fuskarsa ba domin kuwa tana sanye cikin face mask baÆ™i, idonsa kuma na sanye da baÆ™in glass, gaban hussana ba Æ™aramin faÉ—uwa yayi ba duk ta gama tsorata, baba alamu kuwa murya na rawa yashiga cewa "kai...Wai Wanene kai ! daga ina kake? Mai ya kawoka gidan gonata ! ya tambaya yana tada jijiyoyin wuya, Har lokacin bai da alamar yin magana, a hankali ya sanya hannunsa tare da ruÆ™o jaket É—in dake ajikinsa ya cire ta gaba É—aya yayi wurgi da ita, sannan ya mayar da hannun nasa ya tu6e t-shirt É—in dake ajikinsa ya rage babu riga ajikinsa, Hankalin baba alamu ba Æ™aramin tashi yayi ba ganin irin damtsen hannunsa a murmuÉ—e ga Æ™irjinsa dake motsi abun gwanin ban tsoro, tuni zuciyar hussana tayi wani irin bugu nan take ta tafi zata sulale Æ™asa, da Hanzari ya tarbota jikinsa gaba É—aya tafaÉ—a a faffaÉ—an Æ™irjinsa, hakan ya bashi damar zura mata t-shirt É—insa ajikinta donya rufe mata jikinta, bayan ya kammala sanya mata rigar, ya buÉ—e bakinsa ta cikin face mask É—in yayi fito mai sautin gaske har saida baba alamu ya firgita yana faman kwalala ido, Da gudun gaske wani Saurayi ya shigo ya tunkare sa, batare da yace komi ba ya miÆ™e masa Hussana, cikin sauri yasa hannu ya É—auketa tare da azata a kafaÉ—arsa ya fuce da ita, sai lokacin Yasa hannu ya cire glass É—in fuskarsa tare da yin wurgi dashi, Azazafe ya sanya kyawawan idanuwansa waÉ—anda suka Canza Launi izuwa ja saboda tsananin 6acin rai, gadan gadan ya tunkari Baba alamu wanda ke shirin guduwa, hannunsa yakai tare da damÆ™ar wuyan rigarsa ya É—aga shi sama, ya dawo dashi Æ™asa ya buga kansa jikin bulo nan take haÆ™ora biyu daga bakin sa suka fito Jaga-jaga da Jini, saboda tsananin azaba da raÉ—aÉ—i ya sanya Baba alamun sakin futsari a wando yana cewa "Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un na bani na 6atare na lalace nashiga uku, Dan Allah ka Æ™yale ni wlh nabi Allah nabi manzonsa .,........... tsawa mutumin ya daka masa tare da cewa "Kasan da Allah kake Æ™oÆ™arin aikata ma Æ™aramar yarinya faÉ—e tsofe tsofe dakai!! mutun mara imani da tausayi irinka wanda baisan darajar Æ´a' mace ba Sam bai cancanta daya cigaba da rayuwa ba,' É—agowa baba alamu yayi yana ja da baya da baya idonsa jawur, jini na kwaranyowa daga bakinsa yana cewa "Dan Allah kada ka kashe ni ! Kabarni a haka naji jiki sosai, ina da Æ´a'Æ´a da mata in ka kashe ni zasu shiga wani hali.....' bai bari ya Æ™arasa maganar ba, yakai masa wata irin mahangul6a da hanunsa nan take yasake fasa ihu, "Karka kuskura ka sake buÉ—e wannan Æ™azamin bakin naka da sunan zakayi mun bayani ! Bani da lokacin sauraron jawabin Ka, har kana da bakin da zakace mun kana da Æ´a'Æ´a da mata, don ubanka su yaran daka É—auko donka lalata ma rayuwa daga sama suka faÉ—o? Ko su basu da dangi ne da zasuyi kuka in sun rasa su? Idan ka lalata masu rayuwa kana da tabbacin zasu Æ™ara numfashi ne ko baza suyi ba ? Ka yi tunanin hakan? ! idan wani ya lalata rayuwar Æ´arka yaya zaka ji? Ka Æ™iyasta yaya raÉ—aÉ—in yake azuciya............yana faÉ—in hakan yasa hannu ya rarumesa tare da wujijjiga shi ya sake buga kanshi ajikin bulo É—in nan take kansa ya fashe jini ya soma kwaranya, ko shurawa baiyi ba nan take ya mutu a mace............ (Yanzu ina amfanin irin wannan rayuwar? Ka mutu kana aikata irin wannan mummunan zunubin batare da ka shiryu ba? Shin mai zaka ce ma Ubangiji? mutum baison lokacin mutuwarsa ba, shiyasa ake so koda yaushe mutun ya kansance cikin shiri kuma ya kasance yana aikata abun kirkiri, sam baba alamu baisan cewa yau wa'adinsa zai cika ba, Ga yarda Æ™arshem shi takasance Ya Allah kasa muyi kyakkyawan Æ™arshe, kuma ka kare mu daga aikata aikin dana sani ðŸ™ðŸ˜¥
duk da ya mutu amma hakan bai masa ba saboda raÉ—aÉ—in da yake ji azuciyarsa, hannu yasa ya rarumi Æ™aton dutsin dake ajiye a Æ™asan wurin zai rotsa masa kai, cikin sauri matashin nan daya fita da husana ya faÉ—o É—akin ya tunkaresa tare da hanzarin ruÆ™o hannunsa yana cewa "Yalla6ai kabarshi haka mana, ya riga daya mutu," fisge hannunsa yayi yayin da idonsa ke cike tab da hawaye da wani irin huci yake cewa "Kabarni kawai na tarwatsa kansa ko zuciyata ta samu salama, kasan yarda nake ji acikin zuciyata kuwa, tamkar ana rura garwashin wuta acikinta saboda tsantsar baÆ™in cikin da nake ji, WANNAN MUTUMIN YA SHIGA HURUMINA !!!!!!!!!!!!!!!!!!!! â‰â—‼â—â“â“â“â“â“â“ *SHIN WANENE WANNAN MUTUMIN DAYA FARMAKI BABA ALAMU ACIKIN GIDAN GONARSA AYAYIN DA YAKE ƘOƘARIN KETA HADDIN HUSANA*â“≠*WANENE SHI*â“â“ _*amsar tana a wurin hafsat Bature muhammad Boss Lady domin son sanin wanene wannan sai ku antaya kuÉ—inku naira 300 kacal Vip kuma 700 a wannan acct number É—in 3196407426 first bank Bature hafsat Muhammad ku tura shaidar biya ta wannan layin da kuma masu tura recharge card 08103884440 kada ku bari abaku labari , masu karantawa ta facebook masu Æ™aramar waya Recharge card zaku tura koda digits É—insa ne 200 only in kun daure kun biya da dama zaku cigaba da samun posting insha Allah Ku fara biya da hanzari daga yau zuwa monday, har yanzu dae nice dae Hafsat Baturen da kuka sani mai sauÆ™in kai, ban canza ba, kaÉ—anne kawai zasu fahimce niðŸ‘ðŸ‘*
Alhamdulillah finally na kammala
*💋💋okay MAJOR ya sake ruƙo hannunsa tare da cewa"Sorry Sir! Nasan Abun da ciwo, Amma mu gode ma Allah da muka ƙaraso akan Lokaci batare daya kai ga Cutar da ita ba" huci kawai yake yi yana kallonsa da idanuwansa waɗanda suka canza Launi bakomai yake tunawa ba fa ce yarda Baba alamu ya yayyaga ma Husana rigar jikinta, in ya tuna wannan abun zuciyarsa Tafarfasa take yi saboda 6acin rai, muryar major ce ta katse shi da cewa" Allah ya huci zuciyarka yakamata mu hanzarta barin gidan gonar nan domin muyi gaggawar kai su asibiti,
Jin hakan yasa shi yin saurin zura hannu tare da curo wayarsa daga aljihun wandonsa, nan take ya shiga camera tare da saita gawar baba Alamu ya É—auke ta hoto da kyau, bayan ya ammala ya mayar da wayar cikin aljihun sannan ya kalli Major yace "Duba min aljihun wandonsa kona rigarsa kaga ko za'a samu waya,"
Cikin hanzari Major ya zura hannunsa cikin aljihun baba alamu daker ya lalubo wata ƙaramar waya nokia, taji duniya don bala'e batteryn wayar saida aka sanya robali sannan aka ɗaure shi baya cikon da akayi masa,duk ta rakwakkwa6e wayar,
"Sir ga wayar," ya faɗi tare da miƙa masa, bai kar6a ba bin wayr yayi da kallo kafin yace "Major cewa nayi ka ɗauko mun wayarsa ba wannan abun ba," ya faɗi yana nuna wayar hannun major ɗin
Ƙiris ya rage major ya fashe da dariya saboda ya lura cewa Boss Man ɗin nasa baya cikin hankalinsa,
"Sir wannan itace wayar, ka duba da kyau ta tsufa ne sosae shiya sanya ka ganta hakan,"
Ajiyar zuciya ya saki tare da cewa "Keep it in ur place, zan neme ta," yana faÉ—in hakan yakama hanyar fita daga É—akin,
Muryar Major ce ta dakatar dashi da cewa "yalla6ai rigar fa? zan iya É—auko maka ita," ya tambaya yana jiran amsa ,
Bai amsa mashi ba ya fuce kawai cikin sauri major ya ɗauko Jacket ɗinsa da yayi wurgi da ita sannan ya fito daga ɗakin ruƙe da ita a hannunsa a lokacin har yakai wurin motarsu da suka zo da ita, kai kana ganin yarda sukayi parking ɗinta kasancewa a tsiyace suka shigo da ita, domin kuwa har katakon ƙopar gidan gonar duk sun tarwatsa shi,
Cikin sauri Major ya rufa masa rigar abayansa shi kuma ya ƙara gyarata ajikinsa sannan ya zuge zeep ɗinta, buɗe motar yayi sannan ya shige back seat ɗin shikuma major ya shige driver seat sannan ya tayar da motar yayi baya² da ita kafin ya karya kwana ya fito daga gidan gonar da gudun gaske yake driving ɗinsu,
Sam ya gaza ɗauke idonsa akan hosana dake langwa6e asume kusa dashi, duk gashin kanta ya gama tarwatsewa dama a hargitse yake sai kuma aka ƙara hargitsar dashi, duk ya rufe mata fuskarta, lumshe idonsa kawai yayi har lokacin yana mamakin yarda akai wannan Lamarin ya afku amma yana da tabbacin cewa major yana da masaniya akan hakan,"
adai dai hanyar da baba alamu yayi wurgi da jahad Major yayi parking É—in motar, cikin sauri ya buÉ—e motar ya fito gabansa ne kawai ke faÉ—uwa tsoranshi kar ace ta mutu,
wani saurayi ne zuƙunne a inda jahad take yashe, da alama ba ƙaramin taimako yayi mata ba, domin kuwa ya ciccire mata ƙayoyin da suka soki ƙafarta sannan kuma yayi amfani da Mayafinta wurin kekketa shi izuwa kashi uku, ya ɗaure mata goshinta sannan kuma ya naɗe mata ƙafafunta dake zubar da jini,
Fitowa major yayi shima yana kallonsa,
"Major karfa ace yarinyar nan ta mutu," ya faÉ—i a tsananin tsorace
"Sir she's still alive, suma ce kawai," ya bashi amsa,
saurayin yace"yalla6ai tana buƙatar taimakon gaggawa saboda jinin dake bleeding a goshinta da kuma tafin ƙafarta,"
Cikin tsananin tashin hankali ya ƙarasa tare dasa dukkan hannayensa ya tallabo JAHAD ya ɗaukota da sauri Major ya buɗe masa motar ya shigar da ita a kusa da Hossana ya zunar da ita a sume, sannan shima yashiga motar, zuge glass ɗin yayi tare da kallon saurayin yace"Ka shiga mu tafi tare,"
saurayin yace"yalla6ai machine É—ina fa"?
tunkan ya bashi amsa major yayi saurin cewa"daraban kayima arziƙi ƙulli ana maganar arziƙi wake ta wani machine"?
Jin haka yasa saurayin tasowa sai da ya bari major yashiga, sannan shima ya shiga kusa dashi ya zauna, rufe motar su kayi sannan da gudu suka bar dajin suka miƙi santalelen titin da zai sadasu da inda suka dosa
Kallonsu kawai yake yi ransa na ƙara ƙuna ganin irin jigatar da yaran su kayi yaran daya kai Amana, sam kwalwarsa ta rikice yarasa gane ma wannan lamarin ba komai yake son ji ba face yarda akai har tsohon can ya ɗauko yaran izuwa cikin gidan gonarsa don ya lalata rayuwarsu! taya akai ya fito dasu daga gidan general Ishaq? taya akai Aunty laila tayi gangancin da har wani zaizo ya ɗauki twins ɗinsa? da sa hannun wa akayi wannan ƙulla-ƙullar, tabbas kowaye bazai ƙyale shi ba, muddin ya gano gaskiyar lamarin!!, ya ƙarasa zancen zucin nasa adai² lokacin da suka ƙetaro Abuja, kai tsaye suka wuce dasu izuwa katafaren asibitin SGR,
***************SEHRISH***************
Sam bata gane mai ake koyarwa acikin class É—in saboda wata irin yunwa dake jibgarta ga wani irin bacci da take ji, sai faman hamma take yi tana lumshe ido,
Wuraren ƙarfe tara da rabi, time ɗin break yayi gaba ɗaya ƴan class ɗin sai fita suke yi don suje cin abinci, Sehrish na kwance saman desk ɗin gabanta sai faman sharar bacci takeyi,
juyowa Amrish tayi daga seat É—inta tana kallonta, murmushi ta saki tare da sa hannunta taÉ—an bubbigi bayan sehrish tace "Get up baby ! time É—in break yayi, yakamata mu fita,"
daker sehrish ta buɗe ido tare da ɗago kanta daga saman desk ɗin tana kallonta biji², miƙewa Amrish tayi ta fito daga seat ɗinta, sannan ta ruƙo hannun sehrish tana cewa"Get up mana Let's go,ko bakya jin yunwa ne"?
ta tambaya tana kallonta, miƙewa sehrish tayi tare da biyota suka fito daga Class ɗin gabanta nata faɗuwa tsoranta kar ace siyen abincin zasuyi don ko sisi bata fito dasu ba, babu wanda ya bata kuɗi,
saukowa sukayi daga saman benen duk inda suka bi sai an samu wanda zai yi ma Amrish magana, kuma yawanci akan Sehrish suke tambayarta ko Æ´ar uwarta ce, sai dae kawai tace musu eh, saboda tasan son jin gulma ne kawai,
Hanya suka miƙa bada jimawa ba suka ƙaraso Lunch room ɗin makarantar wurin cin abincinsu, lokacin da suka shiga wurin mamaki ya kama sehrish ganin ɗalibai aciki kowa zazzaune saman dining tables masu mazaunin mutun 4, kowa wanne gabansa cike shaƙe da abinci sai ci suke yi,
Ruƙo hannunta Amrish tayi adai² wani tebur da bakowa tace ma sehrish tazauna sai faman zare ido take yi gabanta na faɗuwa tsoranta kar ace tabada kuɗin abinci,
"Me kike so na amso mana muci"? Amrish ta tambaya tana kallonta daga tsaye, zuru sehrish tayi tana tunanin yarda za tace ma Amrish bata da ko sisi,'
"Kin yi shiru baki ce komai ba"? Amrish ta tambaya a ƙagare, murya na rawa Sehrish tace "Ni bana jin yunwa, a ƙoshe nake,"
Cikin mamaki amrish tace "but alamu fa sun nuna cewa kamar kina jin yunwa? Yakamata ko Coffee ne kisha taya zaki zauna da yunwa acikin ki"?
sehrish tace"kada ki damu bana jin yunwa ne kawai," jinjina kai amrish tayi tare da cewa "its ok bazan takura maki ba, tunda kince bakya jin yunwa, ni bari naje na amso abunda zanci," tana faÉ—in hakan ta wuce wurin masu zuba masu abincin,
É—agowa sehrish tayi tana kallon students É—in dake zazzaune suna faman cin abinci hankalinsu akwance, haÉ—iyar miyau tashiga yi ganin yarda suke Cusa pancakes da zuma abakinsu,
sunnar da kai tayi gaba É—aya tarasa yaya zatayi ga yunwa tana ji amma tana tsoran taci musu abinci ba kuÉ—in biya, tana cikin wannan tunanin sai ga Amrish tadawo hannunta É—auke da plate guda biyu da murmushi afuskarta, ta ajiye su saman table É—in sannan ta juya ta koma domin amso masu abunsha,
Zuru sehrish tayi tana kallon plate ɗin mai ɗauke da banƙararriyar kaza ta gasu sosai hada ƙaramar knife wadda mutun zai yanka yaci, ɗayan plate ɗin kuma Snacks ne acikinsa shaƙe, runtse ido tayi tana ji tamkar takai ma plate ɗin hari, sai faman cixon la66a takeyi,
dawowa Amrish tayi hannunta ruƙe da Laca sera mai sanyin gaske roba biyu, wuri tasamu tana fuskantar sehrish tazauna tana cewa "Wai haryanzu kina akan bakan ki na ba zaki ci komai ba"? tun yanzu zamu fara haka dake?
ɗan murmushin yaƙe Sehrish ta saki tare da cewa "ba haka bane just bana jin yunwa ne shiyasa," ta faɗi tamkar zatayi kuka, Ido ya gani rai naso,
Murmushi kawai Amrish tayi kafin tasa hannu ta ɗauki ƙaramar wuƙar dake ajiye saman kazar tashiga yankar naman tana ci,
Ƙiris ya rage sehrish tasaki miyau saboda tsabagen kwaɗaituwa da tayi cikin sauri ta gyara natsuwarta gudun kar tayi abun kunya agaban sabuwar ƙawarta,
Muryar amrish ce ta katse ta da cewa "Ko lemun ba zaki sha ba"? Cikin sauri tace"eh a ƙoshe nake," giɗa kai tayi sannan taci gaba da cin abunta, suna cikin zaman nan sai gasu Naja'at da parveena sun shigo, kai tsaye wurinsu suka nufa suka samu wuri suka zazzauna,
Naja'at tace "Wlh da wata irin yunwa na fito Class ɗin can, sam bana gane ma karatun, dama can nifa ba gane math nake ba,' tayi maganar tare da sa hannu ta ɗauki robar lacasera tare da buɗeta ta kwafa abakinta tana kwankwaɗa, hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba ganin tashanye mata lacasera ɗin da Amrish ta kawo masu, Ana cikin haka parveena ta tsoma hannu suka cigaba da cin roasted chicken ɗin da Amrish ta kawo masu, kafin kace mai tuni sun kwamushe komai, duk tana zaune tana faman haɗiyar yawu, sai da suka kammala sannan ma suka lura da ita, parveena tace "Au! Wai dama Yarinyar nan tana a wurin nan? Yo aini yunwa tasa nagaza gane ku nawa ne zaune a table ɗin muka tarar," ta faɗi da mamaki Naja'at ma tace"ko ni ban lura da ita ba, sai da kikayi magana Allah, sannu ko? Meyasa ke bakici komai ba ne,"
Tamke fuska sehrish tayi rai a6ace tace "bana jin yunwa," jinjina kai su kayi atare naja'at tace "halan kinyi breakfast dayawa ne a gida"?
A ƙule sehrish tace "Bansani ba," acikin zuciyarta tayi maganar a fili kuma tace "eh,"
daganan suka ci gaba da firar su har Parveena ta ƙaro masu abincin duk tana zaune suka zauna suka lamushe suka bar rishi da tanɗar baki, da lokacin komawa Class yayi kowa ya wuce Ajinsu naja'at da parveena class ɗinsu ɗaya don haka suka wuce atare, ita kuma tabi Amrish izuwa nasu Class ɗin,
Sehrish ba ƙaramin jiki taji ba, saboda azabar yunwa har wani jiri take gani, dishi² ta runƙa gani a idonta sam batasan me aka koya masu bama,
Lokacin da suka taso daga school tunani ta soma yi wa zai zo ya ɗauke ta, ga school bus tashigo cikin makarantar amma tsoranta kar ace kuɗi za'a biya,tsayawa tayi hannunta ruƙe da school bag ɗinta sai faman lullumshe ido take yi, suna cikin tsayuwar nan sai ga drivern Amrish ya iso, sallama tayi ma sehrish sannan ta shige cikin motar suka tafi,
Hankalin Sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba, ganin sai zuwa ake ana kwashe sudents ɗin ita gatanan tsaye zugudum babu alamar wani zaizo ya ɗauke ta,
tana cikin wannan tunanin motar JUNAID tashigo cikin makarantar adai² inda take tsaye yayi parking ɗin motar tare da zuge glass ɗin motar yace "madam muje ko," ajiyar zuciya ta saki ba ƙaramin daɗin zuwan shi taji ba, buɗe motar tayi tashiga sannan yaja motar suka fita daga makarantar,
Miƙar hanya yayi dasu yana cikin driving ɗin yaji sehrish ta faɗo masa a kafaɗarsa ta langwa6e, saboda shock ɗin daya ji har saida yaɗan ci burki a tsakiyar titin, aza idonsa yayi akanta, wani irin wahalallan bacci ne ya ɗauke ta batare da saninta ba, shine ta faɗo masa a shoulder ɗinsa, gaza janye idonsa yayi akanta yadda take ta faman sharar baccin ta ba ƙaramin kyau tayi masa ba, ya jima yana kallon kyakkwawar fuskarsa, sam.ya manta cewa a tsakiyar titi suke, sai go slow suke haɗawa batare da saninsa ba, har sai da wani babban mutun yayi masa magana ta waje, sannan ya tashi motar yaci gaba driving ɗinsa cikin kasala,
har suka ƙaraso gidan adai² parking space ɗinsu ya ajiye motar, sannan yajuya ya kalli sehrish tare dasa hannunsa ya shafa gefen fuskarta tare da ambaton sunanta"Sehrish mun iso gida fa, wake up pls ," ya furta yana kallon yadda take motsi da idonta alamun zata tashi,
daker ta iya buÉ—e idonta tana kallon shi sunyi jawur dasu ga bacci ga yunwa, junaid yace "reesh kamar baki lafiya fa? Look at ur eyes fa sun janza kala,
A kasalance tace "yunwa nake ji sosai banci komai ba tunda naje school, ga wani wahalallan bacci da nake ji," ta ƙarasa maganar tana faman yin hamma, har time ɗin suna acikin motar,
Tun da tasoma magana junaid ya saki baki yana kallonta har sai da takai ƙarshen maganarta sannan yace "Kina nufin wai baki ci komai ba a school to saboda me? Ya tambaya yana kallonta
Yamutsa fuska tayi tare da cewa "junaid ban fa da ko sisi balle na sayi abinci, shiya sanya,"
Wani irin kallo junaid ke bin ta dashi kallon na tausaya maki, ga takaicin daya hanasa yin magana,jin yayi shiru yasa ta cewa "ka tashi mu shiga ciki, kuma naga kana kallonta,"
A ƙule yace "Haushi kika ban ne,shiyasa nagaza magana, reesh waya ce maki sai kin biya kuɗi zaki ci abinci? An fa riga anbiya kuɗin komai na school ɗinki, tun daga school fees har kuɗin abincin ki dana school bus da zaki dunga hawa har na tsawon 3 months fa,"
Jin haka yasa sehrish zaro ido waje baki asake tana mamakin ashe itace shashashar batasani ba ta hana kan ta cin haƙƙinta, ashe an biya kuɗin komai ita kanta takaicin ne yasa ta yin kasaƙai,
Fitowa sukayi daga motar atare suka shige cikin gidan a babban falon suka rabu ta wuce bedroom É—inta shi kuma ya wuce upstairs É—akinsa, babu kowa acikin gidan abunda ya É—aure mata kai,
tana shiga ciki tayi wurgi da school bag É—in sannan tashiga tu6e uniform É—in suma duk nan tayi watsi dasu saman gadonta, bayan ta kammala ya rage daga ita sai half vest da gajeran wando, toilet tashige shaf shaf tayi wanka tare da É—auro alwala tafito, cikin hanzari ta buÉ—e wardrobe É—inta ta zumbula doguwar riga, sannan ta zura hijabi tare da shimfiÉ—a darduma ta kabbara sallar, tana kammala sallar ko addu'a bata tsaya yi ba, ta haye saman gadonta ta baje tashiga sharar bacci maganar yunwa kuma wata'kil saita tashi sannan tashiga neman abinci,
Turo ƙopar Azmee tayi ta sameta tana ta jan minshari bin ko'ina tayi da kallo ganin yarda tayi wurgi da school bag ɗinta ga uniform ɗinta data watsar saman gadon, murmushi kawai tayi tare da girgiza kai tace "ƴan makaranta kenan, tun yau anfara wurgi da shool bag ga uniform a watse saman gadon maimakon ta ninke su," ta faɗi da murmushi a fuskarta sannan taja mata ƙopar ta fuce,
ta jima tana bacci sai wuraren sallar la'asar sannan tafarka da wata irin matsiyaciyar yunwa ba arziƙi ta fito ta wuce kitchen, har time ɗin babu kowa, roƙon da take yi Allah yasa babban yaya ba us suka koma ba,
Acikin tray ta haÉ—a abincinta sannan ta zauna a kitchen É—in tana ci tana tunanin duniya,'
**********Twins***************
Duk yinin ranar ba inda suka je saboda tashin hankali sam sun rasa inda zasu tsoma ransu, tun da sanyin safiya bayan sun dawo daga sallar asuba, haroon ya faɗo masu ɗaki domin ya ƙara jaddada masu akan buƙatun daya nema a wurinsa, Jahan ya tsawatar masa akan cewa ko nawa yake so zasu bashi amma kada ya sake yayi kuskuren cewa zai ƙara kusantar ɗaya daga cikinsu, da jin wannan maganar sai haroon yace ya amince amma bisa sharaɗin cewa zasu ƙara mashi miliyan 80 in har suna son ya daina bibiyarsu Kuma cikin sati guda kacal ya basu in ba haka ba zai tona masu asiri 😥😳
tun safe basu ci komai ba, ko fitowa ba suyi ba daga bedroom ɗinsh, kuma babu wanda ya lura da hakan illa junaid da yayi ta tambayarsu har ɗakinsu sai da yazo yayi ta faman knocking yana kiran sunan su, suna jin shi tamkar zasu yi kuka amma basu amsa mashi ba,ƙarshe yayi tunanin cewa basa nan yayi tafiyarsa,
Ayaaan ya sha kuka aduk lokacin daya tuna abunda ya faru dasu daren jiya sai yayi yunƙurin amai, yanzu haka ma yana zaune gefen gadon idonsa jawur ya ɗago ya kalli jahan dake ta faman safa da marwa acikin ɗakin yace "Dan Allah jahan mu hanzarta mu sama mashi kuɗin daya buƙata, if not wlh so yake ya kashe mana rayuwa," ya faɗi yana faman matse hancinsa da yayi jawur saboda matsar daya sha da hannunsa,
Jahan ya dubesa cikin damuwa tare da cewa "Ayaan bansan ya zanyi ba ! Wa zan fara tunkara game da kuɗin nan? duk wanda zamu tambaya acikin brothers ɗin mu ko Abban mu dole sai sunji me zamuyi dasu kafin su bamu, daga baya ma zasu tambaye mu ina abunda muka siya dasu, don haka Mommy ce kawai nake tunanin zata iya bamu kuɗin amma matsalar shine tana fushi da mu saboda bama kiranta a waya muna gaishe ta," Jahan ya ƙarasa maganar tare da samun wuri ya zauna kusa da Ayaan ɗin,
"Jahan mom ita kaÉ—ai ce solution, mu jaraba kiranta kawai mu sanar mata mu ji mai zata ce,"
"Video call zamu kira ta, may be tafi tausaya mana in taga yanayin mu" Acewar jahan, yayi maganar tare da miƙewa ya ɗauko laptop ɗinsu dake ajiye saman drawer ɗinsu, komawa yayi ya zauna dab da Ayaan sannan ya zaro wayarshi tare da buɗe laptop ɗin, duk ayaan na zaune zugudun yana jiransa ya kira,
zama su kayi suka ƙurama screen na laptop ɗin ido suna jiran mommyn nasu ta ɗaga kiran cikin sa'a ta ɗaga masu kiran, har haɗa baki suke yi wurin cewa "Mommy," tana zaune cikin haɗaɗɗen garden saman gujera hannunta ɗauke da cup na coffee da alama sha takeyi, ta jima tana kallonsu sai daga bisani tace "sai yau kuka ga damar kira na"?
"Sorry mom ba haka bane.....," suka faɗi atare, girgiza kai alexandra tayi tare da cewa "to menene? halan wani abu ku ke buƙata shiyasa kuka kira ni"?
Shiru su kayi suna kallonta ba bakin magana, tsoki taja tare da cewa "if u can't talk to me, i will reject the call right now"!
Cikin sauri jahan yace "pls mommy don't reject the call, zamu yi magana, pls Ayaan kayi mata bayani" ya faÉ—i yana kallon Ayaan shima murya tamkar zaiyi kuka yace "Jahan i don't know what to say, kai kayi mata bayani pls," mamaki ne ya kama Alexandra ganin yadda suke ta jayayya akan wanda zaiyi mata bayanin dangane da kiran da sukayi mata,
tsawa ta daka masu tare da cewa "bana son shiriri James! kuyi mun bayanin kiran da kuka yi mun within 5 mins if not zan kashe kiran "
Natsuwa su kayi gaba É—ayan su sannan jahan ya soma cewa "Mom dama.....um......kuÉ—ine...muke....so...awurin ki, ki bamu,"
tana jin haka ta fashe da dariya hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba jin yarda mommyn nasu ke 6a66aka dariya,
Ayaan yace "mom why are u laughing pls, don Allah ki tausaya mana mommy muna cikin wani hali ni da Jahan....' dakatawa tayi sannan ta soma magana anatse "Har nawa ne kuÉ—in"?
Jahan yace "80million,"
É—an zaro ido tayi tare da cewa "har 80m? what are going to do with it?
Ayaan yace "mom dan Allah kada ki tambaye mu me zamuyi dasu, saboda ba zamu iya yi maki ƙarya ba, kawai ki taimaka ki ba mu,"
Murmushi ta ɗan saki tana kallonsu na wani lokacin kafin tace "Ni a wuri na miliyan tamanin tamkar naira tamanin take, naji zan taimaka na baku amma bi sa sharaɗi ɗaya"! Har sun fara sakin fara'a amma jin maganarta ta ƙarshe yasa su dakatawa da murna,
Jiki asanyaye Jahan yace "what mom"?
alexandra tace "Inaso ku sa ROMEO ya kira ni a waya, sannan ya kira ni da sunan mommynsa Kuma ya bani haƙura na bijire mun da yake yi, kiran yakasance video call ne, in har ku ka sa romeo ya amince ya kira ni awaya,i promise to give each one of u 50 50millions,' tayi maganar tare da jaddada musu,
Zaro ido suka yi gaba ɗayansu ga samu ga rashi, domin kuwa sunsan cewa Junaid bazai ta6a kiran mahaifiyarsu ba harya bata haƙuri kuma ya kirata da sunan mommynsu tabɗijancan,
gaba É—aya sun tafi zurfin tunani suka ji tace "i will be waiting to hear from u guys," tana faÉ—in hakan ta kashe video call É—in,
Hannu ayaan yasa ya rufe laptop din sannan ya kalli jahan wanda shima kallonsa yake yi yace "Yanzu ya zamuyi jahan? ga samu ga rashi ! duk da nasan junaid yana son mu sosai kuma yana yi mana biyayya zai iya yi mana komai amma banda wannan ALFARMAR,
zugudum su kayi cikin tsananin tashin hankali da kuma tunanin yarda zasu tunkari junaid da maganar! 😥
***********JAHAD***********"**
a hankali ta soma buɗe idanunta biji² ta dunga gani a idonta, daker take motsa su zata buɗe su, sai faman ambaton sunan Allah take yi a hankali,
lokacin da taƙarasa buɗe idanun nata mamaki ne ya kamata ganin ta kwance a wani ɗaki, komai na cikinsa fari ƙal a tsaftace, ga mutanen dake tsaye akanta farare fat hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, gaba ɗaya ranta ya bata cewa mutuwa tayi ne, saboda yanayin wurin da ta gani fari ga mutanen dake tsaye akanta farare, hawaye ne suka soma zubo mata a idanunta cikin kuka take cewa "Ya Allah kasa ba mutu nayi ba,nabar hussana aduniya wurin wancan fasiƙin mutumin, nashiga uku wa zai taimake ta acan, meyasa mutuwa bata ɗauke mu, mu biyu ba atare? Sai ta ɗauke ni nikaɗae tabar hussana a waccen duniyar mai cike da ruɗani," gaba ɗaya jahad ta fashe musu da kuka, Hankalin nurse ɗin dake tsaye da likitan ba ƙaramin tashi yayi ba, cikin sauri su kayi kanta, ko da jahad tagansu sai ta ƙara sautin kukan tana cewa "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un,! dan Allah su wanene ku farare haka, ina hussana take,
zama nurse É—in tayi daga gefenta sannan tace "Sannu da jiki Æ´ar uwata, ni ce nurse É—in dake kula da ku, sunana Camila ke fa"?
Jin tayi mata magana raÉ—au da hausa yasa jahad dawowa cikin hayyacinta sosai tana kallonta da mamaki, kana kallonta ka ga english woman, Cos majority na ma'aikatan asibin sgr daga u.s suke, wasu daga india, wasu kuma Æ´an nan nigeria, akwai kwararrun likitoci da nurses acikin asibitin,
ƴunƙurawa jahad tayi zata tashi cikin sauri Camila tasa hannu tare da mayar da jahad kwance tace "Ana miki ƙarin jini ne, ko baki lura ba ne"? ta faɗi tana kallonta da murmushi a fuskarta,
ɗan juyawa jahad tayi ta kalli ledar ƙarin jinin da akeyi mata,
sassauta muryarta tayi sannan tace "sister dan Allah ina ne nan? Kuma waya kawo ni nan?
Murmushi Camila tayi sannan tace "nan asibiti ne, sannan yayanki ne ya kawo ki domin mu baki kyakkyawar kulawa!"
Cikin mamaki jahad tace "Yayana kuma? ae ni bani da kowa aduniyar nan Æ´ar uwata ce kawai hussana nasani, dan Allah tana ina"? tayi maganar tana jiran amsa,
duk tattaunawar da suke yi dr Emran na tsaye yana jin su , kafin Camila ta buÉ—e baki tace wani abu sai ga MARSHAL OMAR ya shigo É—akin shida Major, gaisawa su kayi da dr emran, sannan ya matsa wurin da jahad ke kwance,
tsayawa yayi yana kallonta fuskarshi asake saboda ganin yarda ta wartsake alamar tasamu kyakkwar kulawa awurin Nurse É—in,
Sam jahad bata lura da marshal omar ba dake atsaye har sai da ya ambaci sunanta "JAHAD,"
A razane ta wurga kwayar idonta akan shi, ganin Ya Omar É—insu yasa ta zabura zata tashi zaune da sauri Camila ta mayar da ita, duk tabi ta zazzare idonta tana nuna shi da hannu tana ambaton sunan shi cikin tsananin mamaki,
tashi Camila tayi taba Omar wuri donya zauna kusa da jahad saboda ta lura yarinyar nason magana dashi,
Zama Omar yayi saman chair ɗin dake facing medical bed ɗin da jahad ke kwance asama sannan yace "Ya jikin naki"? tana jin haka ta fashe da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita, hannunta tasa ta ruƙe hannunsa tana cewa "Ya Omar ina ka shiga tsawan kwanaki kabar mu, bakasan halin da muke ciki ba..........' tana magana muryarta na shasshaƙewa saboda kukan da take, sam Omar ya gaza cewa komai tuni idonsa sun cicciko da kwalla,
Jahad taci gaba da cewa "Ya Omar har yanzu nagaza yarda cewa kaine! dan Allah kayi mun magana taya akai haka tafaru ya omar, kuma ina hossana take? mutumin nan ya gudu da ita ya omar..........." kasa ƙarasa maganar tayi saboda hannunsa daya sanya ya rufe mata bakinta........................................Bin idanunta yayi da kallo itama tana kallon nashi hawaye ne cike taf da idonta, bai janye hannunsa daga bakinta ba har sai da ya tabbatar cewa ta samu natsuwa sannan ya zame hannunsa yace "Jahad duk wani abu dake faruwa ni bansani ba,bani da masaniya akai,jiya ne aka turomin saƙo da privet number bansan ko wanene be,let me show the message,
Hannu yasa ya curo wayarsa daga trouser pocket ɗinsa kunna wayar yayi sannan ya shiga wurin messages ya buɗe saƙon ya nuna ma jahad don ta gani,
Zuba ma screen É—in wayar tayi da ido tana karantawa kamar haka
_"Omar ka yi ganganci daka bar rayuwar yaran nan a hannun Laila, ina baka shawarar ka hanzarta zuwa ka É—auko su, saboda naji cewa gobe goben nan za'a fitar dasu daga gidan_"
Janye wayar yayi sannan yace"lokacin da message ɗin ya shigo mun bana cikin natsuwa ta, saboda mun shiga tashin hankali,ƙanne na da aka tura aiki miyagu suka farmake su, mun samu nasarar ceto rayuwarsu kuma mun kama wasu daga cikin waɗanda suka farmake sun, yanzu haka da nake maki magana ɗaya daga cikinsu yana kwance a A&E ward, baisan inda kansa yake ba,saboda sai da suka banka mashi kayan miyagun ƙwayoyi sannan suka azabtar dashi, ba don Allah yasa an samu wani daga cikinsu ba yayi mana waya da shikenan ba'asan mai zai biyo baya ba,
Shiru Omar ya ɗanyi na wani lokaci kafin yaci gaba da cewa "tun shekaran jiya da muka fita daga gida muna can wurin cetonsu,a asibitin nan aka kwantar da waɗanda suka raunata sosai daga cikinsu,gaba ɗayan mu babu wanda ya samu runtsawa adaren jiya saboda tashin hankalin kada mu rasa su,kuma a daren jiyan ne acikin asibitin nan saƙon ya shigo mun,duk nabi na rikice saboda narasa yarda zanyi, Major shine babban na hannun dama na, shi na kira na nuna mashi saƙon da aka turomin game daku, koda ya gani sai cewa yayi dama ya jima yana son ce mun wani abu, amma ba zai iya sanar dani ba saboda bayason shiga tsakanina da matar yayana, sai abun ya ɗaure mun kai jin abunda yace,a lokacin ban matsa masa ba akan son sanin wani abu ne yake son sanar dani ba,a time ɗin duk da halin da nake ciki burina kawai inzo in ganku, Major shine yace nabar masa komai a hannunsa kar na damu, sai a washe gari major ya sanar dani cewa mu shirya mu tafi, sannan kuma yaban wata number yace mu bi diddiginta, atare dashi muka fito mu biyu kawai muka miƙi hanya, da wayata nayi amfani wurin bindiddigin numbar daya bani har muka ƙaraso titin da dajin nan yake,mu ka shiga cikinsa kai tsaye, muna cikin tafiya naji an kwala mun kira ta waje "yalla6ai," cikin sauri na zuge glass ɗin motar don naga wanene, shine naga wani saurayi zuƙunne a ƙasa, ga ki kuma kwance a sume duk jini a goshin ki, hankali atashe na zabura zan fito daga cikin motar, kawai sai saurayin nan yace "yalla6ai ya gudu da ɗayar acikin motarsa, gashi can ya miƙi hanyar da tayi dama don Allah ku ceto rayuwarta, " jin haka yasa gaba ɗaya na rikice, cikin sauri major yaja motar mu da gudun gaske muka bi motar wannan tsohon mutumin da gudun gaske har cikin gidan gonarsa, ina shiga najiyo kukan hossana hankalina ba ƙaramin tashi yayi ba, tuni na makance na afka ma ƙopar ɗakin gidan gonar na tarwatsa ta, ina shiga naga hossana a lokacin har yayi nasarar yage mata rigarta ya ruƙe ta a hannunsa, raina yayi mugun 6aci abunda ya hanani yin motsi a lokacin saboda bansan wane irin hukunci zan yanke masa ba,yanzu haka da nake baki labarin nan babu wannan tsohon a duniyar nan saboda na kashe shi,kuma na ɗauko hoton gawarsa don na nuna ma hossana,"
Wani irin murmushi jahad ta saki har ta gaza rufe bakinta don murna,shima Omar É—in murmushi yakeyi yana kallonta,
Nasan dayawa za suyi mamakin yarda akai hakan ta kasance,abun da ya faru shine cikin sojojin dake gadin gidan general ishaq akwai wani matashi Abokin major ne, a lokacin da suka kawo su hussana da jahad gidan Omar ya shiga tare da su ciki , A nan major suka haÉ—e da wannan saurayin abokinsa ne tun suna yara ,sunan Shi Osman bayan sun gaisa Osman ke cewa "Abokina waÉ—ancan yaran fa? dana ga ka shiga ciki dasu Æ´a'yan wanene? ko dai ogan naku ne yayi aure matar ta haihuwa,
Dariya Major yayi tare da cewa "Wai dama Osman har yanzu kana nan da shegen sa idon nan naka? Haba no wonder shiyasa Allah yabarka a matsayin mai gadi, in banda abun ka ina ogan mu yakai shekarun da zai iya ajiye ƴa'ƴa kamar waɗancan? shima fa ba wani babba bane duka shekarunsa bazasu wuce 28 years, matsayi ne kawai Allah ya bashi," jin haka yasa osman ɗan zaro ido tare da cewa "ka ce ashe shima ɗan shila ne, amma dan Allah tun yaushe nake ta fama dakai ka taimaka ka sama mun aiki a ƙarƙashinsa amma ka ƙiya, kafi son kaita ganina a matsayin mai gadin gidan genar, kalli fa yarda na rame nayi baƙi, kai kuwa har wani tumbi kafara ajiyewa saboda jin daɗin rayuwa, wlh abota bata ce haka ba," ya faɗi yana tsuke fuska, dafa kafaɗarsa Major yayi tare da cewa "Ina sane da wannan Osman, kuma insha Allah zanyi ƙoƙari na sama maka gurbi a kusa dashi, mutumin kirki ne sosai yana da sauƙin kai kuma ina jin daɗin aikin dashi,yana kyautatamun domin kuwa kafin ƙarshen wata yayi ina samun ninkin ba ninkin abunda nake samu a albashina wurinsa," jinjina kai Osaman yayi zugudun yayi masa fuskar tausayi kafin yace "Kaji daɗi mutumina,ni dai zan jira naji daga wurinka don Allah karka manta kasa ma mun kusanci dashi, nima na dangwali arxiki,"
Major yace"baka da damuwa, yanzu ma haka ga wani aiki ka samu, waɗancan yaran da kake gani ogan mu yana sonsu sosai, bashi da alaƙar komai dasu hasalima a asibiti ya taimake su,ya kawo su nan ne domin su zauna tare da matar yayansa ishaq, to ni hakan bai kwanta mun araina ba, shi ne nakeso ka sanya mun ido akansu! ka zama tamkar ɗan leƙen asiri duk da nasan hakan ya sa6ama dokar aikin ku amma inaso kayimun wannan Osman,ka lura da duk wani motsinsu acikin gidan nan, so nake kayi aiki tamkar jami'in sirri! dalilin dayasa nayi hakan saboda bana son duk wani abu da zai cutar dasu don na lura da yadda ogan mu ke tsananin ƙaunar yaran,ni kuma bana son duk wani abu da zai 6ata masa rai, ta6a yaran nan tamkar ta6a masa zuciya ne," ya ƙarasa maganar yana kallon osaman da yayi kasaƙai, daga bisani yace "Na amince zanyi hakan, amma wlh ka sani duk ranar da asirina ya tonu, sunanka na ciki ! don ba zan shiga haɗari ni kaɗai ba,"
dariya major yayi sannan yace"Ai ni babu wanda ya isa ya ta6ani muddin ina tare da Marshal, don haka kaima ka kwantar da hankalinka, ba abunda zai same ka face alkhairi,tunda ka amince zaka yi É—in, inaso duk wani hali da suke ciki ka tabbatar da ka kira wayata ka sanar mun,"
Osman ya amsa masa da "toh," daga nan su kayi sallama, a lokacin marshal Omar ya fito daga cikin gidan jikinsa asanyaye suka shiga cikin mota su ka tafi,
tun daga wannan lokacin Osman ya zaman ɗan leƙen asiri duk wani hali da su hossana ke ciki yana sane dashi kaf, kuma duk rana yana kiran major ya sanar dashi halin da suke ciki, Major bai ta6a sanar da marshal Omar ba, saboda gudun karya shiga tsakanin shi da matar yayansa ishaq,kullum yana sanar da osman cewa yaci gaba da sa musu ido,
Idan har masu karatu zasu iya tunawa akwai lokacin da Aunty babba tayima su hussana da jahad bugun mutuwar nan, har suka kaisu asibiti bayan sun dawo suka shige cikin gida ita da hafsat suka bar jahad tsaye gaban motar tana kuka saboda hossana na'a cikin motar kwance rai hannun Allah gashi bata iya ɗaukarta bare tashiga da ita cikin gidan, a lokacin idan zaku tuna akwai wani soja daya zo yana tambayarta meke faruwane, take ce masa ƴar uwartace acikin motar kwance bata lafiya kuma bazata iya ɗaukarta ba, sai sojan yace maza "Can i help," take ce masa eh, yasa hannu ya ɗauki hossana ya shigar mata da ita ciki, ya kwantar da ita saman doguwar kujera, yayin da jahad tabisu, to wannan sojan ba kowa bane face Osman abokin major ɗan leƙen asirinsa, ko lokacin da zai fita daga falon bayan ya kwantar da hossana sai da ya ɗan tsaya daga bakin ƙopar ya juyo yana kallon jahad dake zukunne saman guiwarta agaban hossana tana yi mata addu'a tana kuka, jinjina kansa yayi tare da fuce wa bayan yafita, ya ɗauko wayarsa tare da buga ma major kira, bayan ya ɗaga kiran yake sanar dashi abunda ke faruwa, nace wa shifa yana zargin cewa Matar ishaq tayima yaran mugun bugu har ma ɗaya daga cikinsu ta jigita sosai tamkar ba zata rayuwa,don haka ya hanzarta sanar da ogansu Omar yazo ya kwashi yaran tunkan ta kashe su, har lokacin major bai sanar da Omar ba game da wannan ma, saboda yana tunanin koya faɗi masa daker ya yarda kuma yasan makircin mata, abun zai iya dawowa kansa,
tun fa lokacin da su jahad da hossana ke wanki abayan gidan ita da jahad, Osman yake ganinsu sai yazo ya gifta ta wurinsu tamkar yana yin waya alhalin su yake kallo, har video yake yi masu yana turawa major donya gani," Major ya tsorata da ganin irin uƙubar da yaran suke sha,
Bayan wannan lokacin kuma sai salon ya canza, duk osman na zuba ido yana kallon ikon Allah yarda hafsat ke nuna ma yaran soyayya, aduk lokacin da hafsat ta fita dasu cikin motarta, sai osman ya bisu da machine É—insa dom yaga ina zata dasu, dashi suke yin yawo abayansu batare da sun sani ba, duk inda zasu osman na biye dasu a sirrince,
daya kira Major ya sanar dashi abunda ke faru na cewa yaran fa yanzu suna samun kulawa sosai a wurin mutanen gidan, sai major yace mashi "Wannan salon da suka canza,alama ce dake nuni da cewa sun kusa salwantar da yaran,ina da tabbacin cewa so suke su zubar dasu kaci gaba dasa musu ido,daga yanzu banaso ko bacci ka dunga yi osman, saboda wannan lokacin ne mafi haɗari, aduk lokacin da maƙiyin ka ya canza maka salo na soyayya to kaji tsoransa halakar dakai zaiyi,"
Tun daga lokacin da Major ya sanar dashi haka, bawan Allah osman bai ƙara yin bacci ba, koda bashi ke akan duty ba, yana nan yana lura da shige da ficen da hafsat keyi dasu hossana,
A ranar da baba alamu zai tafi dasu hossana, akan idon osman Aunty babba ta fito tare dasu jahad da hossana,ta buɗe masu motar hafsat suka shiga, duk yana kallonsu, daga bisani kuma sai yaga hafsat tafito hannunta ɗauke da trolley hakan na nufin wani ne zaiyi balaguro, bayan hafsat ta shiga cikin motar taja motar tafito dasu daga cikin gidan, cikin sauri osman ya hau mashine ɗinsa da yake ajiyesa acikin gidan yabi bayansu a hankali yake tuƙa mashin ɗin don kar su ganshi, da hafsat ta tsayar da motar abakin titi tana jiran ƙarasowar baba alamu, sai osman ya dakata da tukin mashin ɗinsa, cikin sauri ya sauka tare da samun wuri ya cire rigar jikinsa ta kakin sojoji ya 6oyeta a ƙarƙashin wani benci dake agaban wani shago dake rufe, sannan ya tu6e wandon jikinsa ma, ya ajiyesa a ƙarkashin bencin bakomai yasa shi yin hakan ba face don karsu ganshi da kakin sojoji yana binsu, Asirin shi zaiyi saurin tonuwa ne,
Sai daya rage daga shi sai farar shirt da gajeran wando ajikinsa a lokacin motar baba alamu taƙaraso,cikin sauri Osman ya zuƙunna agaban mashin ɗin tamkar ya samu matsala yana gyaransa, alhalin nan duk salon dabaru ne na jami'ae,
yana gyaran mashin ɗin yana satar kallonsu, akan idonshi hafsat ta buɗe ma jahad da hossana mota suka fito sannan ta ɗauko masu trolley ɗinsu da food basket ɗinsu ta basu,bayan hafsat ta tafi, baba alamu ya amshi akwatin Su hossana da jahad ya wurga cikin boot ɗin motarsa, daga nan jahad da hossana suka shiga cikin motar, shima ya shiga tare da tashin motar suka tafi, cikin sauri Osman ya haye mashin ɗinsa tare da tashinsa yabi bayan motar baba alamu da gudun gaske amma bai bari ya ƙurewa motarsa ba kasancewar Motar baba alamu glass ɗin jikinta duk ya fashe, muddin osaman ya ƙurewa motar tofa zasu iya hango shi, hakan yasa ya basu tazara sosai, yana cikin tuƙin mashin ɗin ya ɗan jinkirta tare da zura hannu cikin aljihun wandonsa ya zaro wayarsa tare da bugama major kira, bayan ya ɗaga yake sanar dashi duk abunda ke faruwa,
Hankali tashe major yace "Osman kada ka bari ya kubce maka, kaci gaba da bin motarsa, sannan kabar wayarka a kunne zamu biyo diddigin layinka, mu zo inda kuke," bayan osman ya amsa masa, ya mayar da wayar, sannan ya ƙara ma mashin ɗinsa gudu, a lokacin da motar baba alamu tashiga dajin da gudun gaske, jahad na ƙoƙarin fitowa tana ihu bayan ta samu ta harba murfin motar ya buɗe, sai baba alamu ya girgiza motar da mugunta, ta faɗo ƙasa timmmm goshinta ya bugu, ta taso da gudu tana bin motar tana kiran sunan hossana daga bisani ta yanke jiki ta faɗi, adai-dai lokacin shi kuma osman ya ƙaraso ba komai yasa shi yin jinkiri ba fa ce wayar da yayi da major shiyasa bai ƙaraso akan lokaci ba har baba alamu ya kubce mashi,
ganin jahad da yayi yashe a ƙasa ta sume ga jini, ba ƙaramin razana yayi ba, cikin hanzari yayi wurgi da mashin ɗinsa ya nufe ta hankali atashe, ya zuƙunna gabanta yana faɗin "ke!ke!! tashi ki tashi dan Allah, kada ki mutu,"
Adai-dai lokacin kuma motarsu Marshal Omar ta faso cikin dajin ta hanyar tracking layin osman da sukayi yasa har suka ci nasarar cimma inda yake,
Osman na ganin motarsu Marshal yasan cewa sune aciki, a lokacin omar ya zuge glass ɗin motar a tsorace ganin jahad kwance duk jini a goshinta, harya harzuƙa zai fito daga cikin motar, cikin sauri Osman yace "yalla6ai ya gudu da ɗayar, gashi can ya miƙi hanyar dama da ita, don Allah ku ceci rayuwarta," jin haka yasa Omar fasa fitowa daga cikin motar, cikin sauri major yaja motar da gudun gaske suka bi motar baba alamu a lokacin ya ɗanyi masu nisa, hayaƙin da bayan motar baba alamu ke fitarwa shine yasa suka gane hanyar da yabi,
suna isa basu tsaya buɗe kopar katakon gidan gonar ba, kai tsaye major yabi ta ƙopar atsiyace ya tarwatsa katakon gidan gonar suka shige,
Tamkar zaki haka omar ya fito daga cikin motar ya afkawa É—akin da baba alamu ya shige da hossana,
*Wannan shine abunda ya faru taƙaice kenan*
"Ya omar ina hossana take ita'? Omar yace"hossana tana cikin ƙoshin lafiya, itama ƙarin jini akeyi mata, yanzu haka bacci take sha tana a kusa da ɗakin nan," ajiyar zuciya jahad ta saki kafin ta kuma cewa "ya omar kullum hossana saita ambaci sunanka, komai akayi sai tace "ya Omar fa," ita bata son rabuwa da yaya omar ɗinta,"
Murmushi Omar ya saki jin abunda jahad tace,
"Amma ya Omar ba zaka ƙara rabuwa damu ba ko? dan Allah kada ka haɗamu da kowa kabarmu kawai a wurin ka, kai kaɗai ke son mu," tayi maganar idonta akansa tana jiran amsar shi,
Omar yace "ko wancan time ɗin bada son raina nabar ku ba, jahad you're always in my mind ina jin ku araina,amma yanzu komai ya wuce just forget about the past, ku ƙaddara cewa wani abu bai ta6a faruwa da rayuwarku ba na ƙunci, saboda yaya omar ɗinku ya shirya maku kyakkyawar rayuwa ta jin daɗi da walwala, masarauta ce wadda ku kaɗai zaku mulketa sai yadda kuka ga dama zakuyi acikinta, hatta yaya omar ɗinku zai zama tamkar bawa agare ku,"
dariya kawai jahad ke faman tiƙa saboda murnar jin abunda omar ke cewa, hatta dr Emran da Camila dake tsaye murmushi kawai suke saki, shima major dake tsaye daga ƙopar ɗakin murmushi ne a fuskarsa, ƙarasa shigowa ciki yayi yana cewa "Sir idan ba damuwa inaso a bani muƙami acikin masarautar nan, zanso na zama sojan dake kula da princesss ɗin dake acikinta, bama ni kaɗai ba ga abokina osman nan shima yana roƙon gimbiya jahad da ta bashi damar zama ɗaya daga cikin masu kula dasu,"
Abun sai ya zama tamkar shirin wasan kwaikwayo gaba ɗayansu dariya ce a fuskarsu, hakan ba ƙaramin farantawa omar rai yayi ba ganin yadda jahad ke faman tiƙar dariya, sai yaji sanyi aransa sam ya gaza janye idonsa akanta,
Muryar Camila (kameela) ce ta katse su da cewa "Yalla6ai nima idan ba damuwa ina neman alfarmar zama É—aya daga cikin masu yi ma gimbiya jahad hidima, ko da a matsayin jakadiya ne mafi kusanci dasu,"
Fashewa da dariya jahad ta ƙara yi daga kwancen da take har omar na cewa "Bi a sannu my baby, kada ki shaƙe,"
gaba É—ayansu sun natsu sai raha akeyi, suka ji Muryar hosana kamar daga sama tace"YA OMAR,"
Atare suka juya suna kallonta, tsaye take a bakin ƙopar ɗakin daker take buɗe idanunta tana kallonsu, hannu tasa ta murza idonta sannan ta ƙara buɗe su da kyau donta tabbatar da abunda idonta ke gane mata, tabbas kuwa shine wato yaya Omar ɗinta,
tsananin farin ciki ne yasa hossana ƙarasa shigewa ciki da gudun gaske tana isa inda Omar yake ta zube saman guiwowinta tare da kifa kanta asaman laps ɗinsa tana kuka,
Shiru su kayi gaba ɗayansu na wani lokaci suna sauraren kukan da hossana ke yi, gaba ɗaya jikin omar ya gama mutuwa saboda yasan yarda yarinyar ke tsananin ƙaunarsa dole tayi kewarsa, hannu omar yasa tare da shafa gashin kan hossana cikin muryar lallashi yace "Am so sorry hossana,nasan nayi laifi ban ma san da wane baki zan iya baki haƙuri ba,"
Maimakon ta É—ago sai ta daddage ta gartsa mashi ciwo a laps É—insa, runtse ido omar yayi saboda yaji zafin cizon, babu wanda ya lura da abunda ke faruwa sai jahad, tun da taga omar ya runtse ido tasan cewa Hossana Cizon shi tayi,
tayi mashi hakan ne don yasan irin raɗaɗin da suka ji acikin zuciyoyinsu na ƙin zuwan da yayi ya tafi dasu,
buɗe idonsa yayi a hankali yana sauke ajiyar zuciya ya kalle ta, a lokacin itama ta ɗago tana faman huci ta ɗaure masa fuska tare da haɗe masa girar ƙasa da sama tana kallon shi,
Cikin sanyin murya ya sake maimaita "Am sorry again," ya furta tare da kai hannunsa a fuskarta yana share mata hawayenta dake kwaranyowa daga idonta,
Cikin kuka tace "Ya omar yanzu ka kyauta abunda kayi mana? ka tafi kabarmu cikin tashin hankali ko waiwayon mu, ba kayi ba yanzu da mun mutu shikenan bazan sake ganin Ka ba sai dai a lahira ko?
Æ´ar dariya omar yayi tare da cewa "Amma ae yanzun baku mutu ba ko? Kuna raye kuma ga yaya Omar É—inku atare daku, mai yayi saura yanzu"? ya tambaya yana kallonta
Hossana tace "sai ka kaimu gidan ku inda kake rayuwa, don wlh duk inda zaka je, ƙafarka ƙafarmu, mu da kai mutu ka raba takalmin kaza," ta ƙare maganar tana zumbura baki,
Gaba É—ayansu na cikin É—akin dariya kawai suke yi, Kallon dr emran omar yayi kafin yace "yanzu mai ya rage dr?yaushe kake tunanin za'a sallame su, in yaso sai acigaba da basu kulawa acan gida?
dr emran yace "zuwa night, ae jikinsu yayi ƙarfi yanzu saboda ƙarin jinin da akayi masu, idan ma ba damuwa Camila zata iya cigaba da kula da lafiyarsu, in har kana buƙatar hakan, tunda dama naji tace tana son zama hadimar princess ɗin naka,"
Murmushi suka saki gaba É—ayansu banda hossana don batasan zancen ba, tuni ta mayar da kanta akan laps dinsa tana faman sauke ajiyar zuciya,
dukkan tsanani yana tare da sauÆ™i, mahaÆ™urci kuma mawadaci ne wata rana, babu wani yanayi na rayuwa da yake kasance wa na dundundun, Innallaha ma'assabirin tabbas wannan haka yake, iya haÆ™uri dae su hossana sunyi kuma sun jurema duk wata jarabawa da suka fuskanta na Æ™uncin rayuwa, basu fasa yin addu'a ba suna kai kukan su ga Allah ba kuma basu fidda rai da cewa Allah zai kawo masu É—auki ba, idan muka sa haÆ™uri kowa zai cimma nasara, gashi yanzu zamu iya cewa Masha Allah ðŸ˜ðŸ‘‘
**************Twins *******************
daker suka samu suka yi wanka suka canza kaya izuwa jeans da t-shirt suka fito wuraren ƙarfe 5 na yamma, tafiya suke yi gabansu na faduwa tsoransu kar suci karo da haroon don yanzu ya zamar masu tamkar dodo, suna cikin tafiya sai ga Junaid ya fito daga upstairs yana ganinsu ya ɗan zaro ido cike da murna yace "Yaya Jahan ina kuka shiga inata neman ku, naga da safe ko breakfast ba kuyi ba, duk na shiga damuwa," ya yi maganar tare da ƙarasa saukowa down ɗin yayi ya tunkaresu, suna tsaye baki asake suna kallon shi saboda neman shi suke yi ruwa a jallo,
yana ƙarasawa yabi su ɗaya bayan ɗaya yayi hugging ɗinsu tare da manna musu kiss a gefen fuskarsu, irin gaisuwar da suka saba,
Ganin sun zuba mashi ido batare da sunyi mashi magana ba yasa shi bubbuga ƙafarsa tare da cewa "Dan Allah wai menene haka duk kun Canzamin, ko magana ma ba zaku iya yi mun ba why pls? ya faɗi tamkar zaiyi kuka,
gyaran murya jahan yayi tare da cewa "no ba haka bane junaid, ba mu jin daÉ—i ne, ni da Ayaan shiyasa ka ganmu a haka, yanzu haka ma kai muka fito nema akwai maganar da muke son yi dakai, amma ba'a nan ba, acikin É—akin ka,"
junaid yace "magana kuma dani? Allah yasa ba laifi nayi ba"
Murmushi Ayaan ya saki tare da cewa "ba laifi kayi mana ba junaid taimako ne ma zakayi mana,"
ruƙe ƙugunsa yayi sannan yace "Naji toh, amma kafin nan sai naga kun ci abinci tukunna, saboda baku ci komai ba tun safe ina sane da hakan, bayan na hana ku zama da yunwa,"
Yadda yayi maganar tamkar wani yayansu, alhalin sun girme shi,
Murmushi suka saki atare sannan jahan a ruƙo hannunsa tare da cewa "Zamu ci abincin ne,amma kafin nan, mu shiga daga ciki muyi magana,
tasa ƙeyarshi su kayi har cikin ɗakinsu, suka tsaya daga tsaye suna fuskantar shi, gaba ɗaya sun rasa ta inda zasu soma neman alfarmar nan a wurin junaid,
Ganin sun tsayar dashi sun zuba mashi ido yasa shi hasala tare da cewa "Yaya Jahan nifa bansan menene ma'anar zuba mun idon nan da kuka yi kuna kallona ba," ya faÉ—i yana hura hanci,
Ayaan ne ya soma magana "am...junaid ka gane, dama wata alfarma ce muke nema awurin ka,
"Am listening to u," junaid ya faÉ—i yana kallonsu
Jahan ya daura da cewa "junaid sabo da mu zakayi wannan abun, so muke ka kira Mommy a waya video call ka bata haƙuri sanna ka ambaci sunanta ka kirata da Mommy, dan Allah junaid.........' tunkan jahan ya ƙarasa maganar tasa junaid yabi ta gefensu zai fuce daga ɗakin yana cewa "da nasan wannan alfarmar zaku nema awurina, wlh da ban 6ata lokacina wurin sauraronta ba,
Cikin sauri suka ruƙo rigar jikinsa har suna haɗa baki wurin cewa "Janaid dan Allah ka taimaka ma rayuwarmu, kai kaɗai ne a yanzu zaka iya fitar damu daga halin da muke ciki pls junaid do this favour for us"
a fusace junaid ya fusge rigar shi daga hannunsu yace "Wlh bazanyi ba, ni bazan ta6a kiran wannan matar da sunan mommyna ba, saboda bata sona ta tsane ni, Yana faɗin hakan ya kama hanyar fita, Ayaan yayi sauri sake cafko rigarsa, aikuwa a fusace junaid ya sanya hannunsa tare da buge na Ayaan, rai a6ace jahan ya janyo shi tare da kwashe shi da mari, zaro ido junaid yayi yana kallonsu yayin da ya sanya hannunsa ya dafe kuncinsa saboda zafin marin da jahan yayi masa, tunda yake arayuwarsa zai iya cewa ba'a ta6a bugunsa ba, ko da wasa wani bai ta6a yin gigin ta6a fatar jikin junaid ba da sunan bugun, amma sai gashi yau an samu wasu daga cikin yayyansa da yake matuƙar ƙauna yasa hannu ya mare sa, tuni idonsa sun ciko da kwalla red lips ɗinsa har rawa suke yi wurin cewa "Yaya jahan ! Yau kai da kanka, kasa hannu ka mare ni? Saboda na bijire ma buƙatarku? akan abunda yake haƙkina nifa aka cuta, abun har yanzu yana yi mun ciwo azuciyata bana faɗi ne kawai..............' kuka ne yaci ƙarfinsa har ya gaza ƙarasa maganar tasa yaci gaba da sharar kwalla, tuni jikinsu yayi mugun sanyi musamman jahan daya mare sa, baisan lokacin da shima ya fashe da matsanancin kuka ba, hakan yasa junaid dakatawa da kukansa ganin yarda Yayansa jahan ke kuka agabansa tamkar ƙaramin yaro, nan take hankalinsa ya tashi cikin sauri yasanya hannayensa a fuskar jahan yana share masa hawayensa yana cewa "dan Allah yaya jahan ka daina kuka, bana son ganin hawayen nan naka, in dai ni ne na sanya ka, yin kuka wlh zan baka hakuri ka yafe mun bazan ƙara,
Cikin shessheƙar kuka jahan yace "junaid naji na tsani kaina fiye da tunaninka, wai yau ni ne na kasance mutun na farko daya fara ta6a lafiyar jikin ka, da wannan mummunan hannun nawa, ina danasanin wannan ranar kuma bazan ta6a yafe ma kaina ba..........' gaba ɗaya tausayin jahan ya gama kama junaid cikin sauri ya janyo shi ajikinsa tare da rungume shi sosai yana ɗan bubbuga bayansa, cikin muryar rarrashi yake cewa "Ba laifinka bane yaya jahan, Laifina ne nayi rashin kunya, na buge hannun ayaan duk da raina ne a6ace bansan nayi hakan ba, amma ku yafe mun abisa kuskuren da nayi maku bazan ƙara ba,'
gaba É—ayansu sun shiga cikin wani kalar yanayi, Ayaan kam tuni jikinsa ya gama mutuwa saboda tausayin junaid da kuma kansu daya kama shi,
Bayan sun tsagaita jahan ya janye jikinsa daga na junaid sannan yace "Junaid dan Allah kayi mana wannan alfarmar na roƙe ka kai kaɗae ne zaka iya fidda mu cikin halin da muke ciki, kuma nason kana tsananin son mu ba zaka so wani abu ya cutar damu ba,' ya ƙarasar maganar yana kallonsa da idanunsa da suka gama runewa,
Jiki a mace Jahan ya kalli Ayaan cikin tsananin damuwa, ganin junaid yayi shiru baice komai ba yasa su yin saurin zubewa agabansa saman guiwowinsu suna roƙonsa,
Cikin tsananin tashin hankali shima junaid ɗin ya zube saman guiwowinsa agabansu tare da fashewa da wani sabon kukan yana cewa "meyasa zakuyi mun haka?yaya Ayaan da ya jahan saboda me zaku duƙamin nifa ƙaninku ne, ku kuma yayyena ne dan Allah kudaina mun hakan banaso! banaso!!bana so!!" ya ƙarasa maganar tare da cewa "naji na amince zan kirata, Amma ba yanzu ba,"
ajiyar zuciya suka sauke gaba É—ayansu nan take suka ji wani irin sanyin ya ratsa zuciyoyinsu,
Ayaan yace "yaushe zaka kirata"? Junaid yace "an jima kaÉ—an," ya faÉ—i a shagwa6e
Murmushi suka saki gaba ɗayansu har haɗa hannu suke yi wurin goge masa hawayansa da suka wanke masa fuska, har lokacin suna a zuƙunne su duka ukun suna fuskantar juna,
Jahan yace "Am Sorry junaid, ka yafe mun marin da nayi maka, nayi dana sani sosai," ya faÉ—i cikin sanyin murya,
Junaid yace "gsky bazan yafe ba yaya Jahan har sai kunci abinci sannan nagani da idona tukunnan,
Ayaan yace "shikenan junaid komai kake so zamu yi,"
Murmushi ya saki sannan ya ruƙo hannayen su suka miƙe tsaye atare, bayan sunyi wiping tears ɗinsu, Sannan suka fito daga ɗakin nasu,
Ajere suka jera suna tafiya sun sanya shi tsakiyarsu a lokacin Sehrish da azmee suna a cikin kitchen suna aikace-aikacen girkin dinner É—in gidan,
Sai da junaid ya tabbatar Ayaan da jahan sun zauna saman dining chairs É—in sannan yace "ku jira ni, yanzun nan zan kawo maku abinci ku ci," ya faÉ—i da murmushi a fuskarsa sannan ya wuce kitchen É—in,
har lokacin jahan dana sani yake yi akan marin da yayiwa junaid,ya gaza yarda cewa shi da kansa ya ɗaga tafin hannunsa ya zabga ma romeo ɗinsu mari, yana ganin abun tamkar a mafarki,😥Kitchen ya wuce yana ganin sehrish ya soma sakin murmushi, sallama yayi masu sannan ya shiga, amsa mashi su kayi gaba ɗayansu, sannan ya matsa wurin sehrish dake agaban chopping board tana yayyanka kayan lambu,
 "Reesh idan akwai abun da kuka kammala inaso ki shiryamun a tray zan kai ma yaya Ayaan da Yaya jahan ne, yunwa suke ji ssae," ya faɗi yana yamutsa fuska tamkar shike jin yunwar, zuba mashi ido sehrish tayi tare da cewa "junaid ! meya faru dakaine? waya mare ka har haka"?
  Cikin sauri junaid yasa tafin hannunsa ya rufe gefen fuskarsa yane cewa"ki daina É—aga murya sehrish kada wani yaji, banaso wani yaji kiyi shiru kawai da bakin ki,"Â
Jikinta ne yayi wani irin sanyi aranta tana mamakin yarda akai har wani ya aza tafin hannunsa a fuskar junaid ga sahun yatsu nan sun bayyana raÉ—au a fatar fuskarsa yayi jawur wurin,
Jinjina kanta kawai tayi tare da cewa "Shikenan bari na shirya maka abincin ka kai masu," ta faÉ—i tana kallonsa cikin jin tausayinsa,
Ajiyar wuÆ™ar hannunta tayi sannan ta wuce ciki donta haÉ—a masa, hannu yasa ya É—auki knife É—in da ta ajiye yaci gaba da yanka mata lettus É—in data bari,Â
Azmee ce ta taya ta zuba masu acikin warmers duk tana jin magananun da suka yi ita da junaid, aranta tana mamakin marin da taji sehrish ta ambata anyiwa junaid, har satar kallonsa tayi taga yarda fuskarsa tayi jawur gefen da aka maresa ga alama nan tabbas in wani yaji acikin gidan sai an tada husuma,
  Ruƙo tray ɗin tayi a hannunta zata wuce takai masu cikin sauri junaid ya ajiye wuƙar ya tare ta da cewa "kawo na kai masu,"miƙa mashi tayi yasa hannu ya kar6a yana kallon fuskarta da murmushi yace "thank u," itama murmushin ta sakar mashi duk tashiga damuwa akan yanayin fuskarshi,
 Yana karba ya fuce yakai masu, yadda yabarsu haka ya same su, sunyi zugudun suna kallon junansu, Jahan na ganinsa ya saki fara'a tare da cewa "Yawwa heart beat mun gode sosai da irin kulawar daka ba mu, duk ka damu akan mu," murmushi junaid ya saki a lokacin ya ajiye masu tray ɗin kayan abincin asaman table ɗin,
  Jikin Ayaan har kerma ya keyi wurin ɗaukar jug ya zuba lemu mai sanyi acikin cup yana kwankwaɗa, abun ya ɗaure ma junaid kai ashe dai da gaske yunwar suke ji,
  Shima jahan jiki na rawa ya shiga zubama kansa abincin, cikin sauri junaid ya wuce wurin freezer ɗinsu ya buɗe tare da ɗuko masu cool drinks ya kawo masu agabansu,
 Hannu jahan yasa ya É—auki bottle water yana kwankwaÉ—a har yana kusa shaÆ™ewa, agalabaice ya ajiye robar ruwan sannan ya kalli Junaid dake tsaye akansu yace "Allah yayi maka albarka junaid, kaje ka ci gaba da wasan ka,"Â
 Juya junaid yayi ya koma kitchen wurinsu sehrish, tana ganinsa tace "Za'a a ƙara masu abincin ne"? Girgiza kai junaid yayi tare da cewa "zuwa nayi na taya ku aikin, bana jin daɗin zama ni kaɗai ne,"
 Azmee tace"so kake kaja mana ko? taya za'a ganka acikin kitchen kana tayamu aiki, kaima kasan ba zaiyiyu ba,"
 turo bakinsa yayi tare da cewa "Aunty azmee nifa ba wani abu zanyi mai yawa ba, kawai zan taya sehrish yanka kayan lambun ne,"
  "Ban amince ba junaid, wai ni yau ba ka zuwa wurin buga ball ɗinka ne? ina laptop ɗinka ne? kaje ka kunna kallo kayi mana ko ka buga game,"
  Ruƙe qugu yayi tare da cewa "Aunty azmee korata kawai kike son yi ne, to Allah ba inda zani ƙafata ƙafar sehrish, tazo mu tafi tare," ya faɗi da shagwa6a
 Dariya su kayi gaba ɗayansu, sai lokacin sehrish tace "junaid ɗina shigo ciki ka samu wuri ka zauna, zan haɗa maka Cornflakes, kana sha kana kallon yarda muke girki,"
  Murmushi ya saki sannan ya shige ciki tare da samun wuri saman dinning chairs na kitchen din ya zauna yana jiranta,
 Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "Shaƙuwarku fa da junaid ƙara gaba take yi, don na lura kema bakyaso yayi nisa dake,"
 Sehrish tace "Aunty azmee yana ɗebe mun kewa sosai, ina jin shi tamkar ƙanina ne shiya sanya.... . '
Muryar junaid ce ta katse ta da cewa "Wanene Æ™anin naki"?Â
 Cikin sauri sehrish tace "bafa maganarka muke yi ba" tayi maganar yayin da tasa hannu a cup board ta zaro kofin tare da wuce wa wurin dispenser saboda ta ɗebi ruwan zafin da zata haɗa masa dashi,
"Koma meye dae zanji ne," ya faÉ—i yana É—an hararar ta daga inda yake,
Bayan ta haÉ—a masa takai masa nan ya zauna yana sha suna fira tare dashi,
________________________________
After magrib prayer motocinsu suka dunga shigowa cikin gidan da gudun gaske atare suka yi parking ɗinsu, Abbansu ne tare da SGR suka fito, motar dake bayansu kuma Su irfan ne tare da jabeer da khaleed, kana ganin su kasan sunji jiki, amma su da sauƙi babu alamar rauni ajikinsu sun dai jigata ne,
 buɗe motar dake bayan tasu suka yi wadda fawan ne kwance acikinta, gaba ɗaya jikinsa sahun bulali ne ta ko'ina, saboda hasken fatarshi duk zanen bugun da miyagun su kayi mashi ya fito raɗau jawur wani wurin ma harya fashe, amma da yake ya samu emmergency treatment duk ansanya mashi magani awurin, babu riga ajikinsa gajeran wando ne kawai guntu suka barshi dashi, asaman ƙirjinsa hada ɗinki akayi masa, ba ƙaramin jiki ya ji ba yaji gata sosai,
Amstrong ne babban na hannun daman SGR ya fiddo shi tare da Irfan suka tallabo shi sannan suka wuce dashi cikin gidan, har lokacin bai dawo cikin hayyacinsa ba saboda hodar da suka shaƙa mashi,
  Suma sauran mutanen da suka halarta domin yi masu jaje duk suka harhaɗu nan suna tayi ma Abbansu Allah kyauta, daga bisani suka haɗu gaba ɗayansu izuwa cikin gidan,
  Tun da Sehrish taji dirar motaci tarasa samun kwanciyar hankali burinta taga su wanene suka zo, a lokacin sun kammala aikace-aikacensu na kitchen fitowarta kenan daga wanka, ta buɗe closet dinta ta zura doguwar riga sannan ta matsa jikin window tana leƙensu bata samu damar ganinsu da kyau ba saboda mutanen dake zagaye ta ko'ina,
Jiki asanyayae ta rufe window in gabanta na faduwa tsoranta kar ace wani ne ya rasu, hannu ta aza akanta tana ambaton "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un ya Allah kasa ba wani bane ya mutu,"Â
Cikin sauri ta bar wurin tare da buɗe kopar ɗakin nata ta fito waje a lokacin itama Azmee tafito daga ɗakinta a ruɗe jikinta na sanye da zumbuleliyar hijabi alamar salla ta kammala yi, ko addu'a bata tsaya yi ba ta fito saboda jin jiniyar shigowar motocinsu,
  tsayawa su kayi gaba ɗayansu suna son ganin abunda ke faruwa, gaba daya sun rikice ganin yarda Amstrong da irfan suka shigo da Fawan duk ciwuka ajikinsa saman 3 seater suka zaunar dashi saboda masu zuwa dubiya,
Fitowa Ayaan da jahan sukayi daga ɗakinsu suma jin hayaniyar dake cikin gidan ganin fawan a wannan yanayin yasa su ƙarasawa da gudun gaske suka zube saman guiwowinsu agaban shi cikin tsananin tashin hankali suke cewa "fawan meya faru dakai haka? Waye yayi maka haka? Innalallahi wa'inna ilaihirraji'un,
 Daker fawan ke iya kallonsu duk da baya iya tantance su wanene agabansa amma yaji muryarsu, juyawa su kayi suna kallon Irfam da jabeer don son jin ƙarin bayani,
  Jabeer yace "Fawan bazai iya yi maku magana ba a halin yanzu baima san ko ku su wanene ba, addu'a kawai zakuyi masa,' jin haka yasa hawaye soma zuba daga idanunsu,
 Shigowar da mutane suka soma yi ne yasa su samun wuri Æ™asa suka zauna kowa ya zabga tagumi, kana kallon fuskar Abbansu kasan cewa acike take da tashin hankali saboda arayuwarsa ya tsani abunda zai ta6a masa jininsa,Â
Ganin SGR ya shigo yasa sehrish jin faÉ—uwar gaba, gaba É—aya babu annuri a fuskarshi, white shirt É—in dake ajikinsa duk shedar jini ne daya fallatsar masa hada hannunsa,
ba jinin kowa bane face jinin waÉ—anda suka farmaki su fawan, mugun bugu sukayi masu na fitar shari'a gaba É—ayansu suna a headquater dinsu an killace su can domin horar dasu da kuma yin bincike akansu,
Tuni jikin sehrish ya soma yin kerma saboda tashin hankalin da tagani ajikin SGR tunaninta ya gama bata cewa ko harbinsa akayine da bindiga shiyasa taga jini, hannu tasa ta rufe fuskarta tana kuka da gudun gaske ta juya ta koma É—akinta saman gadonta ta faÉ—a tana cigaba da kukan,"
 Abun ya ɗaure ma azmee kai ganin yarda sehrish ta gudu tana kuka kuma tasan ba don komai bane fa ce sai don ganin jini a jikin rigar sgr da hannunsa,
  Ganin manyan mutane sun fara cika babban falon yasa azmee komawa cikin ɗakinta jiki asanyaye, zama tayi tana jiran mutane su ragu sai taje ta dubo shi,
  Hannu Abbansu yasa ya ruƙo na Ayaan yace "taso ina son magana dakai,"
 Tasowa ayaan yayi daga zaunen da suke yabi abbansu suka ɗanyi nisa da mutane sannan ya kallesa yace "Ina junaid yake"?
 Ayaan yace "ina ji yana a ɗakinsa bana tunanin ya fita, Amma abba tayaya hakan tafaru da Fawan? Suwaye suka yi mashi haka? ya fadi idonsa cike tab da hawaye,
 Dafa kafaɗarsa abbansu yayi shima fuskarshi tamkar zaiyi kuka yace "Ayaan bamu son ko su wanene ba, Babban yayan ku da Omar sune suka je wurin da suka farmake su, kuma sun samu nasarar kashe wasu daga cikinsu, yanzu haka akwai mutun 3 daga cikin miyagun suna a headquater ɗin mu,"
  "Abba don Allah karku kyalesu akashe su kawai," ayaan ya faɗi cikin jin ɗaci aransa
 "Ba zamu Æ™yalesu ba ayaan, mutanene masu haÉ—arin gaske, babban tashin hankalin É—aya daga cikinsu da muka aza shi saman kujerar lantarki muka bashi horo ya bamu wasu bayanai nacewa macace take basu Umarni duk wani kashe-kashen da suke yi a Æ™asar nan,"!Â
  waro ido Ayaan yayi cikin tsananin mamakin abunda Abban nasu ya faɗa masa, aruɗe yace "What! Mace kuma Abba? mace wannan dana sani?
 "Of course Ayaan, ba kai kaɗae ba kowa daga cikin mu yayi mamakin jin hakan, yadda akasan mata da rauni amma har acikinsu asamu wata mai ƙarfin halin haɗa tawagar ƴan ta'adda masu farmakar mutane suna kakkashe su, Amma koma wacece insha Allah zamu ganota bi'iznillah zata ɗanɗani kuɗarta!"
  Jinjina kai Ayaan yayi yana cewa "Insha Allah Abba, Allah ya tonu asirinsu aduk inda suke, abun yayi yawa wlh rashin imanin nan har ina? mutun baya tuna cewa shima wata rana zai mutu yabar duniyar ne?shin menene ribarka idan ka kashe wani bayan kai baka isa ka hana kanka mutuwa ba?
  Kafin Abbansu yace wani abu muryar kanal yusif ta katse su da cewa "Abba ka matso kusa mutane suna son magana dakai,"Â
 Amsa mashi yayi da "toh gani nan zuwa" sannan ya kalli ayaan yace "Abun dayasa na tambaye ke game da junaid kasan halin shi, muddin ya fito yaga halin da fawan ke ciki tofa zai iya sume wa ko ya zauce, dan Allah kusan yarda za'ae ku hana shi fitowa daga É—akinsa indae yana ciki,"Â
  Ayaan yace "Shikenan abba bari naje na duba shi," cikin sauri ayaan ya wuce upstairs É—akin junaid, a hankali ya tura Æ™opar É—akin cikin sanÉ—a ya shiga, abun mamaki samun shi yayi saman gadon shi zaune ya toshe kunnan shi da headphone yana kallo acikin laptop É—insa baya jin duk wata hayaniya da akeyi acikin gidan,Â
  Murmushi Ayaan ya saki sannan ya ƙara ja mashi ƙopar ɗakinsa dakyau ya rufe masa ita, sannan ya juya ya sauko down wurin su,
Har wurin dare mutane suna ta zarya agidan sai wuraren Æ™arfe 9:30 sannan suka fara raguwa, tuni Sgr ya wuce part É—insa saboda ya gyara jikinsa ga matuÆ™ar gajiyar da yayi idonsa ma kansu daÆ™er yake buÉ—esu ga yunwa ga bacci, har lokacin zuciyar shi tafarfasa takeyi duk in ya tuna irin artabun da su kayi tare da miyagun nan, duk da sunci nasara akansu sosai, bakomai bane ya tsaya masa aran shi ba face wannan maganar nace wa macace take É—aukar nauyin tawagar miyagun dake kashe-kashen, yaci alwashin cewa sai ya gano ko wacece ita,Â
yanayin salon nata ya nuna cewa hada ɗaukar fansa take yi,' 😳😳😳
A asibiti marshal omar ya barsu hussana a hannun Camila kafin zuwa da safe zaisa a sallame su,
shi da major suka wuce izuwa gida saboda kiran wayarsa da ake ta faman yi ga kuma tsananin damuwar daya shiga game da halin dasu Fawan ke ciki,
daker sehrish tasamu ta fito sam tagaza samun natsuwa ta ko ina, ta damu da yanayin da taga Sgr da kuma halin da fawan ke ciki, a ƙopar ɗakin azmee ta tsaya sannan ta kwankwasa tare da jiran ta buɗe mata,
  tana tsaye azmee ta bude ƙopan tana kallonta tace "kin gama kukan?
 Shiru kawai tayi tana wasa da yatsun hannunta,Â
"hmmmm me kike yi ma kuka ne É—azu"?
Cikin sanyin murya tace"babu komai Aunty azmee kawai nadamu ne da halin dana ga fawan,'
 Jinjina kai azmee tayi tare da cewa "gsky yaji jiki sosai, nima na tausaya masa bawan Allah, Yakamata muje mu duba shi, dama na jira ne mutane su ɗan rage sosai,"
Sehrish tace "ae nagama babu kowa a falon bansan inda suka kai shi ba,"
"Sun kwantar dashi ne, a É—akin da suke kwantar da mara lafiya, bari nazo mu tafi tare, inyaso in mun dawo sai mu jera masu dinner É—in duk da nasan abune mai wuya ma a samu wanda zai iya cin abincin, don duk suna cikin damuwa," tana fadin haka tashige cikin É—akin bada jimawa ba ta fito sanye da mayafi, sannan suka jera da sehrish izuwa É—akin dake anan downstairs,
A buÉ—e suka same shi don haka su kayi sallama, muryar kanal yusif ce ta amsa masu tare da cewa "ku shigo ciki mana,"Â
  shiga ciki sukayi sehrish har tsoran kallon jikin fawan takeyi, wanda ke kwance saman gadon idonshi arufe alamar ya samu bacci,
Ayaan da jahad ne zaune daga gefen gadon sai kanal yusif dake atsaye,
Azmee tace "Yusif ashe haka abu ya faru? Mu ba mu sani ba"!
 Kanal yusif yace "Wlh kuwa aunty azmee abun babu daɗin ji, ƴan ta'adda ne su kayi masu kwanton 6auna, amma anci nasarar Cafke wasu daga cikinsu,"
 Cikin nuna jimami aunty Azmee tace "Allah ya kiyaye gaba, ya tonu asirin waɗannan mutanen, wlh duk jikina ya mutu dana ga fawan acikin wannan halin bawan Allah, Allah dae ya tashi kafaɗunsa,"
 Suka amsa mata da ameen, sai lokacin sehrish tace "Yaya yusif ya mai jiki"?
 Yace "Alhamdulillah da sauƙi sosai harma ya samu bacci,"
  Tace "Allah ya bashi lafiya,"
 "Ameen ," suka amsa mataÂ
Kanal yusif yace "Aunty azmee ku matso kusa dashi kuyi mashi addu'a yana buƙatarta sosai," matsawa su kayi atare kusa da fawan suna yi masa addu'a tare da tattofa masa, daga bisani su kayi masu sallama suka fito waje
 Kitchen suka wuce atare don sun shirya abincin dining azmee tace "bari na haɗa maki, ki kaima babban yayansu nasan zai buƙaci wani abun,"
  "Toh," ta amsa mata, suna cikin kitchen ɗin haroon ya shigo cikin babban falon daga waje ya shigo ciki hango sehrish da yayi yasa shi wuce wa cikin kitchen ɗin, kamar yarda ya saba fado masu batare da sallama ba haka ya shiga,
  ɗagowa su ka yi suna kallon shi hankalin shi kwance tamkar baisan meke faruwa ba, azmee tace "haroon me kake buÆ™ata ne"?Â
 tsoki ya ɗan ja tare da cewa "tun yaushe nake ta faman zarya ina jiran a jera mana abincin dare amma shiru babu, so ake akashe ni da yunwa ne"? yayi maganar fuska aɗaure yana kallon sehrish wadda tuni ta kawar da kanta,
 Azmee tace "kayi haƙuri haroon, saboda halin da su fawan ke ciki ne ga kuma mutane shiyasa ba mu samu damar fitowa ba mun jera,"
 Uban tsoki ya kuma bugawa wanda har sai da suka ɗan razana suka kallesa yace "And then so what? Mutuwa fawan ɗin yayi ne da zaku fake da cewa halin da yake ciki ya hana ku jerawa mutane abincinsu"? Ya tambaya a ƙule
 Mamakine ya kamasu jin abunda yace yadda ya nuna ko ajikinsa halin da fawan ke ciki,
  nuna sehrish yayi da hannu tare da cewa "Ke! ki kawo mun abinci na yanzun nan a bedroom ɗina ina jiran ki,
 Cikin sauri sehrish tace "Ni babban yaya zan kai mawa yanzu, sai dai ko in aunty azmee ta jera a dining ka zauna ka ci,'Â
 Zaro ido haroon yayi afusa ce yace "Ke! Ni kike fadama cewa wani wai babban yaya zaki kaima abinci"? Ke ga futsararra ko"? ya tambaya yana faman huci
  da ido azmee tayi ma sehrish alamar tayi shiru da bakinta, tsit tayi bata kuma cewa komai ba,
 cike da bada umarni yace "Ina jiran ki ki kawo mun idan kuma ba haka ba zaki ga mai zai biyo baya," yana faɗin hakan ya fuce daga kitchen ɗin,
 Murya tamkar zatayi kuka tace "Aunty azmee nifa bazan kai masa ba Allah,"
 Azmee tace "sehrish ki daure ki kai masa, nikaina na tsorata da yarda yake mana magana, ina tunanin kamar yayi shaye-shaye ne baya cikin hayyacinsa,"
  "Aunty azmee nifa bazan kai masa ba,kema da kan ki kince baya cikin hayyacinsa yanzu in naje zai iya kai mun bugu,"
  ganin ta dage akan cewa ba zata je ba yasa Azmee cewa "to shikenan bari ni nakai masa, ke kuma ki kaima Sgr nasa," ajiyar zuciya sehrish ta saki tare da cewa "to,"
bayan sehrish ta kammala shirya masa a tray ta wuce upstairs part É—insa, sallama tayi ba'a amsa ba don haka tashiga daga ciki, babu kowa acikin falon alamar yana a cikin bedroom É—insa,
  takawa tayi izuwa ƙopar bedroom ɗin nasa tayi masa sallama kusan sau uku sannan ya amsa mata da cewa"Come in,"
 Shiga ciki tayi zuciyarta na dar-dar lokacin da ta aza idonta akanshi yana zaune gaban dressing mirror saman chair din dake gaban madubin, ya sanya tafin hannayensa ya tallabo gefe da gefen fuskarsa ya zabga tagumi agaban mirror, sam babu riga ajikin shi daga shi sai short green colour, da alama ma daga wanka ya fito yagaza yin komai shine ya zabga tagumin, Sumar kanshi duk ta barbazo ta rufe masa gefen face dinsa, da wasu siraran gashi da suka sauko ta saman fuskarsa idonshi na arufe saboda gajiyar da ta lullu6e ga66ansa da kuma baccin da yake ji ga kuma yunwa duk shi kaɗai
tsayawa sehrish tayi jiki asanyaye tana kallon shi tsananin tausayin shi ne yakamata ganin yarda ya zabga tagumi da hannayensa biyu, alamar baya jin daÉ—i
 Ta jima tana kallon shi kafin ta ɗanyi gyaran murya tace "dama abinci ne na kawo maka, bansan ko kana buƙata ba," ta fadi adan tsorace gudun kar tayi kuskure a maganarta,
  daker ya buɗe bakinsa tare da cewa"keep it on the table, then i wanna see u," gabanta ne ya faɗi rass ! jin abunda yace na yana son ganinta ƙarasawa tayi ta ajiye masa dinner din saman table ɗinsa, sannan ta matsa kusa dashi ta tsaya sannan tace "gani,"
 Hannu yasa ya ɗauko wata ƙaramar kwalba ta magani daya ajiye a saman mirror din sannan ya miƙa mata tare da cewa "rub it on my back," ya fadi tare da kifa kansa saman gaban mirror ɗin yadda zata samu damar murza masa maganin,
tama rasa ta ina zata fara shafa masa shi, gaba daya duk tabi ta rikice wai yau itace sgr da kansa ya bata magani don ta shafa masa abayansa, jikinta har kerma yakeyi tsoranta kar ta fasa masa fatar bayansa saboda hasken fatar fes tamkar in kasa yatsa jini zai fito,
 Matsawa ta Æ™ara yi dab dashi sosai sannan ta buÉ—e mufin kwalbar, tasa yatsa ta lakuto maganin tare da É—an russinawa ta lakuta masa shi abayan, sannan tasanya hannunta a hankali tana shasshafa masa shi, tun da Allah ya halicce ta bata ta6a jin skin mai tsananin laushi da daÉ—in tabawa ba irin fatar bayan sgr,Â
Shi kuwa ajiyar zuciya kawai yake saukewa saboda relief daya fara samu sosai na ciwon da ga6o6insa suke masa, tun sehrish nayi masa da hannu É—aya har takai ga ajiye kwalbar maganin ta sanya duka hands É—inta a faffaÉ—an bayansa tana yi masa massage, a tunaninsa in ta kammala zata cire hannunta ne, amma sai yaga ta zarce gaba É—aya babu alamar zata daina shafa masa gashi kuma yaji ko'ina na bayansa yaji maganin sosai, shiru kawai yayi bai ce komai ba, almost one hour kenan sehrish na shafa masa magani har sai da ya É—an É—ago da kansa daga kwancen da yake tare da cewa "Har yanzu maganin bai shafu bane"? Cikin sauri ta janye hannunta tare da É—agowa tana kallonsa suka haÉ—a ido ta cikin mirror,
 gabanta ne taji ya Æ™ara faÉ—uwa rass ganin yarda kwayar idonsa ke shining sai taga tamkar tana canza launi ne daga blue zuwa green,. Â
 sunnar da kanta tayi ƙasa tana faman haɗe yatsun hannunta dake dankare da maganin data shafa mashi,
lumshe idonsa yayi tare da sake buɗe su yace "kin haɗo mun da coffee ne? ya tambaya a kasalance hakan ba ƙaramin kashe ma sehrish jiki yayi ba, tuni ta nemi natsuwarta tarasa sai ta kama en ena tana faman wurwurga ido
 "Its ok, idan babu akawo mun shi," ya faɗi tare da mayar da idonshi ya lumshe su,
Juyawa sehrish tayi cikin sauri ta fuce izuwa kitchen donta haÉ—o masa, a lokacin har azmee ta kammala shirya masu abincin dinner É—in a dining amma babu kowa asaman shi alamar basu kaiga fitowa ba,
 tayi mamakin hakan duk da tasan cewa duk suna cikin damuwa ne,bata ji daɗin hakan ba, tasa ba ganin mutanen gidan cikin raha suna nishaɗi suna cin abinci yau kuma wayaam babu kowa, Yau da gobe kenan,
  tana acikin kitchen ɗin bayan ta kammala haɗa masa coffee din ta ruƙo cup ɗin a hannunta, sai ga haroon ya faɗo mata kamar daga sama cikin sauri taja da baya hankalinta atashe, daga shi sai vest da singlet, shu'umin murmushi ya saki yana kallonta yace "ke shine nasa ki kaimun abinci kika ƙi ko? Ke ga isassa mai walkin sa harni ɗan masu gida zan saki aiki, ki bijire mun," ya faɗi yana kallonta
 Murya na rawa sehrish tace "kayi hakuri dama na fara kaima babban yaya ne, kafin na kawo maka nakan......'
 Bata ƙarasa ba ya katse ta da cewa "Sorry for your self sehrish! wlh kin shiga uku ! kin jefa kanki cikin masifa, daga rana irin ta yau inaso kullum ki kasance cikin yin sallar dare kina rokan Allah akan ya kare ki daga Sharrina," zaro ido tayi tana kallonsa jin abunda yace cikin tsananin tashin hankali tace "saboda me zaka ce haka"? laifin me nayi maka, dan Allah kabarni inyi rayuwata cikin salama,"
 Fashewa da dariya yayi kafin ya tsagaita da cewa "kinsan wani abu?kina da kyau sosai musamman idan kika tsorata idanunki ba ƙaramin fizgata sukeyi ba, idan kika amince a shirye nake dana aure ki, kuma zan shiryu nadaina duk wani abu da nake yi, amma idan kika bijire mun I pity u wlh," cikin sanyin murya yake yi mata magana,.
 Tamkar zatayi kuka tace"Dan Allah na roƙe ka kayi hakuri nidai ka fita daga cikin rayuwata, kabarni dan Allah kaje can ka samu mace irinka ka aura, amma ni ina da wanda nake so," tayi maganar tare da bi ta gefensa gabanta na faduwa ta wuce cikin sauri,
 murmushi kawai haroon yayi tare da jinjina kansa aransa yace "nasan ba kowa take hari ba face wancan mai zubin ifritan, ni kuma ba zan ta6a bari hakan ta faru ba, target ɗina na farko da zanyi zan fara 6ata sunanki ne a wurinsa," yana fadin hakan ya saki shu'umin murmushi tare da wuce wa room ɗinsa
Â
Maganganun da haroon ya faÉ—a mata sun tsaya mata arai, tunaninta ya rayuwarta zata kasance nan gaba acikin gidan batasan me haroon zai yi mata ba,
tana tunanin tana tattaka stairs ɗin jiki amace, adai² lokacin Marshal ya shigo gidan cikin sauri saboda yarda yake agajiye shima, har sai da ta juyo daga saman stairs din ta ɗan kalle sa, ta other side ɗin yabi ya wuce part ɗinsa da hanzari sam bai lura a ita ba,
  bakomai bane ya faÉ—o mata arai face yaran da taji yace zasu zauna gidan Uncle Abusufyan É—insu, ko ya É—auko su? ta tambayi kantaÂ
cikin sauri ta wuce part É—insa bedroom É—insa ta shiga da sallama ya iznin shiga, a lokacin harya dawo gefen bed É—insa ya zauna yana cin abincinsa, yau ba sai ya jira anyi saving É—insa,
 ƙarasawa tayi kusa dashi sannan ta samu wuri agefen plate É—in abincinsa ta ajiye masa cup É—in,"Â
A hankali ya furta "thanks,' a tunaninsa zata tafi amma sai yaga tayi masa tsaye akansa, sam bata son ta tafi tabarshi saboda a ganinta in ta tafi bazai ƙarasa cin abincin bacci zai iya ɗakarsa,
Hannu yasa ya É—auki cup of coffee É—in data kawo masa sosae yasha, bayan ya kammala ya ajiye shi, sannan ya gyara kwanciyarshi ya kwanta luf abunsa, ya janyo blanket É—insa ya rufe har zuwa chest É—insa nan take bacci ya É—auke sa,Â
bata bar bedroom É—in nasa ba sai da ta tabbatar tayi masa addu'a tukunna tasa hannu ta kwashe kayan abincin acikin tray ta fuce dasu a hannunta,
  Kitchen ta koma da hanzari ta haɗa ma Marshal Omar nasa shima acikin tray sannan ta wuce masa dashi part ɗinsa,
tana shiga a lokacin ya fito sanye da jallabiya fara wuri ya samu asaman 3 seater ya zauna hannunsa ruƙe da wayarsa ganin sehrish yasa shi sakar mata murmushi tare da cewa "kamar kinsan a yunwace nake abunda nake jira kenan,"
 Murmushi ta saki tare da ƙarawa ta ajiye masa tray ɗin asaman table ɗin dake a gabansa sannan tace "Ya mai jiki ya omar, naji abunda ya faru Allah ya kiyaye gaba, ya tonu asirin su,"
 "Ameen Ameen," ya amsa mata, hannu tasa ta buɗe warmer tare da ɗaukar plate da saving spoon zata zuba masa abinci taji yace "baki tambaye ni twins ɗina ba"? Murmushi ta ɗanyi tare da ɗagowa ta kalle shi tace "dama ƴan biyu ne"? Yace "eh kamannin su ɗaya sak, ke ma haka fuskarki irin tasu ce sak komai da komai,"
  gabanta ne taji ya faɗi jin abunda omar yace dakatawa tayi da zuba mashi abincin tana son tunano wani abu arayuwarta amma sam takasa tunawa, tabbas tana jin cewa akwai wani abu da ta manta arayuwarta mai matuƙar muhimmanci agare ta, a duk lokacin da tayi ƙoƙarin tunawa sai taji zuciyarta tayi mata wani irin nauyi sosai,
"Wata rana zan kawosu ku ga juna, saboda inaso ki ga abun al'ajabin da nake son nuna maki,"
Cikin sauri tace "Shikenan ya Omar Allah ya kaimu lokacin nima zanso nagansu,"
ta jima suna dan fira dashi kafin daga bisani ta bar part É—in nasa ta koma É—akinta,Â
 Bayan Omar ya kammala cin dinner ɗinsa fitowa yayi tare da wuce wa ɗakin da suka kwantar da fawan
 Yanayin daya samu Twis zaune zun zuba mashi ido ga kanal yusif shima zugudum duk cikin jimami, gyaran murya yayi duk suka É—an É—ago kana yace "ku tashi ku je ku kwanta, tun da ya samu bacci"Â
 Amsa mashi su kayi da "toh" sannan suka miƙe tare da fuce wa daga ɗakin shima yusif yayi yabi bayansu, zama Omar yayi daga gefen fawan dake ta faman sharar bacci, addu'o'i ya shiga karantowa yana tatto fa masa, ya jima yana yi masa addu'a sannan ya tashi yabar ɗakin tare da tufe masa ƙopa,
****************
Wuraren ƙarfe sha biyu ya fito cikin sanɗa hannunsa ɗauke da pillow yana duddubawa yaga in ba kowa duk sunyi bacci lokacin murmushi ya saki tare da cewa "sheggu saboda wancan ɗan shilan shine duk suka susuce har suka gaza cin abinci, bari na ƙarasa shi lahira sai in ga ya zasu yi, zasu bi shi ne
 Yana faɗin hakan ya wuce ɗakin da suka kwantar da fawan cikin sanɗa ya tura ƙopar tare da sa ƙafa yashiga cikin, bin shi yayi da kallo jinjina kansa yayi sannan ya lalla6a ya haye saman gadon tare da ɗaga pillow ɗin ya taushe ma fawan hancinsa dashi , nan take fawan yafarka tare da zazzare idanunshi yana mutsu-mutsu sam bashi da sauran ƙarfi ajikinsa da zai iya kwatar kansa........... ... ...
sai faman kiciniya fawan yake yi saboda ya kwaci kansa daga hannun haroon wanda ya taushe masa fuska da pillow da mugunta ma yake kara danna masa shi, tun fawan yana wutsil wutsil da ƙafafunsa numfashinsa na kokarin daukewa gaba daya har jikinsa ya fara saki, suna cikin wannan halin aka kwankwaso kopar da karfin gaske,a wani irin tsorace haroon yayi wurgi da filon dake hannun shi, yayi wuff tamkar giftawar walkiya ya afka bayan labule ya boye yana faman zazzare idanun shi kamar na mujiya tsoran shi kar ace wani ne ya taso cikin daren nan, Hannu yasa a hankali yaɗan buɗe labulen don yaga kowanene, gabansa ne yayi bugun bugu ganin Abbansu ya shigo ciki jikinsa sanye da jallabiya fara, cikin sauri haroon ya mayar da labulen ya rufe ruff tuni zufa ta soma tsattsafo masa a jikinsa tamkar wanda aka tsamo daga kogin maliya,
ï¿?
  ganin yarda fawan ya tashi zaune saman gadon yana faman hargowa yana fadin "zasu kashe ni ! bansan me nayi masu ba! Sun biyo ni don su kashe ni, ku ce musu su daina azabtar dani !!!! Gaba É—aya ya zauce sai zuba sambatu yake yi yana zazzare ido,   A hanzarce Abban nasu ya Æ™arasa tare da haye wa saman gadon dab dashi yana cewa"fawan sannu ya jikin? ka dawo cikin hayyacin ka ko? ka kwantar da hankalin ka, kana a gida yanzu babu wanda zai iya cutar da kai,'.Â
ï¿?
  girgiza kai fawan yashiga yi yana sake maimaita cewa "Har yanzu suna nan, bibiyata suke yi so suke su kashe ni, ni bansan me nayi masu ba," yana magana daker daker yake sakin numfashi, hancinsa har ya fara bleeding kaɗan jinin ke ɗigowa,   tallabo fuskarsa Abban nasu yayi tare da ɗago da ita don ya kalle shi sosai yace "fawan Ni ne fa,Abban ku ina tare dakai, babu wani anan da zai cutar da kai,"  A hankali fawan ke kallon Abban nasu yayin da idon shi ke rurrufe wa yace "Abba ruwa zan sha," ya faɗi agalabaice,
ï¿?
  Cikin sauri Abban nasu ya matsa tare da kai hannun shi saman bedside drawer ganin dakwai bottle water mai sanyi ajiye asama, ɗauko wa yayi tare da buɗe murfin ya kwafa masa abaki yana sha, jikin shi har wani kerma yake yi tamkar zai kwace roban ruwan daga hannun Abban nasu daya kwafa mashi, ganin yarda yake shan ruwan throat ɗinsa har wani sauti yake fitarwa kwattt!kwattt!! Saboda yarda yake kurbarsa a zafafe,
ba ƙaramin tausayi yaba Abban nasu ba, tamkar ya zubar mashi da kwalla haka yake ji, daurewa kawai yake yi  Sai da ya shanye kusan rabin ruwan sannan ya janye mouth ɗinsa alamar ya ƙoshi, sannan Abban nasu ya rufe robar ruwan ya mayar da ita saman side drawer din ya ajiyeta,  Sannan ya mayar da idon shi kan fawan dake ta faman sauke ajiyar zuciya yana fidda sound na radaɗin ciwo abakinsa,  Haroon daka la6e acikin labule yace "shegen yaji dannar manya,an gaya ma jin ƙamshin mutuwa wasa ne,dole ka nemi ruwa yaro, ba don jatuminka ya faɗo cikin ɗakin nan ba, da yau saina aika ka barzahu wurinsu munkar, gskiya Abba ya kawo mun cikasss amma ba komai mu haɗe gaba,' ya faɗi yana cizon la66ansa,  Haroon kenan duk da yana cikin tashin hankali amma hakan bai hana shi sambatun nan nashi ba, mutuwa ce kawai zata iya zuge zeep ɗin bakinsa, muryar shi na rawa yace "Abba ashe zan ƙara rayuwa? abba nasha wahala sosai tamkar bazan rayu ba,ashe da rabon na sake ganinku a idona"? Ya faɗi yayin da idonshi ke zubar da kwalla,   shima Abban nasu jiki asanyaye yace"Fawan nasani wlh,nashiga damuwa sosai game da halin da kake ciki har nagaza runtsawa saboda son nazo naga wani hali kake ciki,kayi haƙuri fawan iya cuta dae sun cuce ka sosai sun raunata dukkan ga66an jikinka, amma nayi maka alƙawarin cewa ɗaya daga cikinsu bazai sha ba, wlh muddin ina da raina da kuma lafiyata saina ƙuntata duk wani jin daɗinsu na duniyar nan,"  Lumshe ido fawan yayi tare da kwantar da kanshi a kafaɗar Abban nasu yana sauke ajiyar zuciya sannan yace "Abban sunce fansa suke ɗauka akan family ɗin mu,wannan harin da suka kai mana, ba don kowa su kayi shi ba face saboda mu kawai," Jin wannan maganar ta fawan tasa zuciyar Abban nasu yin wani irin bugu duk da yasan maganar revenge ɗin amma baisan cewa akan ƴa'ƴansa bane abun zai afka,  "Insha Allah, Allah bazai ta6a Basu nasara ba fawan,zamu tashi tsaye wurin ganin mun kawar da koma su wanene su,Kuma zamu dage da addu'a akan Allah ya tonu asirinsu ya Kuma Kare Mana zuri'ar mu da dukkan al'umar musulmi,"  "Ameen Abbana," ya amsa mashi daker,  Haroon dake a la6e bayan curtains duk yana sauraronsu gaba daya ya ƙagu abban nasu ya fuce daga dakin shima ko ya samu ya gudu,tuni kafafunsa suka soma daskare wa suna mashi raɗaɗi saboda tsayuwar da yayi, ga wani irin fitsari daya matse shi, sai uwar zufa ke wanko masa daga fuskarshi, runtse idanun shi yayi yana cewa "wayyyo Allah na, ko yaushe wannan tsohon zai ware nima in samu in gudu,lallaima mutumin nan wato saboda wannan ɗan shilan shine harya gaza yin bacci, ya wani kwaso kafafunshi yazo don ya gan shi,ina sane da komai wato ya daura son duniya ya aza masu,duk ranar dana hallaka ɗaya daga cikinsu zanga in haukacewa zaiyi ko kuma zaiyi suicide ne,'  Ya faɗi yana cizon lips dinsa yana wani irin huci, bude idonshi yayi tare da sa hannu ya sake bude labulen a hankali ya leƙa su, har time din abban nasu na zaune dirshan saman bedmattress din, fawan kuma ya kwantar da kanshi a kafaɗar shi,da alama ma bacci yayi awon gaba dashi gaba ɗaya ya lafe masa kwance luffff abunsa,  Tuni ran haroon ya ƙara 6aci saboda takaici da baƙin cikin dayake ji aduk lokacin daya ga Abbansu na nuna ma ƴa'ƴan alexandra soyayya,zuciyar shi tafarfasa take yi saboda jin haushi, mayar da idon shi yayi kan pillow dinshi da yayi wurgi dashi kasa, nan gabansa ya faɗi tsoranshi kada abban nasu yaga fillon don za'a iya samun matsala,  Bari dae in taƙaice maku zance,Abban su bai bar ɗakin ba anan bacci ya ɗaukesu su duka biyun azaune fawan kwance a shoulder ɗinshi,  Kamar yarda suka kwana a zaune suna bacci haka Sir Commender Haroon ya kwana a tsaye ba bacci duk yarda yayi motsi zai fito sai Abban nasu ya buɗe ido, hakan ne ya hana shi fitowa daga bayan labule,  ya kuke tunanin wanda ya kwana atsaye idonshi buɗe fuskarshi zata kasance, koda yake fa soja ne 😂
  (Wata dae tace commendern ƴan Iska dae, Bana sojoji ba)😹😹😹
****************************Morning
tun da sassafe sehrish tafarka daga guntun baccin daya ɗauketa bayan Sallar asuba anan saman sallayar ta kwashe da bacci, duk jikinta amace tafarka sai faman hamma takeyi saboda yunwar da take ji, gashi yesterday night bata samu enough sleep ba saboda tayi nafilfilin dare,   tunawa da school yasa ta yin hanzarin tashi tashiga toilet shaf shaf tayi wankan ta, fitowa tayi jikinta ɗaure da towel fari, a bakin ƙopar toilet ɗin ta tsaya tana kallon uniform ɗinta da sukayi uban squeezing tun jiya da tadawo school ta cicciresu ta jefar saman gadonta bata ninke su ba kuma anan tabarsu,girgiza kai tayi sannan ta ƙarasa agaban mirrow ta tsaya tana shafa body oil ɗinta,bayan ta kammala ta feshe jikinta da turare sannan ta koma ta buɗe wardrobe ɗinta, hannu tasa ta ɗauko ɗayan uniform ɗinta mai pencil skirt ɗin nan sannan ta dawo ta ajiyesu gefen gadon tashiga zura su ajikinta, tana cikin sa kayan maganar haroon ta faɗo mata aranta nace wa ta fara sallar dare domin neman tsari daga sharrin shi, tabbas maganarsa ta girgiza ta saboda tun daga lokacin da ta dawo daki at midnight tafarka tayi nafilfili saboda neman tsari daga sharrin shaiɗanin mutun irin haroon, ta jima tana jin cewa wasu abubuwa zasu faru tabbas acikin gidan!!!!! duba da irin mafarkin da tayi a baccinta na jiya, kuma taci Alwashin cewa ashirye take data fuskanci duk wani abu da zai taso ta ɗaura ɗamarar yin yaƙi da duk wani da zaizo don tarwatsa rayuwarta ko kuma family ɗin SALAHUDDEEN HUSSEIN, Hakan na nufin SEHRISH ta shirya zama AYYANA wato mai bama family ɗinsu kariyyya daga miyagu irinsu Haroon da kuma ire-irensa masu irin wannan mummunan kuɗirin,nace ba Allah ya ba mai rabo sa'a,   Tana cikin wannan tunanin azmee ta kwankwaso ƙopar ɗakin tana cewa "Allah sa dai kin tashi," Murmushi sehrish tayi a lokacin ta kammala sanya uniform ɗin, ba ƙaramin kyau sukayi mata ba tafito ɗass especially skirt ɗin da ya bi shape ɗin jikinta sosai,  ƙarasawa tayi ta buɗe mata ƙopar ɗakin tana cewa "ae tun ɗazu na tashi nama kammala shirya wa,"  Bin ta da kallo azmee tayi tana jinjina kai kafin tace "To fa yau wankan skirt aka ɗauka? masha Allah kinyi kyau ƙanwata, ya maganar breakfast fa? ta tambaya tana kallon ta,  Sehrish dake ta faman murmushi tace "aunty azmee yau a school zanci abinci na gaskiya,amma zansha koda tea ne,"  Azmee tace "okey, shikenan bari na kawo maki tea ɗin,' gefen gado ta Zauna tana jiran dawowarta,
A 6angaren haroon kuwa bashi ya samu damar barin ɗakin da fawan ya ke ba har sai wuraren sallar asuba bayan abbansu ya kwantar da fawan dake ta faman sharar bacci a kafaɗarsa, sannan ya samu yabar ɗakin don zuwa yin sallah, sir commender haroon na ganin haka ya lalalla6a ya fito ya sungumi pillow ɗinsa daya shigo dashi, sai da ya jinkirta abakin ƙopar ɗakin ya tabbatar da cewa sun harhaɗu sun tafi gabatar da sallar asuba sannan ya koma ɗakin shi, agalabaice ya hankaɗa kopar bedroom ɗin nasa yayi wurgi da filon hannun shi,sannan ya afka toilet don tuni mararsa ta ɗaure saboda fitsarin dayayi ta ruƙo har na tsawon awannni, fitowa yayi daga toilet ɗin har wani biji biji yake gani saboda yarda idanun shi suka galabaita sun kumbura sunyi jawur saboda rashin baccin da baiyi ba, saman gadon shi ya afka batare da tunanin yin sallar asuba ba, sai ma addu'a daya shiga yi yana cewa "ya Allah ka yafe mun,zan ɗan rama baccin da banyi ba da safe in na tashi zanyi sallar anjima,'yana faɗin hakan ya shiga sharar baccin shi,
Babu wanda ya tayar da junaid daga bacci saboda basu son kwata-kwata yaga fawan ko kafin su tafi yin sallar asuba sai da Abbansu ya buÉ—e door É—in É—akinsa ya same shi baje magashiyyan yana sharar bacci rungume da pillow, murmushi kawai yayi tare da rufa masa door É—in suka wuce mosque,
turo ƙopar azmee ta ƙara yi hannunta ɗauke da tea set ta miƙa ma sehrish cikin sauri sehrish tasa hannu ta kar6a tana cewa "Nagode aunty azmee," Azmee tace "ki hanzarta fa kada kiyi late dayawa,"  "Toh," ta amsa mata sannan ta shiga shan tea ɗin, . har azmee zata fita sehrish tayi saurin cewa "Aunty azmee dama inaso nakaiwa babban yaya nashi kafin natafi school,"   tsayawa azmee tayi hannunta ruƙe da door handle ta juyo ta kalle ta tana ɗan murmushi tace "i knew, raina sai da ya bani cewa sai kinyi magana akan RAFAYET, ,ɗan sunnar dakai sehrish tayi tana kallon tea ɗin dake hanunta yana faman tiririn zafi   "Ni nake maki magana ba tea ɗin dake hannunki ba, naga kin zuba mashi ido,' guntun murmushi sehrish ta saki kafin ta ɗago tana kallonta daƙer ta iya cewa "aunty azmee baya jin daɗi jiyan nan that's why nake so nakai masa breakfast ɗinsa,nasan zai buƙace shi,"  Sakin baki azmee tayi irin mamakin nan tace "to ko dai kece ALEXANDRA ban sani ba,'  shiru sehrish tayi tana sakin murmushi saboda tagane cewa wannan sunan mommynshi ne,shiyasa azmee ta kirata da sunanta,   fuce wa azmee tayi tana cewa "shikenan kiyi sauri kizo ki kai masa breakfast ɗin," tana jin haka tayi saurin ajiye tea ɗin hannunta asaman bedside drawer inda kayan tea ɗin suke,   hijab ɗinta ta ɗauko ta zura ajikinta yar dai² shoulders ɗonta, sannan ta wuce kitchen ɗin tayi mamakin ganin yarda azmee tayi uban aiki duk ita kaɗai, da alama ma tun bayan sallar asuba bata koma bacci ba,saboda tasan cewa dole manyan baƙi su hallara saboda zuwa duba fawan, ..shirya ma sehrish tayi breakfast ɗin SGR acikin ƙayataccen tray sannan ta miƙa mata, ruƙo wa tayi a hannunta sannan ta miƙi hanyar zuwa part dinsa, tana cikin tafiya taji anyi gyaran murya juyowa tayi da sauri don taga wanene junaid ne tsaye jikinsa sanye da shirt pulover tare jeans, ......har ya kammala shiryawar shi cike da ɗaukin kaita makaranta ya fito, sai faman zabga murmushi yake yi sam baida wata damuwa, ɗan dawowa baya tayi dai² saitinsa sannan tace "junaid ! Ya akai naga kana ta faman zabga murmushi, kai bakasan meke faruwa ba acikin gidan nan"? tayi maganar tana kallon shi, ..cikin mamaki junaid yace "kamarya kenan? meya faru ne ni bansan komai ba,"  Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"jiya wani abu ya faru mai matuƙar raxanar wa, zan faɗi maka amma bari nadawo," ta faɗi tare da saurin haye wa upstairs tana murmushi, taso ta faɗama junaid abunda ya faru amma azmee dake tsaye daga kitchen tayi mata alamar karta kuskura ta faɗa masa, shine dalilin dayasa tace mashi ya bari tadawo, . tuni jikinsa yayi sanyi a ƙagare yake daya ji mai reesh zata sanar dashi,  Kitchen ya wuce wurin azmee da sallama ya shiga sannan ya gaishe ta yana cewa "Aunty azmee a shirya mun breakfast a yunwace nake, gashi inaso nayi sauri nakai sehrish school,  Sakin baki azmee tayi tana kallon shi kanta ya gama ɗaure game da lamarinsu su duka biyun, ita tagaza samun natsuwa saboda son takaima babban yaya breakfast ɗinshi, shi kuma junaid damuwarsa yakaita school,kowa da wanda ya damu dashi kenan,  Zama yayi saman dining chairs yana jiran azmee dake shirya mashi bf ɗinsa ta kawo mashi yaci,
Acan ciki kuwa bayan sehrish ta isa part ɗinsa da sallama ta shiga baya cikin falonsa don haka ta wuce bedroom ɗinsa tsayawa tayi daga bakin door ɗin sannan tayi masa sallama, da wannan sexy voice ɗin nashi ya amsa mata, tare da bata permission din shiga daga ciki, .a hankali tasa ƙafarta ta shiga ciki tsayawa tayi zuciyarta na faman bugawa ba ƙaramin kyau yayi mata ba,
ya juya bayansa yana tsaye a agaban mirrow jikinsa na sanye da bathrobe white colour wadda ta tsaya mashi dai² guiwarsa,a buÉ—e rigar take bai É—aure igiyarta ba, amma akwai shorts ajikinsa,sumar kan nan tashi ta zubo mashi tayi irin Curly É—in nan dark brown very smooth ta rufar masa abayansa, da alama bai jima da fitowa daga wanka ba, ...gaba É—aya jikin sehrish ya gama mutuwa murus cos aduk time É—in da tayi arba da wannan kyakkyawar surar jikin tashi rasa hankalinta take yi gaba É—aya duk ta bi ta susuce,tana hangen shi ta cikin mirror saboda madubin yana facing dinta,  tabbas yaji alamar shigowar mutun tun da harya bada iznin shigowa daga ciki amma har yanzu baiji an motsa ba, a hankali ya É—ago da blue eyes É—insa ta cikin mirror É—in karaf suka sauka akan na rishi dake tsaye jikinta na rawa É—an zaro idanun nata tayi tana kallon nashi dake kallon cikin nata ta cikin mirror, hankali atashe cikin tsananin tsoro tayi saurin sunnar da nata Æ™asa gabanta na faÉ—uwa,  gyaran murya ya É—anyi kafin yace"a ajiye mun shi a palor, sannan agyara mun bedroom dina,' amsa mashi tayi da "toh" sannan ta juya ta fuce tana faman sauke ajiyar zuciya, a saman table ta ajiye masa sannan ta É—an tsaya tana jiran ya kammala kimtsawa,after some minutes ya fito jikin shi sanye da tunic shirt milk colour tare da trouser, sai Æ™amshi yake fitarwa, shiga cikin falon yayi ya samu wuri ya zauna saman royal sofa É—in sannan ya shiga yin breakfast É—insa anatse, Wuce wa sehrish tayi cikin bedroom É—insa ta shiga gyara masa shi komai agyare yake,bedsheet É—inne kawai da yayi squeezing ya tattare inda ya kwanta, cire shi tayi sannan ta musanya masa wani sabo mai kyan gaske ta shimfiÉ—a masa, bayan ta kammala gyara ko'ina cikin sauri tafito saboda tunawa da school karta yi late, a lokacin da ta fito samun shi tayi yana yin waya da alama kan fawan suke magana da mutumin daya kira shi awaya,Â
   Kama hanyar fita tayi har takai baƙin ƙopa ta ɗan juyo tana kallon shi gudun kar ace yana buƙatar wani abu gashi zata tafi batare daya bata izni ba, ganin alamar mutun ta wutsiyar idonshi yasa shi ɗan juyawa karaf suka haɗa ido da sehrish dake tsaye tana kallon shi cikin sauri tace "Can i go"? tayi maganar aɗan tsorace,  Lumshe idonshi yayi tare da ɗan jinjina kai alamar eh,  Murmushi sehrish ta saki sannan ta fuce cikin sauri aranta tana cewa "Sannu bata hana zuwa,"😇
 Saukowa down tayi cikin sauri adai dai lokacin ta ji saukar motoci cikin gidan alamar sunyi baƙi, kitchen ta wuce anan tasamu junaid zaune saman dinner table harya kammala cin breakfast ɗin shi, yana ganinta yace "dama yanzu nake shirin biyo ki, bansan meya tsayar dake ba gashi har time ya ƙure ma,da ace ana bugu a school ɗin wlh da kinsha bulala yau," dariya sehrish tayi jin abunda yace  "Bari na ɗauko school bag dita," ta faɗi tare da juyawa cikin sauri ta koma bedroom ɗinta,  Sallama junaid yayi wa aunty azmee sannan yabaro kitchen din, jin sallamar Cg Abbas yasa shi ɗagowa cikin tsananin farin ciki yace "Yaya Abbas kaine tare da Aunty Amani !!!" murmushi suka saki gaba ɗayansu da yake tare suka zo shi da AMANI yana sanye cikin shigar shadda maroon color ita kuma tana sanye da Arab gown white colour mai kwalliya ajikinta na duwatsu tayi rolling veil a kanta, ba ƙaramin kyau tayi ba,  sam junaid ya gaza rufe bakinsa don murna, buɗe mashi hannu abbas yayi cikin sauri junaid ya ƙarasa tare da faɗawa ya rungume shi sosai ajikinsa yana cewa "i really missed u our last born, duk da ina fushi dakai saboda baka son zuwa kawo min ziyara,' yayi maganar a lokacin da ya raba jikin shi dana junaid,  ɗan turo mouth dinsa yayi cikin shagawa6a yace "Yaya Abbas saboda me zaka ce kana fushi dani dan Allah, bakasan yarda na damu dakai ba koda yaushe inason zuwa amma shaiɗan ya hanani zuwa,' dariya sukayi gaba ɗayansu jin abunda junaid yace,  ɗan gyaran murya amani tayi masa tare da cewa"Junaid ni baka ganni bane"?  matsawa yayi tare da kai hannu zai rungumeta ajikin shi, ae kuwa a razane Abbas ya finciko rigarshi tare da janyo shi baya baya yana cewa "Sannu mati na mata,!matar tawa zaka rungume agabana? salon mu koma gida ta juya mun baya ko?"  Fashewa da dariya Amani tayi shima junaid ɗin dariyar yake yi cikin jin kunya ya sunnar dakai, shi aganin shi ba wani abu bane don ya rungume matar yayan shi, duk cikin waye wa ne,  Abbas ya kuma cewa "Oh ni junaid? Yanzu fa in na ƙyale ka sai ka rungume ta ko"?  ɗaga mashi kai yayi alamar Eh, hannu abbas yasa tare da ɗan jan kunnan shi har yayi ƴar ƙara yana faɗin "wayyo yaya Abbas karka cire mun kunne na in rasa na jin magana,"  "Hanzarta ka cire masa kunnan, hukuma ce zata raba ni dakai," acewar Abbansu wanda bai jima da fitowa ba ganin su yasa shi tunkaro su,   Murmushi suka saki gaba ɗayansu, adai dai lokacin Sehrish tafito daga ɗakinta, harta sanya Sandals ɗinta taruƙo school bag ɗinta, ƙarasawa tayi inda suke,  tunkan taƙaraso Amani ke kallonta cikin jin bugun zuciya, shi kanshi Abbas kallon matashiyar yarinyar yake yi cike da mamakin ina aka samu yarinya mace acikin gidan, Ganin duk hankalinsu yadawo kanta yasa jikinta ya soma yin kerma, dakatawa tayi da tafiya sannan cikin en ina tace "umm....ina kwananan ku,"  atare abbas da abbansu suka amsa mata banda Amani dake tsaye ƙiƙam tana kallonta cikin tashin hankali, ita kanta sehrish atsorace take da kallon da Amani ke yi mata,  "Zonan My daughter nayi missing ɗin ganinki, gashi bakya zuwa kina gaishe da Abbanki ko"? Yayi maganar yana kallonta,  Ƙarasawa sehrish tayi gab da Abban nasu ta tsaya tana faman ƙaƙume hannun jakarta da ta sargafo a kafaɗarta, Hannu yasa tare da shafa gefen fuskarta yace"yaushe kika fara zuwa school ne ba'a sanar mun ba"? ....daker sehrish ta iya cewa "jiya ne nafara zuwa," Jinjina kansa yayi tare da cewa "okey,ki maida hankali sosai akaratun ki kinji ko? Banda biye ma ƙawaye  "Insha Allah Abba," ta amsa mashi, Baki asake Abbas yace "yakamata a wayar mun dakaina mana, ina aka samu yarinya kyakkyawa kodai daga cikin danginmu ne na damaturu ko zariyya"?  Ya tambaya aɗan ruɗe yana kallon Abban nasu, tunkafin Abban nasu yace wani abu junaid yayi saurin cewa "ƙanwata ce yaya Abbas, sunanta Sehrish kuma abbane yayi mun ƙanwa da ita, itama ƴar Abban mu ce, ba'a jima da haihuwarta ba, nasan zakayi mamakin yarda tayi saurin girma har haka, ka tambayi Abba zaiyi maka bayanin komai,'  yana faɗin haka yaja hannun sehrish suka bi ta gefensu suka fuce,  Dariya kawai Abbansu ke saki hada shi Abbas ɗin,  "Ji wata shiririta irinta junaid,hakanan kawai ya zabga mun ƙarya, ina na ajiye matar bare harna haifi ƴa kamar wannan,' Ya fadi tare da yi masu alamar su shiga daga ciki, bin shi su kayi tare da samun wurin saman royal sofa mai mazaunin mutun uku suka zauna, Amani na kusa da Abbas yayin da Abban ke fuskantar su yace "sannun ku da zuwa,nayi mamakin ganinku da wuri haka," Abbas yace "tun jiya muka so muzo,amma dare yayi sosai lokacin, wlh sam nagaza samun natsuwa ne game da halin da naga fawan a asibiti, shine nace mata tashirya muzo har gida mu duba shi,"  yayi maganar fuskarshi dauke da damuwa, Amani ma tace "Abba ya mai jiki? sai jiya da daddare yake faɗamun abunda ya faru dasu fawan hankali na ya tashi sosai, tun jiya nima naso ko wayane nakira na tambayi jikin shi amma duk layin dana kira ba'a ɗagawa,"
Abba yace "ae ba zaki same su ba, saboda duk muna cikin damuwa ne,bakowa ma yasan inda ya jefa wayarshi ba,abun ne ya tayar mana da hankali sosai, Cikin sanyin murya tace "Allah sarki Allah ya bashi lafiya,ya tashi kafaɗun shi, su kuma waɗanda sukayi mashi wannan aika aikan Allah ya toni asirin su,"  "Ameen Ameen," suka amsa mata Daga bisani Abbas yace "bari mu shiga ciki mu dubo shi,"  Miƙewa su kayi hada Abban yayi masu jagowa izuwa ɗakin da aka kwantar da fawan,  Da sallama suka shiga ciki, har lokacin fawan na kwance sai faman sharar bacci yake yi, Abbas yace "masha Allah jikin nasa yafara sauƙi, tun da harya samu bacci,"  "Ae tunjiya dana shigo ɗakin na same shi yana ta faman fisge-fisge yana cewa sun biyo shi zasu kashe shi,saina zauna wurin shi anan zaune muka kwana ni dashi da asuba ne nabar ɗakin," Abban nasu ne yayi maganar ayayin da yake samun wuri gefen gadon tare da zama yana kallon fawan ɗin dake kwance magashiyyan yana kwasar bacci,  matsawa Abbas yayi shima tare da samun wurin kusa da Abban nasu ya zauna sannan yakai hannun shi ya dafa forehead din fawan yana cewa "Baƙaramin jiki yaji ba gaskiya,sun azabtar dashi sosai bawan Allah, amma asannu zai warware insha Allah,  Kafin Abban nasu ya kuma cewa wani abu wayar Amani dake acikin handbag ɗinta tashiga yin ringing da ƙarfin gaske,  Kallonta Abbas yayi tare da cewa "ki fita waje ki amsa wayar," cikin sauri ta amsa mashi da toh sannan ta fuce,  dama so take ta fita daga ɗakin saboda gulmar data ciyota kunsan mu mata abun ajinin mu yake,da zarar abun gulma ya samu nan take zaka ga jikin mutun har rawa yake yi don ya faɗama ɗan uwansa, (Amma fa ni bana gulma) 😒
Cikin sauri Amani ta sauko down stairs jikinta har rawa yake yi ganin Azmee na jera masu breakfast a dining table, yasa cikin sauri ta wuce wurinta  Azmee naganin ta ta soma sakin fara'a tana cewa "aaa yau kune agidan namu? saukar yaushe," Batare da Amani ta amsa mata ba tace "Yawwa Aunty azmee dama akwai abunda nakeso na tambaye ki,"!  Cikin mamaki azmee tace "meke nan"?  "Ga me da Yarinyar dana gani acikin gidan nan, wata ƴar matashiyya shin ita ɗin jinin su Abba ce?  murmushi azmee ta saki aranta tace "Gulma ajali, in ba'ayi ba a mutu," a fili kuma tace "abokiyar aikina ce a aka kawo don ta runƙa tayani aiki,"  yamutsa fuska amani tayi kan ta yagama ɗaurewa ta kuma cewa "ƴar aiki fa kika ce? But i was confused ya akai naganta cikin uniform kuma har junaid na kiranta da ƙanwarshi? Kuma naji Abba ma ya kirata da My daughter,duk kuma a matsayin mai aikin?  dariya azmee tayi ganin yarda amani ta ɗaga hankalinta akan sehrish  "tabbas mai aiki ce itama, amma abba ya mayar da ita tamkar ɗiyarsa,bata da banbanci da sauran ƴa'ƴanshi a yanzu, saboda yana son Yarinyar sosai,"  Jin haka yasa Amani ɗan zaro ido waje bata ƙara cewa komai ba saboda wayarta da ta ƙara yin ringing, cikin sauri ta zura hannu tare da buɗe handbag din ta zaro wayarta, tare da duba screen din wayar don taga mai kiranta, sunan Aunty laila ne ya bayyana asama, kallon Azmee tayi tare da cewa "ina zuwa," tayi maganar tare da kama hanya ta danyi nesa da azmee sannan ta ɗaga kiran tare da kara wayar a kunnanta tana cewa "barka da safiyya Auntyna fatan kin tashi lafiya," Murmushi Aunty babba tasa ki daga can 6angaren tace "Lapiya lou Alhmdllh my sister, nazo maki da labari mai daɗi ina fata kina da kunnan saurara,"  Amani tace "nima ae ina tafe da labari zazzafan gaske, amma bansan wa zai fara bada labarin shi ba acikin mu,"  Saurarawa tayi tana jiyo dariyar aunty babba ta cikin wayar sai da ta tsagaita da dariyar sannan tace "ina tunanin labarina yafi naki daɗi kuma zaifi ƙayatarwa, bari dae ni nafara baki,"  murmushi Amani tayi tamkar tana agabanta tace ina sauraronki auntyna,  gyaran murya Aunty babba tayi sannan tace "ina yaran nan da nake baki labari Omar ya kawo mun gidana?  Amani tace "eh nagane su," Aunty babba taci gaba da cewa "ae tuni nasa an kwashe su, an jefar mun dasu bayan gari,yanzu haka hankalina kwance na rabu da alaƙaƙai, yanzu banda wata sauran damuwa saura target ɗina nagaba nake jira...." tunkan taƙarasa maganar Amani ta kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya, Jin dariyar da amani keyi ne yasa aunty babba dakatawa da maganarta tana sauraronta ta cikin wayar, ganin cewa amani bata da alamar jinkirtawa da yin dariyar da takeyi ne yasata cewa "ke bana son iya shege, na ji kina mun dariya kodai daɗin labarina ne yasa ki jin daɗi har haka," ta tambaya tana jiran jin mai amani zata ce,  daƙyar Amani ta tsagaita da yin dariyar sannan tace "Aunty laila an fa yanka ta tashi,labari da ɗumi ɗuminsa idan ma kina atsaye to wlh ki zauna don kar in sanar dake ki yanke jiki ki faɗi,"  Jin maganar Amani yasa hankalin aunty babba ɗugunzuma,murya na rawa tace "ba atsaye nake ba,ina zaune saman 2 seater ne ina shan tea,dan Allah ki sanar mun wane irin labari ne wannan,"  wani irin shu'umin murmushi amani tayi kafin ta soma cewa"Yanzun nan muka zo gidansu Abbas saboda mu duba jikin fawan da miyagu suka kai masu hari, ina fata kinsan wannan labarin"? Ta tambaya tamkar tana agabanta, Aunty babba tace "eh nasani,ae muna nan muma zamu zo tare da ishaq don mu duba jikin shi,"  Jinjina kai Amani tayi sannan taci gaba da cewa "Shin ko kinsan cewa akwai wata matashiyyar yarinya kyakkyawar gaske da muka tarar acikin gidan !!!'  darammm !!!gaban aunty babba ya faɗi rasss a firgice ta saki cup ɗin dake hannunta ya tarwatse ƙasa, zumbur ta miƙe tsaye tana cewa "kamarya Amani ! Bangane abunda kike cewa ba anya ba kunne na bane suka jiyo mun hakan"?  dariya amani tayi kafin tace "ba kunnanki bane Aunty laila,zahiran ne wannan nake faɗa maki, wlh da ido na naga yarinyar,kyakkyawar gaske har na tambayi azmee nake cewa wacece ita yarinyar kodai cikin danginsu Abba take, sai azmee ke sanar dani cewa house maid ce itama amma Abba ya mayar da ita tamkar ƴarsa, har fa school sun sanya yarinyar babban abunda zai tayar maki da hankali sai kin ga yarda Abba ke kiranta da ɗiyarshi, yarinyar ba ƙaramin wuri ta samu ba....... Fuska a damuje aunty babba tace "nifa hanyanzu ban fahimta ba, shin yarinyar ƙarama ce sosai ko babba"?  Amani tace "ina fa, wlh balagagga ce nace maki fa matashiyar budurwa kyakkyawar gaske mai cikar sura,ni kaina dana kalle ta sai da gabana ya faɗi to ina ga matasan gidan da suka kasance maza ne dukansu,  Jin wannan maganar yasa aunty babba dake atsaye tana zarya a falon nata, aza hannunta na dama akanta, ɗayan kuma na ruƙe da wayar tashiga cewa "Ae shikenan wlh an yanka ta tashi, ni ina nan sake da baki ina murnar rabuwa da waɗancan tagwayen da Omar ya kawo min ashe abanza ga wata can ta riga ƙetare iyakar da bana so aje,amma an gama dani wlh ya akai har takai wannan lokacin gidan baki sanar dani ba,"? ta tambaya a kiɗime,  Amani tace "nafa ce maki ni kaina bansan da zamanta ba, yau ɗin nan muka ganta kwatsam tafito ɗas da ita cikin school uniform wlh abun ba'a magana yarinya haɗaɗɗiyar gaske,tasamu wuri fa sosai agidan, kuma yarda naga Abbansu na kiran sunanta da daughter dinshi kinga kuwa hakan na nufin nan gaba ma da sunan Surikata zai kirata,"  ƙasa ƙasa amani ke sakin dariya tana sauraron aunty babba dake faman Zabga salati, dama dagangan take tunzurata don ta rikitar da ita, "Nashiga ukuna,wannan masifar har ina matashiyar budurwa kuma agidan surikina, wlh hakan bazai ta6ayiyu ba, wlh saina son yarda zanyi na rabata da gidan, badai zamu zo da ishaq ba hmmmm zanganta ne !! zanga KOWACECE ITA 😳😳😳  Sun jima suna waya da aunty laila kafin daga bisa ni sukayi sallama da juna amani ta koma daga ciki, ranta fess don tasan yau ko bacci aunty babba bazata iya yi ba har sai taganta a Abuja, gata ga yarinyar data bata labarinta,
Fitowa hafsat tayi daga bedroom ɗinta jikinta sanye da sleeping dress ganin mommyn nata tsaye tana ta faman zarya a falon tana zazzaga bala'e ita kaɗai kamar zararriya, hakan yasa hafsat ƙarasawa kusa da ita tana cewa "wai mommy lafiya kuwa kike ta faman tada jijiyoyin wuya duk akan wanene? Uban tsoki Aunty babba ta saki sannan tace "wani mummunan labari amani ta sanar dani yanzun nan, wlh nagaza samun natsuwa, so nake kawai naganni a abuja wlh,"  Wuri hafsat ta samu tare da zama saman 2 seater sannan tace "mommy wannan wane irin labari ne haka daya tayar maki da hankali haryasa kika fasa cup ɗin da kike shan tea dashi," tayi maganar ayayin da take kallon kofin da aunty babba ta saki ƙasa ya fashe,  juyo tayi ta kalle ta rai a6ace tace "ba dole hankali na ya tashi ba, ina murnar rabuwa dasu hossana da jahad sai gashi yanzu Amani ta kirani awaya tana sanar dani cewa sunje gidan su Abba, sun tarar da wata matashiyar budurwa wai mai aikice fa, amma abba ya mayar da ita tamkar ɗiyar cikinsa," tayi maganar tana huci,  Shiru hafsat ta ɗanyi na wani lokaci kafin daga bisa ni ta saki ƙayataccen murmushi tace "Mommy kenan, dama kina tunanin haƙƙinsu hossana da jahad zai barki ne? to inaso ki sani haƙƙinsu ne yafara bibiyarki, kuma ba zaki ta6a cin nasara ba akan wannan yarinyar da aka baki labarinta yanzu, saboda mommy sam baki kyauta ma rayuwar yaran nan ba, basu miki laifin komai ba kinsa an kwashe su,ki kayi mun ƙaryar cewa gidan marayu za'a kaisu ashe zubar dasu kikasa ayi,yanzu wayasan wani hali suke ciki.........' hawaye ne suka soma zarya a fuskarta saboda raɗaɗin da take ji aduk lokacin da ta tuna dasu hossana da jahad,tun jiya da aunty babba ta sanar da ita cewa ba gidan marayu tasa akaisu ba, zubar dasu tasa ayi bata ƙara samun kwanciyar hankali ba, abun namata ciwo azuciyarta . kallonta kawai aunty babba keyi ganin yarda take zubar da tears ɗinta akan tsintattun yaran da bata haɗa alaƙar komai dasu ba,  tsoki ta sake ja tare da cewa "kin dai ji haushin rayuwarki wlh, saboda waɗancan marasa galihun kike ta faman sharara kuka,har kina ikirarin haƙƙinsu ne ke bi na,to ki zuba ido ki gani saina sa anyi waje da waccen yarinyar da amani taban labarinta,"  afusace hafsat ta miƙe tana kallonta tace "mommy! Ina miki fatan nasara," tana fadin hakan ta juya tare da komawa bedroom ɗinta,  Jinjina kai aunty babba ta shiga yi tana faman sakin huci kamar zakayan, afili tace "Tabbas dole nasan kowacece wannan yarinyar dake ƙoƙarin tarwatsa mun plan ɗina, yakamata nasan abunyi dole na kira HAYAAM awaya in sanar da ita cewa ta tattaro kayanta itama ta koma gidan da zama, tunda har ƴar aiki ta samu irin wannan gatancin ina ga ita da take ƙanwata !!!!!!🤠 Sai faman balbali bala'e take yi ita kaɗae tana ci gaba da zarya a falon,
*******************************
tun bayan da junaid ya sauke sehrish a school su kayi sallama ta shige ciki shi kuma yakama hanyar komawa gida yana driving yana tunanin fuskar rishi ɗinsa tsantsar sonta ne ke sanya shi jin wata irin kasala a jikinsa, lokacin da ya ƙaraso gida sai da gabanshi ya faɗi rass ganin dandazon motoci suna ta shiga gidan nasu,manya manyan mutane ne aminnan abbansu suke ta zuwa dubiyar fawan, wasu daga cikinsu manyan shuwagabannin sojoji ne da kuma mr president da kanshi ya tako yazo don duba jikin ɗan aminin nasa atare dashi hada mataimakinsa da kuma babban ɗansa Captain Shattima wanda ya kasance aboki ne ga Marshal Omar da SGR tun a U.s don acan shima yayi karatunsa na Airforce, halayyarsa da ɗabi'unsa sak irin nasu ne shiyasa tafiyar tasu tazo ɗaya, ƙwararre ne a6angaren aikin shi, sannan kuma shima mace sam bata gaban shi,tamkar dae su ɗin dae,  Gida fa ya ɗinke ɗuff da mutane tamkar rasuwa akayi, ta ko'ina jinsin bil'adama ne ke ta shigowa,  Hankalin junaid ba ƙaramin tashi yayi ba tunkan yayi parking ɗin motarsa yake ta faman sharar hawaye tsoran shi kar ace wani abune ya faru dasu fawan saboda yasan sune basa a gida anturasu aiki,a hankali ya tsayar da motar sannan ya buɗe murfin motar ya fito yana kallon mutanen dake shigowa, ...jingina bayansa yayi ajikin motar tashi sannan ya zura hannun shi cikin trouser pocket ɗinsa, wayar shi ya zaro tare da shiga contact ɗin wayarsa, lambar abbansu ya gano sannan ya buga masa waya,  ta jima tana ringing kusan sau uku kafin Abban nasu ya ɗaga kiran,  Kara wayar yayi a kunnansa tare da fashe mashi da kuka,  Shiru Abbansu yayi yana sauraran kukan da junaid ke yi masa acikin wayar,  Cikin shesshekar kuka yace "Abba......wanene ya mutu, naga dandazon mutane acikin gidan...'daker ya iya yin maganar zuciyar shi na faman bugawa,   "Kana ina ne"? abban nasu ya tambaya .."gani awaje abba, nakasa shigowa,ina jikin motata yanzu haka ban jima da shigowa gidan ba, saboda nakai sehrish school ne,"  Ajiyar zuciya abbansu ya saki kafin yace "sauraran ni kaji da kyau, babu wanda ya mutu, nasan halinka ne shiyasa tun jiya ban sanar maka ba, amma yanzu zan faɗa maka, but promise me first cewa zaka daina kuka,"  Ajiyar zuciya junaid ya shiga saukewa yana cewa "Okey, abba nadaina tell me pls,"  gyaran murya abban nasu yayi tamkar yana agaban shi sannan yace "abunda ya faru shine, su irfan da aka tura aiki,miyagu suka farmake su amma alhmdllh duk suna cikin ƙoshin lafiya, fawan ne kawai suka samu nasarar cutar dashi harya zauce ssae tun shekaran jiya suna asibiti ana duba su sai jiya ne muka dawo gida tare da su............'  tunkan abban nasu ya ƙarasa maganar tashi tuni Junaid ya saki wayar dake hannun shi sakamakon faduwar da yayi nan take ya sume...................dama abunda abbansu ke gudu kenan
 hankali atashe yake cewa "junaid!junaid !!! Kana jina kuwa !! Meya faru ne,  yarda yake fidda sautin maganar yasa kowa dake a falon kallon shi, dama duk suna a falon sun hallara saboda sun fiddo da fawan yana kwance asaman 3 seater yana amsa ya jikin da mutane keyi masa, gaba ɗaya hankalin kowa ya tashi,suka shiga tambayar shi meke faruwa ne, zumbur ya miƙe yana cewa "wlh junaid ne daga faɗi mashi halin da fawan ke ciki shikenan ya yanke jiki ya fadi ina tunanin ya suma ne awaje,' "Subhanallahi," mutanen wurin suka haɗa baki wurin cewa haka, fawan dake kwance kuwa tuni ya shiga kiran sunan junaid yana fadin "Abba akawo mun junaid inason ganin shi," ya faɗi akasalance,tun jiya dama yake so yasa shi a idonshi amma bai samu dama ba,  atare abbansu da cg abbas suka fito domin ɗauko shi, tun kan su isa sai gashi ɗaya daga cikin soldiers din dake cikin gidan ya ɗauko shi sa6e a kafadarshi, cikin sauri Abbas ya kar6e shi tare da yima sojan godaiya, sannan su ka koma ciki dashi,
********************SGR hospital
tun safe su hossana da jahad suke ta faman jiran yaya Omar ɗinsu saboda yazo ya ɗauke su amma shiru babu alamarshi, suna kwance a gado ɗaya saboda since yesterday night hossana ta maƙale ma jahad aɗaki ɗaya suka kwana tana agefenta,hankalinsu kwance saboda kyakkyawar kulawar da suka samu a wurin nurse Camila,tun da sukayi breakfast wanda anan asibitin suke rabawa marasa lafiya abinci kyauta kuma lafiyayyen gaske,sunci sunyi hani'an suna jiran omar yazo, duk in Camila tashigo duba su sai sun tambayeta yaya Omar dinsu yazo? Sai tace musu a'a su ƙara jira kaɗan tun suna tambayarta har suka gaji suka daina,
Around 12 na rana, Motar Omar ta shigo cikin asibitin, bai samu damar zuwa ba saboda busy É—in daya shiga hakanne yasa shi aiko major domin ya É—auko su kamar yarda yayi musu alÆ™awarin cewa da safe zai sa asallame su, dalilin dayasa ya turo masu da major kenan amaimakon shi,  Bayan major yayi parking É—in motar sannan ya fito ya shiga ciki, kai tsaye É—akin dasu su hossana ke ciki ya nufa,  suna ganin shi suka fara murna don sunsan cewa yana tare da Ya omar,   "Ya jikin naku"? Cikin sauri suka amsa mashi da cewa "Alhmdllh jiki da sauÆ™i," Yace "masha Allah,kun ganni ni kaÉ—ai ko? Hossana tace "eh, ina ya omar din, shi bai zo ba tun É—azu muke jiran shi,"  Murmushi major yayi kafin yace "kuyi mashi Uziri yana busy sosai, amma ya aiko ne nazo don na duba ku,sannan nasa a sallame ku mu tafi gida,"  ba Æ™aramin daÉ—i suka ji ba, don aÆ™agare suke da su ga inda zasu zauna wurin da zasu fara sabuwar rayuwa,  "bari naje naga dr, yanzu nan zan dawo," yayi maganar tare da fuce wa daga É—akin,  Cike da murna hossana tace "Shikenan mun rabu da wahala, yanzu zamu fara kyakkyawar rayuwa, saboda nasan yaya omar har makaranta zai samu,har na hango ni yarda zan koma nan da 1 month," Kallonta jahad tayi da yake sun tashi daga zaune tace "jibgegiya zaki koma kamar buhun fulawa,nikaina naÆ™osa naga yarda rayuwarmu zata canza,abu biyu nake tunawa da suke sani kwanciyar hankali na farko shine bani da wata sauran damuwa dama hossana ke nafi ji, damuwata aduk lokacin da muka shiga hadari kece ina tsoran kar na rasaki,abu na biyu kuma shine Æ´ar Uwarmu SEHRISH,duk da bansan a ina take ba amma inaji araina cewa TANA TARE DAMU, INA NUFIN TANA A KUSA DAMU SABODA INAJI A ZUCIYATA!! With confidence tayi maganar in serious matter,  jinjina kai hossana tayi kafin tace "Jahad nima inaji araina cewa REESHI TANA A KUSA DAMU,komai ma zaizo mana cikin sauÆ™i yanzu tunda zamu samu kwanciyar hankalin nemanta,ga kuma YA OMAR,NASAN DAGA MUN FAÆŠA MASA CEWA ƳAR UWARMU TA 6ATA MUNA NEMANTA KUMA KAMANNIN MU ÆŠAYA SAK MU TRIPLET NE,SAI MU FAÆŠA MASHI SUNANTA NASAN ZAI TAIMAKA MANA WURIN GANO TA.................âœï¸ðŸ’‹
Shin mai zai faru idan Aunty babba tayi arba da fuskar Sehrish😳 yaya zata kasance tsakanin Haroon da twins? Baku tunanin cewa dole ALEXANDRA tazo nigeria domin duba jikin fawan😲? haka zalika AMMI ma muna hasashen zuwanta domin ganin fawan😲, ga kuma goggon katsina karfa ace itama zata zo domin ganin fawan shin ya zatayi a lokacin da tayi arba da fuskar sehrish wadda takasance kamanninta ɗaya da ƴa'ƴan abusufyan ɗinta?🤣, to kodai shima abusufyan dake zaune ƙasar turkey zaizo nigeria ne?😯, ni duk bama wannan ba🤨 abunda yafi damuna shine HAYAAM ƙanwar aunty babba wadda ke shirin dawowa gidan da zama 🥱 in har dagaske ne kenan sehrish itace a tsaka mai wuya tabɗijan can, ga haroon ga aunty babba ga wata wai hayaam🥴 wayyo har kaina yafara ciwo don tunanin yadda zatakasance, yakamata naje na kwanta fa, amma kafin nan akwai hasashe ɗaya daya rage mun shin ya zata kasance idan Hossana da jahad suka sanar da Omar game da ƴar uwarsu wadda takasance ita ɗin ƴar ukunsu ce kuma sunanta SEHRISH 🥺🥺🥺    💋Boss Bature💋_
dawowa major yayi shida dr Emran,a cikin ɗakin da aka kwantar dasu hossana,fuskar major ɗauke da murmushi yace. "An yi discharge ɗinku,kwanan asibiti ya ƙare yanzu zamu wace gida,"  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,jiki na rawa hossana ta sauko daga saman gadon,itama jahad lalla6awa tayi a hankali ta sauko saboda ƙafarta,  Kallonsu dr emran yayi tare da cewa"zamu yi missing ɗinku sosai gsky,amma tun da a wurin omar ku ke, zamu dinga zuwa muna ganinku,"  Murmushi suka saki gaba ɗayansu,gaisawa major ya ƙara yi da dr emran sannan yayi mashi sallama,
ï¿?
 shiga gaba yayi su hossana suka bi bayanshi, daker jahad ke taka ƙafarta da taimakon hossana take tafiya saboda ta dafa kafaɗarta gudun karta fama ciwon ƙafarta,   A haka har suka ƙaraso harabar asibitin wurin ajiye motocinsu, hannu major yasa tare da buɗe masu ƙopar back seat don su shiga su zauna,har jahad tasa kai zata shigo suka jiyo muryar nurse camila tana cewa "wait !! Wait !!,  Dakatawa su kayi gaba dayansu suna kallonta dama kuma sun so su tambaye ta,ɗan zaman da su kayi da ita ba ƙaramin shiga ransu tayi ba, ƙarasowa tayi kusa dasu tana faman sauke ajiyar zuciya hannunta na ruƙe da jakar kaya, daga bisani ta ɗago fuskar nan ɗauke da murmushi tace"ba sallama twins?yanzu da banzo ba shikenan zaku tafi ko? Ku barni da kewarku,  murmushi sukayi gaba ɗayansu jahad tace "a'a bamu ganki bane shiyasa,"   kallon major tayi tare da cewa "tare dani zaku tafi, saboda already mun yi magana da marshal omar, ya dauke ni amatsayin wadda zata cigaba da kula da lafiyarsu,inaso naga gidan saboda in na tashi zuwa,  wani irin farin ciki ne ya rufe su hossana da jahad saboda sun lura da irin mutuncin dake gare ta, ba ƙaramin kula zasu samu a wurinta ba,  Murmushi major yayi tare da cewa "naji daɗin jin hakan sosai,saboda na lura da yadda kikeson yaran ina fata zaki kasance tare dasu,kuma zaki riƙe su amana,".   Jinjina kai Camila tayi tare da cewa "NA RIƘE AMANA,"  daganan suka shiga cikin motar jahad da hossana suna a back seat,major na a mazaunin driver yayin da Camila ke Zaune a other seat ɗin,"   a hankali yake driving dinsu harya fuce daga asibitin,ya miƙi shantalelen titi dasu, ajiyar zuciya kawai suke sauke wa ga wani farin ciki daya baibayesu, ba don komai ba sai don sanin cewa Ƙarshen wahalarsu yazo, yanzu lokacine da zasu huta ma rayuwarsu,suyi rayuwa ta ƴanci kamar kowane ɗan adam, batare da an ƙuntata masu ba ko an cutar 😇  Lokacin da suka ƙaraso gidan Uncle Abusufyan nan fa hossana ta zaro ido tare da buɗe baki alamar mamaki yarda kasan ƴar babyn roba haka ta koma sam bakinta yaƙi rufuwa don murna, ita kanta jahad bakinta a buɗe don murna fararen hakoran nan nata kamar gonar auduga, adai dai bakin gate ɗin major ya tsayar da motar sannan ya danna horn da ƙarfin gaske,  sai gashi an buɗe masu gate ɗin ta ciki, ba kowa bane face abokin Major ɗan leƙen asirin shi, acikin gidan ya kwana saboda omar ya dauke shi aiki, bayan alherin da yayi masa na kyautar mota sabuwa mai kyau da tsadar gaske, ga kuma uban salary daya yanka masa,😇   A hankali major ya shigar da motar cikin gate ɗin ɗan dagatawa yayi da driving ya zuge glass ɗin motar ya kalli osman yace "Shege mutumina, ka ga yarda ka canza jiya izuwa yau har wani haske ka fara? Cike da zolaya yayi maganar,  Dariya Osman yayi tare da cewa "ba dole kaga canji ba,an gaya ma yin karin kumallo da farfesun kaza wasa ne? mutun ya kwana a ac,sannan yayi wanka acikin kwami haba ae dole ma ne in canza,"  gaba ɗaya suka fashe da dariya jin abunda yace,   Major yace "nifa wasa nake maka malam, taya zaka canza kawai daga jiya zuwa yau don ka kwana a ac, kayi breakfast da farfesun kaza? Nace sannu ko uban son banza ae sai nan da irin one month haka,nan zamu ga canji,  Murmushi osman yayi tare da cewa " ka shiga ciki ka sauke su,in ka dawo zamuyi magana dakai, akwai labari mai daɗi,"
ï¿?
  Major yace "okey bari nazo," yayi maganar tare da sauke glass din motar ya wuce dasu ciki, adai adai stairs ɗin da zai sadaka da main palour ɗin gidan ya sauke su,   Buɗe motar Camila tayi ta fito, sannan suma su jahad suka fito daga ciki suna ƙarewa katafaren gidan kallo ya haɗu iya haɗuwa abun ba'a magana, Omar yasa an canza mashi komai nashi an ƙara ƙawata gidan sosai,   gaba dayansu sun ƙame suna kallon haɗuwar gidan, ganin basu da niyyar shiga daga ciki yasa major cewa "let's go in pls,"  Cikin rashin sani jahad ta take ƙafarta ba don komai ba sai don hankalinta daya tafi wurin ƙarewa gidan kallo,ƙara tasaki tana yarfa hannu tana faɗin "wash Allah na," jin haka yasa camila tayi saurin dawowa ta inda suke, ta taimaka mata wurin yin tafiya don su shiga ciki, Major ne yayi masu jagora su kuma suna abayan shi, har suka shiga cikin haɗaɗɗen jigunannan falon,nan fa suka baza ido suna kallon haduwarshi, wasu irin matsiyatan royal sofa set ne acikin sa masu numfashi ɗunɗuma ɗunɗuma a jere launin su brown colour,ga wasu set na Cushions Jere asamansu difference colour,duk gasu nan ba ƙaramin ƙawata kujerun su kayi ba, daga tsakiya wani ƙayataccen table ne legs dinshi brown ne, while daga saman glass ne, an ajiye flower asaman shi, ga fruits basket mai dauke da kayan mar mari, ba komai yafi tafiya da hankalin hossana ba face tanƙameman kwan filitar dake bama ɗakin haske tamkar zai faɗo ma mutun akai haka yake, sai kuma tv stand din dakin faskekiyar plasma ma ce mai dauke da speakers na jin sauti, ga wani telephone table dage a gefe, bari dae in taƙaice maku zance komai wannan da kuka sani a palour an zuba masu shi,  Sai faman yarfa hannu hossana take yi, yarinya fa takusa zauce wa ganin irin gidan da yaya Omar dinsu ya gwangwaje su dashi, wani abun ma sai mun shiga bedroom,   Jahad kuwa murmushi kawai take saki tana bin ko'ina da kallo,ita kanta Camila gidan ba ƙaramin burgeta yayi ba komai tsaf a natse ba tarkacen hauka,   Can dae hossana tace "Allah yasa ba mafarki nake yi ba,dan Allah koma mafarki nake yi jahad kada ku tashe ni," ta fadi tana faman hadiyar yawu, Dariya su kayi gaba ɗayansu, Major yace "wannan zahiran ne ba mafarki ba ne, kaɗan daga cikin irin son da ya'ya omar dinku yake yi maku kenan,zai iya yin komai akanku more than u think, ni dae fatana agare ku shine ku kasance masu yi mashi biyayya, ku bishi sau da ƙafa kada kuyi amfani da son da yake yi maku wurin karya mashi zuciya,ko ku ce zaku canza halayyarku saboda wata dama da kuka samu, yanzu lokaci ne da zaku more rayuwarku bayan duk wahalar da kuka sha,"  Sosai major yashiga yi masu nasiha, duk sun kasa kunne suna sauraronshi,sannan kuma suna amsa mashi da insha Allah,  Bayan ya kammala daga ƙarshe yace "ku samu wuri ku zauna mana,nasan kuna jin yunwa yanzu zan sa ayi maku oder na abincin da zaku ci, sannan ga bedroom nan zaku iya shiga ciki ku huta,"  A natse suka ƙarasa tare da samun wuri suka zauna fuskar nan fa awashe,  Mayar da idonshi yayi kan Camila yace "zamu tafi tare ne? Na sauke ki a asibitin ko kuwa,"  cikin sauri tace "no i will stay here wit them,cos i ave done my work bani da sauran duty till tomorrow,"  Murmushi kawai major yayi sannan yace "okey," sannan yasa kai ya fuce, A jiyar zuciya ta sauke tare da samun wuri itama ta zauna, bayan ta ajiye jakan kayan data zo da ita,  kallon juna suka shiga yi suna murmushi,yanayin iskar falon badae daɗi ba yadda sanyin ac ke ratsa sassan jikin mutun,   Ganin sun zauna shiru yasa Camila cewa "ba ku buƙatar shiga daga ciki ne? ta tambaya tana kallonsu  Jahad ce tafara cewa "inason nayi wanka, hossana ma tace "nima,"  tashi camila tayi tare da cewa "mu shiga daga cikin ɗakin to, nima inason nayi wankan," tayi maganar tare da ɗaukar jakar kayanta,  gaba tayi suka bi bayanta ɗaya daga cikin bedrooms ɗin suka tunkara, ƙoparsa a rufe take amma bada key aka datse ta ba, hannu tasa ta tura nan take ƙopar ta buɗe, shiga ciki su kayi atare, haɗaɗden bedroom mai ɗauke da tafkeken gado fankacece, yaji lumbutsetsiyar katifa lallausar gaske ga wasu matassan kai masu laushi asama an jera su, irin gadon da kana hawa saman shi ko bakayi niyyar yin bacci ba nan take zai ɗauke ke saboda daɗinsa 🥱 an gyare komai an shimfiɗe shi da bedsheet,side by side na gadon akwai side drawers, masu ɗauke da lamps, daga can ɗayan bangaren ɗakin kuwa wurin Closet dinsu ne, ga wani haɗaɗɗen Dressing mirror an cika masu front dinshi da kayan make up da tsadaddun mayuka na jiki, komai an sanya masu, jerin wurin takalmansu,hand bags da sauran abubuwa da dama ba abun da omar yabari komai ansa masu,   jahad ce tafara shiga toilet ɗin don a ƙagare take da tayi wanka,lokacin da ta shiga cikin toilet nan fa taga zallar haɗuwa ta jima tana bin ko'ina da kallo kafin daga bisa ni tayi wankar daker tare da yin alwala saboda in an kira sallah tayi, fitowa tayi a hankali waist dinta daure da towel mai ɗan tsayi wanda ta samu acikin toilet ɗin, hannunta na ruƙe da doguwar rigarta da ta cire, samun su tayi zazzaune daga gefen gadon suna fira da hossana da Camila,  Ganin ta fito yasa camila tashi ta shiga toilet ɗin, a cikin laundry basket ta turo rigar, sannan ta ɗan juya ta kalli hossana dake ta faman lumshe ido alamar bacci tace "karfa kiyi bacci don na son halinki, ki bari kiyi wanka ke ma,"  Murmushi tayi kafin tace"ae bazan iya bacci ba jahad, saboda gani nake kamar in na kwanta zan farka na ganni a gidan wannan matar da ta azabtar damu,nakasa yarda cewa wai mune acikin wannan katafaren gidan nan mu kaɗai abun mu,gsky yaya omar ba ƙaramin ƙaunarmu yake yi ba,"   Jahad tace"nikaina ina mamakin hakan hossana,ashe akwai wata rana da zato mana irin wannan,mun samu yaya mai son mu tamkar ƙannensa duk don saboda mu ya Omar yabar komai nasa don ya ceci rayuwarmu,har yanzu ina mamamkin hakan hossana, yaya omar ya sanar dani cewa ɗan uwanshi yana kwance rai hannun Allah babu tabbacin cewa zai rayu,amma a hakan ya tsallake shi yazo wurin mu wannan wane irin mutun ne?samun mai iri Kyakkyawar zuciyarshi zaiyi wuya a faɗin duniya (shiyasa Hafsat bature take kamu) 🙄   ta yi maganar ne a lokacin datakai wurin closet tana neman ta inda zata buɗe shi,tana aza hannunta a jikin closet din nan take doors din dake jiki suka zuge da kansu, har sai da jahad ta ɗan tsorata tayi baya,tasowa hossana tayi itama tana kallon wurin kayan nasu, yadda suke tagwaye haka omar yasa aka jera masu komai kala biyu, jerin wurin pyjamas ɗinsu daban, jerin wurin dogayen riguna daban,jerin wurin jeans da t shirt daban, ga jerin under wears shima daban, komai nasawa ajiki an zuba masu shi,har sun wuce iyaka,  "jahad har naji inason nayi wanka wlh,saboda in canza kayan jikina," acewar hossana dake ta faman yarfa hannu tana kallon kayan,  Hannu jahad tasa tare da curo wasu pakistan masu kyan gaske,tana shafa jikinsu tunkan tasa har ta gano kyan da zasu mata,    a gefen gado ta ajiye su, sannan ta koma gaban mirror tana shafe jikinta da ɗaya daga cikin mayukan da tagani ajare, bayan ta kammala ta kuma feshe jikinta da turare mai ƙamshin gaske,   Sannan ta dawo ta tsaya a gefen gadon tana zura kayan ajikinta, duk hossana na can tsaye wurin closet ɗin tana ƴan ta6e ta6e,ji take tamkar tabi kowannansu ta gwada ajikinta,  Bayan jahad ta gama kimtsawa cikin pakistan din komawa tayi gaban mirror tana kallon jikinta,riga ce mai dogon hannu har guiwar ƙafarta sai wandon burgujeje irin nasu,ta yafa mayafin asaman kafaɗarta, sumar kanta kuma ta zubo a bayanta, murmushi kawai takeyi tana kallon kanta a cikin mirrow,  Muryar hossana ce ta katse ta da cewa"kinyi kyau sosai jahad saina ga kin koma mun tamkar ketrina kef,"   Jahad tace"sannu shugaban makaryata ni bada ketrina nake kama ba sai dae helen,oumma tace kamannin mu sak irin nata,' tayi maganar tana gyara gefen gashinta da hannunta,  Hossana tace"wacece helen kuma"?  "Ƴar film ce mana ta ƙasar ethiopia," Jahad ta bata amsa atakaice, kafin hossana ta ƙara cewa wani abu, sai ga Camila tafi to daga toilet din daga ita sai ɗan pant da bra, cikin sauri suka sanya tafukan hannayensu tare da rufe fuskokinsu cikin jin kunya,  tsayawa tayi tana kallonsu cikin mamaki take cewa"why are u hidding ur face pls? Can i know  Jahad tace"mun ji kunya ne,"  Murmushi camilla tayi tare da girgiza kai tace"kuna da kunya sosai,in dae haka ne kam ba zaku iya rayuwa a ƙasar mu ba,"   "Wata ƙasa ce"? Hossana ta tambaya,  Camila tace "Mexico," Jinjina kai tayi tare da cewa"ni ko sunan ƙasar ma ban ta6a ji ba gsky...."jahad ce ta katse ta da cewa "hossana zoki wuce kije kiyi wankan kema," Amsa mata tayi da toh sannan ta wuce cikin toilet ɗin,  Ita kuma jahad ta kama hanyar fita daga ɗakin har lokacin fuskarta na rufe da tafin hannayenta, abun sai ya ba camilla dariya sosai,  Sai da ta fita daga bedroom ɗin sannan ta soma sauke ajiyar zuciya, shiga cikin falon tayi, tana ƙare masa kallo, zagaye shi ta shiga yi tana tatta6a dogayen curtains ɗin dake kewaye dashi,   Sallamar Osman ce ta dakatar da ita, cikin sauri ta amsa mashi da wa'alaikum salam,sai da ya fara tambayar iznin shiga daga ciki, ta amsa mashi sannan yasa kai cikin falon,   Hannun shi na ruƙe da manya ledoji na abincin da yayi masu oder a restaurant,yarda yaga jahad ta kimtsa tamkar ba ita bace ya gani acikin daji ba sume cikin ciyayi,ba don akwai dressing na ciwo a forhead dinta ba, da bazai iya shaida taba, .murmushi kawai yayi tare da miƙa mata ledojin hannun shi, cikin sauri tasa hannu ta kar6a tana yi masa godiya,  Har ya juya zai fita sai kuma ya juyo ya kalle ta yace"pls game da abunda ya faru da ku a gidan yayan Omar,wurin matar yayan shi kada ku sanar dashi komai don nasan zai tambaye ku ne,  Murmushi jahad tayi tace"insha Allah ba zamu sanar mashi ba,"  "Yawwa" ya faɗi tare da juyawa yasa kai ya fuce,   Ajiyar zuciya ta sauke tare da ajiye ledojin a saman table,tana jiran su kammala kimtsa wa su fito suci atare,   Goya hannayenta tayi a ƙirjinta tana faman sakin murmushi,bakowa ne ke faɗo mata aranta ba face yaya Omar dinsu,ta ƙosa ta sashi a idonta saboda tayi mashi godiya sosai,kuma tayi missing din wannan kyakkyawar fuskar tashi,   tana cikin wannan tsayuwar sai ga Camila ta fito fes abunta har ta canza kayan jikinta,v neck shirt ce ajikinta fara sai wando jeans, ta ɗaure sumar kanta da ribbom,fuskarta asake ta ƙaraso tare da samun wuri saman 3 seater ta zauna tana kallon jahad tace"kina so ciwon naki ya dawo sabo mu koma asibiti gobe ko?  Girgiza kai jahad tayi tare da cewa"a'a bansan na take ta bane,ciwon bai mun zafi yanzu ina ji kamar naji sauƙi ma,"   Tace "duk da haka yakama ki kula just in case,"  Amsa mata tayi da toh sannan tace "ga abinci nan,an aiko mana shi," ta fadi tare da ƙarasawa wurin table ɗin ta matsar mata dashi kusa da kujerar da take zaune,   Sannan itama ta samu wuri ta zauna a kusa da ita,hannu camila tasa ta buɗe ledar ta farkon,kayan ciye ciye ne gasu nan chips, bugger, shawarma da sauran wasu tarkacen, ɗayar ledar kuma da ta bude masu fried meat ne (tsiren nama) mai yawan gaske yaji kayan haɗi sai ƙamshi yake yi,  Dole ne su buƙaci plate don haka jahad ta tashi tare da cewa "bari na ɗauko mana plate," camila tace "plate yayi kaɗan tray zaki samo mana," Amsa mata tayi sannan ta tunkari doors din dake a cikin falon tana neman kitchen babu alamar kitchen na a wurin,  "Ki duba down stairs baza arasa acan ba," acewar camila,  Cikin sauri jahad ta hau benen da zai sauke ta a dowm stairs tana sauka cikin sittingroom din ta hango kitchen ɗin, tasha mamakin ganin yarda aka ƙawata ɗakin,  Cikin hanzari ta wuce kitchen ɗin an tsara shi sosai,ƙarasawa tayi jikin kitchen shelves anan ta samu trays a jere ta ɗauki ɗaya,komai na cikinsa sabone wasu acikin kwalinsu wasu kuma a buɗe suke, tare da cokali ta haɗo masu da knife saboda taga tsiren naman basu zuge shi ba acikin tsinken shi yake,zasu buƙaci su yayyanka shi in zasu ci,  Fitowa tayi daga kitchen ɗin sannan ta koma upstairs ɗin, tunkan ta ƙarasawa ta samu hossana zaune agefen camila hannunta ɗauke da tsiren naman nan ta tura abaki sai ci take kamar kura,hankalinta kwance, bakomai bane ya burge jahad ba face ganin yarda hossana tayi wani irin kyau cikin gajeran skirt mini tare da riga ƴar t shirt tabi shape din jikinta, hada ƴar hoda ta shafa ma fuskarta da jan baki,   Ganin jahad ta soma washe mata baki, girgiza kai jahad tayi tare da cewa "dama nasan dole kiyi ƙara'e hossana irin wannan ɗaukar wanka haka,"   "Kaɗan kika fara gani ma,aunty camila ma tace in ta samu hutun aiki zata kaimu saloon a gyara mana gashi tare da ƙunshi ma duka za'a yi mana,"  murmushi jahad tayi a lokacin taƙarasa wurin table ɗin, aza tray ɗin tayi asaman shi sannan ta samu wuri ta zauna itama suka saka Camilla a tsakiyarsu,   ita ta baje masu tsiren acikin tray ɗin ta jera masu shi,sannan ta zuba masu chips ɗin daga gefe,   Nan fa suka gyara zama duka ukun suka tasar ma kayan lashe lashen, ba baka sai kunne, ba kaji komai sai sautin taunar shi da suke abakinsu,
**********************SEHRISH
tun da english teacher ɗinsu ta fita daga class ɗin, sehrish ta kifa kanta asaman desk din gabanta tana ta sharar bacci, har amrish ta gane mata daga jiya izuwa yau sam bata gajiya da yin bacci,alamu ma sun nuna cewa bata fahimtar komai kanta dashi da kwankwon ashana duk ɗaya suke,tashi amrish tayi tare da fitowa daga seat ɗinta ta ɗan sa hannunta tare da bubbuga bayan sehrish tace"ki tashi mu tafi time ɗin break yayi," kusan sau uku tana tashinta daƙer ta buɗe idonta da suka canza launi saboda bacci, miƙa tayi tare da yin hamma alamar yunwa take ji ga baccin ma bai isheta ba, fitowa tayi daga seat ɗin nata tana cewa"ashe har lokacin break yayi " Amrish tace"taya za'ae ki sani, bayan baccinki kawai kike tasha, anya kuwa ma kina yin bacci a gida ne? Ta tambaya tana kallonta a yayin da suke fita daga class ɗin,  "Ina yin bacci mana sosai,"_ "To meyasa kike yin bacci a class?ko karatu ma bakya saurara salon azo yin test ko exam kiyi ta baza idanu kina kallon question paper kina cizon biro ko? Ta fadi fuskarta ɗauke da dariya, itama sehrish din dariya tayi tana cewa "insha Allah hakan ma bazata faru ba,kafin lokacin zanyi karatu sosai,"  Suna tafiya suna fira har suka isa Lunch room ɗin nasu atare suka shiga ciki, students duk sun hallara suna ta having lunch dinsu,  ruƙo hannun sehrish tayi tare da kaita gaban table ɗin da zasu zauna,sai da rishi ta zauna saman table chairs din sannan amrish ta wuce ciki don ta amso masu abunda zasu ci,  Ajiyar zuciya sehrish ta saki tana kallon students din dake zaune a wurin suna cin abincinsu suna shan fira abunsu,zahiri su take kallo amma abaɗi ba komai take tunawa ba face fuskar SGR ɗinta,murmushi ta saki aranta tana cewa "koyana ina yanzu?me yake yi?ko yaci abincinsa?Allah yasa dae baibar cikin shi da yunwa ba, babu mai bata amsar tambayarta, cigaba da cewa tayi"bani da wani burin daya wuce naganshi cikin nishaɗi batare da wata damuwa ba,amma narasa dalilin dayasa kullum fuskarshi aɗaure baison yin fara'a,inaso na kawo sauyi a cikin zuciyar shi ya Allah ka bani wannan damar da zan zama ɗaya daga cikin farin cikin ran shi,"   Gaba ɗaya tayi nisa acikin tunaninta, batasan meke wakana ba kwatsam taji hannun mutun a ƙirjinta an shafa mata, a wani irin firgice ta buɗe idanunta gabanta na faɗuwa,   Bin su da kallo tayi atsananin tsorace, kai kana ganinsu kasan tantiran ƴan iska ne,su biyu ne mata jikinsu na sanye da uniform riga da wannan mini skirt ɗin,kai kace ba musulmai ba saboda ko head babu akansu, iya gashi ne kawai suka ɗaure abayansu shima ɗin na ƙari ne, ga uban bleaching sun sha abun dae kawai ba'a magana,.  Kallon juna su kayi suna dariya kafin ɗayar tace "wow gaskiya an mana nisa, Sofia tun yaushe aka kawo wannan zazzafar a school ɗinmu batare da sanin mu ba"? ta tambaya tana faman sakin murmushi gefen fuska, tuni jikin sehrish yayi mugun sanyi bakomai ta tuna ba face nasihar da kanal yusuf yayi mata kafin tafara zuwa school,  wadda ta kira da sofia tace"ni kaina bansani ba, amma yanzu tunda Allah ya haɗamu da ita, zatayi mana bayani ne, ta faɗi tana kallon sehrish tare da kashe mata ido ɗaya tace"ƴan mata,naga kin ɗaure fuska may be don na shafa chest ɗinki ne batare da izninki ba,ae mun afwa irin salon tamu gaisuwar kenan,ya sunanki ne"?   ƙara tamke fuska sehrish tayi jikinta na rawa Allah Allah take yi Amrish tadawo don tasan ita zata iya dasu,   ɗan ta6e baki zeenat tayi tare da cewa"Can't u talk to us? May be don baki son ko mu su wanene ba a school ɗin nan ba,zamu yi maki uziri ne," ta faɗi tana yarfa hannunta, yatsun nan zira zira tayi fixing nails dogaye a hannunta,   shiru sehrish tayi burinta amrish ta ƙaraso in ba haka ba tashi zatayi tabar musu table din gaba ɗaya ta koma Class, duk da yunwar da take ji acikinta,  Suna cikin zaman ne sai ga Amrish ta ƙaraso fuskar nan ɗauke da murmushi ta ruƙo tray a hannunta mai ɗauke da plate biyu na abincinsu tare da coke,  Sehrish na ganinta ta shiga sauke ajiyar zuciya,amma abunda ya daure mata kai time ɗin da amrish ta ƙaraso kai tsaye bayan ta ajiye masu tray ɗin asaman table din, sai ta miƙa ma Zeenat hannu suka gaisa tare da cewa"Am really glad to see u guys, nayi missing ɗinki sosai my zeenat," murmushi zeenat tayi tare da cewa"nayi missing ɗinki nima,bcox of u na matsa wa mommy sai mun dawo nigeria sbd a ƙagare nake da na haɗu dake ko fa isasshen bacci bana samu saboda rashinki,"   bin su da kallo kawai sehrish takeyi baki asake, yarda suke magana tamkar irin mace da namijin nan,  Muryar sofia ce ta katse su da cewa "oh ni ba'a ma ta tawa ko Amrish? Zeenat kaɗai kika gani shikenan bari na tafi," ta faɗi tana ƙoƙarin tashi cikin sauri Amrish tayi holding hands dinta tana cewa"am sorry kada ki tashi pls, in naga zeenat ina mantawa da komai ne,"  ɗaure fuska sofia tayi tace"i can't stay here,cos am getting jealous bazan iya jure yarda kike son Zeenat ba,  Dariya zeenat tayi tana cewa"in dai akan Soyayyata da amrish ne ke 6ata maki rai sai dae ki mutu,"   ta faɗi tana mayar da idonta akan sehrish da tayi zugudun tana kallon ikon Allah,  wuri Amrish tasamu ta zauna, kusa da sehrish suna facing ɗin su Sofia da zeenat,  ɗan kallonta amrish tayi tare da cewa"am sorry my friend nabarki da yunwa ko"? ta faɗi tana kallon Sehrish wadda jikinta ya gama mutuwa,  "A'a" ta bata amsa a takaice, Mayar da idonta tayi kansu zeenat tace"bansan zaku zo ba ae dana haɗo mana abincin tare,amma bari na tashi yanzu naje na ƙaro mana yadda zai ishe mu,"  cikin sauri zeenat tace"no ba sai kinje ba its ok ba mu jin yunwa a ƙoshe muke,"   murmushi amrish ta saki tare da kallon sehrish tace"bismillah mufara ci time ɗin komawa class ya kusa,"   Gaba daya hannunta kerma yakeyi a haka ta ɗauki spoon ɗin zata fara cin fried rice din da takawo masu shaqe da plate,tana ɗebowa shinkafar na zube wa saboda rashin natsuwar da take ciki ba don komai ba sai don zeenat data tsare ta da waɗannan manyan idanun nata zubin na karuwai a tsaitsaye suke ga eye lashes da tayi fixing sinsu kamar ɗiyar roba,  Ganin yarda hannun sehrish ke kerma ta kasa kai koda one spoon ne yasa Amrish ɗagowa ta kalli zeenat wadda ta zuba mata ido ko kyafta su bata yi,  ɗan gyaran murya Amrish tayi tare da cewa"Zeeta pls kidaina kallonta hakan na hana ta samun natsuwa,class mate ɗina ce jiya tafara zuwa school bata saba da kowa ba,"  ƙayataccen murmushi zeenat ta saki tare da cewa"its okey,ashe new comer ce, tayi mun kyau ne shiyasa nagaza janye idona akanta,ina fata kin sanar da ita komai game da zama cikin team ɗin mu?  Cikin sauri amrish tace"a'a pls mubar maganar nan,ita ba'a team ɗinmu take ba kawai class muka haɗa da ita,"   zeenat tace"that's impossible amrish tun da har kina yawo da ita a school dole ta zama ɗaya daga cikin mu,not only that yarinyar ta burgeni sosai........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda ƙarar cokalin amrish data bugi gefen plate dinta dashi tace"Zeeenat! Nace kidaina wannan maganar agabanta bana so," rai a6ace tayi maganar sannan ta mayar da idonta kan sehrish tace"pls ki ci abincin ki,"  gyaɗa kai sehrish tayi tare da mayar da hankalinta akan abincin dake gabanta,ci take amma batasan inda abincin ke zuwa ba,saboda tsoro da ruɗin da ta shiga,  yunƙurawa su kayi su biyun atare suka miƙe, cikin sanyin murya amrish tace"Am sorry zeenat i don't mean to hurts u,just bana son muna wannan maganar agabanta ne,saboda batasan komai ba ko mutane batason shiga cikinsu," hankali atashe take maganar tana kallon su,  atare suka yatsina fuska sannan zeenat tace,kinsan bana fushi dake amrish shiyasa kike mun duk abunda kika ga dama,amma ina so ki sani 6ata mun rai tamkar 6atawa mommynki raine, kuma kinsan mai zo biyu baya ya zama dole kibi umarnin duk abunda nace, don haka wannan yarinyar dole tashiga team ɗin mu !!!  tana gama faɗin hakan taja hannun sofiya suka fuce daga lunch room din  ita dae sehrish zuru tayi tana kallon ikon Allah bayan sun fuce ta mayar da idonta kan amrish wadda jikinta yayi mugun sanyi tuni kuma idonta sun cicciko da kwalla, amma bata bari sun zubo mata ba, sai ma kallon sehrish da tayi tare da ƙaƙaro murmushi tace"ki ci gaba da cin abincin ki mana,naga kin tsaya,"  jiki asanyaye sehrish ta mayar da hankalinta kan abincin tana ci amma zuciyarta ajagule saboda halin da taga Amrish ta shiga akan waɗannan ƴan matan da suka zo,ko su wanene oho, Ta tambayi kanta,
***************************Twins
Fitowarsu kenan daga wanka atare kamar yarda suka saba kwatsam sai ga haroon ya turo Æ™opar É—akin nasu fuskarshi É—auke da wannan shu'umin murmushin nashi, tsayawa yayi yana binsu da wani irin kallo jikinshi na sanye da Crazy jeans tare da wata figaggar riga daya sanya, ya tada kwalar rigar tsaye,sam haroon baya kama da musulmai ko a fuska, balle ma daya kasance yana sanya chain a wuyan shi da kuma earrings irin yarda jigunannun Æ´an iska ke sakawa,  Kallon juna su kayi atare kafin suka mayar da idanunsu akanshi,tuni ran Jahan ya 6aci ganin yarda yake bin jikinsu da kallo kamar wani tsohon maye, dama daga su sai short towels ajikinsu, farar surar ne mai jan hankali ta bayyana muraran,  ɗaure fuska jahan yayi tare da cewa "me ya kawo ka É—akin mu? me kuma kake buÆ™ata,indai kuÉ—i ne suna nan zamu baka,"  ta6e baki haroon yayi tare da yatsina fuska yace "yakamata kasan yarda zakayi magana dani with respect,ko don darajar wannan videon dake ajiye acikin wayata,'  tsuke fuska su kayi atare zuciyarsu na tafarfasa tamkar su rufe shi da bugu haka suke ji,   Cigaba da magana yayi "zuwa nayi don na Æ™ara tunasar daku, don na lura kamar kun manta da maganar dukiyata dake a wurinku, saboda waccan farin balbelen É—an uwan naku da bai lfy na lura duk kun wani tashi hankali akanshi,'  Buga tsoki ayaan yayi yace "kada ka sake kiran shi da sunan balbela kadaina haÉ—a sunayen mu dana dabbobi domin kuwa mu bamuyin munayen É—abi'un da za a haÉ—a sunan mu dana dabba, domin kuwa dabba yasan inda yake"  waro ido waje haroon yayi jin abunda ayaan yace a tsananin mamaki yace "Ayaan ni kake kira da sunan dabba"?! Ya tambaya a dan fusace  Cikin sauri jahan yace"kayi shiru ayaan kada kaja mana wani bala'en don na lura bai da Imani ko misÆ™ala zarratin, tunda har bai damu da halin da É—an uwansa ke ciki ba, burinsa kawai ya Æ™untata ma rayuwarmu," yayi maganar yana jefar haroon din da mugun kallo,  fashewa da dariya haroon yayi hada dafe cikinsa kafin yace "Waye kuma É—an uwana? ae ni bana É—aukarku jini na,ko ajinsi ku farare ne ni kuma baÆ™ar fata ne, in fact ni bani da wata alaÆ™a daku, Uba fa kowa muka haÉ—a uwa kuma kowa da tashi, bayan shi kuma sai me?  shiru su kayi suna sauraron shi gaba É—aya tsanarshi Æ™ara ninkuwa take yi acikin zuciyarsu,   juyawa yayi tare da cewa "Zan wuce ni ku huta lpy Æ´an samari," yana faÉ—in hakan ya fuce yana sakin dariya kamar zautacce,  Mayar da ido ayaan yayi kan jahan yace "bro i ave an advise abt that bastard, why not mu kashe shi kawai kowa ya huta, cos i don't think ko mun bashi kuÉ—in zai goge videon,"   aÉ—an razane jahan ya kalle shi yace "ashe baka da hankali ayaan, kisa fa kace? Mu zamu kashe shi? In muka jefa kanmu cikin matsala fa? ya fadi yana kallon sa,   Ayaan yace "ba wata matsala jahan, just lettus kill him kowa ya huta !!!!!!!!!   "Mu bashi time in har muka bashi kuÉ—in bai goge videon ba, sai mu kashe shi kawai,don da abunda zai ta6a mutuncin family dinmu gwara abunda zai tada masu hankali na É—an wani lokaci ya wuce" Acewar jahan,  Gaba daya sun amince da shawarar kashe haroon 😳 Duk mutanen da suka zo duba fawan duk sun ragu, har sun mai dashi daki sun kwantar dashi tun É—azu,  Junaid kuwa lokacin da Abban su yashigo dashi É—akin shi ya wuce dashi tare da kwantar dashi ya farfaÉ—o daga suman da yayi amma ya dasa da bacci,Â
 Yanzu wanda suka rage a cikin gidan daga su matasan gidan sai abokin su sgr Shattima sun hallara a garden din gidan suna tattaunawa tare da marshal Omar dashi babban yayan,   Cg Abbas ya jima da tafiya amma yabar Amani a gidan saboda yace zai dawo da daddare ya ɗauke ta, duk ita ta taya azmee rarraba ma masu zuwa dubiya lemun a cups har suka lafa,
  shigowa ɗakin Abbansu yayi yana kallon junaid dake baje asaman bed dinsa yana ta sharar bacci, ƙarasawa yayi wurin shi tare da zama daga gefen gadon nashi, sannan yaɗan sa hannun shi tare da bubbuga ƙafar junaid kamar mai jira aikuwa a firgice ya tashi zaune yana faman zazzare kyawawan idanun shi da suka canza launi saboda bacci, yana jin muryar abbansu ya kira sunan shi nan take ya fashe da wani sabon kukan yana cewa "Abba yaya fawan ! Yana ina ! meya faru dashi.....' Murmushi abbansu yayi yana kallon shi yarda yake kuka yana magana red lips din nan nashi na shagwa6a66u sun tatta6e,   Cikin natsuwa abban nasu ya soma cewa "Calm down ur mind junaid,ɗan uwanka yana cikin ƙoshin lpy yanzu haka yana can medical room dinmu mun kwantar dashi, shima sai kiran sunanka yake yi yana cewa Abba ina junaid akawo mun shi in ganshi, inaso in ganshi,"   jin wannan maganar ta abban nasu yasa junaid dakatawa da yin kukan nashi ya zuro da ƙafarsa zai sauko daga saman gadon, abbansu ya ruko hannun shi tare da cewa "pls junaid kada kaje mashi kana wannan kukan saika tayar mashi da hankali yaga kamar mutuwa zaiyi,  Cikin sauri junaid yasanya tafin hannayenshi tare da share hawayen dake zubo masa sannan abban nasu ya saki hannun shi, jikin shi har rawa yake yi wurin saukowa daga gadon, bin shi da kallo abban yayi har cikin ranshi yana mamakin yarda junaid ke tsananin son ƴan uwanshi don ji yake yi da wani abu ya same su kwara shi ya same shi koda mutuwa ce,akwai wani lokaci da abbansu bazai ta6a mantawa ba in ya tuna abunda ya faru har dariya yake yi wani sa'in kuma yaji saukar hawaye, wannan ba kowane lokaci bane face lokacin da junaid yana da kananun shekaru, idan suka je masallaci tare dashi suke zuwa saiya bari an kammala salla an natsu liman na kora addu'a, sai shi kuma ya ɗaga hannayen shi sama ya ɗaga murya yana cewa "Ya Allah ya Allah kasa na riga Abbana mutuwa da ƴan uwana,ya Allah kafara ɗaukar raina kafin nasu," a lokacin kowa mamaki ya kama shi jin abunda ƙaramin yaron kecewa, har wasu ke tambayarshi dalilin dayasa yake son ya riga abban nasu mutuwa da yan uwan shi sai cewa yayi "Saboda idan na riga su mutuwa bazan ga tasu mutuwar ba in tazo,zuciyata zata samu salama akan na rasa su da raina," gaba daya mutanen dake a masallacin abun ya basu mamaki sosai, kuma ka'ida ne duk in suka je masallaci tare dashi dole liman ya jira shi ya kammala addu'o'in shi mutane na amsa mashi da ameen, kafin shi liman yayi tashi addu'ar saboda rigimarshi,  Murmushi abbansu ya saki lokacin daya kammala tunanin nashi aranshi yace "Allah yabar mana kai junaid,ni kuma banaso naga mutuwarka nafiso nariga kowannan ku mutuwa don bazan juri ganin gawar ɗaya daga cikinku ba a kan idona," jikin shi a kasalance yake wannan zancen zucin,
 Wayarsa ce ta soma ringing daga cikin aljihun rigarsa ta yadi, cikin sauri ya zura hannu ya ɗauko ta tare da duba sunan mai kiran nasa sunan AMMI ne ya bayyana akan screen din wayar hakan na nufin mahaifiyarshi ce Ammi ke kiransa
  Nan da nan ya shiga natsuwarshi tare da É—aga kiran ya kara a kunnan shi ya zabga sallama,  daga can bangaren Ammi ta amsa mashi sallamar sannan tace"yaro na ya kake ya kuma jikokin nawa? Naji abunda ya faru da fawan shiyasa ma na kira don na tambayi ya jikin nashi,   Tamkar yana agabanta cikin biyayya ya soma magana "lpy lou ammi suna cikin Æ™oshin lpy,amma ba zaki zo gida ki duba jikin nashi ba?  "Hmmmm ni me zanzo inyi agidanka? Ae yafi Æ™arfi na, daga nan ma zan iya yi masa ya jiki ba sai na kwaso jiki nazo ba balle inga abun tashin hankali abun kunya,'   nan da nan fuskar Abban nasu ta canza jin abunda tace,   "Ammi dan Allah kidaina faÉ—in hakan bana jin daÉ—i saboda me zaki ce gidana yafi Æ™arfinki bayan nikaina a Æ™arÆ™ashin ikonki nake ke fa kika haife ni, kuma wane irin abun tashin hankali da abun kunya kike magana akai"? yayi maganar fuskarshi a yamutse,  tsoki taja tamkar zata fasa screen din wayar sannan tace "babu wani iko da nake dashi akanka hussein! Tunda har ban isa nasaka abuba kayi, wato son Æ´a'Æ´a ya rufe maka ido ko? ka daina ganin kowa da gashi? ba yarda banyi dakai ba akan ka tattara Æ´a'Æ´an nan duka ka haÉ—asu ka aurar kaÆ™i jin maganata, ka tara Æ™attan maza,garada acikin gida sai sinturi suke yi acikin gidan ka,kaine jagoransu kai Gwauro su kuma tazurai gasu nan jibga jigba dasu kaÆ™i aurar dasu, daga anyi magana sai kace baka son ka takura masu ko kace ba su isa suyi aure ba don ka rainawa mutane hankali, dukansu kaf babu wanda in aka aura masa mace bazai iya yi mata ciki ba hatta wancan shagwa6a66en daka sangarta.......'  runtse ido abbansu yayi tare da saurin cewa "Ammi dan Allah kidaina fadin hakan, aure fa lokaci ne kuma in yayi duk zan aurar dasu ne.....'   wani tsokin ta sake buga mashi kafin ta kuma cewa "haka kullum kake faÉ—amin, narasa meyasa Æ´a'Æ´ana duk basu jin maganata,daga kai har azeeman da wancan fitsararren da yayi hijra yabar Æ™asar batare da sani na ba, ban ta6a tunain hussein zaka yi mun haka ba saboda duk kafi yi mun biyayya acikinsu amma yanxunn. .....' kukan da ta fashe dashi ne ya yasa ta kasa Æ™arasa maganar nan take hankalin abbansu ya tashi, muryarsa har rawa take yi wurin cewa"Ammi dan Allah kidainamun kuka, ke fa mahaifiyata ce saboda me zakiyi mun kuka, hakan zai iya jefa rayuwata cikin matsala,dan Allah kidaina na roÆ™e ki mommyna indai akan wannan maganar ne yasa kike mun kuka wlh ashirye nake da nayi maki biyayya koba da son ransu ba, zan aurar dasu ne kawai saboda farin cikin ki !!!!!  jin abunda yace ne yasa ta sassauta kukan nata tace "yaushe kenan zaka aiwatar da hakan? kasan natsufa sosai kada na mutu ba'ayi auran nan ba, dan Allah hussein ka tattarasu duka ka aurar a lokaci É—aya in har kayi mun hakan zan shaida cewa kai hussein É—inane dana haifa,'   Ajiyar zuciya abban nasu ya sauke yana kara gyara wayar a kunnan shi yace "Insha Allah ammi nan bada jimawa ba,amma ki ban time saboda yanzu muna cikin fargaba game da waÉ—anda suka kaima su fawan hari,kin san sunce fansa suke É—auka,kuma babban tashin hankalin ma maca ce AVENGER É—in,'  shiru ammi ta É—anyi kafin tace "Shikenan hussein,nima na shiga damuwa dana ji hakan,dama nasan dole hakan ya faru saboda mahaifinku kafin yabar duniya ya tara maÆ™iya sosai kasancewarshi kwararren jami'en Soja sun halaka dubban masu tada Æ™ayar baya a Æ™asar nan, shiyasa nake tunanin ko daga 6angarensa ne maÆ™iyan suke son É—aukar fansa,duk da nasan cewa wannan mai shuÉ—in idon baya rasa maÆ™iya don mutun ne mai haÉ—arin gaske shima baya gajiya da kame Æ´a'Æ´an mutane yana kaisu lahira, kaga kuwa dole su É—auki fansa suma,yakamata kasanya tsaro sosai agidanka, kuma akwai shawarwarin da nakeso na baka,"   Abba yace "Ammi dan Allah kixo gida mana,ina ga zaifi in kika zo sai mu zauna mu tattauna akan matsalar tunda wannan abun ya shafi zuri'armu, kuma nama fi jin cewa akaina abin zai Æ™are tunda ni ne na tara Æ´a'Æ´a,"   Ammi tace "shikenan zan fidda lokaci nazo insha Allah, amma inaso ka sani in zanzo saina tattara Æ´an matan family É—inmu gaba É—aya na kwaso su don suzo ayiwa Æ´a'Æ´anka baiko dasu,"  dariya kawai abba yayi yana sauraronta sun jima suna fira kafin daga bisani su kayi Sallama 😊  ya ajiye wayar gefen shi yana É—an murmushi,   A can kuwa junaid na isa É—akin da fawan yake kwance yana bacci, cike da tausayi yake kallon shi yadda yake jan numfashi da Æ™arfi da Æ™arfi,  ƙarasawa yayi tare da hayewa saman gadon yayi zaman cin tuwo tare da zabga uban tagumi yana kallon shi hawaye na zuba a fuskarshi,  Jin shessheÆ™ar kukan junaid a kunnan shi yasa shi farkawa daga baccin da yake yi, ya buÉ—e idon shi a hankali yana kallon shi, yarda ya tallabe fuskarshi hannu bibbiyu ya tasa shi gaba yana sharar kwalla,a hankali fawan ya furta "junaid "  Kallon shi kawai junaid yake yana cigaba da matsar kwallo,hankalinsa ba Æ™aramin tashi yayi ba ganin yarda jikin fawan yayi ruÉ—u ruÉ—u da bulali wurin yayi jawur ya faffashe duk da anyi masa dressing na wurin an shafa masa magunguna,ga kuma É—inkin da akayi masa a chest É—inshi,  dakyar ya daddage ya tashi daga zaune yana fuskantar junaid É—in daya tasa shi gaba,   "Junaid," fawan ya sake ambaton sunan shi a karo na biyu ganin yarda ya zabga tagumi yana kallon shi hawaye na zubowa gefe da gefen fuskarshi, zama su kayi suna fuskantar juna, kallon shi kawai junaid keyi batare da yace uffan ba,  daÆ™yar fawan ya Æ™aÆ™aro murmushi yana kallon shi, hannun shi yakai tare da shafa gefen fuskar junaid yace "bari nabaka wani labari Æ™anina," junaid ya zuba mashi ido yana sauraron shi,  fawan yace "lokacin da waÉ—annan miyagun suka É—auke ni ko, suka shiga dani wani Æ™ogon dutse mai rikitarwa, suka ban za6i biyu, su kashe ni ko su azabtar dani wanne nakeso, kasan me nace masu? ya fadi yana kallon shi, girgiza kai junaid yayi alamar a'a,  Fawan yaci gaba da cewa "a lokacin kai kawai ka faÉ—o mun araina, aranar da zamu tafi kai ta zabga kuka kana cewa babu inda zamuje Æ™afarka Æ™afarmu dakyar abba ya shawo kanka, ka tuna abunda ka faÉ—amun lokacin?  shiru junaid yayi yana tuna lokacin daya cakumi rigar fawan yana ce "ya fawan kayimun alÆ™awarin cewa zaka dawo araye inaso na sake ganin ka,' a lokacin fawan yace mashi "junaid ae tafiya ba mutuwa bace, insha Allah zan dawo araye in Allah ya yarda," murmushi junaid yayi tuna wannan  shima fawan murmushin yayi sannan yaci gaba da cewa "saina ce masu ni bana tsoran mutuwa, ban isa na hana kaina mutuwa ba in lokacina yayi, kamar yarda kuma baku isa ku hana kan ku mutuwa ba idan tazo maku, sai É—aya daga cikin su yace mun "Ka za6i ka mutu kenan? mu kashe ka kawai? Saina girgiza kai nace "a'a ku azabtar dani kuyi mun duk irin hukuncin da zakuyi mun amma kubar ni da raina saboda akwai Æ™aramin Æ™anina da nayi ma alÆ™awarin cewa zandawo da raina, inaso na cika mashi wannan alÆ™awarin nasa na gani na araye, bana so na karya mashi zuciya nafiso ko mutuwarce ma to na mutu agabanshi yadai ganni da raina...............' dakatawa fawan yayi da maganar saboda hawayen da suka zuzzubo mashi, junaid kuwa tuni ya fashe da wani irin matsanancin kuka mai cin rai, haÉ—e kansu su kayi wuri É—aya suna faman shessheÆ™ar kuka atare,  dakyar fawan yaci gaba da cewa "Shine suka bankamun kayan maye sannan suka É—aure ni tamkar dabba, su ka dunga zuba mun bulali da kaca a jikina har saida suka ga jini na zuzzuba ajikina amma hakan bai ishe su ba, ba don su babban yayan mu sun zo ba to da tabbas kashe ni sukayi niyyar yi a lokacin, Amma alhamdlh naji daÉ—i sosai da Allah yacika mun burina na ganin na rayu don na cika maka alÆ™awarinka...... .. murmushi junaid ya saki tuni ya ji sanyi ya ratsa mashi zuciyarsa,  janye kansa yayi daga na fawan sannan yace "kana jin yunwa in kawo maka abinci"?   girgiza kai fawan yayi tare da cewa "junaid a Æ™oshe nake,É—azu azmee ta haÉ—amun kakkauran tea tare da fruits na sha,naji daÉ—in su sosai,"   "Bari nabarka ka huta sosai, na katse maka baccinka, amma ka sani zan dawo don atare zamu kwana," yayi maganar yana Æ™ara jaddada masa ayayin da yake sauka daga saman gadon,  Murmushi kawai fawan ke bin shi dashi harya fice daga É—akin,komawa yayi a hankali ya kwantar da bayansa saman filonsa tare da lumshe idon shi,   Cikin sauri junaid ya fito tare da tunkarar hanyar fita saboda tunawa da sehrish wadda ke a school, lokacin tashin su yayi gashi time na salla na kokarin wuce shi, yana dab da fita daga Æ™opar Amani ta kwada masa kira, dakatawa yayi tare da juyawa yana kallon ta da murmushi a fuskarsa, cikin sauri ta Æ™araso gab dashi tana cewa "ina zaka je ne? Junaid yace "inaso zance masallaci ne nayi sallah, daganan zan wuce na dauko sehrish daga school,"  ɗan jinjina kai tayi kafin tace "wannan yarinyar da muka gani É—azu itace sehrish"? Ta tambaya tana kallon shi duk da tasan akanta yake magana  "Yeah itace," ya bata amsa atakaice tare da fucewa yana cewa "Sauri nake aunty amani time É—in sallah zai wuce ni,"   Juyawa amani tayi tana jinjina kai, a Æ™agare take da junaid ya dauko yarinyar daga school saboda tana son ta sake ganinta har ma ta yi magana da ita, *wannan kenan*ðŸ˜ðŸ‘
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 ï¿? ï¿? ï¿? *Boss Bature*
Who's the AVENGERâ—‼ï¸â‰ï¸
**************************
Har suka koma Class jikin sehrish a sanyaye ita kuma amrish fuskarta ta nuna alamun damuwa sosai game da abun da zeenat tace mata, gaba ɗayansu dae babu daɗi har suka taso daga school ɗin,tsayawa su kayi daga wajen school din sai ga drivern Amrish ya ƙaraso, juyawa tayi ta kalli sehrish tace"Ni zan wuce,sai mun haɗu gobe in Allah yakaimu,"  Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"Allah yakaimu lpy,"  "Ameen" ta amsa mata sannan ta wuce cikin motar,  ta jima a tsaye tana jiran ƙarasowar motar junaid dalilin dayasa bata hau bus ba kenan saboda tasan dole yazo ɗaukarta,masu motoci saiyi mata tayi suke don tazo su rage mata hanya amma taƙi yarda tahau motar kowa saboda tasan cewa ba kowa bane zai ɗauke ta don Allah ba, tana cikin wannan tsayuwar ta hango motar junaid ya shawo kwana,murmushi ta soma saki tamkar tayi tsalle don murna tunkan ya ƙaraso ta tunkari motar da sauri,  yana tsayar da motar ta sanya hannu ta buɗe motar sannan tashiga ciki tare da rufe motar,  juyawa tayi ta kalle shi tare da cewa "ka manta dani ko"? Ina ta faman jiranka,"   ɗan murmushi yayi yace "am sorry ba da son raina ba reesh, kina araina ynx ma daga mosque na wuto nan,' ya ƙarasa maganar yana kallonta, bin fuskarshi tayi da kallo alamun damuwa ta gani sosai atattare dashi,tuni itama taji zuciyarta babu daɗi, cikin sanyin murya tace "junaid kayi kuka yau ko? kuma kana cikin damuwa"?   jinjina mata kai yayi alamar eh,  ɗan 6ata fuska tayi tare da cewa "dan Allah junaid kadaina sa damuwa aranka wlh bana so, natsani naga mutun mai cike da farin ciki irinka a Yanayi na damuwa,'   A kasalance yace "don't worry ur self,zan daina ne reesh da zarar nasamu abunda nakeso, ki sani acikin addu'arki da kuma sauran ƴan uwana,'  "Insha Allah junaid bana mantawa da kowannan ku acikin addu'a ta," ta fadi tana jaddada masa maganarta,   "Yanzu kayi mun dariya in gani magana kona samu kwanciyar hankali,"  tunkan takarasa maganarta, ya wage bakinsa yana dariya,bin fararen haƙoransa tayi da kallo a jere tsaf suke tamkar mai tallar maclean saboda kyal ɗinsu, ga 2 dimples dinsa da suka lotsa sosai,  Yatsanta takai acikin dimple ɗinsa ta zura shi saboda burgetan da yayi, sun jima suna shiririta acikin motar kafin ya tayar da motar suka miƙi hanya, cike da nishaɗi suke sauraron waƙar da junaid ya kunna masu ta lilin baba,natsuwa yayi a hankali yake driving yana sauraron muryar rishi dinsa dake bin waƙar  "Kaine zuciya take ta yabo🎶kaine nawa in da rai da rabo, amanar zuciya ka damkeee, da kaine zanyi Wuff, zanyi wuff zanyi wuff🎶🎶  Fashewa da dariya junaid yayi saboda daɗin waƙar da yaji, sai yaji tamkar dashi take, musamman da tadinga nuna shi da hannu tana cewa(dakaine zanyi wuff)   Tana kai baitin ƙarshe shima ya ɗauka,   "Ke ce zuciya take ta yabo kece tawa inda rai da rabo,amanar zuciya ki damkeee, da kece zanyi wuffff !🎶   Zuba mashi ido sehrish tayi tana kallon shi, yana driving yana raira wakar kuma yana ɗan waiwayon ta,  gaba ɗaya sun shagala basuyi aune ba, suka ji wata mota a bayanzu ta bugi motarsu da karfin gaske,ƙarar da sehrish ta saki ne yasa junaid sakin sitiyarin motar gaba ɗaya, aikuwa nan take motar ta karkace ta nufi wata tamkekiyar bishiya da gudun gaske,  Waro ido sehrish tayi tare da cewa "Junaiiiid !! Innalallahi wa'inna ilaigirraji'un,  Ƙanƙame shi tayi ajikinta saboda gaba ɗaya yagama rikice wa, gaba ɗaya sun ƙanƙame juna, maimakon Sehrish ta taimaka mashi ya rike sitiyarin motar yayi control dinta, Amma saita janyoshi jikinta ta kankame suka bar motar Tana control din kanta,   Cikin ikon Allah motar ta kashe kanta adai dai bakin bishiyar ƙiris ya rage su gabje ta da ba ƙaramin buguwa zasu yi ba,   Ajiyar zuciya suka shiga sauke wa tare da dagowa atare suna kallon bishiyar, Allah ya takaita wahala da motar ta kashe,   Sai faman zazzare Ido suke Yi su duka biyun, sun ji kamshin mutuwa, juyawa Sehrish yayi tare dasa hannu ta zuge glass din motar Don taga wanene ya bugi motarsu,  wata bakar motace Mai black tunted kirar range Rover, Kamar jiranta suke ta leƙo,suma na cikin motar suka zuge nasu glass din motar,  Gabanta ne yayi mugun bugawa daraaam !! Ganin mutanen dake cikin motar, giggan Yan iska ba Imani a fuskarsu bakeke ne wulik, kana ganinsu kasancewa turo su akayi, da gangan suka bugi motar Junaid din,"  duk Tasha jinin jikinta, ɗaya daga cikinsu ne ya ɗago mata hannu tare da cewa"hi We're sorry guys mun bugi motarku batare da mun sani ba,kuyi mana afwa,amma yakamata kija masa kunne ya dinga kulawa wurin yin driving yana yin tukin ganganci, hakan zai iya halakar daku wata rana,"  Suna faɗin hakan suka ja motar tasu da gudun gaske suka bar wurin,  Ajiyar zuciya ta sauke tare da juyawa ta kalli junaid wanda yayi wuri wuri da ido, duk a tsorace yake da abunda ya faru dasu,   Murya asanyaye tace "junaid kayi sauri mubar wurin nan,"  daker ya iya tashin motar sannan yaja ta da baya baya suka baro jikin bishiyar, ya hau kan titi dasu sannan ya miƙi hanyar gidan,.   gaba ɗaya sehrish jikinta ya gama yin sanyi saboda ta hasko wani abu game da bugun motar junaid da sukayi,maganar da sukayi mata tamkar gargaɗi ne sukayi mata akan wani abu da zai faru dasu,tabbas tashiga ruɗani,  A hankai suka shiga babban entry din gidan, yayi parking motar sannan suka fito atare kowa na faman sauke ajiyar zuciya,atare suka jera suka nufi cikin gidan  ɗan kallon sehrish yayi ganin tamkar ranta ya 6aci don haka yace "am sorry rishi laifina ne,nayi ganganci dana kunna mana waka acikin mota har muka shagala sosai,"  fuskarta a yamutse tace "its not ur fault junaid, ba ka yi tuƙin ganganci ba,da gangan suka bugi motar mu,karka sama kanka damuwa ni bana ganin laifinka, Allah zai saka mana ma,"  tuni yaji sanyi ya ratsa ransa, bayan sun shiga babban falon ta wuce bedroom ɗinta, shima kuma ya wuce nasa ɗakin,   Shaf shaf ta tu6e uniform ɗinta, asaman gadon tabarsu tare da school bag din duka, toilet ta fada tayi wanka tare da dauro alwala, tana fito wa ta bude wardrobe dinta tare da ciro wata gown mara nauyi ta zura, sannan ta shimfiɗa carpet ta zura hijab tare da kabbara sallah, anatse tayi sallarta, bayan ta kammala bata ko nemi abinci ba saboda taci tayi hani'an a school, gado kawai ta haye tare da baje wa tana bacci,  Shima junaid daya wuce nashi dakin nashi ya faɗa toilet ya yi wanka tare da canza kayan jikin shi izuwa riga da wando,   Yana kokarin fitowa daga ɗakin sai ga su twins sun faɗo ciki atare sun ɗau wankan jeans da t shirt,  Yana ganin su ya saki fara'a tunkan su fara magana yace "maganar kiran mommy ce ko"?  dariya su kayi atare, ayaan yace "ashe dae ka gane,Allah yasa bamu takura maka ba,"  girgiza kansa yayi tare da cewa"a'a yanzun nan zan kirata insha Allah,"  Jahan yace "yawwa masoyi junaid mai son farin cikin ƴan uwan shi,pls idan ka kirataa wayar,kayi mata biyayya kaji? kada kace zaka ƙi mata magana, ita mahaifiyarmu ce,idan bata son ɗaya daga cikin mu ae bazama ta ɗauki cikinmu ba balle har ta ruƙe sa na tsawon wata rana, kuma tayi naƙudar haihuwarsa,nasan kai mai ilmi ne junaid kasan hukuncin wanda ya sa6a ma iyayensa dan Allah ka manta da komai," yarda jahan ke yi masa nasiha cikin daɗin rai yasa shi jin sanyi aransa harma yaji cewa ya ƙosa ya kirata a wayar,   "Shikenan ya jahan da ya ayaan,zan kirata yanzun nan amma ba a gabanku zanyi wayar ba,idan nagama dae zan sanar daku duk yarda mukayi da ita,"  Cike da farin ciki suka ce "yawwa ɗan ƙanin mu, yanzun nan kuwa zamu fita daga ɗakin,sai mun ji ka," suna fadin hakan suka juya tare da fucewa daga ɗakin hada rufo masa ƙopar da kyau,  ɗan murmushi junaid yayi sannan ya koma gefen gadonsa ya zauna tare da kai hannu ya ɗauki wayarsa dake asaman side drawer,   Zuba ma screen ɗin ido yayi yana tunanin ta yarda zai fara kiran mommyn tasu, for the first time zaiji muryarta,a lokacin baya kusan kullum saita kirashi awaya bai ɗauka don ko saving na numbarta baiyi ba,saboda haushin ta da yake ji,   A hankali yashiga danna wayar, kai tsaye cikin messages yashiga saboda akwai last messages da ta tura mashi, buɗe sakon yayi ya ƙara karanta shi "Thanks 4 ignoring me, i won't call u again bye,"   tanan ya ɗauki number tare da danna mata kira, ta shiga ringing,  Almost 3 times tana ringing ba'a ɗauka ba,ana huɗunne yana ƙara kira tayi picking,shiru yayi baice komai ba,har sai da tashiga tambayar wanene jin anyi mata shiru, yanayin muryarta akasalance saboda bacci,    Cikin harshen spanish take tambayar wai wanene,  Sai a lokacin junaid ya ambaci sunan "Mommy," shiru tayi tana nazari don ta gano muryar wacece wannan acikin ƴa'ƴanta,bakowa bane ya faɗo mata aranta ba face Romeo ɗinta duk da basa waya amma abbansu na turo mata voice ɗinshi da yake mata recording aduk lokacin da suke fira dashi ko kuma lokacin da yake tsaka da shagwa6a,  tuna wannan yasa Alexandra cewa "Romeo ɗina ne"? Ta tambaye shi donta tabbar cewa shiɗinne da take hasashe,   Ashagwa6e yace "junaid ɗin abbana ne," Jin hakan yasa alexandra tashi daga kwancen da take asaman shimfiɗeɗen gadonta, cikin sauri takai hannu ta kunna bedside lamp, bedroom ɗin nata ya ɗanyi haske tamkar zata iya gashinin zahiran agabanta, cikin tsananin farin ciki tace "allah yasa ba mafarki nake ba,romeo da kan shi yau ya kira ni a waya, harya kirani da sunan mommyn shi, cikin tsantsar farin ciki take maganar, Duk junaid na sauraronta sai da takai aya sannan yace. "Mom ki ƙaddara cewa mafarkine, saboda bashi da banbanci da mafarkin cos i called u by force ba don son raina ba, ya faɗi with angry face tamkar yana agabanta,  murmushin takaici tayi kafin tace"na sani dama saka akai ka kira ni,koma manene laifina ne nasan fushi kake yi dani,baka sona romeo ni kuma nadamu dakai sosai.....' ta faɗi cikin muryar kuka,  "Mom ba ki sona,da ace kina sona da baki tafi kinbarni ba a lokacin da bansan komai ba soyayyarki kawai nake buƙata da kulawarki, amma duk wannan bai dame ki ba,kin tafi kinbar ɗan jinjiri ya yi rai ko kar yayi duk bai dame ki ba,kashe ni kika so kiyi............' Fashe mata da kuka yayi mai cin rai, nan da nan hankalinta ya tashi duk yadda taso ta lallashe shi ya daina kukan amma yaƙiya,janye wayar tayi daga kunnanta tare da zuba ma screen ɗin wayar ido tana sauraron kukan shi, har cikin ranta ba ƙaramin ɗaci ta ji ba, tama rasa ta yarda zata fahimtar dashi, Sai da junaid yayi mai isar shi sannan ya tsagaita yana faman sauke ajiyar zuciya,   Jin haka yasa tace "pls can i turn it to video call,cos i wanna see u face to face," Rai a6ace junaid yace "ban amince ba mommy,if u really want to see my face then come to nigeria,"  Murmushi taɗanyi sannan ta kuma cewa "ka yafe mun junaid ɗin abbansa,ba don bana sonka ba na tafi nabarka, nafi kowa sonka junaid saboda ni na haifeka,duk da nasan cewa a wurinka bancancanta na amsa sunan mahaifiya ba, amma inaso kaa sani nikaina ba'a son raina nabar ƴa'ƴana ba, bakowa bane ya son da wannan ba saboda ba kowane zai yarda dani ba, amma an takuramun an ƙuntatamun ko bacci bana iyayi a ƙarshe ma naji ƙasar gaba ɗaya tafita raina na dinga jin tamkar ƙona fatar jikina akeyi wannan shine dalilin dayasa nabar ƙasar, kai kuma abunda yasa ban tafi dakai ba shine, soyayyar da mahaifinka ke yi maka,idan na tafi dakai ya zai ji a zuciyar shi? shi kan shi bai fahimci hakan ba kowa tunaninsa na tafi don son raina ne amma ba haka bane junaid, akwai wani 6oyayyen lamari dake faruwa acikin gidan nan,nayi ƙoƙarin na fahimtar da abbanku saboda ni ina da masaniya akan wani abu, amma abbanku sai ya nuna mun cewa kawai don na tsani baƙar fata ne yasa nake zargin wasu,bayan ba haka bane ni duk wanda na tsana hakanan batare da wani dalili ba to yana da wata muguwar manufa ne... '  Shiru junaid yayi yana sauraronta, bai cika ɗaukar komai serious ba arayuwarshi amma maganar mommynsa taɗan ta6a shi kaɗan, bazai ce ƙarya take masa ba saboda shi kanshi ya jima yana tunanin dalilin dayasa mom ɗinsa tabarshi, saboda shi ya kasance yaron da kowa ke so mai farin jinin gaske, taya za'ace uwar da ta tsugunna ta haife shi, itace zata ƙisa ta guje shi just without any reason !?
Idan ka samu kaɗan ka gode ma Allah gobe saiya baka mai yawa😠Cikon page din ɗazu dama 3 page nace zan haɗe maku, sa'an nan ku gyara zama 😱😨 Ina guga ina editing gashi nan har na ƙona mata hijabi ynx jira nake tadawo inga mai zatayi mun😇🤣
   Hafsat Bature      (Boss Lady) _💋Boss Bature💋_
Murmushi taɗanyi sannan ta kuma cewa "ka yafe mun junaid ɗin abbansa,ba don bana sonka ba na tafi nabarka, nafi kowa sonka junaid saboda ni na haifeka,duk da nasan cewa a wurinka bancancanta na amsa sunan mahaifiya ba, amma inaso kaa sani nikaina ba'a son raina nabar ƴa'ƴana ba, bakowa bane ya son da wannan ba saboda ba kowane zai yarda dani ba, amma an takuramun an ƙuntatamun ko bacci bana iyayi a ƙarshe ma naji ƙasar gaba ɗaya tafita raina na dinga jin tamkar ƙona fatar jikina akeyi wannan shine dalilin dayasa nabar ƙasar, kai kuma abunda yasa ban tafi dakai ba shine, soyayyar da mahaifinka ke yi maka,idan na tafi dakai ya zai ji a zuciyar shi? shi kan shi bai fahimci hakan ba kowa tunaninsa na tafi don son raina ne amma ba haka bane junaid, akwai wani 6oyayyen lamari dake faruwa acikin gidan nan,nayi ƙoƙarin na fahimtar da abbanku saboda ni ina da masaniya akan wani abu, amma abbanku sai ya nuna mun cewa kawai don na tsani baƙar fata ne yasa nake zargin wasu,bayan ba haka bane ni duk wanda na tsana hakanan batare da wani dalili ba to yana da wata muguwar manufa ne... '  Shiru junaid yayi yana sauraronta, bai cika ɗaukar komai serious ba arayuwarshi amma maganar mommynsa taɗan ta6a shi kaɗan, bazai ce ƙarya take masa ba saboda shi kanshi ya jima yana tunanin dalilin dayasa mom ɗinsa tabarshi, saboda shi ya kasance yaron da kowa ke so mai farin jinin gaske, taya za'ace uwar da ta tsugunna ta haife shi, itace zata ƙisa ta guje shi just without any reason !?
ï¿?
 gaba ɗaya ya tafi duniyar tunanin ya amince da zancen mahaifiyar shi ko kuwa, shessheƙar kukanta daya ji ne yasa shi dawowa cikin hayyacinsa cikin sauri yace "its okey mom,ni banason nayi sanadin da zan zubar da hawayen wani,bare ke da kike mahaifiyata ma,"  Ajiyar zuciya alexandra tashiga saukewa jin kalamansa masu daɗin gaske, muryarshi ce tasake katse ta da cewa "pls wipe ur tears mom,"  Murmushi ta saki tamkar tana agabansa,hannu ɗaya tasa tana share hawayenta kamar yarda ya umarta tayi,
ï¿?
. bayan ta gogesu tace "baka son ganin hawaye ne? amma meyasa baka amsa kirana duk in na kira wayarka, ko na kira wani nace ya baka muyi waya,a duk lokacin da hakan ta faru ina zubar da hawaye na sosai,  Murya asanyaye take magana, har cikin zuciyarshi yake jin maganar mommyn nashi,  "Mommy inaso zan aje waya,i wll call u next time, Cikin sauri tace "ka haramta mun ganin fuskarka ko? Shikenan my romeo,ka faɗi kome kake so zan maka shi"  "Komai nace kiyi zaki yi ne"? Ya tambaya yana jiran amsa  "zan yi maka shi koma menene,"  murmushi junaid yayi sannan yace"yaya ayaan da jahan suna son wani abu wurin ki, kiyi masu shi, sannan ki dawo gida ki bani kulawar da baki bani ba tun ina yaro,"  Murmushi tayi sannan tace"shi kaɗai kake so"? Yace "eh,"   Jinjina kai tayi tare da cewa"duk abunda kace zanyi saboda in tabbatar maka da cewa ina tsananin ƙaunarka my romeo,sannan koda daga bayane kaga wani abu kana so ka sanar mun, zanyi maka koma menene shi indae acikin duniyar Nan yake, sun jima suna yin wayar daga bisani su kayi sallama, bayan ya ajiye wayar ya dinga jin wani irin sanyi na ratsa zuciyarshi ga wani irin kwanciyar hankali da yazo mashi yasan cewa duk saboda wayar da yayi da mom in shi ne yasamu wannan natsuwar,
Sai wuraren ƙarfe 4'dai dai sehrish ta farka tana faman yin hamma, ba ƙaramin daɗin baccin taji ba,saukowa tayi daga saman gadon nata ta wuce toilet jim kaɗan tafito da alwalarta, hijab ta dauko ta zura a jikinta sannan ta kabbara sallah, tun tana cikin yin sallar taji ana knocing ƙopar ɗakin nata, don haka tana kammala shafa addu'a ta miƙe a hanzarce ta buɗe ƙopar,gabanta ne taji ya faɗi rass ganin matar nan ta ɗazu,murya na rawa tace "ina yini," murmushi Amani tayi tare da cewa "lpy ya kike,"? "Ina lpy," ta bata amsa ataƙaice, dan ta6e baki amani tayi kafin tace"naso ɗazu dana ganki da safe muyi magana amma naga kina cikin sauri ne zaki school," ta fadi a wayance  Sehrish tace"eh hakane," duk tarasa natsuwarta, tsoranta me take son ce mata,
ï¿?
 Amani taci gaba da cewa"Tun yaushe kika fara aiki a gidan nan ne"? Saboda ni ban ta6a ganinki ba gsky,"  Sehrish tace"banjima da farawa ba,"  "Amma nayi mamamkin yarda shaƙuwa ta shiga tsakanin ki da mutanen gidan har abbansu ya mayar dake ɗiyarshi,kuma naga kina da kusanci ssae da junaid har yana ruƙe maki hannunki kamar wata ƙanwarsa, bayan matsayinki bai wuce na ƴar aiki ba," ɗagowa sehrish tayi a ɗan rikice tana kallonta jin abunda tace,   Murmushi amani ta kuma saki kafin tasanya hannu ta dafa kafaɗar sehrish tace"idan ba damuwa inaso in baki wata shawara wadda zata amfane ki, domin na lura kinason jefe kanki cikin hatsari, karfa ki ruɗa kan ki,".  Jinjina kai sehrish tayi tare da cewa"ina sauraronki," amani taci gaba da cewa"ki nisanta kanki daga kowa na cikin gidan nan,ka da ki bari wani ya so ki acikin matasan gidan nan,kuma kada ki kuskura ki bari zuciyarki ta faɗa tarkon son wani,idan da hali ma ki tsaya a iya matsayinki na ƴar aiki,zaki fi samun kwanciyar hankali,"  Tun da tasoma magana sehrish ke bin ta da kallo fuskarta ta nuna alamun rikicewa don sam batasan inda zancen matar ya dosa ba,  "Kada kice na cika ki da surutu,its just an advise in kinyi amfani da ita ke zata amfana,but if u don't hmmmmm u can even lost ur life........' Wani irin bugu zuciyar sehrish taji saboda abunda amani tace, na cewa zata iya rasa rayuwarta, tuni jikinta ya shiga yin kerma alamomin tsoro sun bayyana a fuskarta, hankali atashe take cewa"meyasa kika ce haka?saboda me zan rasa rayuwa ta?don kawai naso wani ko wani ya so ni acikin gidan nan"? Ta tambaya tana kallon Amanin,   Kafin Amani tace wani abu, muryar Azmee ta katse mata hanzarinta da cewa"tsayuwar me kuke yi ne, ke da nace ki kira mun ita don tazo mu haɗu mu fara girkin da wuri"? Ta tambaya tana kallon Amani, . cikin sauri Amani ta dan basar tare da sakin fara'a a fuskarta tace"dama muna ɗan tattaunawa ne,kinsan bata sanni ba nima kuma haka, so ina gabatar mata dakaina ne don musan juna,"  Zuba mata ido sehrish tayi kawai baki asake tana kallonta,  Azmee tace"Hakan na da kyau, sehrish wannan matar yayanku ce Abbas sunanta AMANI,ina fata zaki saki jiki sosai da ita domin kuwa tana da mutunci sosai,  daƙer sehrish ta ƙaƙalo murmushi tace"Insha Allah aunty azmee,"   tayi maganar tana kallon Amanin ita ma kallonta takeyi har lokacin, Azmee ta lura da kallon kallon da suke yi don haka tace"Amani mu wuce kitchen,ke ma sehrish ki ajiye hijabin jikinki ki zo mufara aiki,"  Juya ciki sehrish tayi su kuma suka wuce kitchen ɗin, kanta ya gama ɗaurewa da maganganun da Amani ta gaya mata,amma duk da hakan ba tajin zuciyarta zata karaya saboda wasu ƴan kalamanta,hannu tasa tare da tu6e hijabin ta ajiye ta nan saman gadon, sannan ta ɗauko ɗan mayafinta cikin wardrobe tayi rolling ɗinsa,  A dai dai lokacin da ta fito daga ɗakin ta tunkari hanyar kitchen ɗin sai ga haroon ya fito daga part ɗinsu,sai da taji gabanta ya faɗi don ita yanzu kallon shaiɗan take yi mashi saboda ƙahone kawai babu akanshi,   Ƙarasowa yayi inda take suna facing ɗin juna yace"mutuniyar ba hello ba hi,laifin me nayi maki ne"? Yayi maganar yana ɗaga mata gira tare da kashe mata ido,  Tsuke fuska tayi tare da bi zata wuce cikin sauri yasha gabanta tare da ware hannayensa yace"daga kin ƙara motsowa zan rungume.........' kasa ƙarasa maganar yayi gabansa na faduwa ba don komai ba sai don ido biyun da su kayi da SGR wanda ke shigowa cikin babban falon su biyu ne tare da shattima suka shigo,banda omar wanda tun a masallaci suka rabu,  Cikin sauri haroon ya canza kalamansa da cewa"kin gane dole kisa tsoran Allah acikin zuciyarki idan kinason rayuwarki tayi kyau,amma in kika ce zaki biye ma ƙawayen banza zasu kaiki ne su baro ki," ya dage sai zuba yake yi mata,juyawa tayi don taga wanene ya shigo saboda ganin yarda haroon yabi ya susuce ya sauya magana,   hada ido su kayi da shi adai dai lokacin yana ƙoƙarin kawar da nashi idon daga na haroon,har cikin zuciyarta taji wani irin sanyi aranta dama da kewarshi tadawo gidan,ganin shattima na kallonta yasa tayi saurin cewa"ina yinin ku"? "Lafiyalou Alhmdllh ƴan mata," ya amsa mata fuskarshi asake,sannan suka wuce upstairs part dinshi,sam takasa janye idonta daga kallon Bayan sgr da takeyi ko kyaftawa ba tayi har suka 6ace ma ganinta,hakan ba ƙaramin fusata haroon yayi ba rai a6ace tace"Ke!!kina a gabana kuma kike kallon wani"?  ƴar dariya sehrish tayi kafin tace"Namiji nake kallo," tana faɗin hakan tabi ta gefenshi ta wuce izuwa kitchen,baki asake haroon ya tsaya yana huci jin abunda tace,aransa yace"lallai ma ƴar shilan can harni zata ce ma Namiji take kallo,hakan na nufin ni kallon ɗan daudu takeyi mun,zan yi maganinta ne! Watan fara shan uƙubarki yayi acikin gidan nan !!zan 6ata maki suna a wurin shi dama kowa na gidan nan"!!! Yana gama faɗin hakan ya gyaɗa kanshi yana sakin shu'umin murmushi ya fuce daga falon. Shiga kitchen din tayi ta same su har sun fara aikin girkin,sallama tayi masu suka ɗago suna kallonta atare, azmee tace"sannu da zuwa za'a fara aikin ne,"  Ɗaga kai tayi tare da cewa"eh amma inaso nafara kaima su babban yaya abunsha naga sun shigo tare da wani ynx," zuru amani tayi tana kallon ikon Allah,  Azmee tace"toh bari na haɗa maki tare da snacks ki kai masu,"  ɗan murmushi sehrish ta saki tana jiranta duk in ta ɗago sai sun haɗa ido da Amani,sai tayi saurin kawar da idonta,  Bayan azmee ta kammala haɗa mata two cups na coffee a saman tray tare da plate mai ɗauke da snacks ta miƙa mata,kar6a sehrish tayi ta rike da kyau a hannunta sannan ta juya ta fuce daga kitchen ɗin tana faman sauke ajiyar zuciya,   Wuce wa tayi upstairs tayi a bakin falon ta tsaya tare da yin sallama,muryar wannan abokin nan nasa taji ya amsa mata da cewa"wa'alaikum salam," sai da ta dai dai ta natsuwarta sannan tashiga ciki gaban ta na faɗuwa kamar kullum,   Shattima ne kawai ta samu zaune saman 3 seater yana danna wayarshi, Ƙarasawa tayi tare da ajiye tray din saman table din gabansa,maimakon ta tafi saita tsaya tana faman wasa da yatsun hannunta burinta kawai taga sanyin idaniyarta tasan cewa zai fito shiyasa ta tsaya,  Hannu shattima yasa ya ɗauki cup of coffee din yakai bakinsa yana kurba da alama ba ƙaramin daɗi yayi masa ba,sam takasa tafiya saboda bata ga sgr ba,ganin tayi masa tsaye yasa shi jinkirtawa da shan coffee ɗin da yake yi yace"Ya sunanki ne"? firgit ta ɗanyi tare da kallon shi tace"Sehrish," jinjina kan shi yayi kafin ya ƙara cewa wani abu sai ga Sgr ya fito sanye da short ajikinshi tare da singlet,nan da nan sehrish ta shiga natsuwarta, wuri ya samu ya zaune gefen shattima, cikin sauri ta ɗauki cup ta miƙa masa hannu yasa tare da kar6a yana dan sipping dinshi a hankali,  Mayar da idon shi yayi kan sgr yace"wannan fa ban ta6a ganinta ba is she ur sister? Ya tambaya yana kallon shi,  "U can ask her," ya faɗi batare da ya dago ya kalle shi ba, murmushi shattima yayi tare da mayar da idon shi kan sehrish yace"kina da connection dasu ne,ko yar wurin Aunt dinsu ce ko uncle dinsu"?  ɗaga mashi kai tayi alamar"eh" sunnar da kai tayi cikin jin kunyar ƙaryar da tayi,  Shattima ya kuma cewa"amma Abba yayi maki miji kuwa"? ɗagowa tayi tare da dan zare ido saboda jin abun yace mata,mamakin ta yadda yake ta tambayarta bayan sam ko a fuska baiyi kama da mai son surutu ba shima,   girgixa kai ta kuma yi tare da cewa"a'a bai mun ba" "Because of what?ko babu wanda kike so acikin matasan gidan nan"? maimakon ta bashi amsa sai ta ɗan saci kallon Sgr dake kur6ar coffee din hannun shi,  Wani irin murmushi shattima ya saki saboda yaga inda sehrish take kallo, acikinsa ransa yace"hmmmm dama nasani,"  A fili kuma yace"yana da kyau ko'? A firgice sehrish ta mayar da idonta kan shattima tace"Wa"? da ido yayi mata nuni da Sgr, sunnar da kai tayi tana murmushi tace"eh,"   "Shi bai yarda da mace ba,yace mata matsala ne arayuwar namiji,but i want to ask u something a misali mace ta samu righteous husband kamar wannan lu'u lu'un,wanda ya haɗa komai ga kyau ga ilmi ga dukiya, kina tunanin akwai macen da zata yi gangancin Mallakarsa har ta zama matsala arayuwarshi balle ta 6ata mashi rai"?  jikin sehrish tuni ya soma kerma saboda tsoran dogon sharhin da abokin sgr ɗin ke yi mata,babban tashin hankalin ma gashi a kusa duk da yayi tamkar baya jinsu,ammma ae kunnan shi a buɗe suke ba'a toshe ba dole ne yaji abunda suke cewa,muryarta na rawa ta buɗe baki zatayi magana kenan kwatsam taji wannan sanyayyiyar muryar tashi tace"ba kowace mace bace zata so ni dan Allah in fact duk macen da zata soni sai don waɗannan abubuwan daka lissafa," yayi mgnar again batare da ya kalle su ba, sai ma hannun shi daya zura cikin short pocket dinsa ya ciro wayarsa dake ringing tare da yin picking ya kara a kunnan shi yana magana cikin harshen turanci,  gaba ɗaya jikin sehrish yayi mugun sanyi kalamansa akwai ƙamshin gsky acikinsu,yanzu ta ƙara gane dalilin dayasa mace sam bata agabanshi,saboda yasan cewa duk wadda zata so shi,ba zata so shi dan Allah ba face sai don wani abu daya mallaka,kamar wannan kyakkyawar surar tashi mai matuƙar jan hankali,da dukiyarsa kuma, ga kuma ilmi duka dai😇 Amma har ga Allah ita ba don dukkan waɗannan abubuwan ba take son shi ba,ataƙaice ma tunkan taga fuskarshi tunkan tasan koshi wanene ta afka ma tarkon son shi ta hanyar sunan shi kawai da taji suna faɗi BABBAN YAYA,  gaba ɗaya ta tafi zurfin tunani muryar shattima ta dawo da ita daga dogon tunanin nata da cewa"dagaske ne abunda ya faɗa"? ya tambaye ta yana jiran amsa,ba komai yasa shattima sakin jiki da sehrish ba face tun da yaga yarinyar da suka shigo ta gaishe shi da ya kalle ta ba fuskar kowa ya gani ba a fuskarta ba face fuskar SGR bi ma'ana sun dace sosai,saboda tunda yake arayuwarshi bai ta6a ganin yarinyar da ta dace da Sgr ba face wannan yar matashiyar duk da ya lura cewa kamar tayi masa ƙanƙanta,yarinya ce ssae amma kuma tana da duk wani abu da namiji zai buƙata ajikin ƴa mace,🥱  A hankali sehrish ta buɗe bakinta tare da cewa"hakane gskya ya faɗi....." daƙer takai ƙarasa maganarta, cikin sauri tace"kuna buƙatar wani abu"? shiru shattima ya ɗanyi saboda ya lura da chanjin da yarinyar tayi,kuma yasan saboda kalaman sgr ne,may be tana son shi ne da alama, ya faɗi aranshi a fili kuma yace"just its okey zaki iya tafiya,mun gode da wannan,"  Murmushi ta ɗanyi sannan ta juya da sauri saboda kukan daya ciyo ta har takai bakin ƙopa ta ɗan juyo tana kallon shi, anatse yake yin wayarshi ya jingina bayansa ajikin kujerar,sa kai tayi ta fuce wuri tasamu anan upstairs ɗin ta zuƙunna ta cigaba da shan kukanta jikinta har rawa yake yi,tuni eyes dinta sun canza launi, fuskarta ta tur6une saboda kuka sai faman murzar hancinta takeyi kamar zata 6alle shi,sam ta manta da aikin dake gare su a kitchen su azmee nacan da amani sun taƙarƙare suna ta aikace aikace ba sehrish, gashi Amani sai faman tambayar azmee take yi na cewa har yanzu yarinyar bata dawo ba daga kai ma Sgr coffee,ko mai ta tsaya yi? Ita dae azmee bata ce komai ba, da tacika ta da tambayar ne tace"may be shi ya tsare ta,kinsan ita ke kula da apartment dinsa, Jin hakan ba ƙaramin tayarwa Amani hankali yayi ba,daure wa kawai take yi tana aikin,   Hawansa kenan upstairs ɗin ya miƙi hanya yana cikin tafiya yaji shessheƙar kukan ƴar mace,mamaki ne ya kama abbansu ganin yarinyar zukunne ta takure kanta sai faman matse hanci take yi tana kuka,tuni hankalinshi ya tashi ƙarasawa yayi inda sehrish take zukunne,a firgice ta miƙe tsaye lokacin da tayi arba da Abban nasu sam bata lura dashi ba sai da taji takon takalminsa na tunkarota,   lokaci guda ta rikice duk ta susuce tsoranta mai zata sanar mashi in ya tambayeta dalilin yin kukan nata,  Ko da ya isa dab da ita sai ya tsaya yana ɗan nazarin fuskarta,tsananin tausayin yarinyar ne ya kama shi,dama ita mace abun tausayi ce musamman in ta kasance ba'a gaban iyayenta ba,babu kowa nata a kusa da ita da zai lallashe ta ya kuma janyo ta jikin shi don jin damuwarta,ya mayar da ita yar shi amma kuma bai da isasshen lokacin jin abunda takeso ko me ke damunta,   Sunnar da kai sehrish tayi ƙasa murya na rawa tace"ina yini abba,"  bai amsa mata gaisuwarta ba sai cewa yayi"meya faru ne naga kina kuka? cikin en ina tace"babu komai," hannun shi yakai gefen fuskarta yace"ko da zaki yi ma kowa ƙarya,kada kice zaki yi ma abbanki,ga hawaye nan nagani suna zuba a idonki,kawai dai bakya son faɗamun ne," shiru tayi bata ce komai ba tana faman wasa da yatsun hannunta,  Murmushi yayi ganin tana ɗan satar kallon shi kamar wata mara gaskiya,  Cikin zolaya yace"faɗa mun gaskiya kodai aure kikeso ne?kin rasa wa zaki faɗamawa shine kika la6e anan kina kuka ko"? ɗagowa sehrish tayi taɗan zare ido can kuma ta fashe da dariya gaba ɗaya, shima dariyar yayi dama yayi hakan ne don yasata farin ciki yasan mata daga anyi masu maganar aure sai jin kunya da dariya,  ganin haka yasa shi ƙara cewa"hmmmmm dama nasani,mu aje wannan maganar a gefe nasan cewa akwai wanda kike so acikin ƴa'ƴana don na iya haihuwa gasu nan tubarkalla masha Allah ƴan mata sai rububi sukeyi hada masu kirana awaya duk safiyar Allah suna gaishe ni wai nan suna yi ma kansu ko ƴa'ƴansu kamun ƙafa,ni kuma har yanzu basu kwanta mun araina ba,Amma ke ɗin nan ko ta dabance in har kinaso in baki ɗaya daga cikinsu dole kema ki fara kamun ƙafa daga yanxu," Magana yake a natse sehrish kuwa ta kasa kunne tana sauraron shi,mamaki ya gama kamata yarda Abban nasu sukutun da guda yake fira da ita lallai ba ƙaramin wayayyen mutun bane,  bayan yakai ƙarshen maganar tashi tace"amma Abba,ni bansan yarda ake yin kamun ƙafar ba," ta faɗi cikin jin kunya,  dariya yayi tabi shi da kallo sai taga ya koma mata junaid saboda tsananin kamanceceniyar dake a tsakaninsu don dai shi fuskarshi akwai manyantaka, Bayan ya tsagaita da dariyar yace"kina nufin baki san yarda ake kamun ƙafa ba in mutun nasan abu,to ki tambayi AZMEE ta faɗa maki zata koya maki,  Jinjina kai tayi tare da cewa"insha Allah zan tambayeta,"  Murmushi yayi kafin yace"daga ynx zan fara zuba ido in ga yadda zaki fara kamun ƙafar naki,idan kinyi abu mai kyau sai na duba na gani wanne ya dace acikinsu na baki,idan marks ɗinki yakai matakin A1 to zan aura maki ɗaya daga cikin manyan ne, idan kuma Credit kika samu zan haɗaki da ɗaya daga cikin youngers ɗinsu,amma fa ki sani idan marks ɗinki yazo da matsayin(f)to zan aura maki Haroon ne........... " dariyar da sehrish ta fashe da ita ne ya hana shi ƙarasa maganar, zuba mata ido yayi yana kallonta sai ya dinga ganin kamanceceniyar fuskarsu da ta yarinyar sam yarasa gane dawa take masa kama nan da nan kan shi ya ɗaure yashiga mamakin kamannin daya gani kodae idonshi ne ke nuna mashi hakan tabbas fuskarta tayi tamkar photocopy ɗin fuskar ƙanwarsa AZEEMA,
 daker sehrish ta tsagaita da dariyar tace"Abba zan tafi kitchen nabarsu suna aiki,"  Murmushi yayi tare da cewa"hakan nada kyau,kwara tun ynx ki koyi girkin shima yana daya daga cikin jarabawar da zan maki don bazan aura ma ƴa'ƴana macen da bata iya girki ba,then idan nasamu free time zan wa junaid magana ya kira mun ke don mu ƙara tattaunawa,"  Amsa mashi tayi fuskarta cike da annashuwa tabi ta gefenshi tana faman sakin murmushi ba don komai ba sai don maganar Abban nasu dayace idan marking ta F9 ne zai aura mata haroon hakan na nufin shi kanshi yasan cewa haroon cikon bencin gidan ne 🤣😂😅  Har juyawa abban nasu yayi yana kallonta a lokacin tayi nisa wurin sauka daga stairs ɗin,ajiyar zuciya ya saki saboda ganin farin ciki a fuskar yarinyar, dama yayi hakan ne don ya mantar da ita damuwar da ta shiga har ta la6e tana kuka,kama hanya yayi ya wuce,dama bedroom ɗin junaid ya nufa,
*************************** Tun ɗazu da suka kammala lunch ɗinsu after Azhar hossana da Camila suka koma bedroom din saman katafaren gadon suka baje suna bacci abun ba'a magana,ita kuwa jahad sam tagaza yin bacci tun da tayi sallar la'asar tafito daga ɗakin ta tsaya a falon tana zagaye, bakomai take burin gani ba face Ya Omar dinsu ko zafin ciwon ƙafarta yanzu tadaina ji,har wurin ƙarfe biyar da wani abu tana wannan safa da marwar in betwn seater's ɗin dake a palourn,tana cikin wannan zagayen MARSHAL OMAR ya shigo falon da sallamar shi, sam bata ji shi ba saboda ta juya masa baya tamiƙi hanya tana tafiya,  Murmushi ya saki ya tsaya yana tunanin wacece acikinsu jahad ko hossana,koma dae wacece ba ƙaramin kyau tayi masa ba acikin kayan,yaji daɗin hakan saboda dama burinshi ya gansu cikin jin daɗi da walwala,ganin bata da alamar juyowa yasa shi yin gyaran murya da ɗan ƙarfi, cikin sauri jahad ta juyo tana faman zare ido don batayi tsammanin ganin mutun ba,nan da nan wani irin farin ciki ya mamaye fuskarta da karfi ta furta"Ya Omar," lumshe idonshi yayi tare da buɗe su yana murmushi,  Watsa wa tayi da gudu tamkar zata rungume shi,sai da taje dab dashi sannan taci burki tana dariya,yana ganin hakan ya gane cewa Jahad ce,don da ace hossana ce sai tayi hugging dinshi,  "Fatan na same ku lafiya"? Ya furta yana kallonta,fuskarta awashe tace"Alhmdllh ya omar,dama tun ɗazu nake jiran zuwan ka, ashe zaka zo da har na fidda rai,   Omar yace"naso nazo ɗazu to bansamu hali ba,shiyasa na aiko maku da major don ya ɗauko ku,ina fata gidan yayi maku?  "ya omar ni nama rasa da wasu kalmomi zanyi amfani dasu wurin yi maka godiya Allah.........."tuni idanunta sun cicciko da kwalla sun soma gangarowa daga cikin idanunta,  Cikin sauri yace"Why jahad?me yasa zakiyi mun kuka bayan kinsan bana son ganin hawayen ku,sannan bana son godiya kada na sake ji,duk wani abu da nayi maku nayi shi ne don Allah,kuma haƙƙin ku ne dake akaina har yanzu ma ni ji nake kamar akwai sauran abubuwan da banyi maku ba, ..kallon shi kawai take yi yana bayani har yanzu tana mamakin kyakkyawar zuciya irinta Marshal omar, Cikin shessheƙar kuka tace"ya omar kai wane irin mutun ne?narasa dame zan fasalta ka,kyawawan ɗabi'unka da halayenka da kyakkyawar zuciya irin taka bana tunanin a doran duniyar nan za'a samu mai irinsu,koda za'a samu sai anci baƙar wahala kuma cikin kashi 100 bai wuci asamu kashi biyu ba,kai na musamman Ne ya omar,ina taya iyayenka farin ciki sosai da samun ɗa kamarka,saboda kai abun alfahari ne........ni bansan da me zamu saka maka ba ya omar,ka bamu kyakkyawar rayuwa ka cire mu daga ƙangin rayuwar da muke ci,a lokacin da muke tunanin cewa kowa ya tsanemu bai son mu mutuwa ma kawai muke jira,sai gashi Allah ya haɗamu dakai,tun a lokacin nasan cewa kai kyauta ne daga Allah...........  tun da jahad ta soma kora jawabi ya goya hanneyen shi a faffaɗan kirjinshi ya natsuwa yana sauraronta fuskarshi ɗauke da murmushi,saboda kalamanta ba ƙaramin shigarshi su kayi ba yadda take magana a natse ga wata irin murya dake gareta mai sanyin gaske irin muryar da duk 6acin ran da kake ciki in. Ka ji ta sai ka manta dashi,ae jahad akwai natsuwa ga tawakkali nima na shaida hakan 😘 "Ya omar ka faɗamun dame zamu saka maka?nasan ma babu Ba mu da abunda zamu iya saka maka aduniyar nan face addu'a itace kawai ke gare mu,i will keep pryaing 4 u ya omar hada family ɗinka duka zan saku a addu'ata till the end of my life bazan manta ba aduk lokacin da nayi sallah ko nayi karatun alkur'ani har night prayers ma zan dinga tashi inayi just because u ya omar and ur family,  ta ƙarasa maganar tana faman sauke ajiyar zuciya har lokacin hawayen fuskarta basu tsaya da kwarara ba,  Hannu omar yasa tare da zaro handkerchief ɗinsa dake front pocket dinsa dake a t shirt din jikinshi,  Da hannun shi yasa yana wiping tears dinta a hankali,runtse idonta tayi tana jin wani irin yanayi mara misaltuwa a tattare da ita,  Muryarshi ce ta tsinkaye ta da cewa"jahad ngde ssae kalamanki kawai da kikayi mun a yanzu ma sun wadatar dani,sannan idan kuna so ku saka mun abunda nakeso shine koda nan gaba kada ku juyamun baya bana son ku canzamin inaso ku tsaya a yarda nasan ku,ina tsananin ƙaunarku sosai bana son abunda zai raba ni daku,inason zumunci ya ɗaure a tsakanina daku daganan har can...... katse shi tayi da cewa"har ina kenan ya omar,"  Cikin zolaya yace"gidan Aljanna mana," dariya tayi sosai kafin ta tsagaita da dariyar tace"insha Allah ya omar ba zamu ta6a baka kunya ba,zamu kasance kamar yarda kakeso,"  Jinjina kansa yayi sannan yace"where's my hossana banganta ba,ko tana ciki ne? Ya yi nuni da hannun shi,  Jahad tace"hossana suna ciki tare da wannan nurse camila din sai sharar bacci suke yi tun ɗazu,"  Murmushi yayi tare da cewa"naso na ganta,"  Cikin sauri tace"ya omar ka shigo daga ciki mana ka zauna na kira maka ita don itama hossana a ƙagare take data ganka,"  Omar yace"sauri nake na koma gida yanxu,ki gaishe mun da ita dae,ko kuma zan kira wayane ae akwai telephone sai mu gaisa," jinjina kai tayi tare da cewa"shikenan zan sanar mata,amma nasan zatayi kuka in taji cewa kazo kuma ka tafi bata ganka ba,   juyawa yayi yana faman sakin murmushi har ya kusa fita daga falon tace "ya omar," juyowa ya kuma yi yana kallonta,  "Tun jiya inata so in kazo inyi maka ya mai jiki,abun yana araina ɗan uwanka daka sanar mun cewa bai lpy,"   Omar yace"oh fawan da sauƙi jikin shi sosai,kada ki damu zan bashi waya inyaji sauki ssae sai kiyi mashi ya jiki,"  Jinjina kanta tayi alamar toh daga nan sukayi sallama ya fuce daga falon,  Ajiyar zuciya ta saki tare da wuce wa ciki fuskarta asake 😇
****AUNTY BABBA****** 💋Boss Bature💋_
********AUNTY BABBA************
Zaune take agaban dressing mirror ranta a matuƙar 6ace fuskar nan tayi jawur saboda kukan da taci,ta zabga uban tagumi zuciyarta sai faman tafarfasa take yi,bakomai bane ya haddasa mata wannan 6acin ran ba face General ishaq daya hanata zuwa abuja,duk yarda ta kwallafa rai akan zuwa abujan ya hanata,sai da ya bari tasha wankanta ta kimtsa cikin leshi ta yafa mayafi ta ruƙo jakarta, tana fitowa ta same shi zaune a falo jikin shi sanye da gajeran wando baki,wani irin kallo yabi ta dashi tare da cewa"Ina zuwa," washe masa baki tayi tare da cewa"Abuja mana,kai fa kace zamuje duba jikin fawan," kai tsaye yace"ae nafasa wannan,ni kaɗai zanje inyaso ko a waya ne kun kira Abba kuyi masu Allah kyauta," Tur6une fuska tayi tare da cewa"dan Allah idan wasa kake mun ka daina,"
ï¿?
 Shima ya tamke fuskarshi yace"ba wasa nake ba,ni kaɗai zanje inyaso saina wakilce ku,"  Hankali tashe tace"Haba Abban hafsat sai da na kammala shirina, tafiya kawai ta rage zaka ce wai an fasa gaskiya ni sai naje," ta faɗi tare da ruƙe qugunta tamkar zata buge shi,  Miƙewa ishaq yayi fuskarshi ba wasa yace"to ki sani muddin kikasa ƙafarki kika bar gidan nan without my permission hmmmmmm ke kinsan mai zai biyo baya,  Yana faɗin hakan ya fuce ma daga falon yabarta,  da gudu ta koma bedroom ɗinta a ƙasa ma tayi wurgi da handbag ɗinta saman gado ta faɗa tadinga shan kukan baƙin ciki har bacci ya kwashe ta, Ta jima tana baccin kafin ta tashi cike da kunci ta koma gaban mirror ta zabga tagumi rai a6ace,
Download>>>Â Dangin Rabi Complete Document
Ta jima tana tunanin meyasa general ishaq ya hanata zuwa gidansu don ta duba jikin fawan,abun ya É—aure mata kai saboda shi da kansa yace zasu je dubiya atare amma ya canza ra'ayinsa yanzu, Â Â tsoki ta buga tare da kai hannu ta É—auki wayarta dake agaban mirror É—in,contact É—inta ta shiga ta lalubo numbar wayar HAYAAM ta danna mata kira,ringing ta shiga yi kusan sau uku ba'a É—aga ba,
tana a cikin toilet kiran ya shigo a lokacin wayar na hannun wani matashin saurayi dake zaune saman wani haÉ—aÉ—É—en gado, daga shi sai shorts ajikin shi ya baje abun shi, ganin sunan Aunty Layla ya bayyana akan screen É—in wayar yasa shi É—aga murya tare da cewa"babe!babe!ur phone is ringing, Â Daga cikin toilet É—in tace"wanene ke kirana?in dae mommy ce ko Abi ka kashe wayar gaba É—aya bana son takura, Â "No basu bane,wannan auntyn naki ne Layla,"
Jin sunan Aunty laila yasa ta yin wuff ta fito daga cikin toilet ɗin, doguwa ce sosai fara sol babu ko tabo ajikinta kai kana ganin fatar nan zakasan cewa ba ƙaramin kuɗi take kashe mata ba saboda yarda take ɗaukar ido,
ta ko'ina Allah ya bata ga dogon wuya, Bin ta da kallo saurayin yayi sam yagaza janye idonshi akanta sai kace batare suke rayuwa acikin gidan ba, Towel ne kawai ta ɗauro ajikinta cikin hanzari ta miƙa hannunta tare da kar6ar wayar tana cewa"nashiga ukuna Aunty laila kuma a awaya?yanzu zata rufe ni da faɗan ba gyara ba dalili mtswwwwww
ï¿?
 Ta ƙarasa maganar tare da ɗaga kiran ta kara a kunnanta tana faman zazzare manyan idanunta, A ƙule aunty babba tace"ina kika je ne inata faman kira ba'a ɗagawa? Cikin en ina tace"Nashiga toilet ne yanzu na fito na sami wayar tana ringing asaman gado, aunty babba tace"hmmmm kina a gida ko kina awaurin yawon gantalin naki? Cikin sauri tace"am....ina a gida......" bata bari ta ƙarasa ba a tsawace tace"Karki kuskura kiyimun karya Hayaam ina sane da duk wani yawon gantali da kikeyi ana sanar mun da komai,saboda tsabagen iya shege da fitsara idonki ya buɗe wuyanki ya isa yanka hada tattara kaya da komawa gidan saurayi da zama koba haka akai ba? Ta tambaya azafafe tamkar tana a gabanta,tuni ran Hayaam ya 6aci juyawa ta ɗanyi ta kalli Sofwan dake kallonta bai sauraron me suke cewa amma ya lura da yanayin fuskarta daya canza saboda hayaam bata iya 6oye 6acin ranta duk mun ƙanƙantarsa,  sassauta muryarta tayi tare da cewa"Aunty layla mgnr da kika faɗa gaskiya ne,i can't hide it 4 u ni bazan iya rayuwa a cikin gidan nan ba saboda baida marar raba da kwango a wurina,fentin gidan duk ya ƙoƙe kamar munfi kowa talauci a layinmu,bama wannan ba ɗakinmu bai da banbanci da kwankon ashana katifa ce kawai duk ta gwaigwaye sai akwatin kayan mu, ko na fidda kuɗi na siyi furnitures mommy bata barin komai sai dae kawai nadawo na taras ta siyar da komai ta hanani jin daɗin rayuwa kuma kinsan ni macace mai son rayuwar hutu rayuwar ƴanci wannan shine dalilin dayasa nabar masu gidan don wlh ko abincin da suke ci ynx 6ata mun ciki yake yi saboda wannan yarinyar ƙanwar Amani ita suke ba girkin gidan,yarinyar da bata wuci 14years duk wani aiki na gidan ita take yin shi har yanzu mommy bata haƙura ba akan ɗaukar fansar abunda mommynsu tayi mata" yadda take magana kaɗai ya isa ya tabbatar maka da cewa ba ƙaramar ƴar duniya bace magana take tana faman wurga ido tana kora jawabi Jinjina kai aunty babba tayi tare da cewa"ae ni tayimun dai dai,wato wayewa tasa kin manta da irin azabtarwar da matar nan tayi mana shine har kike ganin laifin mommynmu,kwara su kashe yarinyar ma kowa ya huta ae ni nafison su wulaƙantata," ta fadi tana faman huci kamar tana agabanta,
Download>>>Â Yaro Ne Complete Document
Ganin wayar tasu ba mai Æ™arewa bace yasa Sofwan tasowa daga saman bed dinsa ya sauko, takawa yayi izuwa bayan Hayaam dake atsaye ya rumgumota tare da zagayo da hannayen shi ta waist É—inta sannan ya kwantar da kanshi daga gefen wuyanta yana cewa"babe yaushe wayar zata Æ™are?nifa a Æ™agare nake, Æ™asa Æ™asa da murya tayi tare da cewa"pls karkaja min bala'e,"Â
ï¿?
Muryar aunty babba ce taci gaba cewa"Yanzu abunda nakeso dake kibar komai da kike yi ki tafi abuja gidan surukaina acan nakeso ki cigaba da zama,  Ƙiris ya rage hayaam ta saki wayar dake a hannunta saboda jin sa6on da auntyn nata ke faɗi, cikin ruɗu tace"haba dae Auntyna amma dae wasa kike yi ko?if not ni mai zai kaini gidan in-lows din mu da zama abun ma babu daɗin ji........, Tsawa aunty babba ta daka mata tare da cewa"ke dalla yi mun shiru!duk ƙoƙarin da nakeyi akanki bakya gani!kina nan sake da baki ga wata can a gidan matsayin yar aiki Abbansu ya mayar da ita ɗiyarshi sun gatanta yarinyar har makaranta take zuwa,idan har kikayi gangancin rasa wannan damar ta komawa gidan da zama ina mai tabbatar maki da cewa Kin rasa cikar burinki na har abada," shiru hayaaam ta ɗanyi gabanta na faɗuwa saboda ba abunda ta tsana fiye da ace zata Rasa SURGEON GENERAL RAFAYET saboda mutuwar son da take yi mashi ta kwallafa rai akanshi a lokacin baya tasa naci sosai akan shi sa'adda suke zuwa gidan sosai,amma tun da ta lura cewa kafin ya ma ɗaga idonshi ya kalli mace aiki ne don sai da ta share 2 weeks a gidan sau ɗaya suka ta6a hada ido shima ɗin by mistake ne ya ɗago a lokacin,abun ya tsaya mata arai, yadda take da kyawun surar nan babu namijin da zaiganta ya kawar da ido batare da ya neme ta ba sai akan SGR,tun a lokacin ta soma fidda rai akan shi amma yanzu aunty laila ta soma dawo da ita kan network, lumshe idonta tayi tana tuna kyakkyawar fuskarshi har lokacin sofwan na manne da jikinta ya lafe mata kamar wani maye,  ƙara kara wayar tayi akan kunnanta tace"Aunty laila komai zan iya yi akan na mallake shi,saboda shine namijin daya haɗa komai da nake kwaɗayi nake tsananin so a jikin ɗa namiji,amma abunda bansani ba aunty layla shin kina ganin zasu kar6e ni in naje gidan a matsayina na ƙanwar matar yayansu? Wani irin shu'umin murmushi Aunty babba ta saki wato anzo dai dai wurin da tafi so, miƙewa tayi daga zaunen da take agaban mirror tashiga zagaye bedroom ɗin nata tana cewa"Hayaaam baki da Matsala indae a gidan nan ne! Kinsan yarda Abbansu ke da son ƴa'ƴa hannu biyu zai kar6eki abu daya kawai nasani shine dole sai da iznin Abi sannan zai kar6eki don haka kibarmun wannan a hannuna ni zanyi magana da mommynmu tunda ita ke juya shi da zarar tayi mashi magana zai amince!abunda kawai nakeso dake hayaam shine kiyi gaggawar komawa gidan da zama acikin watan nan!Ke bama sai kin je da komai ba tsurarki zaki tafi batare da trolly na kayanki ba,saboda inaso ki fara fakewa da cewa kinje duba Fawan ne da bashi da lafiya daga nan kawai saikiyi zaman ki dirshan babu mai tanka maki saboda duk matasan gidan miskilai ne babu ruwansu,da ace dae yana da ƴa'ƴa mata shine za'a samu matsala kinsan mu mata da bakin ciki da hassada muke....'  Murmushi kawai hayaam ke saki tana faman lumshe ido tare da cizon pink lips dinta saboda shock ɗin da takeji na sofwan dake bin jikinta da hannun shi yana shafa ko'ina,Auntyna indae ni ce just karki samu damuwa,ki ƙaddara cewa gani can ma acikin gidan ina watayawa ta,ita kuma wannan yarinyar da kika sanar mun cewa tana zaune a gidan tuni zansa su yi mata checking out badai ni bace ba hmmmmmm,  Dariya aunty babba ta saki tare da cewa"har naji sanyi araina,burina na dab da cika,"
Download>>>Â Yar Harka Complete Document
 Sun jima suna wayar kafin daga bisani suka yi sallama da junansu,   Buge hannun sofwan tayi tare da cewa"duk kabi ka takuramin wai kai wani irin jarababben mutun ne mai nacin tsiya haba mtwww,"taja dogon tsoki  Baki asake yabi ta da kallo tare da cewa"ni kike ma tsoki wai?wato wannan haɗamammar auntyn taki takira duk ta tunzuraki akan abunda bazai ta6a faruwa ba,duk naji mai kuka tattauna da ita,  ya fadi yana faman sakin hucin 6acin rai,murmushi hayaam ta saki tare da cewa"Sofwan zamana dakai ya ƙare!!!!!!!
ï¿?
 Zaro ido waje yayi yana kallonta hankali atashe yace"saboda me hayaam?kada kiyimun haka don Allah!amma dae nasan wasa kike mun ko?  ƴar dariya tayi kafin tace"na ta6a maka wasa irin wannan?zanje na nemi namijin duniya ne!cikakken namiji jarumin gaske wanda ya kasance burin kowace ƴa mace ne shi bazanyi gangancin rasa cikar burina ba sofwan....... Bata ƙarasa ba ya dauke ta da mari ji kake faaaauuuu!  Rai a 6ace yace"Wlh baki isa ba hayaam ki katse mun jin daɗina ba!!saboda ke dakikiya ce sam bakisan meke maki ciwo ba wannan wani irin abun kunyane zaki kwasa kawai ki koma gidan surukanku da zama?Anya kuwa yayarki ba mahaukaciya bace.....   bata bari ya ƙarasa maganar tashi ba ta zame hannunta data dafe kuncinta dashi ta daddage ta zabga mashi zafafan maruka har guda uku sannan tace"karka kuskura ka ƙara kiran auntyna da sunan mahaukaciya!!maganar tafiya kuma ba fashi sofwan inka ga ban tafi ba to wlh numfashi na ne ya tsaya don ko ba ƙafa saina je,😳  Tuni sofwan ya rikice ganin yarda hayaam ta zabga masa mari batare da jin komai ba,duk irin yarda yake tarairayarta don karya rasa ta amma lokacin guda auntynta ta canza mata tunaninta,  Kallonta ya shiga yi yana girgiza mata kai yayin da idonshi suka cicciko da kwalla muryarshi a kasalance yace"Hayaam kada kiyimun haka dan Allah!saboda ke na wulaƙanta iyayena na baro komai nawa don muyi irin rayuwar da kikeso,wannan gidan fa duk don saboda ke na gina shi hayaam,ki duba gidan da iyaye na suke ciki duk ya rakwakkwa6e amma saboda ke na gidan wannan katafaren gidan ko don saboda wannan pls hayamm kada kibarni komai kikeso zanyi maki shi," yayi maganar tare da zubewa saman guiwowin shi a gabanta yana faman sharara hawaye,amma maimakon yaga alamun tausayi a idonta saima ta fashe mashi da dariya tashiga tafa hannaye tana cewa"sofwan kaifa dakanka kace ka wulaƙanta iyayenka saboda Ni?shin ni wacece a wurinka?mutumin da bai daraja iyayensa ba musamman uwarsa data tsugunna ta haifeshi taci baƙar wahala kanshi!ga kuma mahaifinsa daya fitar da gumi wurin nema masa kyakkyawar rayuwa duk bai duba wannan ba,burinka kawai ka farantama wasu can waɗanda basu son ciwonka ba,waɗanda ko yau ka faɗi ka mutu wlh shewa zasu yi suce Allah raka taki gona,shine har kake mun kwatance da ka wulaƙanta iyayenka don saboda wata banza can Ni?hanyar Aljanna nake sanya ka kota wuta?ko zan taimake ka ne ranar lahira?sofwan haƙƙin iyayenka ma kawai ya isa ya tarwatsa dukkan wani farin ciki na rayuwarka!!idan ma naci gaba da ra6arka nima zan shiga matsala ne don haka kawai muyi break up kawai kowa yayi rayuwarshi,"  ta ƙarasa maganar tare da ruƙe waist dinta tana kallon shi a tsiyace,  Miƙewa yayi daga kneel down din da yayi ya kalleta da fuskar tausayi yace"kada kiyi mun haka hayaam indae alaƙata da iyayena ne zan gyara komai...'  girgiza mashi kai tayi tare da cewa"na yaushe sofwan?hmmm ba don Allah zama kayi masu ba sai don saboda ni abanza kam,shiyasa koda yaushe soyayyar SGR take ƙara ninkuwa araina duk da irin tarin dukiyar dake gare shi hakan baisa ya canza ma iyayenshi ba ko wani nashi,zokaga Namijin gaske mai tsananin biyayya ga iyayensa wanda yasan darajarsu yake binsu sau da ƙafa kaifa? Har yau mahaifinka bai daina siyar da kifi a gefen titi ba, ga Mahaifiyarka cen kullum safiyar Allah sai tafito da murhu kopar gida tana suyar ƙosar da kunu,taya ma zan cigaba da kasancewa dakai!!? Kana da arziƙin da zaka iya ciyar da karuwai ka gina ma iyayensu gida ka kuma gina masu su kansu Amma iyayenka fa!!!?  shiru Sofwan yayi yana kallonta idanun shi sunyi jawur dasu ga wani ƙululun baƙin ciki daya tsaya masa a maƙoshinsa,  Wuce wa hayaaam tayi wurin wardrobe dinshi saboda anan kayanta suke nasawa, hannu tasa ta buɗe wurin kayanta tana raira waƙar nan ta namej dayake cewa"ko babu mota ba abun hawa wlh saina jee,"  A wani irin fusace Sofwan ya cafki hannunta data ruko bra dinta dashi,dakatawa tayi da yin waƙarta ta tace"Malam sakarmin hannu na,"  Yana wani irin huci yace"Hayaam baki isa kibar gidan nan ba, batare da kin mayar mun da duk wani abu dana kashe maki ba!!wlh bazaki ci bulus ba,duk kin taƙaitani duk ƙarshen wata saina kawo maki kayan abinci kwalin indomie kwalin taliya da sauran kayan abinci, sannan duk ƙarshen sati muna zuwan shopping mall dake nayi maki siyayya kuma mu fita restaurant cin abinci,ga kuma kuɗin mayukan da nake siya maki su kansu kudinsu yakai na dubu dari biyar,in kin ga kin bar gidan nan to ki tabbata kin haɗa mun kuɗaɗe na kin mayar mun dasu," ya ƙarasa maganar yana jifanta da wani irin kallo,  ta6e baki tayi tare da cewa"Naji duk zan biyaka ni kuma da me zaka biyani jikina da kayi amfani dashi?donni ma bazaka Ci bulus ba tunda ba uwar mutun ta haife ni ba,ka biyani budurcina nima saina biyaka kudinka"A shagale take maganar tana faman sakin murmushi,  Shiru sofwan yayi yana faman mazurai aransa yana tunanin taya zai biyata virgin dinga da take magana akai?  tsoki taja tare da buge hannunshi tabar shi tsaye a wurin ta koma daga gefe tana zura brazier dinta,  Muryarshi ce ta kuma katse ta da cewa"naji wannan tabbas bazan iya biyanki budurcinki ba,amma inaso ki sani bazan bari ki ɗauki ɗaya daga cikin abunda nasiya maki ba da kudina,daga ciki kuma hada kayan sawa don dama a tsiyace kikazo gidan nan,
Download>>>Â Babban Yaya Complete Document
 harara ta wurga mashi tare da cewa"Matsalarka ce wannan!ae ni abun kunya gaba na bashi ba baya ba,in ka hanani sa sutura sai in tafi a zir abuna," ganin tana shirin ɗaura mashi hawan jini yasa shi buga jikin wardrobe din da hannunshi yana kallonta idonshi jawur rai a tsananin 6ace ya fuce yabar mata ɗakin gaba daya, Murmushi tasaki tana cizon la66anta aranta tace"ƙaramin ɗan duniya har ni zakayi wa barazana,"
*******************
Tsare ta da ido hafsat tayi wadda shigowarta kenan bedroom din ta, Ta jima a la6e tana sauraron firar da mommyn nata keyi da Hayaam a waya, sai da tabari ta kammala sannan tashiga daga cikin ɗakin tana kallonta, tunkan tace wani abu aunty babba tayi saurin cewa"to ƴarsa ido uban me yakawo ki dakina? murmushin takaici hafsat tayi kafin tace"narasa meke damunki mommy!gaba daya naji wayar da kikayi da aunty hayaam,saboda me zaki ce ta tattara kaya ta koma gidansu Abbana da zama?wannan wane irin abun kunya ne ace ƙanwar matar yayansu tana rayuwa acikin gidansu? menene alaƙarta dasu?gsky wannan tsarin sam baiyi ba mommy yakama ki dakatar da hayaam daga zuwan gidansu........' tunkan taƙarasa aunty babba ta kwatsa mata tsawa tare da cewa"munafuka!!ashe la6e kikeyi mun ni narasa gane meke damunki hafsat!!tunda waɗancan yaran da omar yakawo mun suka zo gaba ɗaya duk sun canzamin ke, yanzu bakya goyon bayana......' Tana magana tana yin nuni da hannunta dake ruke da wayarta, ta6e baki hafsat tayi tare da cewa"Mommy kenan,mgnr da kika faɗa gaskiya ce,Jahad da hossana ba ƙaramin sauyani su kayi ba saboda akansu na fara tausayin wani dan adam a duniya,sun goga mun kyawawan ɗabi'unsu da halayansu waɗanda ke baki ta6a gwadamun ba,haƙiƙa nayi rashinsu sosai kuma ina fata Allah ya ƙara hadani dasu wata rana.....' murya asanyaye tayi maganar,  Sakin baki Aunty babba tayi tana kallonta kamar me son gano wani abu can dae tace"Hafsat kodae kece kika sa Abbanki ya hanani zuwa abuja ganin jikin fawan?ina zargin hakan!! kaitsaye tace"Nice mommy!ni nasame shi na roƙe shi akan cewa kada yabari ki tafi ke kaɗai sai tare dani saboda bana jin daɗi yanzu bazan iya zuwa ba,"  a fusace tace"Meyasa"! Murmushi hafsat tayi tare da cewa"Saboda ba don Allah zakije ba!bakuma don kije duba jikin fawan ba face donki je ganin yarinyar da Aunty Amani ta sanar dake, ni kuma gsky bana son ma ki ganta balle har kiyi yunƙurin cutar da ita, don kuwa bazan sake bari ki cutar da wani ba saboda wani buri can da kike dashi wanda bazai ta6a cika ba.......' Da gudu hafsat ta fuce daga dakin ganin yarda Aunty babba ta zabura zata cafkota takai mata bugu,'  bedroom ɗinta ta koma tana faman tiƙar dariya hadasu dafe ciki, Ita kuwa aunty babba tuni idonta sunyi jawur saboda 6acin rai,tama rasa me zatayi ta huce,ashe hafsat ce ta hana ishaq barinta taje abuja yau lallaikam zata ci ubanta ne dani take magana, Ta fadi tana faman huci,
*********AFTER 2WEEKS************
*Bayan Sati uku*
Tuni jikin fawan ya ɗan murmure yaji sauƙi sosai har yana iya miƙewa ya taka yaje inda yake so hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba,a 6angaren su twins kuwa murna har ba'a magana saboda alert ɗin kuɗin da mommynsu ta turo ta wayar jahan a cikin dollar acct dinsa, a tsakar dare alert din yashigo a lokacin suna maƙale da juna kamar yadda aka saba,gaba ɗayansu suka buga shewa cikin jin daɗi ba don komai ba sai don zasu rabu da matsin Haroon su huta,a daren ranar har nafilar dare sukayi atare suka roƙi Allah akan ya yaye masu masifar dake damunsu, sun sha kuka kamar kamar me,sannan kuma sun shirya zuwa bank domin su kar6o masa kuɗinshi miliyan tamanin su damƙa mashi,😣 dama sai zarya yake yi masu kullum safiyar Allah yana musu barazana,ba don sun nuna mashi kuɗin ba dake cikin acct dinsu ba ya gani awayarsu, da bazai ƙyalesu ba,
DOWNLOAD:Â "HARIJI BOOK 1 COMPLETE DOCUMENT"
A 6angaren Hossana da Jahad kuwa hmmmmm just speechless,wata irin rayuwar hutu da jin daɗi suke gudanarwa acikin hamshaqin gidansu,babu ruwansu da kowa su biyu abunsu sai Camillah dake yawan zuwa dubasu wani lokacin takan tsaya ta kwana ma acikin gidan,ba ƙaramin gyarasu tayi ba,domin kuwa sun canza fiye da tunanin mai tunani,fatarsu kanta abun kallo ce, ga wasu irin surorin kyau da suka bayyana ajikinsu,sun koma rainon Madara rainon bonvita 😂 Ƴancin da su hossana suka samu ko mutanen nigeria a 1960 basu samu makamancin shi ba,hossana fa har wasu kumatun jin daɗi tafara ajiyewa🤣 dama bata wasa da abinci gashi Omar ya cika masu store da kayan abinci kala kala, ga freezer dinsu dake shaƙe da kayan sha,kullum in jahad tayi mata maganar tadinga ci ahankali sai tace"ina ruwanki!In suka ƙare yaya Omar zai siya mana wasu," 🥱 Marshal omar bai barsu hakanan ba, sai da ya ƙara masu security guards har mutun huɗu, Osman kuma shine a matsayin drivern da zai dunga kaisu School da wuraren shaƙatawa,tuni ya cike masu form na school koda akazo wurin sanya sunan uba ya tambayesu sunan mahaifinsu sai cewa suka yi "kasa mana sunanka kawai ya omar,mu bamu da uba," wani irin kallo yayi masu tare da cewa"ban shirya haramta ma kaina ɗaya daga cikin ku ba,don haka zan sanya maku sunan Uncle ɗina ne a matsayin Mahaifinku amma banawa ba,' Sam basu gane mai ya omar ɗinsu ke nufi ba da cewa bai shirya haramta ma kanshi ɗaya daga cikinsu ba,sun dai bar abun ne kawai azuciyarsu,  Alhamdulillah Omar ya kammala cike masu form da sunan Uncle dinshi,JAHAD ABUSUFYAN da kuma HOSSANA ABUSUFYAN,ba ƙaramin daɗi suka ji ba saboda jin ya saka masu sunan mutumin nan da goggon katsina ta ƙaƙaba masu amatsayin Ubansu, sunan makarantar da suka fara zuwa D.A International acadermy wato makarantar da Sehrish ke zuwa🤔
_💋Boss Bature💋_
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990
11:30 na dare
Fitowarta kenan daga toilet jikinta ɗaure da towel,ba ƙaramin canzawa tayi ba gaba daya ta sauya saboda hutun da take samu ga kuma kwanciyar hankali,tun daga kan natural skin colour dinta zaka gane hakan,yanzu bata wasa da tsaftace jikinta kullum cikin ƙamshi take,
 Ƙarasawa tayi gaban mirror tana cigaba da tsane jikinta da towel ɗin hannunta,bayan ta kammala tayi hanging dinsa daga gefen mirror din,sannan ta kai hannunta jikin drawer chest na mirror,janyowa tayi tare da zura hannunta ta ɗauko hand dryer,jona ta tayi ajikin socket nan take ta soma buso da iska, cikin sauri ta kanga ta saitin kanta taci gaba da busar da gashinta,cikin nishaɗi take yi saboda ta mayar da abun tamkar na wasan yara, natsuwa tayi tana tunano abunda suka tattauna da Azmee acikin kitchen bayan ta sanar da ita maganar da sukayi da abbansu nacewa tafara kamun ƙafa tun daga yanzu,  dariya sosai azmee tayi tare da cewa"Abba da zolaya wato in marks dinki yazo da F shine zai aura maki haroon gsky kwara ki dage,"  Murmushi sehrish tayi tare da cewa"Amma aunty azmee ya akeyin kamun ƙafa inaso na iya"?   ɗan gyaran murya azmee tayi kafin tace"Kyautatawa mana,kinsan ita zuciya nason mai kyautata mata,kamar abbansu atlease yakamata ace duk safiyar Allah kina zuwa har bedroom ɗinshi kina miƙa gaisuwa hakan zai ƙara maki daraja a idanunshi kuma zai tabbatar da cewa kina da tarbiyyya sosai,sannan 6angaren girki yakamata ace ma yanzu kinfi ni iya girki,tuntuni dama inaso nayi maki magana akan koyon girki,saboda maza nason macen da ta iya girki,kin ga mazan gidan nan basa wasa da abinci akwai son cin mai daɗi,shiyasa nake da kusanci dasu sosai saboda yarda nake masu girki,don haka kema daga yanzu ki fara trying bafa dole sai irin nawa ba a'a salo na daban yakamata ki koya,bari na baki satar amsa kamar abincin gargajiya haka namu na hausawa saboda a gidan nan sunfi sabawa da abincin turawa,yakamata ki fara jaraba yi masu shi,ki koyi sarrafa abinci kala kala hada abunsha da kuma irin kayan makwalashe haka da sauransu,sannan 6angaren tsafta domin kuwa itace gaba da komai,idan ma kina da tsafta to ki ƙara akan wadda kike da ita,saboda mazan gidan nan basa son ƙazanta ko miskala zarratin,tun daga kan tsaftar jiki yakamata ki fara kulawa,wurin yin shaving na armpit dana under,da kuma kula da teeth dinki wurin yin brush akai akai banda barin datti ajiki,da kuma kula da gashin kanki wurin gyare shi,hatta nails ɗinki ki runƙa kula wurin yankesu banda tara akaifa,ina fada maki wannan ne domin amfanin kanki,don ita mace da tsafta akasanta da son ado,inaso kema ki kasance haka.........  Sosai azmee ta koyar da ita abubuwa da dama na rayuwa waɗanda zasu amfane ta,kuma tun daga lokacin duk in suka shiga kitchen suna aiki tana ƙara ilmantar da ita,hakan yasa sehrish ta soma canzawa sosai, yanzu kullum cikin gyara kanta takeyi,sannan bata wasa wurin koyon girki dalilin hakan yasa tashiga whatsapp grp na koyon girki,kullum tana cikin ɗaukar videos ɗin girki tana kallo donta koya,a hankali a hankali yanzu harta fara jin zata iya jaraba yi masu abinci acikin gidan 😇
murmushi ta saki bayan ta kammala tunanin a fili tace"bansan da wasu kalmomi zan iya godema aunty azmeena ba,saboda tagama yi min komai a rayuwa ina jinta tamkar mahaifiyata ne,Ya Allah ka barni da aunty azmee na,"â?   jin alamar shigowar motocinsu yasa ta yin saurin cire hand dryer É—in daga socket ta mayar da ita inda ta É—aukota, sannan ta taka izuwa wurin wardrobe ta buÉ—e tana neman kayan da zata sanya,wurin jerin kayan baccinta ta duba,wasu riga da wando ta dauko Æ´an qasar indonesia masu matuÆ™ar kyan gaske ga laushi jikinsu,launinsu maroon colour ne masu É—igon baÆ™i baÆ™i ajikinsu, cikin sauri ta zurasu ajikinta sannan ta É—auki mayafi tayi rolling dinsa akanta, sai da ta tabbatar da cewa sun shigo ciki kusan 15 mins ta Æ™ara sannan ta buÉ—e Æ™opa tare da fitowa daga É—akin nata,Æ™afarta na sanye da flat shoes,miÆ™o hanya tayi tana tafiya a hankali ta biyo ta main palour din babu kowa har sun wuce ciki,kitchen ta wuce don ta haÉ—a mashi tea tare da kayan marmarin dayake buÆ™ata kamar kullum,
Tare da Marshal Omar suka bar gidan,amma SGR ne kawai ya dawo saboda Omar ya wuce wurin su Hossana,tun akan hanya suka rabu dashi, a galabaice ya shiga part dinsa saboda rashin jin daɗin jikinshi dayake yi,tun safe bai da lafiya amma saboda juriya irin tashi da ƙarfin hali ba wanda ya lura da hakan,wani irin sever headache tare da zazza6i mai zafine ya rufe shi, Jikin shi na sanye da Army trouser tare da shirt light green colour,kai tsaye yana shiga bedroom dinsa ya faɗa saman bed dinsa batare da ya rage kayan jikinshi ba,saboda rashin ƙarfin jikin shi da yake ji,abun yazo mashi wani iri saboda kafin yayi ciwo da wuya mutun ne mai cikakkiyar lafiya,sam bai sanarwa kowa ba saboda baya son tayar masu da hankali kuma baison aga raunin shi,
Sehrish
Fitowa tayi daga kitchen ɗin hannunta ruƙe da tray mai ɗauke da ƙayataccen plate na fruits sai cup mai ɗauke da Hot tea sai faman tiririn Zafi yake yi,a natse take tafiya kai tsaye ta nufi stairs ɗin tana cikin tafiya kamar daga sama taji muryar haroon yana cewa"Wurin Namiji za'a ne"? A wani irin firgice ta juya tana neman ta inda zata ganshi,  Yana zaune saman 3 seater shi kaɗai abunshi jikin shi na sanye da night dress riga dai dai guiwa,ya aza ƙafa ɗaya bisa ɗaya yana faman sakar mata murmushi,    Ba ƙaramin tsoro ya bata ba saboda bata tsammace shi a wannan lokacin ba,cikin sauri ta wuce upstairs gabanta na faɗuwa aranta tana cewa"Anya haroon Ba Aljani bane?in ba haka ba yaushe har ya shigo babban falon nan amma banga gifcin shi ba," tana tafiya tana sambatu aranta har ta ƙarasa part dinsa, sai da ta tsaya tare da dai daita natsuwarta sannan tashiga ciki, wayaam babu kowa a falon hakan na nufin yana a cikin bedroom dinsa, Takawa tayi a hankali har zuwa ƙopar bedroom din nashi sannan tayi sallama,kusan sau uku ba'a amsa mata ba sai a na huɗun ne taji muryarshi ƙasa ƙasa ya amsa mata "come in,"  a hankali tasa ƙafarta tashiga ciki,lokacin da ta ɗago da idanunta nan take taji faɗuwar gaba rasss!yanayin da taganshi yayi uban goho saman gadon yana fitar da numfashi daƙer daƙer ba ƙaramin tayar mata da hankali yayi ba,tuni jikinta yayi mugun sanyi,ƙarasawa tayi ciki tare da ajiye mashi tray din saman table tace"Sannu da dawowa ga tea nan na kawo maka,ko akwai wani abu da kake buƙata"? shiru bai bata amsa ba sai numfashi kawai da yake fitarwa mai hucin zafi,bin shi tayi da kallo sumar kanshi ta rufe dukkan fuskarshi side by side,tana so ta tambaye shi ko lpy amma tana jin tsoro,  Kusan 15 mins tana a tsaye bai ce komai ba ƙoƙari yake ya tashi amma sam jikinshi ya hana shi,sai da yayi dagaske sannan ya samu ya miƙe tare da matsowa ya sauko da legs dinsa ƙasa idanunshi a rufe rufff,fuskarshi ba ƙaramin canzawa tayi ba,jikin shi sai kerma yake yi tamkar wanda yashiga snow hatta pink lips dinsa sun gaza tsayuwa,tsananin tausayin shi ne ya kama sehrish saboda ta tabbatar da cewa bai da ƙoshin lpy sbd alamomin da tagani atattare dashi,tuni taji hawaye na ƙoƙarin zubowa daga idonta,  muryarshi ce ta tsinkayeta da cewa"ki duba a cikin side drawer ɗina thete's a jotter wit pen pls bring it 4 me," cikin sauri sehrish ta matsa tare da kai hannu jikin side drawer ɗin,ta janyo gida na farko ajikinta, anan ta samu Jotter ɗin tare da biro,ɗaukowa tayi tare da miƙa mashi,  daƙer ya cire hannunshi ya kar6a har lokacin eyes ɗinshi na'a rufe,aza jotter ɗin yayi daga gefen table ɗin gabanshi,buɗe papers din ciki yayi kafin ya aza biro din ya soma rubutu bayan ya kammala yayi tearing wurin da yayi rubutun ya ɗauko takardar ya miƙa ma Sehrish,cikin sauri tasa hannu ta kar6a tare da aza idonta kan rubutun wani irin handwritting gare shi domin koda ta kalla ko *A* bata iya ganewa ajiki ba hakan yasa ta kalle shi tare da cewa"Bangane menene ka rubuta ba,"ta faɗi a ɗan tsorace "Go nd bring it 4 me," shine kawai abunda ya iya furta mata, Cikin sauri sehrish ta kama hanyar fita daga bedroom ɗin nashi tana waiwayonshi,  Saukowa down stairs tayi tana faman cizon yatsa saboda tarasa gane menene ya rubuta mata,tamkar zatayi kuka,tana cikin wannan halin muryar haroon ta katse ta da cewa"Can I help u"? ɗagowa tayi aɗan razane tana kallon shi,fuskarnan tashi nadauke da murmushi yasa hannu ya kar6i takardar yana duba rubutun jiki,daga bisa ni yace"Ki jira ni anan yanzu zan dawo," yana fadin hakan yajuya da sauri ya shige part ɗinsu na nan downstairs, ajiyar zuciya ta saki aranta tana Allah Allah saboda tsoron kada haroon ya tafka mata kuskure don tasan halin shi,bai da tabbas gajiya da tsayuwa tayi,don haka ta samu wuri saman last step na benen ta zauna tana jiran dawowarshi,.
Ba da jimawa ba sai gashi ya fito daga part din nasu, sai faman sauri yake yi irin da himmar nan hannun shi na ruƙe da syringe da kwalbar injection,tunkan ya ƙaraso sehrish ta miƙe tare da sa hannu ta kar6a tana yi mashi godiya,,
 da buɗar bakinsa sai cewa yayi"Ba sai kin gode mun ba,Aikin lada ne fa nidae burina ki kai mashi allurar ya hanzarta yi yanzu,in ma godiyar ce gobe da safe kinzo ki same ni kiyi mun ita," yana magana yana sakin wannan shu'umin murmushin nasa, jiki asanyaye tasa hannu ta kar6a tana kallon fuskarshi shima kuma ita yake kallo da wannan murmushin nashi, cikin sauri ta juya tare da hayewa upstairs cikin sauri take tattaka matattakalar benen har ta wuce part dinsa
Ruƙe qugu haroon yayi tare da sakin wani irin bazawarin murmushi yace"Lokacin Bacci yayi bari naje na kwanta gobe da safe akwai labari zazzafa,ƴar shila zata zo miƙo mun godiya da kanta," ya fadi tare da sakin dariya ya wuce sashen shi
 Lokacin da sehrish ta koma É—akin nashi yarda tabarshi haka ta same shi zaune idonshi a rufe, cikin sauri ta Æ™arasa tare da miÆ™a mashi allurar da sirinjin tace"Ga allurar," hannu Sgr yasa ya kar6a daÆ™er ya iya buÉ—e idonshi sam baya iya gane wace kalar allura ce yarinyar ta kawo mashi saboda idanunshi biji biji suke gani hakan bai bashi damar karanta abunda aka rubuta ajikin Æ™aramar kwalbar allurar ba,   fasa bakin kwalbar yayi tare da curo sirinjin ya fiddo da kan allurar ya tsoma acikin kwalbar ya zuÆ™o ruwan allurar iya yadda yasan ya dace yayiwa kanshi, .Tuni jikin sehrish ya soma rawa saboda tsoron allura gareta,cikin sauri ta kama hanyar fita daga dakin saboda ta bashi damar yin allurar,  Muryarshi ce ta tsinkayeta da cewa"kada ki tafi," ya furta yana faman sakin huci daga bakin shi da hancinsa, A bakin Æ™opar ta tsaya idonta a rufe jikinta na kerma,muryarshi ta kuma ji yace"ki zo," cikin sauri ta koma ajiyar zuciya tasaki ganin harya kammala yin allurar, miÆ™a mata kwalbar allurar yayi tare da syringe din duka yace"kisa a dustbin," amsa mashi tayi tare da kar6a ta wuce wurin bedroom dustbin dinshi ta saka tarkacen allurar, sannan ta dawo ta tsaya tana jiran jin ko zai buÆ™aci wani abu tunda ya nuna baison ta tafi,  Lokacin da allurar ta gama gauraye ko'ina na jikinshi da wani irin Æ™arfi ya ware idanunshi azare,har sai da sehrish taÉ—an ja da baya saboda firgitar da tayi,bin yatsun hannunshi tayi da kallo ganin yarda yake wawwaresu suna miÆ™ewa tsaye,tamkar dae yadda mutun ke komawa Zombie acikin film,gabanta ne yashiga faÉ—uwa saboda tsoran da taji murya na rawa tace"Zan iya tafiya"?  ɗagowa yayi da wannan sexy blue eyes din nashi da launinsu ya Æ™ara Cizawa gwanin ban tsoro kai kana ganinsu kasancewa akwai matsala,ido cikin ido yake kallonta batare da ya kawar da idonshi ba hakan yasa zuciyarta Æ™ara karaya ga wani irin fargaba daya zo mata,ganin irin kallon da yake yi mata ne yasa nan take tadinga jin bugun zuciya,ja da baya ta soma yi jikinta na kerma har lokacin bai janye idonshi daga kanta ba bin ta kawai yayi da kallo,sai da taga taÉ—anyi mashi nisa sannan ta nufi hanyar fita daga bedroom din nashi da saurin gaske sai dai ina, kafin ta Ankara tuni SGR yayi wani irin kwakkwaran motsi tare da miÆ™ewa tamkar wani Zaki ya bi bayanta azafafe yakai ma Waist É—inta wani irin ruÆ™o ya É—aga ta sama gaba É—aya ta saki wata irin razananniyar Æ™ara mai rikitarwa bata gama rufe bakinta ba yayi wani irin wurgi da ita kai tsaye ta faÉ—a tsakiyar gadon shi yaraaaff tuni mayafin da tayi rolling dashi ya jima da barin jikinta !!!! Ba Æ™aramin buguwa sehrish tayi ba daÆ™er ta iya tayar da kanta daga jikin bedmattress É—in ta É—ago hankali a matuÆ™ar tashe take kallon shi ganin yasanya hannayenshi tare da ruÆ™o shirt É—in dake ajikinshi ya cire ta gaba É—aya tare da yin wurgi da ita Æ™asa,   gabanta ne yasake yin wani irin mugun bugu tuni hawaye sun soma wanke mata fuskarta cikin tsananin tashin hankali take girgiza mashi kai tana cewa"innalalahi wa'inna ilaihirraji'un nashiga uku !!!!"   Sam babu alamar sassauci a tattare dashi kai kana ganin yanayin action dinsa zakasan cewa ba a hayacinshi yake ba, Hatta Æ™arfin jikinshi bana shi bane a matsayin shi na wanda bai da Cikakiyar lafiya, Ganin ya zame belt É—in wandon jikinshi gaba daya yayi throwing dinsa, tare da sa hannu yana Æ™oÆ™arin zame wandon dake jikinshi, hakan ya Æ™ara tsoratar da sehrish yunÆ™uri tayi da Æ™arfi zata diro daga saman gadon ta gudu,aikuwa batayi wani aune ba taji saukarshi saman gadon gaba É—aya ya afka mata tare da yi mata Rumfa da faffaÉ—an Æ™irjinshi tsulundum taji ta ajikinshi,🙆ðŸ½â€â™€  nan fa ido ya raina fata,dukkan ilahirin jikinta rawa yake yi gaba É—aya tagama rikicewa muryarta har wani shaÆ™ewa take yi wurin cewa"Dan Allah kayi haÆ™uri kabarni na tafi,ni nasan cewa ba halinka ba....ba yin kanka bane.......' kasa Æ™arasa maganar tayi saboda idonshi dake kallon cikin kwayar idon nata,SGR fa a halin yanzu zamu iya cewa baya ji baya gani,   Wani irin huci yake yi yana groaning just like a hungry lion,runtse idonta tayi saboda bazata juri kallon cikin nashi ba yayin da idonta ke cigaba da zubar da hawaye...........🙆ðŸ»â€â™€ï¸ðŸ™†ðŸ»â€â™‚ï¸ðŸ˜?
Zuwa ga masu share na littafina lokacin da mutun zai sayi littafin nan ba muyi yarjejeniya nacewa zai turama wasu ba, amma sai gashi grp ba iyaka ana tura littafin koma waye yaje don kanshi kuma yasani akwai haƙƙina akanshiðŸ‘ya Allah kashiga tsakanina da koma waye,
*************
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi bakuðŸ˜u  💋Boss Bature💋
runtse idonta tayi saboda bazata juri kallon cikin nashi ba yayin da idonta ke cigaba da zubar da hawaye........... Jin shiru yasata ta sake buɗe idanunta don taga me ya dakatar dashi har lokacin blue eyes ɗinshi na akan fuskarta tamkar mai nazarin wani abu,Allah sarki duk da bai a hayyacinsa yana ƙoƙarin ya dakatar da kanshi yayi control na kansa,Amma ina allurar ƙara zaburar dashi takeyi,sai faman ciccije pinkish lips dinsa yake yi,gaba ɗaya sumar kanshi ta lullu6e fuskarsu su duka biyun,   wata irin Zufa tagani tana tsattasofa mashi daga fuskarshi hakan ba ƙaramin razanar da ita tayi ba,ɗigowa sweat din tadinga yi daga fuskarshi tana sauka a fuskar Sehrish,
  tuni ta soma haɗiyar yawu ganin yaƙi moving daga rufe ta da yayi hakan yasa,ta tattara dukkan ƙarfinta gaba ɗaya don ta ingije shi kota samu yayi gefe ɗaya ita kuma ta gudu,amma abun mamaki koda tasa hannunta tayi attempting ingije shi,ko motsi wannan baiyi ba saboda wani irin ƙarfine yazo mashi bana wasa ba, ..zaro ido tayi tana kallonshi hankali atashe,abun mamaki for the first time saita samu fuskarshi ɗauke da wani irin ƙayataccen murmushi naban mamaki lokaci guda yagama kashe mata jiki gaba ɗaya taji wata irin kasala ta rufar mata,   kwakkwarar damka yakaima wuyan rigar jikinta ya yage ta biyu nan take big boobs dinta suka bayyana gashi bata saka brazier ba,kokawa suka shiga yi dashi domin kuwa ta damƙe rigarta da yake ƙoƙarin yin wurgi da ita,sai faman ƙoƙarin rufe ƙirjinta take yi da ita,a ƙarshe daya fi ƙarfinta sai ta fashe mashi da wani irin matsanancin kuka da ƙarfin gaske take cewa"...Ya Allah ka kawo min ɗauki......Ya Allah ka dawo dashi cikin hayyacinshi ni nasan cewa ba yin kan shi bane.....  tuni ya afka ma ƙirjinta ya tasar masu, hannu takai tana ƙoƙarin janyo bedside lamp ɗinshi amma koda ta ruƙo fitilar ji tayi bazata iya cutar da shi ba kokaɗan saboda tsananin son da take yi mashi,tana jin duk wani motsin shi ajikinta,   Har bakinta takai a damtsen hannunshi don ta gartsa mashi cizo amma ina koda ta aza teeth ɗinta a fatar jikinshi sai dae kawai tafashe da kuka saboda bazata iya ba😢   Suna cikin wannan yanayin Marshal Omar ya faɗo cikin falonsa dawowarshi kenan daga wurinsu hossana bakomai ne ya kawo shi ba face message ɗin da sgr ya turo mashi a wayarshi nacewa bashi da lafiya,bai sanar mashi ba a lokacin da suke atare sai da suka rabu yana acikin mota ya rubuta mashi message ɗin, ganin saƙon da yayi ne yasa shi yin hanzarin dawowa gidan don ya duba shi,   Yana shigowa falon yaji sautin kukan Sehrish acikin ɗakinsa ga wani irin gurnani da sgr keyi na irin kura taga naman nan, hankalin shi a matuƙar tashe ya afka bedroom ɗin nashi,ba ƙaramin razana Omar yayi ba ganin yarda Sgr ya rufar ma Yarinyar gaba ɗaya ya danneta a lokacin harya zame dogon wandon jikinshi,shorts ne kawai ya rage mashi shima ƙoƙarin zame shi yake yi daga jikin shi,   A tsawa ce Omar ya kwaɗa mashi kira da ƙarfin gaske ya furta "RAFAYET!!!!!!!!!!!!!!!!! Tamkar maƙoshin shi zai 6allo waje haka ya ambaci sunan har kunnan sehrish, amma shikuwa gogan sam ba alamar yaji balle ya ɗago,   Ganin hakan yasa Omar yin hanzarin ƙarasawa tare da kai hannunshi a matuƙar zafafe ya damƙi sumar kanshi da karfin gaske ya janyo shi yayi wurgi dashi gefe guda saman gadon,  Cikin sauri sehrish ta rufe ƙirjinta da rigar ta wadda sgr ya yage mata ita,tashi tayi zaune tana ta faman sessheƙar kuka ga jikinta dake ta faman kerma,   tamkar zaki haka Sgr ya kuma ɗagowa daga wurgin da Omar yayi dashi gaba ɗaya ya makance,wani irin ihu sehrish tasaki ganin yasake nufota yana wani irin gurnani,  Cikin hanzari Marshal Omar ya damƙo damtsen gannunshi yana cewa"Wai meyake damunka ne!!!me kake ƙoƙarin yi ne!!!   Juyowa sgr yayi yana wani irin huci ya kalleshi tamkar baisan omar ba haka ya zabura ya miƙe tsaye tare da dirowa daga saman gadon ya daddage ya dunkule hannunshi yakai mashi kwakkwaran naushi a saman ƙirjin shi,ba ƙaramin zafi Omar yaji ba,rai a6ace shima ya cakume shi tare da kai mashi naushi,nan fa suka kaca me gaba ɗayansu tamkar ƴan wrestling haka suka shiga bugun junansu,  ganin haka yasa sehrish saukowa daga saman gadon dama ta samu ta zura rigar ajikinta duk da ta yayyage daga gabanta sai dae ta sanya hannu ta ruƙo rigar ta tattare wurin daya yagen,cikin sauri ta kama hanyar fuce wa daga ɗakin,aikuwa karaf akan idon Sgr a wani irin zafafe yayi wurgi da Marshal Omar gefe guda, da gudun gaske yabi sehrish tare da cafkota jikinshi nan take ta sake fashewa da wani irin matsanancin kuka,   Da hanzarin gaske Omar ya yunƙura ya taso yabi bayanshi tare da rurruƙe hannunshi tabaya da ƙarfin gaske,sai da yayi da gaske sannan yayi wurgi da sgr gefe guda, hakan yaba sehrish damar watsawa a guje tabar ɗakin,  Kafin Sgr ya yunƙura ya taso tuni Omar ya janyo ƙopar ɗakin ya datse ta, ya rage daga shi sai shi acikin ɗakin suna kallon kallon,   Omar bai ta6a tsorata da sgr ba sai ranar ganin yadda yake zazzare mashi ido tamkar baisan shi ba, gaba ɗaya kanshi ya gama ɗaurewa saboda yasan cewa ba Halin shi bane,shi da sam mace bata agaban shi ko kallo wannan amma kuma ace yau shi da kanshi yake ƙoƙarin yiwa Mace fyaɗe,bayan shike hukunta masu aikatawa da hannunshi,lallaikam akwai matsala,   ganin yadda yake ta faman huci yana cizon la66a yana kallonshi yasa shi saurin dakatar dashi da hannu yana cewa"Look rafayet!!! Ni nasan ba yin kanka bane,nasan ɗan uwana bazai ta6a aikata hakan ba,dan Allah ka amsa mun don na tabbatar da cewa ba yin kanka bane.......'kafin Omar yakai ƙarshen maganar tashi tuni sgr ya kai mashi kwakkwaran ruƙo duk irin nauyin marshal Omar sai da sgr ya ɗaga shi ya ɗaɗɗagoshi tare da yin wurgi dashi,aikuwa ba ƙaramin buguwa Omar yayi don gaba ɗaya yatafi ya zube gaban drawer dinsa nan take forehead dinsa ya bugu ajikinta har wurin yaɗan fashe kaɗan dafe goshin sa yayi tare da ɗagowa da idonshi ya kalli sgr cikin sanyin murya yace"Ni fa ne Omar ɗinka yau da kanka kake buguna?so kake ka kashe ni,   tamkar tunzura shi yayi maganar da yayi aikuwa gadan gadan ya tunkare shi da wannan tafiyar ta basawa,  "In fa na biye mashi wlh naƙasa ni zaiyi da alama," ya fadi acikin ranshi, cikin sauri Omar ya tashi tare da yin hanzarin afkawa cikin toilet ɗinsa ya rufe ƙopar,yayi hakan ne saboda tsoran karsu raunata junansu don inya bugeshi ba ƙyaleshi zaiyi ba ƙarfine zai haɗu da ƙarfi daganan kuma abunda zai biyo baya su dukansu bazasu ji daɗin shi ba,  Tamkar zai 6a66ake ƙopar toilet din haka yadinga bugun ƙopan saboda Omar ya buɗe mashi yashiga,su cigaba da gashi don ba ƙaramin fusata shi yayi ba so yake ya karairaya ƙasusuwan jikinshi,   "Wlh ka yi mai isarka,bazan buɗe ƙoparba," yana magana dariya tana cin shi saboda lamarin ya gama ɗaure mashi kai,   tuni jiri ya soma ɗibar sgr ja da baya baya yadinga yi yana ambaton sunan Allah nan take ya yanke jiki ya faɗa saman gadonshi abaje ya sume,  jin shiru tsit yasa Omar sanya hannu tare da buɗe ƙopar toilet ɗin yaɗan leƙo,ganin shi kwance saman gadon ya sume ba ƙaramin sanyi yaji ba aranshi,  fitowa yayi daga cikin toilet ɗin yana faman sauke ajiyar zuciya,ƙarasawa yayi inda sgr ɗin yake,hannayen shi yasanya tare da tattaro dogayen ƙafafuwanshi ya azasu saman gadon gaba ɗaya, sannan ya gyara mashi kwanciyarshi tare da janyo blanket dinsa ya lullu6e mashi jikinshi,   Addu'o'i ya tattofa mashi sannan ya kama hanyar fuce wa daga ɗakin harya kai baƙin ƙopa karaf idonshi ya sauka kan Syringe din allurar da sehrish ta zuba acikin dustbin,cikin sauri yakai hannunshi cikin dustbin ɗin tare da ɗauko kwalbar allurar yana karanta rubutun dake ajikinta,nan da nan hankalin shi yayi wani irin mugun tashi tuni kanshi ya gama ɗaurewa tunaninsa taya akai SGR yayi ma kanshi wannan allurar!!!!?  "I can't believe it!!!" ya furta yana sake jujjuya kwalbar dake hannunshi,   Tare da ita ya fito daga ɗakin yaso yaje wurin Yarinyar saboda ya rarrashe ta ya fahimtar da ita amma dare yayi sosai baisan awane hali take ciki ba yanzu,wuce wa bedroom ɗinshi kawai yayi tare da kwalbar ruƙe a hannunshi saboda yin Investigation akanta,dole ya binciki yarda akai akasamu allurar acikin gidan saboda dama sun jima suna neman haramtaccen companyn miyagun kwayoyin dake sarrafa allurorin a 6oye masu cire imanin mutun lokaci guda,
😳😳😳
 *** A 6angaren sehrish kuwa abun gwanin ban tausayi haka ta faɗa ɗakinta tana faman shan kuka,gefen gadonta tazauna domin ƙarashe kukan nata,ta jima batare da yin motsi ba,hannunta na ruƙe da rigarta sai ƙara matse wurin take yi tana kuka,duk wurin da sgr ya damƙa ajikinta ba ƙaramin raɗaɗi yake yi mata ba saboda baiyi mata ruƙon wasa ba,idanunta sun kumbura sosai saboda kukan da tasha.......'  Bakomai tafi ji ba face yarda taga Omar na bugunshi,tsoranta karya lahanta shi akan abunda take da tabbacin cewa ba yin kanshi bane,😢
Daƙer ta iya miƙewa ta wuce toilet saboda ta tsarkake jikinta,rufe ƙopar toilet ɗin tayi kusan 15 mins sai gata ta fito ɗaure da towel tana faman sauke ajiyar zuciya,har cikin ranta ba ƙaramin sanyi taji ba da Marshal Omar yazo don da baizo ba adai dai wannan lokkacin da SGR ya jima da yin raping dinta,kuma babu tabbacin cewa zata rayu saboda ba ɗigon Imani atattare dashi lokacin,
   Wardrobe ɗinta ta buɗe tare da curo wata rigar baccin ta zura ajikinta, sannan ta koma tare da hayewa saman gadon,janyo bargonta tayi tare da lullu6e jikinta dashi, rufe idanunta tayi nan take brain ɗinta,ta tariyo mata fuskar sgr lokacin da yake kallon cikin idanunta sweat dinshi na zuba a fuskarta nan take wata irin kasala ta rufe mata jikinta,sam bacci yaƙi ɗaukarta saboda daga tazo runtse idonta sai taji kamar SGR zai faɗo mata cikin ɗakin,firgita ta dinga yi duk tabi ta tsoratar da kanta duk da ta rufe ɗakin ammma ji take kamar zai biyota ne,saboda yarda taga ya buge omar ya afko mata ɗazun,tana cikin wannan halin wayarta ta buga uban ringing aikuwa a gigice ta wuntsila ta faɗo ƙasa daga saman gadon tana ƙoƙarin shigewa ƙarƙashin gadon,yadda kasan wadda sanyi ya kama,haƙoranta sai kerma sukeyi kaf!kaf!!kaf, yatsun hannunta kuwa kamar waɗanda aka sanyawa battery sai rawa sukeyi ba ƙaƙƙautawa,ta jima a haka tana faman zazzare ido, sai daga bisani ta gane cewa wayarta ce ke ringing,lalla6awa tayi tataso tana tafiya cikin sanɗa har ta ƙarasa wurin side drawer ɗinta buɗewa tayi tare da ɗaukar wayarta ta dake ringing,tamkar wayar zata sul6e daga hannunta saboda kermar da fingers din nata keyi,Sunan AMRISH ne ya bayyana akan screen din wayar,lokaci ta duba kusan ƙarfe ɗaya da rabi na dare,katsewa kiran yayi saiga message ya shigo nata,cikin sauri ta buɗe tare da karantawa kamar haka  _Hi reesh,nayi missing ɗinki sosai shiyasa na kira don na tsoratar dake saboda nasan cewa zaki firgita in kirana yashigo a wannan lokacin,May be ma kina nan kina Jan minshari ne_   Murmushi sehrish tayi sosai bayan tagama karanta,reply ta mayar mata da cewa"i missed u too my lovely friend,kinci nasara akaina saboda kin tsoratar dani sosai,gobe ba school amma zamuyi video call ne,"  Bayan ta kammala tura mata saƙon ta mayar da wayar asaman drawer din ta ajiye,safa da marwa tashiga yi acikin bedroom dinta tana tunanin taya akai Sgr yyi attempt na raping ɗinta!!!? tsayawa tayi cak lokacin da zuciyarta ta ambaci sunan HAROON,gabanta ne taji ya faɗi bakomai ta tuna ba face maganar daya yi mata nacewa"Basai kin gode mun ba Aikin ladane,nidai burina ki kaima shi ya hanzarta yi gobe da safe kinzo kiyi mun godiyar,   Dafe ƙirjinta tayi cikin tsananin tashin hankali, hannu ta aza akai muryarta na rawa tace"innalallahi wa'inna ilahirraji'un nashiga ukuna!!haroon yaja mun bala'e...tabbas shine silar komai !! Shiya bani allurar dana kaima babban yaya, wayyo Allah na...yanzu dole su tuhume ni akanta!!Haroon ya gama dani.............  A daren ranar sehrish bata runtsa ba yarda taga rana haka taga dare,tasha kuka kamar kamar me ƙarshe ma tashiga toilet tayo alwala tafito ta shimfida carpet tashiga jera salloli har sai da ƙafafunta suka soma raɗaɗi sannan ta dakata tare da ɗaga hannayenta sama tana roƙon Allah ya tsareta daga sharrin Haroon,sai wuraren asuba bayan tayi salla sannan bacci yayi awon gaba da ita a saman sallayar,💔
    Morning â¤â¤â?
Wuraren Æ™arfe takwas azmee tashiga bugun Æ™opar bedroom dinta,har cikin tsakiyar kanta tadinga jin bugun,a gigice tafarka tare da miÆ™ewa ta nufi kopar ta buÉ—e tana tambayar wanene,  Bin ta da kallo azmee tayi ganin yarda fuskarta ta kumbura suntum ga idanunta ma sun Æ™ankance saboda rashin isasshen bacci,hankali atashe tace"Lafiyarki kuwa sehrish?Anya ma kinyi bacci jiya? Fuskarki kamar ta wanda yasha kuka?   Maimakon ta bata amsa sai ta fashe da wani kukan saboda tunawa da halin da take ciki,ganin hakan yasa azmee shiga cikin É—akin tare da rufo masu Æ™ofa,.   ruÆ™o hijabin sehrish tayi taja ta suka zauna daga gefen gadonta sannan ta kalle ta anatse tace"faÉ—amun meya faru Æ™anwata?meyasa ki shiga cikin damuwa....."   cikin shessheÆ™ar kuka sehrish ta Zayyana mata dukkan abunda ya faru adaren jiya ta Æ™are da cewa"a....Aunty azmee wlh ba laifina bane Haroon ne ya bani allurar, banyi tunanin zai cutar dashi bane,yanzu ni bansan ya zanyi ba! Idan babban yaya ya tuna abunda ya faru jiya dole ya tuhume ni akan ni na kawo mashi allurar.........'kasa Æ™arasa maganar tayi saboda kukan daya zo mata,  Shiru azmee tayi kamar mai nazarin wani abun kafin daga bisani tasanya hannunta a kafaÉ—ar sehrish din tace"Just Calm down ur mind!ki share hawayenki,ynx yakamata muyi tunanin samun solution before ya tuna din, amma nayi mamakin a ina haroon ya samu allurar daya baki ashe dama kuna Æ´ar tsama dashi baki ta6a sanar mun ba!?  cikin shessheÆ™ar kuka sehrish tace"bansan me nayi mashi ba aunty azmee haroon ya tsaneni nima bana son ganinshi saboda ya jima yana Æ™untatamun bana son na tayar maki da hankaline shiyasa ban ta6a sanar dake ba......'   Jinjina kai azmee tayi kafin tace"Kinyi kuskure sehrish!!baki É—aukeni kamar yarda na É—auke ki ba,rashin gayan mun da kikeyi shine zai jefa ki cikin matsala....'rai aÉ—an 6ace azmee keyi mata magana,  "Aunty azmee kiyi hakuri nasan nayi kuskuren rashin sanar dake yanzu nagane hakan,"   ajiyar zuciya azmee ta saki kafin tace"shikenan ya wuce,naji daÉ—i sosai da yakasance Omar ne ya Æ™waceki a wannan lokacin da bansan mai zai biyo baya ba,ynz babban matsalar dole ne suyi zargin wani abu akanki,koda Omar ya tambayeki wanene ya baki allurar ki sanar mashi kawai that's the only solution!!!   girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"a'a aunty azmee bazan iya cewa haroon ne ya bani allurar ba,saboda bakowa ne zai yarda dani ba,kuma zai iya Æ™ullamun sharri ne,ina tsoran hakan,"   gyaÉ—a kai azmee tayi tare da cewa"hakane kuma kin faÉ—i gsky,abun zai iya juyewa ya dawo kanki,amma naso ki sanar dasu cewa shi ya baki allurar saboda ki samu ki tsira,amma bakomai nasan cewa Omar zai fahimce ki in kikayi mashi bayani,babban tashin hankalin shine idan shi Sgr din ya tuna abunda yafaru gsky akwai matsala!!!!   Sun jima suna tattaunawa kan yarda zasu shawo kan matsalar kafin daga bisani Azmee tace"ki kwanta ki huta don nasan jiya bakiyi bacci ba,ni bari na wuce kitchen,"  Amsa mata tayi da toh,sannan ta cire hijab É—in jikinta ta kwanta saman lallusan katifan gadon,lamo tayi a hankali brain din tadinga tariyo mata abunda ya faru adaren jiya,musamman yarda yayi mata rumfa da wide chest dinshi yana faman gurnanin nan yana kallon cikin idonta,wani irin yanayi mara misaltuwa, ba Æ™aramin shock taji ba alokacin duk da tana cikin tashin hankali hakan bai hanata jin emotion dinshi ba,   Hannu tasa tare da janyo fillow ta rungume shi sosai ajikinta saboda yanayin daya zo mata tuni taji wata irin kewarshi ta lullu6eta kamar maijin zazza6i,runtse idonta tayi nan take wannan Æ™ayataccen murmushin daya sakar mata jiya yadawo mata a idonta,cikin sauri ta buÉ—e su tana faman sauke ajiyar zuciya,ban ta6a ganin kyakkyawan murmushi ba sai adaren jiya Ya Allah ka mallaka mun shi â¤ðŸ’‹Â?  Ta furta fuskarta dauke da murmushi daga bisani wani baccin ya kuma yin awon gaba da ita, ****** fitowa Omar yayi daga bedroom dinshi jikin shi na sanye da jallabiya maroon colour,jiya da tunanin abunda ya faru tsakanin SGR da yarinyar nan ya kwana,burin shi kawai yaje yaga ya rabin ranshi ya kwana, shiga part dinsa yayi tare da wuce wa bedroom dinshi, abun mamaki samun shi yayi tsaye agaban mirror jikinshi na sanye da bathrobe ya É—aure suman kanshi ta baya,da alama fitowarshi kenan daga bathroom,  shiga ciki omar yayi tare da yi mashi gyaran murya,juyawo sgr yayi ya kalle shi tare da 6ata fuska yace"Am angry wit u omar,bana son ganinka cos i even texted u about my sick amma shine ko kazo ka ganni ko? Ya fadi tare da tsuke mashi fuska,  Tsayawa Omar yayi yana kallon shi kamar mai nazarin wani abu,yayi wani fresh dashi sam babu alamun damuwa attare dashi,   Cikin mamaki yace"Oh kana nufin ka manta abunda ya faru jiya"?  "Meya faru"!? Ya tambayana yana kallonshi aÉ—an ruÉ—e,   matsawa kusa dashi Omar yayi tare da aza hannnayenshi akan shoulders É—in Sgr yace"Wai dagaske kamanta komai?duk abunda ya faru jiya"?  girgiza mashi kai yayi tare da cewa"Omar ni fa i don't know what are u talking abt explain to me pls,  fashewa da dariya Omar yayi daker ya tsagaita yace"pls ka tuna mana ko kaÉ—anne,  Shiru sgr yayi yana bin shi da kallon bana son raini, can dae yace"Jiya ni bansan ina kaina yake ba,i Can't remember,   jinjina kai Omar yayi har lokacin fuskarshi Æ™umshe da dariya yace"kaine kayiwa kanka allura jiya?  ɗan yatsina fuska yayi kafin yace"yeah its me meya faru ne?  girgiza kai omar yayi tare da cewa"babu komai kawai inaso inji kaine ka É—auko allurar?kuma kasan wace allurace kayi ma kanka"?  ɗan shiru Sgr yayi yana kallon fuskar Omar na wani lokacin a Æ™oÆ™arinshi na ya tuna meya faru,ajiyar zuciya yasaki tare da cewa"Bani bane,wannan yarinyar ne, itace ta É—aukomin,"   ruÆ™o hannunshi Omar yayi yaja shi suka zauna daga gefen gadonshi sannan yace"da ka tashi yau da safe kana nufin kwata kwata baka ga wata alama ba ajikin ka ba"?   ɗaure mashi fuska yayi yace"Omar banason wannan tmbyar nifa ban gane me kake nufi ba,"   Hannu omar yasa yana shafa Æ™irjinshi yace"kwantar da hankalin ka mana,just tell me da wani yanayi ka tashi yau ajikin ka,  Shiru sgr yaÉ—anyi na wani lokacin kafin yace"bro i can't explain it,yanayi mara misaltuwa jiya na kwanta da ciwo, but dana tashi naji ni'ima atattare dani ga wani Æ™arfi da nake Ji not only that omar When I went to the toilet, I saw something that really confused me because I had never seen it before..................🙊
Weekend mu haÉ—u on monday insha Allah, don't forget to follow me on tiktok boss_batureâ¤ï¸ 💋Boss Bature💋
Follow this link to join my tiktok acct 👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
"What's it"? Omar ya tambaya yana kallon shi, ganin yarda Omar ke kumshe dariya yasa shi fasa yin maganar ya ɗan ɗaure face ɗinshi yace"omar banason wasa fa pls tell me the truth, Did something happen last night? Naga bed sheet dina duk yayi wani squeezing kamar anyi dambe asaman shi,   dariya sosai Omar yayi kafin yace"no ba wani abu just forget about it, na same ka ne kawai a wani yayi na ciwo so na ɗan taimaka maka ne har nasamu bacci ya ɗauke ka," ta6e baki sgr yayi yana kallon shi don bai yarda da abunda ya faɗa mashi ba, hakanan omar bazai tasa shi gaba yana mashi dariya ba just without any reason,   miƙewa Omar yayi tare da kallon shi yace"bari na sauka down ko kana buƙatar wani abu ne nasa akawo maka"?  juyawa sgr yayi ya kalli tray din da ke ajiye saman table ɗinshi yace"wannan yarinyar tazo ta tattara wannan kayan,ga bedroom dina ma inaso a gyaramun,"   "Okey zan faɗa mata, ka huta my man,"  Juyawa omar yayi zai fuce har yakai bakin door din ya waiwayo don ya kalli sgr karaf suka haɗa ido, cikin mamaki yace"Omar nifa wani kallo naga kana min irin kallon jarababben namijin nan......' ya faɗi yana tsuke mashi fuska,  Fucewa omar yayi yana ƴar dariya, yamutsa fuska sgr yayi tare da cewa"Omar nason haukata ni, bansan wannan dariyar nashi me yake nufi ba," yayi maganar tare da kwantar da bayanshi saman lallausar mattress ɗin, kwakkwaran juyi yayi asaman gadon, kai tsaye idonshi ya sauka akan siraran gashin dake zube saman bedsheet dinsa, cikin sauri ya ɗago da kanshi tare da zuba ma gashin ido, mamaki ne ya kamashi taya akai gashin kanshi ya zuba don kuwa yana da tabbacin cewa sumar kanshi bata kakka6a saboda gyaran da take sha, hannun shi yakai a hankali tare da ɗauko siraran gashin guda uku ya zuba masu ido yana kallonsu, dogon gashi ne mai tsayin gaske, sak irin launin sumar kanshi wato dark brown colour, natsuwa yayi yana nazarin gashin, kafin yasanya hannunshi tare da ɗaukar siraran gashin a hannunshi,yunƙuwa yayi tare da miƙewa daga saman gadon, ya nufi gaban dressing mirror dinshi, zama yayi asaman front chair din madubin, sannan ya ajiye siraran gashin asaman shi, hannu yasa tare da tsinko gashin kanshi siriri guda ɗaya, sannan ya ajiye shi a gefen waɗancan sauran guda ukun, within 5 mins ya gane difference ɗin dake tsakanin su,tabbas wannan ba hairs ɗinshi bane to na wanene, asaman bedsheet ɗinshi kuma? hannu yasa ya ɗauki siraran gashinan guda uku, sannan ya tashi tsaye ya nufi bedside drawer ɗinshi, buɗewa yayi tare da buɗe jotter ɗinshi dake ajiye acikinta, a shafi na farko ya saka siraran gashin sannan ya rufe jotter ɗin, tare da mayar da drwer chest din ya rufe, wuce wa yayi wurin closet ɗinshi domin shirya kanshi,
***********💋Â
bayan fitar marshal omar daga part din Sgr kaitsaye down stairs ya wuce wurin dining area dinsu ya nufa ganin aunty azmee nata faman jera masu breakfast dinsu, tunkan ya ƙaraso ta soma sakar mashi murmushi tana cewa"Omar barka da fitowa fatan ka tashi lafiya,"?   fuskarshi asake yace"lafiya lou Alhmdllh,"   shiru ya ɗanyi kafin yace"am ina wannan yarinyar take ne sehrish"? Har sai da gaban azmee ya fadi rass jin abunda yace,dama tasan saiya tambayeta akan maganar nan,   murya na rawa tace"bata jin daɗi ne tana a bedroom ɗinta,ni nace mata ta kwanta ta huta shiyasa bata fitowa. Ba.......'  "Ta sanar dake game da abunda ya faru jiya"? Ya katse ta da tambaya,   "Eh ta sanar dani komai," ta fadi adabarbace,   Omar yace"okey ina son magana da ita, ki ce tazo tasame ni a part ɗina ina jiranta,"  Cikin sauri ta amsa mashi da toh, sannan ta bar jera abincin da take yi ta wuce ɗakin sehrish,   A hankali ta tura ƙofar tashiga da sallama, kwance ta same ta sai faman sharar bacci take yi, har lokacin jikinta bai daina yin kerma ba,   matsawa tayi dab da ita tare da sanya hannu ta ɗan bubbugi kafadarta "Sehrish !!sehrish!!  Har cikin dodon kunnanta taji kiran a firgice tafarka tare da miƙewa tsaye tana cewa"La'ila ha'ilallah.........' rufe mata baki azmee tayi tare da cewa"ki natsu ni ce" a hankali tashiga sauke ajiyar zuciya tana kallon azmeen da idanunta da suka canza launi saboda bacci,  Janye hannu azmee tayi daga bakinta sannan tace"Omar ne ke son magana dake yace ki same shi a part ɗinshi yanzu,"   zare ido sehrish tayi murya na rawa tace"Aunty azmee ni kuma.....na shiga uku....me zai tambaye ni......'. Katse ta azmee tayi tare da cewa"kada ki damu nasan game da allurar nan ne zai tambaye ki, kawai ki fada mashi gaskiya a wuce wurin,"   fuskarta tamkar za tayi kuka tace"Aunty azmee ina tsoro fa kada naja ma kaina,"   girgiza kai azmee tayi tare da cewa"ba wani tsoro omar zai fahimce ki, kina 6ata lokaci fa ki tashi ki tafi,  Tana kai ƙarshen maganar ta juya ta fuce daga ɗakin, jiki asanyaye sehrish ta sauko daga saman gadon, hannu tasa ta ɗauki hijab ɗinta wadda ta ajiye asaman gadon milk colour ta zura ajikinta,  Buɗe ƙopar ɗakin tayi ta fito tare da miƙar hanya ta wuce part dinsa, tsayawa tayi daga ƙopar shiga tana ƙoƙarin dai daita natsuwarta,sallama tayi mashi amma shiru ba'a amsa ba, ƙafa tasa tashiga daga ciki,babu kowa a falonsa komai anatse yake sai ƙamshi dake tashi,   Shiga ciki tayi tare da samun wuri ta tsaya a kusa da royal sofa din dake a kewaye, gabanta sai faɗuwa yake yi kamar mara gaskiya,
  "Ya Allah ka bani ikon amsa tambayar da zaiyi mun,bana son nashiga matsala da kowa acikin gidan nan, nasan zasu iya zargina wayyo Allah na," ta furta tana faman yarfa hannunta, cike take da zullumin me zai biyo baya,
 tana cikin wannan tsayuwar wayar shi ta shiga ringing a firgice taÉ—an ja da baya saboda bata tsammaci jin sautin wani abu ba, bin wayar tayi da kallo tana ajiye asaman 3 seater din don anan yabarta,   katsewa kiran yayi sai ga wani ya kuma shigowa, matsawa tayi a hankali saitin kujerar tana kallon wayar, ranta ne yabata ta É—aga kiran taji wanene wata'kil kiran gaggawa ne,   Tamkar ana tunzurata haka taji, hannu takai tare da É—aukar wayar tayi picking call din tare da karawa a kunannta, tun kafin tayi sallama taji ance"Ya Omar shi ne jiya kace in ka koma zaka kira ni awaya amma naji shiru ko? Muryar hossana ce ke magana,  Shiru sehrish tayi tana sauraron maganarta,.   Acan kuwa jin tsit Omar É—in yayi mata shiru yasa ta cewa"kana ji na kayi mun shiru ko, Allah idan bakayi magana ba yau ko breakfast bazanyi ba....' ashagwa6e tayi maganar,   murmushi sehrish tayi jin yarda yarinyar ke magana, sai a lokacin tace"bashi bane, baya kusa ne,"Â
ï¿?
 Jin muryar mace yasa hankali hossana tashi ruƙe qugu tayi dama tana atsaye jikinta nasanye da kayan bacci riga da wando red colour, ta ƙara kara telephone din a kunnanta, tace  "ƙanwarshi ko budurwarshi ko matarshi wacece ke aciki ? ta tambaya a ƙule,   "Matar shi ce," sehrish ta faɗi cike da zolaya, aikuwa nan take hankalin hossana ya tashi, muryarta tamkar zatayi kuka tashiga kwalama jahad kira tana cewa"Jahad!!Jahad!! ashe dama ya omar yana da aure shine bai fadamana ba,   Yadda hossana ke kwala mata kira yasa ta fitowa daga kitchen cikin sauri ta nufe ta tana cewa"Hossana lafiya meya faru ne kike kwalamun kira? Ke da waye a waya? Ta tambaya a yayin da take ƙarasawa wurinta,  duk sehrish ta kasa kunne tana jinsu, Cikin shessheƙar kuka hossana tace"Ashe dama ya omar na da aure bai fadamun ba,"  Cike da mamaki jahad tace"kai haba wai dagaske?  "Eh mana gatanan muna magana awaya," ta faɗi rai a6ace tana miƙa ma jahad telephone ɗin,,  Hannu jahad tasanya ta kar6i wayar sannan anatse tace"Assalamu Alaikum," fuska dauke da murmushi sehrish tace"Wa'alaikum salam,"  Jahad tace"ina kwana aunty,"  "Lafiya lou," sehrish ta amsa,  Jahad ta kuma cewa"dagaske ne kece matar yaya Omar"? ta tambaya tamkar tana a gabanta, Sehrish tace "eh nice,"  jinjina kai jahad tayi tare da ɗan ta6e baki tace"Amma bai ta6a sanar mana ba, dan Allah sabon aure ne ko tsoho "  Ƙiriss ya rage sehrish ta fashe da dariya daƙyar ta basar da ita tare da cewa"tsoho ne, mun jima atare ynx haka ma ina ɗauke da juna biyu ina fata zaku zo suna in na haihuwa,"   Jiki asanyaye jahad tace"insha Allah idan ya barmu zamu zo, amma aunty baki faɗa mana sunanki ba"?   Ƙara kashe murya sehrish tayi tare da cewa"sunana Zainab amma mijina yana kira na da Hayaty,"
KARANTA ZAFAFA 2022
✓Gurbin Ido... Na Huguma (Zafafa2022) ✓Inaya By Mamuhgee (Zafafa2022) ✓Sanadin Labarina By Hafsat Rano (Zafafa2022) ✓Babu So... By Billyn Abdul (Zafafa2022) ✓Farhatal Qalb By Mss Xoxo (Zafafa 2022)
 Jinjina kai jahad tayi tare da kallon hossana wadda ke tsaye cikin ƙunar rai,  Sun jima suna waya da sehrish kafin suyi sallama, mayar da wayar sehrish tayi ta ajiye saman seater ɗin, sannan ta koma tana faman tiƙar dariya,
  ɗagowa jahad tayi ta kalli hossana gaba ɗayansu jikin su yayi mugun sanyi, duk basu ji daɗin cewa ya omar yana da mata ba, sam hossana ta gaza jurewa komawa tayi saman 2 seater ta faɗa tare da kifa kanta tana kuka, jahad kuwa kitchen ta wuce saboda tabaro dankalin da take soya masu, ita kanta jurewa kawai take yi amma ba ƙaramin ɗaci taji ba na jin cewa ya Omar dinsu yana da aure, tsayawa tayi agaban fan din dake asaman gass sam ta kasa juya dankalin saboda tashin hankali, cikin sanyin murya tace"koma wacece matar shi ina tayata murna sosai, domin kuwa tayi dacen miji nagari........' kwalla ce ta zubo daga idonta ɗas ta zuba ƙasa, 😖
ï¿?
  Shigowa omar yayi cikin falon nashi, sehrish na ganin shi nan da nan ta shiga natsuwarta,  "Ina kwana ya omar"?  kallonta yayi tare da sakar mata murmushi yace"lfy lou Alhmdllh, ki zauna mana," ya faɗi tare da samun wuri ya zauna asaman 3 seater, wuri tasamu itama ta zauna suna fuskantar juna,   sunnar dakai tayi ƙasa tana jiran jin mai zai ce mata,  Cikin natsuwa ya soma magana "Am really sorry abt wht happend last night, banji daɗin abunda sgr yayi maki ba, nasan abun zai tsaya maki aranki,amma inaso ki sani ba yin kanshi bane! wannan allurar ce da kika kai mashi ya sanar dani cewa ke kika kai mashi ita...........' hankali tashe sehrish take kallon shi a tunaninta sgr ya tuna abunda ya faru ne,  Cigaba da magana omar yayi anatse yace"Calm down ur mind, sgr ba zai iya tuna abunda ya faru ba a yanzu amma fa dole ya tuna wata rana abun zai dawo mashi ne akan shi, so nake ki fadamun a ina kika samu allurar da kika kai mashi ? Da sanin ki kika kai mashi ita? Ya tambaya yana kallon fuskarta cike da tuhuma ,  Lokaci guda duk ta dabarbarce ta rasa natsuwarta,   " Tell me the truth who brought it to u? don nasan ba ke kika dauko ta ba, in fact bamu da irinta acikin gidan nan...'   shiru tayi tana kallon shi zuciyarta na raya mata ta fada mashi gaskiya kawai,   murya na rawa tace"Ya omar ni ba da sani na ba Allah, babban yaya yayi mun rubutu a paper ya bani, ko a lokacin sai da nace mashi ni bansan meya rubuta ajiki ba, amma yace mun naje na ɗauko mashi kawai saboda baya cikin hayyacin shi ne, lokacin dana fito da takardar a hannuna ina zullumin meya rubuta ajiki shine kawai sai ga h.....h.....' wani irin ruƙo taji anyima maƙoshinta tamkar wani abu ya tokare wurin,nan take taji numfashinta na shirin ɗaukewa gaba ɗaya, kakari tashiga yi tana ƙoƙarin furta sunan haroon amma sound ɗin ya ƙi fidduwa daga bakinta, abun mamaki abun al'ajabi,  Ganin yarda zufa ke tsattsafo mata gefe da gefen fuskarta gashi sai faman numfarfashi take yi sama sama,  Hakan ba ƙaramin tayar mashi da hankali yayi ba cikin sauri yace"Ke lafiya meke faruwa ne? Ko baki da lafiya ne?   cikin kuka tace"maƙoshina ne ke mun ciwo, nagaza furta sunan wanda yaban allurar raɗaɗi nake ji a wurin,   tashi marshal omar yayi tare da ƙarasawa wurin frigde din dake a falon shi, buɗe wa yayi tare da ɗauko bottle water mai sanyi, sannan ya dawo ya zauna dab da sehrish ya buɗe murfin robar ya miƙa mata, cikin sauri ta kar6a tana sha sai da tashanye kusan rabi sannan ta janye tana faman sauke ajiyar zuciya,  Hannu omar yasaka tare da kar6a robar daga hannunta yasanya murfin ya rufe sannan ya ajiye robar ruwan a ƙasa, mayar da idonshi yayi akan sehrish sannan cikin natsuwa yace"pls taimako nake so kiyi mana,bansan wacece ke ba amma har a raina naji, na yarda dake dan Allah karki sa na fara zarginki, ki fadamun gaskiya wanene ya baki allurar da kika kai mashi? allura ce mai haɗarin gaske a lokacin da Allah baisa na faɗo na ceceki a hannun shi ba tabbas ba zaki rayu ba....   Hankali atashe sehrish ta ɗago idanunta tana kallon shi, nan da nan taji wasu hawayen sun sake wanko mata fuskarta cikin shessheƙar kuka tace"ya omar wlh ni bansan komai akai ba bazan iya cutar dashi ba kuma nima bazan so na cutar da kaina ba..........'   jinjina kanshi yayi tare da cewa"to ki fadamun wanene ya baki allurar"?  buɗe baki tayi zata furta haroon nan take ta sake ji an damƙi maƙoshinta saboda zafin da taji kawai saita fashe mashi da kuka saboda ta rasa yarda zata yi ta sanar mashi........'  Zuba mata ido yayi yana kallonta tana ta faman shan kuka, tuni yaji tsananin tausayinta ya kamashi,musamman daya dinga ganin fuskarta kamar su jahad ne ke kuka,   Cikin sauri ya dakatar da ita da cewa"its okey, kiyi hakuri banyi hakan dan na 6ata maki rai ba, inaso kawai na gano wanda ya baki allurar ne don inyi investigation akan shi, amma tunda bakison faɗi, zaki iya tafiya,   tsagaitawa tayi da kukan tana kallon shi cikin sanyin murya tace"dan Allah kada ka zargeni wlh bazan iya cutar da wani acikin gidan nan ba, saboda na ɗauke ku tamkar ƴan uwana na jini na.......'    murmushi Omar ya ɗanyi kafin yace"don't worry ur self nima kamar yarda kika ɗauke mu haka muka ɗauke ki, ki kwantar da hankalin ki komai ya wuce insha Allah,amma aduk lokacin da kika tuna sunan wanda ya baki ita, ki hanzarta sanar mun pls......'   "Insha Allah zanyi hakan," tashi tayi tare da yi mashi sallama ta nufi hanyar fita daga falo dinsa, a hankali take tafiya hannunta dafe da saitin zuciyarta, muryar shi ce, ta sake katse ta da cewa"yana buƙatar a gyara mashi bedroom ɗinsa yakamata ki je, a firgice ta juyo tana kallon shi, ganin yarda ta razana ne yasa shi cewa"ki kwantar da hankalin ki, kada abunda ya faru jiya yasa ki dinga jin tsoranshi, nasan ko wanene ɗan uwana, am really proud of him, ki saki jikin ki in ba haka ba zai gane cewa wani abu ya faru adaren jiya,   jinjina mashi kai tayi tare da cewa"toh zanyi yarda kace," tana fadin hakan tasa kai ta fuce,   Murmushi Omar yayi saboda tunawa da babban aikin da sgr yaso yayi jiya, tabbas da yarinyar ta rasa ranta don ayadda yake jin wannan ƙarfin ba ƙaramin illatata zaiyi ba,   "godiya ta tabbata ga Allah subhanahu wata'ala da yabani ikon zuwa adai dai wannan lokacin har na ceci rayuwarta, na kuma taimaki ɗan uwana daga aikata wannan aika aikan," ya furta yana faman sauke ajiyar zuciya,
*************💋
Gaba ɗaya sun hallara a saman dining chairs suna yin breakfast dinsu, Abban su tare da junaid, sai Ayaan da jahan ga kuma su irfan khaleed da jabeer da kuma Fawan, har yanzu bai fara sanya riga a jikinshi ba sai dae gajeran wando kawai yake zurawa yayi ta yawon shi,  "Aunty azmee ina reesh take ne, banganta ba"? Junaid ya tambaya yana kallon azmee dake tsaye tana saving dinsu,   Abbansu ma yace"tun ɗazu nake so in tambaye ta nima, yau banga daughter ɗita ba ina tashiga ne?  Murmushi azmee tayi tare da cewa"tashiga sashen Omar ne,"  cike da mamaki jabeer yace"wacece kuma sehrish? ko dai wannan yarinyar dana gani tana yawo acikin gidan nan? Ya tambaya yana kallonsu,  irfan yace"nima ina taso na tambaya wlh, naga kyakkyawar yarinya tana ta yawo acikin gidan nan gwanin burgewa,"  da buɗar bakin fawan sai cewa yayi "Oh wai dama mutun ce? Ae ni nayi tunanin ko idona ne ke ganemun ita shiyasa ban ta6a tambaya ba," dariya suka fashe da ita gaba ɗayansu banda shi fawan din da yayi mgnr, saboda shi bada wasa yayi maganarshi ba, duk a tunanin shi ko ya samu ta6uwa ne shiyasa yake ganinta,    "Sunanta Sherish tare da azmee suke aiki, amma na mayar da ita ƙanwarku ina fata zaku ji daɗin hakan, tunda dama baku da ƙanwa mace," acewar abbansu,   kallon juna su kayi atare kafin fawan ya kuma cewa"ni duk ba wannan ba, wai ina tukur mai aikin mu ne? Nayi kewar shi sosai tunda muka dawo banga gifcin shi ba acikin gidan nan,"? ya tambaya yana kallon junaid dasu twins,  murmushi suka shiga saki gaba ɗayansu batare da sunce komai ba,   Khaleed yace"wannan sullu6iyon mai aikin namu, dama nasan bazai kai labari ba halan an kore shi daga aikine"?   Junaid ne yace"kai yaya fawan yanzu kuna nufin baku gane wanene tukur ba? Wannan yarinyar fa itace fa tayi shigar maza tana mana aiki........'  Saboda tsabar ruɗu har suna haɗa baki wurin cewa"Are u serious!? ɗaga kai yayi tare da jaddada masu maganar shi yace"of course ku tambayi abba kuji,"   Kallon abban nasu sukayi suna jiran jin bayani murmushi yayi tare da cewa"itace mai aikin da kuka bari a matsayin namiji,"   cikin mamaki suke kallon shi sam sun gaza cewa komai saboda abun yafi ƙarfinsu wai tukur mai aikinsu ne ya koma mace ? dama maca ce tayi shigar namiji kenan? Murmushi fawan yayi aranshi yace "lallaikam nama har gida," kamar abbansu yaji mai yace sai ɗagowa yayi ya kalli fuskokinsu yace"ko da gigin wasa bana son wani ya ta6a mun ɗiyata,ko kallon banza wannan ban amince wani yayi mata ba,"   har suna haɗa baki wurin cewa"Insha Allah hakan ma bazata faru ba, ae ƙanwarmu ce," dariya junaid yayi ƙasa ƙasa saboda yasan halinsu sarai musamman fawan,
 Sehrish~  Koda ta fito daga part ɗin omar, wuri ta samu anan upstairs ɗin ta zuƙunnna tana shan kuka ba don komai ba sai don baƙin cikin kasa furta sunan haroon da tayi, taso ta sanar ma Omar kodan ta fita zargi amma hakan yaci turo saboda maƙoshinta da taji an shaƙe mata shi, babban abunda take fargaba shine kada su fara zarginta akan abunda ba laifinta bane, yanzu kuma duk ranar da sgr ya tuna da wannan abun daya faru a tsakaninsu dole ya tuhume ta, batasan wane irin kallo zaiyi mata ba,😖  "Ashe so yayi ya kashe ni !" ta furta cikin sanyin murya, "ni bansan me nayi mashi ba, ya Allah ka kare ni daga sharrin shi, ya Allah kada ka bashi nasara akaina,"  tana cikin wannan tunanin sam bata ji takon tafiyarshi ba, fitowarshi kenan daga part dinsa ya kimtsa cikin suits farare ba ƙaramin kyau suka yi mashi ba,  tsayawa yayi yana kallon ikon Allah yarinyar da yake ta faman jira ta gyara mashi bedroom dinshi itace zuƙunne tana shessheƙar kuka, cike da mamaki ya ƙarasa har inda sehrish take sam bata zaci ganin shi ba, sai dae taga ƙafafunshi masu sanye da haɗaɗɗun takalma, gabanta ne taji yayi wani irin bugu duk da bata san wanene ba amma tana da tabbacin cewa shi neeee saboda ƙamshin turaren nan nashi,   ƙara ƙanƙame jikinta tayi tana faman zazzare ido a tsorace, muryarshi ce ta ratsa kunnanta da cewa"ke tashi tsaye,"  cikin sauri sehrish ta miƙe tsaye jikinta na kerma kamar wadda taga wani horror sam taƙi yarda ta kalli fuskarshi saboda ta tsorata dashi,   shiru ya ɗanyi baice komai ba tamkar mai nazarin wani abu, hannunta yabi da kallo sai faman kerma yatsun hannun suke yi,  "Are u okey"? ya tambayeta,cikin sauri tace"eh"   "Okey agyaramin bedroom ɗina," yana faɗin hakan ya kama hanya ya wuce,  Sam takasa janye idanunta daga kallon bayanshi har sai da ya 6ace ma ganinta, sannan ta wuce part din nashi, lokacin data shiga bedroom dinshi ba komai ta tuna ba face abunda ya faru atsakaninsu daren jiya, bin shimfiɗeɗen gadon shi tayi da kallo har yanzu zanin gadon a cukuikuye yake, saboda damben da suka sha jiya, hannu takai tare da yaye bedsheets ɗin nashi ta rungumo shi a kirjinta tana shinshina ƙamshin turarensa, ita kaɗae tasan irin yanayin da tashiga a wannan lokacin duk da firgicin da take ci amma hakan bai hanata jin wannan yanayin ba.............💋😉
*💋Boss💖Batureâ?*âœï¸
A galabaice take hura wutar murhun wani irin uban hayaƙi yake fitowa baƙiƙƙirin duk ya cika kitchen din, idanunta sunyi jawur kamar na mai shan taba, matashiyar yarinyace da bazata wuce shekara goma sha huɗu ba aduniya, a wani matsakaicin gida na masu rufin asiri, jikinta na sanye da koɗaɗɗen zani na atampha tayi ɗaurin gaba dashi, duk ya yayyage jikinshi yayi baƙiƙƙirin saboda dauɗa, gaba ɗaya ita kanta yarinyar abun ban tausayi ce, ta bushe ta rame ta ƙanjame yadda kasan skelaton haka take, saboda kasusuwan wuyanta da suka firfito mata waje kamar zasu fito daga fatar jikinta saboda tsabar rama, saboda koɗewar da fatar jikinta tayi baza ma a iya tantace launin fatarta ba, fara ce ko baƙa 😢
sai faman goho take yi agaban murfin tana hura wutar da bakinta amma wutar taƙi kama wa, zuƙunnawa tayi gaban murhun ta zabga uban tagumi hawaye na faman kwararowa daga idanunta, cikin murya kuka ta soma cewa"Ya Allah ka kawomin karshen wahalar da nake sha acikin gidan nan........'   Muryar mammynsu ce ta katse ta da cewa"AMAL!! wai uban wa kike so yayi wankin nan ne? zaki fito kiyi shi ko saina maki dukan tsiya ne? Hankali atashe tace"mammy iccen girkin ne ɗanye baya ci, tun ɗazu nake faman wahalar hura shi amma yaƙi ruruwa,"  Uban tsoki matar ta buga tare da cewa"wannan ba damuwa ta bace ba, ki tabbatar da kin hura wutar ta kama,sannan ki fito ki wanke mana kayan mu, bayan kin gama kuma ki share gidan,"   cikin ƙunar rai ta amsa mata da "toh," Sannan taci gaba da hura wutar don ta kama,   cigaba da magana matar tayi tana cewa"Yayarki nacen gidan huta, ta manta dake gaki nan a wulaƙance kin zama tamkar baiwa a wurin mu, da ace tana sonki ae bazata barki a hannun mu ba,"   Shiru Amal tayi hawaye na zuba daga idonta, har yau tagaza yarda cewa yayarta zata iya yi mata hakan, saboda me zata tafi tabarta hannun waɗannan mugayen? Ta tambayi kanta,   muryar mammyn tasu ce ta sake katse ta da cewa"hmmm dama tsiyar talaka kenan anyi mata hanyar arziƙi amma ta manta da mutane, baƙin halinku iri ɗaya dana uwarku, ae duk laifin laila ne ko uban waya faɗa mata ana yiwa ƴa'ƴan kishiya abun arziƙi," tana zaune saman gujera ƴar tsugunno sai faman sambatu takeyi kamar zautacciya, wata tsamurarriyar mata ce fara siririya ta fara tsufa don gashin kanta harya fara hurhura, jikinta na sanye da atampa riga da zane, ta tsoge ɗaurin ɗankwalin nan ture kaga tsire, hannunta na ruƙe da aswaki sae faman kwalkwalar haƙoranta takeyi wadanda sukayi jawur saboda tsabar cin goro, kai kana ganin ta zaka shaida cewa ba ƙaramar jarababbiya bace, irin tsaffin nan da basa gajiya da mita,   daƙer Amal tasamu wutar ta huru, sannan ta fito agalabaice, kai tsaye ta wuce inda uban kayan wankin suke dila guda,gaba ɗaya kayan sawarsu ne su duka dana uwar dana su abra da hayam, ga zannuwan gado da barguna duk sun tara mata su don ta wanke, abun babu imani acikin shi, babu irin wahalar rayuwar da yarinyar bata shaba,uƙuba iri iri suke yi mata, ko bacci bata samu, in ma tayi baccin da duka suke tashinta, ko kuma taji saukar ruwa bokiti guda ajikinta, fatar jikinta duk cizon sauro ne gashinan ruɗu ruɗu, saboda awaje take kwana, su kuma su shige ɗaki sai ita kaɗai ga tsora da Allah yayi mata, kullum cikin zullumin mai zai faru da ita take yi, duk yarda taso su haɗu da yayarta abun yaci tura, a halin da ake ciki ita kanta Amani batasan cewa yarinyar na raye ba, tun wani zuwa da tayi suka sanar da ita cewa yarinyar ta 6ace an neme ta an rasa, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, a lokacin tasha kuka sosai wurin neman yarinyar amma babu ita babu alamarta, tun tana sanyawa a nemo mata ita har tagaji ta daina saboda kullum babu labarin anga yarinyar shiyasa ta fidda rai da ita, ashe lokacin 6oye yarinyar sukayi a gidan makwabtansu acikin wani ɗaki aka rufe ta kamar akuya, duk in amani zataso maiduguri sai su kaita can gidan ajiya har tazo ta tafi bazata sani ba, hakan yasa basu ta6a haɗuwa da ita ba tun auranta da Abbas na wata takwas a lokacin abun ya faru, taso ta ɗauki yarinyar ta zauna a wurinta amma saboda baƙin hali irin nasu sun hanata ganin ƴar uwarta....😠  "Maza ki hanzarta ki wanke mana kayan," muryar mammynce ta katse ta,   Hannu tasa ta ɗauki bokitin dake ajiye awurin kayan, sannan ta wuce izuwa inda fanfonsu yake,ruwa ta tarbo acikin shi sannn ta ɗauke shi tadawo ta ajiye, ledar klin ta dauka tare da fasawa ta zazzaga aciki sannan tashiga tsoma kayan aciki tana wankewa idonta na zubar da kwalla,    suna cikin wannan zaman suka ji ƙarar dirar mota a ƙofar gidan, washe baki mammy tashiga yi tana cewa"ƴar albarka ta iso, nasan tadawo mana da abun arziƙi, ni dae naji daɗi ƴa'ƴana badae farin jini ba........' bata ƙarasa maganar ba Hayaam tashigo cikin gidan ba ƙaramin wanka ta ɗauka ba, jikinta na sanye da swiss lace ash colour, doguwar riga akayi mata dashi, ta matse ta tsam tamkar in tayi motsi rigar zata yage saboda yarda tayi tighting ɗinta, ta kashe ɗaurin kallabi nan, mayafin kuma ta aza shi a kafaɗa,   fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙarasa wurin mammyn tasu, tashi tayi ta rungumeta tana cewa"ƴar albarka sai yau zan saki a idona"?  Murmushi hayamm tasaki tare da cewa"Ammi yau ɗin ma sa'a kika ci, ki gode ma Allah da kika ganni yau, domin kuwa gobe zan wuce abuja nazo ne nayi maki bankwana saboda zan koma can da zama ina fata Aunty laila ta sanar dake game da komawa ta can? Ta tambaya tana kallonta,   gaba ɗaya Amal ta kasa kunne tana sauraronsu,   Washe baki tayi tare da cewa"ta sanar dani mana, ae ba ƙaramin daɗi naji ba kwara ki tattara ki tafican kema ki shafo mana arziƙi,"   Fari da ido hayaam tayi tare da cewa"baki da damuwa in dae nice mommy, arziƙi mun gama yin shi, muddin burina ya cika tuni zan canza maku tamfatsetsen gida na kece raini, na siya maku manyan motoci na alfarma sannan na biya maki aikin hajji, mommy kuɗi fa har sai kin gaji dasu wlh," ta faɗi tana faman sakin murmushi,   Cike da farin ciki mammy tace"Allah?  "wlh kuwa mommy," hayamm ta bata amsa,   ganin amal na kallonsu yasa mammyn kwatsa mata tsawa tace"zaki mayar da hankalin ki kan kayan da kike wankewa ko saina zo nan na karya maki wuya, magulmaciyar banza ƴar sa ido," jiki na rawa amal ta mayar da hankalinta kan kayan da take wanke wa,    ruƙo hannun hayamm mammyn tayi sannan tajata suka shige cikin ɗakinsu, don kar taji me zasu ce,   a hankali take wanke kayan tunani iri iri na zuwa mata aranta, tana yawan jin suna ambaton abuja abuja, kodai can aunty amani take zaune ne? Ta tambayi kanta, jinjina kai tayi tare da cewa"ina da tabbacin cewa auntyna tana zaune acan itama, dole na nemi mafita bazan zauna su kashe ni ba, zan gudu ne batare da saninsu ba," ta fadi tare da tsame rigar da ta sanya acikin ruwan wankin..........'😳
 **************** A 6angaren su hossana kuwa saboda damuwar da suka shiga na jin cewa ya Omar ɗinsu na da aure gaba ɗayansu ba wanda yayi breakfast saboda damuwa, su kansu sun rasa gane dalilin dayasa suke jin kishin matar shi data kirasu a waya, abincin da jahad ta shirya masu har yayi sanyi saboda tun safe yake ajiye saman dining table babu wanda ya ta6a shi, gashi har ƙarfe ɗaya yanzu yayi na rana,   A tare suke kabbara sallah bayan sun kammala suka zauna suna addu'o'i, shiru jahad tayi tana sauraron addu'ar hossana da take yi,   "Ya Allah kasa mafarki ne ba gaske ba na cewa ya Omar yana da mata, in ma dagaske ne ya Allah kasa ya sake ta su rabu, zuciya ta tafarfasa takeyi mun bazan iya jurewa ba........'   katse ta Jahad tayi da cewa"hossana kina a hayyacinki kuwa? ya sake ta fa kika ce? Idan yana son matar shi fa?  harara hossana ta jefa mata tare da cewa"waya faɗa maki yana sonta? Auren dole ne akayi masu, da ace yana sonta ae da bai 6oye mana cewa yana da mata ba har da ciki...'    Itama jahad ɗin harar ta mayar mata tare da cewa"baki da hankali wlh,dagaske ɗin ke zararriya ce, yaya omar yana son matarshi, ke bakiji muryarta ba yarda take magana daga gani tana cikin kwanciyar hankali, kuma tana samun soyayyar mijinta tunda gashi har tana da ciki zata haifa mashi baby..........' jahad bata ƙarasa maganar ba, hossana takai ma wuyan hijabinta cakuma tana cewa"Ni ce zararriya? ɗaga kai jahad tayi alamar e,   Bugu hossana tashiga kai mata, ganin bazata iya jurewa ba yasa suka kacame da faɗa, abu kamar wasa sai da dukkansu suka sha kuka, dama ransu a6ace yake, duk don saboda matar Omar,   (Sehrish tayi tsiya)
tsaf ta kammala gyara mashi bedroom dinshi da toilet dinshi da falonsa duka ko'ina a kimtse tabar mashi shi, fitowa tayi ta sauko down stairs a lokacin duk sun kammala yin breakfast É—in nasu babu kowa a falon, kai tsaye ta wuce bedroom É—in Haroon gabanta na faduwa rass rass, Æ™opar a rufe take don haka saita sanya hannu tare da yin knocking É—inta, daga cikin É—akin tajiyo muryarshi yana cewa"Wanene"?   "Ni ce," ta bashi amsa cike da Æ™arfin guiwa,   buÉ—e mata Æ™opar yayi fuskar nan É—auke da murmushi, jikinshi na sanye da singlet fara tare da shorts baÆ™i,  "shigo daga ciki mana," ya faÉ—i yana nuna mata hanya, kallon shi kawai takeyi , sa kai tayi ta shiga ciki daga tsaye ta tsaya tana kallon shi, rufe Æ™opar yayi sannan ya juyo ya kalle ta yace "wlh har naji sanyi araina dana ganki cikin Æ™oshin lafiya,ae nayi tunanin e warhaka kina asibitin kwance magashiyyan rai hannun Allah.....' bai Æ™arasa maganar tashi ba tace"me nayi maka? Meyasa kake son kashe ni? saboda me ka bani wannan allurar?   tafi yayi da hannunshi yana dariya, wuce ta yayi tare da samun wuri daga gefen gadonshi ya zauna yana facing É—inta yace"Ko da ace zan iya kashe kowa a duniyar nan, ni bazan iya kashe abunda raina ke so ba!!! nasan cewa ba zaki mutu ba, akwai wanda zaizo ya taimake ki shiyasa nayi hakan ! kinfiye taurin kai shiyasa na gwada maki kaÉ—an daga cikin shaiÉ—ancina, kin manta maganar da kika faÉ—a mun nacewa NAMIJI kike kallo? Shiyasa na haÉ—aki da namijin...........' Æ™arasa maganar yayi yana faman tiÆ™ar dariya, sakin baki sehrish tayi tana kallon shi. Da Æ™yar ya tsagaita da maganar tashi yana kashe mata ido yace"Yarinya taji maza,baki ban labari ba ya kuka Æ™are jiya?   shiru tayi tana kallon shi kawai saboda abun yafi Æ™arfinta haroon ba Æ™aramin shaiÉ—ani bane,   ta6e bakin shi yayi yana kallonta sannan yaci gaba da cewa"wannan allurar da na baki, miyagu irina suke amfani da ita, aduk lokacin da mutun yayiwa kanshi allurar nan, imanin shi gaba É—aya take cire wa, zai iya yi ma mata sama da goma sha biyar raping a lokaci guda batare da ya gaji ba tamkar engine zai dinga aiki, sannan koda ace mahaifiyarshi ce akusa dashi itama hakan ce zata faru da ita ba zai iya tantance fari ba balle baÆ™i, saboda gaba É—aya take tayarwa mutun da wata irin jarababbiyar shawa'a da kuma Æ™arfi na ban mamaki, kuma muddin a lokacin bai samu ya kawar da sha'awarnan ba, to fa zuciyarshi zata iya bugawa nan take,.......'  tunda ya soma bayani sehrish ke kallon shi cikin tsananin tashin hankali har sai da yakai Æ™arshe sannan cikin sanyin murya tace"me yasa ka fita daban acikinsu ne? Saboda me kake son cutar da shi ne? idan ni nayi maka laifi saboda me laifin zai shafe shi?    shu'umin murmushi haroon ya saki kafin yace"tun ina yaro nake da son yin mugunta, ni ko dariya ban cika yi ba sai in anyi abun mugunta sannan take zuwa mun, burina kawai naga kowa cikin masifa da tashin hankali,natsani inga ana ta rayuwar farin ciki mai É—aurewa, wannan ne dalilin dayasa nakeson in kawo canji acikin gidan nan,". Hankali kwance haroon ke kora mata bayani batare da nuna alamun wasa ba,   tuni taji idonta sun ciko da kwalla cike da takaici tace "tausayinka nake ji ! kana bani tausayi saboda kai abun tausayi ne, ban ta6a tunanin cewa a jinin abba za'a samu mai irin waÉ—annan mugayen É—abi'un da halayen irin naka ba, saboda me yasa kai ba zaka yi koyi da sauran ba? ka zama mutumin kirki tamkar sauran"?   tasowa haroon yayi daga zaunen da yake ya Æ™arasa dab da inda take a wannan karan fuskarshi babu wasa acikinta yace"kina so in shiryu ne? In zama mutumin kirki?   ɗaga mashi kai tayi alamar eh,  Murmushi haroon yayi kafin yace"kece mutun ta biyu, da kikayi mun fatan shiriya arayuwata, sai dae kash hakan bazai ta6a yiyuwa ba sehrish ni ba cikakken mutun bane kamar yarda kike tunanin....................' a wani irin firgice sehrish ta É—ago tana kallon cikin idanunshi fuskarta cike da tsoro tace"kana nufin kai ba mutun bane"?   dariya ya É—anyi kafin yace"kona faÉ—a maki ba zaki yarda ba, amma bari na sanar dake wani abu da baki sani ba, ni da kaina na turo marshal Omar É—akin sgr domin ya taimake ki ! kuma ni ne nan na hana ki furta sunana agaban Omar, na shaÆ™e maki maÆ™oshinki na hana sautin fita daga bakin ki, shin bakiyi mamakin taya akai duk nasan da wannan ba !!!!!!!!!!!   Zazzare ido sehrish tayi gabanta na faÉ—uwa, tuni zufa ta soma tsattsafo mata, ja da baya da baya tadinga yi tana kallon shi.....  dariya sosai haroon yayi kafin yace"Shiyasa nace ki nemi tsari daga sharrina wlh ni shaiÉ—anin aljani ne ba mutun ba..........'  tunkan ya Æ™arasa maganar tashi Da gudun gaske sehrish ta juya tare da buÉ—e Æ™opar É—akin nashi ta fuce ji kake garam !!!! Ƙopar ta datse,   Fashewa da dariya haroon yayi hada dafe cikin shi, daga bisani kuma ya É—an tsagaita da dariya tare da cewa "Yarinyar tana da kyau, shiyasa na tsoratar da ita saboda inga kyawawan idanuwan nan nata masu kashe mun zuciya," ya furta tare da kai hannun shi saitin zuciyarshi yana faman sakin murmushi...............😳 tashin hankali anya kuwa haroon 👹😈    Ko kallon gabanta ba tayi saboda gudun da take yi gaba É—aya ta gama firgita da haroon, bata yi wani aune ba ta faÉ—ama junaid wanda ya nufo part din nasu, aikuwa gaba É—aya suka faÉ—a Æ™asa a manne da juna, atare zuciyoyinsu ke bugawa, musamman sehrish yana jin yarda zuciyarta ke faman bugawa da Æ™arfi da Æ™arfi, sun jima a haka kusan 8 mins sannan junaid ya ambaci sunanta "Sehrish,"   lamo tayi a jikinshi tana faman sauke ajiyar zuciya sai da ta samu natsuwa sosai sannan ta É—ago daga jikinshi,tayi gefe guda zaune dirshan tana kallon shi, tasowa yayi daga kwancen da yake yana faman sakar mata murmushi, tun safe yakeson ganin ta amma basu haÉ—u ba sai yanzu, shima zama yayi suna fuskantar juna da ita, wankan jeans da t shirt red colour ne ajikinshi, sai faman Æ™amshi yake yi,    "Me ya faru ne naga kina ta tiÆ™ar gudu kodai motsa jiki kike yi ne? ae muna da wurin gym acikin gidan nan,'  Ya faÉ—i yana kallonta, tayi mashi zuru da ido,   Ganin bata da niyar yin magana yasa shi cewa "Labari mai daÉ—i "! cike da zumuÉ—i tace "dagaske ? Wani irin labari ne wannan,  "Mafarki nayi jiya," "Me ya faru acikin mafarkin"? ta tambaye shi cike da son ji,   gyara murya yayi tare da cewa" mafarki nayi da wani narkeken zaki acikin wani Æ™urmin daji ya biyo ki da gudun gaske, kamar zaki tashi sama haka kika dinga gudu kina ihu, kinsan waye ya cece ki a wannan lokacin"? Ya jefa mata tambaya, hankali tashe tace "A'a," Æ´ar hararar ta yayi tare da cewa"Ni ne nan, nazo da suffar jemage na É—auke ki da fika fiki na mukayi sama can cikin gajimare...........' ganin yarda sehrish ta fashe da dariya yasa shi dakatawa da labarin yana kallonta, nuna shi tayi ta yatsa tana cewa"junaid kaji tsoran Allah, jemage fa kace? taya jemage zai iya É—aukar mutun ? sannu malam fesal ka feso mun Æ™arya,  gaba É—aya suka sanya dariya, ba Æ™aramin nishaÉ—i junaid ya sanyata ba duk da fargabar da take ciki, sun jima a zaune Æ™asa suna fira, kafin daga bisa ni suka tashi, shi ya wuce mosque ita kuma ta wuce bedroom É—inta saboda tayi sallar itama,``The father Of Soldiers```  Story &  Written     By    Hafsat Bature ********** zaune take agaban mirror ta kammala shiryawa cikin doguwar rigar material blue colour mai kyan gaske, rigar tabi shape É—in jikinta daga can Æ™asa yayi Æ´ar baza tamkar mermaid haka shape É—in ya bada,hoda ta É—auka tana shafa ma fuskarta, bayan tagama ta É—auki jan baki red colour ta murza, ba Æ™aramin kyau tayi ba, set na brushes É—inta ta É—auko ta gyara eye brows É—inta,bayan ta kammala gyara gashin giran, ta É—auki ribbom É—inta data ajiye saman mirror É—in, tattara sumar kanta tayi tana kiciniyar É—aure gashin amma sam tagaza saboda yawan da yayi,ita kanta tayi mamamkin yarda gashinta yake toho,ba Æ™aramin tsayi yayi ba ga yawan gaske dami guda dashi,bakomai ya jawo hakan ba face mayukan da take amfani dasu na gyaran gashi sun amshi kanta sosai,   Sakin gashin tayi ya tarwatse a bayanta,saboda gajiyar da tayi da ruÆ™on shi,hannu takai cikin jerin perfumes dinta ta dauki kwalbar turaren flower bomb wanda junaid ya É—aukar mata a lokacin da suka je siyayya saboda shima yana da irin shi, shiyasa ya haÉ—a mata dashi don suyi anko, feshe jikinta tayi da turaren ko'ina ya ji, nan take daddaÉ—an Æ™amshinsa ya gaure ko'ina na É—akin gaba É—aya,mayar da kawalbar turaren tayi bayan ta kammala fesa wa, sannan ta zuba ma madubin ido tana kallon fuskarta,fuskar sgr ta dinga gani acikin mirror É—in,nan take ta tuna lokacin da ta watsa a guje zata bar É—akin ya biyota da gudun gaske tare da ruÆ™ota a jikinshi,tafin hannunta tasa tare da rufe fuskarta tana faman sakin murmushi,sake tunawa tayi da lokacin da ya yage rigar jikinta kai tsaye ya afka mata,nan take taji wani irin sanyi da kasala sun rufar mata,gaba É—aya fa sehrish ta shiga yanayi cike da shauÆ™i take tariyo duk wani abu da ya faru da ita a daren jiyan ta shagala sosai, taji knocking daga waje, muryarta cike da kasala tace"Wanene"? .muryar Azmee tajiyo tana cewa"Auntynki ce," jin hakan yasa sehrish tashi tare da Æ™arasawa ta buÉ—e mata Æ™opar,tana a tsaye jikinta sanye da jallabiya ta mata maroon colour, ta yafa mayafi akanta ba Æ™aramin kyau tayi ba,  sakin baki tayi tana kallon Sehrish kafin tace"Masha Allah, irin wannan kyau haka? sai kace sabuwar amarya,kinyi kyau sosai,"murmushi kawai sehrish ke saki,   matsa mata hanya tayi tare da cewa"Aunty azmee ki shigo daga ciki mana,"  "A'a basai nashigo ba, dama nazo naji ya kuka Æ™are da Omar?ina fata kin sanar dashi gaskiya?   shiru sehrish tayi tana tunanin amsar da zata bata,ranta ne ya bata cewa kawai ta amsa mata da eh,saboda tana da tabbacin cewa muddin ta faÉ—a mata cewa takasa furta sunan haroon agaban Omar to tabbas azmeen zata iya cewa zata sanar dashi ita da kanta,idan kuma hakan ya faru to tabbas itama azmeen zata fuskanci irin abunda sehrish ta fuskanta wurin Furta sunan Haroon,kuma bazata so hakan ya faru ba don ba Æ™aramin raÉ—aÉ—i taji ba,.  Sam ta tafi duniyar tunani taji muryar azmee ta katsa ta da cewa"Lafiya kuwa naji kinyi shiru baki ban amsa ba"?.   cikin sauri sehrish tace"aunty azmee na sanar dashi gaskiya kuma yace zaiyi bincike akan haroon É—in,"  "Kin tabbata"? É—aga kai sehrish tari alamar eh,  Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"kayan sunyi maki kyau sosai Allah," murmushi sehrish tayi tana sunnar dakai,   Azmee ta kuma cewa"Munyi magana da junaid akan kayan nan naki da aka kai É—inki,yace mun tailor din ya kammala É—inki shi zaije ya amso maki kayan," cike da farin ciki sehrish tace"ngde sosoe aunty azmee na,"Â
ï¿?
 Murmushi azmee tayi tare da kai hannu taja kumatunta tace"bani zaki godemawa ba, ko kin manta waÉ—anda suka bada kuÉ—i akayi maki siyayyar ne"?  girgiza kai sehrish tayi tare da cewa"a'a ban manta ba,amma ina jin kunyar zuwa inyi masu godiya,"   "Gaskiya yakamata kije kam,zasu ji daÉ—i sosai su son cewa kinji daÉ—in abunda sukayi maki,ki same su kiyi masu godiya,"  "Insha Allah zanje," ta amsa mata, sakin kumatun nata tayi sannan ta juya zata futa, har ta ruÆ™e Æ™opar zata buÉ—e ta jinkirta kamar mai tunanin wani abu, sake juyowa tayi tare da kallon Sehrish dake a tsaye tace"wai nikam akwai abunda nake taso in tambayeki tuntuni sai in ta mantawa,"  cike da kulawa sehrish take kallonta don jin me zata ce,  Cigaba da cewa tayi "a kwanakin baya kinyimun magana akan cewa kinason zuwa garinku domin ki duba Æ´an uwanki da basa lafiya ko"? ta tambaya tana kallonta,   A ruÉ—e sehrish tace"Æ´an uwana kuma aunty azmee? Su wa kenan ? ni ba muyi wannan maganar ba kodai kin manta ne"?  hararar wasa azmee tayi mata tare da cewa"banason wasa fa, kinsan me nake magana akai mana, nan kwanaki kikazomin kina kuka kina cewa in taimaka maki kije kiga Æ´an uwanki shine kuma yanzu zaki ce mun har kin manta?  Hankali tashe sehrish tace"aunty azmee ni bani da wasu Æ´an uwa, bani da kowa wlh, bansan akan me kike magana ba,"   mamaki ne ya kama azmee ganin yarda sehrish ta haÆ™iÆ™ance akan cewa bata da wasu Æ´an uwa kuma fuskarta babu alamun zolaya,bayan ita da kanta ta sanar da ita game dasu,   ɗaure mata fuska tayi tare da cewa"banason rainin hankali sehrish!kina nufin dama baki da wasu Æ´an uwa!Æ™arya ce kawai kika shirga mun?tun farkon zuwanki gidan nan aiki, kika sanar dani cewa Æ´an uwanki ne basu da lafiya shiyasa kikazo neman kuÉ—in da za'ayi masu aiki, har na ranta maki kuÉ—i dubu É—ari tara domin ayi masu aiki a amatsayin kuÉ—in aikin ki na shekara É—aya da rabi, shima wannan duk plan ne kika tsara mun !!!!? Rai a6ace azmee ke magana hakan ba Æ™aramin É—aga mata hankali yayi ba, tuni idonta suka soma zubar da hawaye saboda tagaza gane kan me azmeen ke magana akai,.Â
ï¿?
  "Aunty azmee wlh ni duk bansan anyi wannan ba! Bamu ta6a magana dake akan cewa ina da wasu ƴan uwa ba,kuma ni ban amshi wasu kuɗi ba saboda ayi ma wasu aiki ba.....'  tunkan ta ƙarasa maganar azmee ta kwatsa mata tsawa tare da cewa"Ya isa haka Sehrish!!ashe dama ke maƙaryaciya ce!! kin cuce ni kinyi mun karyar cewa kina da ƴan uwa,ashe duk tsara ni kikayi saboda ki samu kuɗi,danasan haka kike da tunfarko ban yarda dake ba, wlh sehrish kinban mamaki kuma na gama yarda dake.......' tana kai ƙarshen maganarta, a fusace ta juya zata bar ɗakin cikin sauri sehrish ta ruƙo jallabiyar jikinta,muryarta na rawa cikin kuka tashiga cewa"wlh aunty azmee bansan komai game da abunda kike faɗa ba,na rantse maki da Allah wlh bani da wasu ƴan uwa aduniyar......'
Karanta>>> Taswirar Ƙaddara Complete Novel Document
 girgiza kai azmee tashi ga yi tana cewa"wlh kin ban mamaki sehrish,bansan haka kike ba ae da tun farko ban bari kin fara aiki agidan nan ba!!kin cuce ni kin rushe duk wata yarda da nayi maki,sai faman rantse rantse kikeyi mun ko tsoran Allah bakiji," rai a6ace azmee tayi maganar tare da fusge rigarta daga riÆ™on da sehrish tayi mata, cikin sauri tasa kai ta fuce daga É—akin,  A wani irin yanayi sehrish ta zube saman guiwowinta tana faman sharara kuka,mutun É—aya da ta yarda da ita aduniyar nan ayau ta juya mata baya akan abunda batasan dashi ba,har ga Allah ita gaskiyarta take faÉ—i amma azmee taÆ™i fahimtarta,tuni zazza6i ya fara hawa jikinta,sam tagaza tashi daga kneel down din da tayi ðŸ˜
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �    Tun da azmee ta fuce daga ɗakin sehrish, kai tsaye ta wuce nata bedroom ɗin, shiga ciki tayi tana faman safa da marwa,ranta ba ƙaramin sosuwa yayi ba,gaba ɗaya taji sehrish tafara fitar mata arai,saboda ƙaryar da ta shirga mata,cikin ƙunar rai take cewa"kin cuce ni sehrish,banta6a tunanin zakiyi mun haka ba,natsani makaryaci arayuwata, me yasa tunfarko bata fito fili ta faɗamun cewa kuɗi takeso ba,don me za tayi mun ƙarya?  tuni idon azmee sun cicciko da kwalla saboda ƙululun baƙin cikin daya tsaya mata arai,daƙyar ta iya samun wuri ta zauna daga gefen gadonta tana cigaba da tunani acikin ranta,  "ɗan adam kenan!yanzu duk yardkyautatama yarinyar can sai da ta butulce mun,saboda farin cikinta nakeyin wasu abubuwan don na faranta mata,amma hakan bai hana tayi mun ƙarya ba!!idan har dagaske ne sehrish ba ta da wasu ƴan uwa ƙarya ne tayimun,TO WAYE TASA NA TURA MA KUƊIN!!!!!!? miƙewa azmee tayi lokaci guda gabanta yashiga faɗuwa tuni taji zufa tasoma tsattsafo mata,hankali tashe tace"nashiga uku!! tabbas na tafka kuskuren yarda da yarinyar can!! meyasa tunfarko najata ajikina?kada fa ace da wata manufa tazo cikin gidan nan!!!  abubuwa iri iri suka dinga zuwa mata acikin ranta game da SEHRISH,😥 Lamarin dae ba daɗin ji
💋BOSS BATURE💋
A 6angaren su hossana kuwa tun bayan da suka yi faɗan nan atsakaninsu,su kayi fushi da junansu,saman gado hossana ta haye tana baccin wahala bayan ta gama shan kukan nata,Jahad kuwa bayan sun gama faɗan toilet tashiga tayi wankanta,bayan ta fito ta shirya cikin riga fara off shoulder tare da dogon wando baƙi,ba ƙaramin kyau tayi ba,musamman gyaran gashin kanta wanda akayi masu a wurin saloon ya ƙara ƙawata ta sosai,  komawa tayi ta zauna daga gefen gadon kusa da hossana, bin ta da kallo tayi sai faman sharar bacci takeyi tana jan minshari,haryanzu kayan baccin nan ne ajikinta tun na daren jiya,
ï¿?
  Hannu tasa tare da bubbuga bayanta a hankali tana cewa"hossana ki tashi!ko baki jin yunwa ne?   tsoki taja tare da juya mata ƙeya don karta takura mata, sake bugun bayanta jahad tayi tace"wai ba zaki tashi bane!?   buge hannunta hossana tayi tare da cewa"ki rabu dani, babu ruwanki dani,idan banyi wankan ba jikinki ne ko nawa?ko kin ta6a ganin zararre mara hankali yayi wanka ne? ni mahaukaciya ce kibarni inyi rayuwata.......'cikin kuka hossana ta ƙarasa maganar,da alama abun ya ta6a mata zuciya dama ta tsani akirata da zararriya,  Cike da lallashi jahad tace"am really sorry hossana nasan ban kyauta ba,raina ne ya 6aci shiyasa har na gaya maki hakan,bazan ƙara ba insha Allah,"   tayi maganar tare da ruko hannun hossana donta tashi,fisge hannunta tayi daga cikin nata tace"pls jahad leave me alone,zuciyata ba ta mun daɗi,yaya Omar kawai nake jira yazo,"   Murmushi jahad tayi tare da janyo gashin kan hossana tana wasa dashi a hannunta tace"faɗa mun gsky hossana kodae son yaya omar kike ne"?   juyowa hossana tayi tare da kallonta fuskarnan ɗauke da murmushi tace"eh ina son yaya omar sosai ke fa"?   jiki asanyaye jahad tace"Wani kalar so kike nufi? Na soyayya da aure? ta tambaya tana kallonta,  hossana tace"shi nake nufi,jahad inason ya omar sosai,"  shiru jahad tayi gabanta na faɗuwa tuni yanayin fuskarta ya canza izuwa matsananciyar damuwa,ganin hakan yasa hossana tashi zaune tana kallonta tace"jahad naga kamar fuskarki ta canza meya faru ne"?  cikin sauri ta basar tare da ƙaƙaro murmushi tace"bakomai hossana,ni zan wuce kitchen na shirya mana lunch," tana faɗin hakan ta miƙe da hanzari tabar bedroom ɗin nasu,saukowa daga saman gadon hossana tayi tare da wuce wa cikin toilet don tayi bath,   sam jahad tagaza jurewa tana fitowa daga bedroom ɗin ta wuce cikin falon tare da samun wuri saman 3 seater ta zauna jiki amace,  "dagaske ne hossana ya Omar take so?amma hossana ba ta da cikakken hankali bana tunanin tasan menene *SO* ya Allah kasa hakane saboda bazan iya jurewa ba......' ta furta tare da kai hannunta saman goshinta,bakomai bane ya faɗo mata aranta ba face farkon haɗuwarsu dashi a asibiti,lokacin ba ƙaramin tafiya yayi da zuciyarta ba saboda yarda yake acting dinsa,kyawawan ɗabi'unsa da halayansa sune suka sa jahad faɗawa tarkon shi, ita kanta bata tashi tabbatar da hakan ba sai ranar daya sanya handkerchief dinsa yana goge mata hawayenta..........."   tayi nisa cikin tunanin nata muryar hossana ta katse ta da cewa"jahad nayi tunanin zanzo na sameki a kitchen ne ashe kina nan zaune," firgit jahad tayi tana kallonta sai da ta dai²ta natsuwarta sannan tace"har kinyi wankan kenan," ta faɗi tana kallon hossana dake nufota jikinta na sanye da gown black colour, ta saki curly hairs ɗinta ya barbazo mata abayanta,   Amsa mata tayi da cewa"Eh baki ga har na canza kaya ba," ta faɗi tare da jujjuya mata donta gani,  Murmushi jahad tayi tare da cewa"kinyi kyau sosai," ta ƙarasa maganar tare da miƙewa tsaye tace"kizo muje kitchen ɗin atare saiki tayani aiki, muyi sauri mu kammala,"  Amsa mata tayi da toh, sannan suka wuce atare kitchen ɗin atare,
 ***************
Zaune yake acikin motarsu Ƙirar mercedes S450,ash colour,jikin shi na sanye da kakin sojoji,sai faman duba wrist watch ɗin dake hannun shi yake lokaci zuwa lokaci,gajiyar da yayi da jira ne yasa shi ɗauko wayarshi daga cikin trouser pocket dinsa ya buga ma Jahan kira nan take kiran ya shiga bada jimawa ba Ya ɗaga kiran, tsoki ayaan yaja tare da cewa"Wai kuɗin sunƙi fidduwa ne? Nifa nagaji da jira wlh," fuskarshi a yamutse yayi maganar,.   on the other hand jahan yace"Am sorry yanzu haka ma na fitowa daga bankin gani nan zuwa,"
ï¿?
  katse kiran ayaan yayi tare da mayar da wayar inda ya É—aukota ya ajiye,  Cikin Æ´an mintuna saiga Jahan ya fito daga cikin bankin hannunshi ruÆ™e da jaka,  Yana Æ™arasawa gaban motar ya buÉ—e back seat dinta tare da yin wurgi da jakar ciki, sannan ya rufe ya kuma buÉ—e front seat É—in ya shiga ya zauna a gefen Ayaan dake zaune a driver seat,  "Yau dae zamu jefar da kwallon mangwaro mu huta da kuda," acewar Jahan,murmushi ayaan ya saki yana kallon shi yace"baka ji daÉ—in da nakeji ba wlh,saboda a Æ™agare nake da mu bashi kuÉ—in nan mu huta da shegen nacin nan nashi,ya takurama rayuwarmu gaba É—aya,Haroon bai da imani jahan," fuskarshi a yamutse yayi maganar.Â
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �      "har yau in na tuna abunda yayi mana zuciyata tafarfasa takeyi mun saboda 6acin rai,haroon ya wulaƙanta arayuwarmu,Allah bazai ta6a barin shi ba, Insha Allah ƙarshen shi bazaiyi kyau ba," acewar jahan  Jinjina kai Ayaan yayi kafin yace"amma Jahan kana tunanin in muka bashi kuɗin nan zai goge video ɗin duka?am just doubting about it,don na lura ba ƙaramin shaiɗani bane,   jahan yace "ae ba zamu bashi kuɗin ba har sai mun tabbatar daya goge videon agabanmu mun gani,"   "Duk da haka nidae ina fargaba wlh," cike da damuwa ayaaan yayi maganar,  Sun jima suna magana kafin daga bisani Ayaan ya tashi motar suka miƙi hanyar gida,babu wanda ke ma wani magana acikin motar saboda duk sun tafi duniyar tunani, gaba ɗaya zulluminsu akan haroon,  Koda suka ƙarasa cikin gidan basu shiga da kuɗin ba,acikin motar suka barsu cikin jakar saboda tsaro, sun ajiyeta ne da nufin in dare yayi suzo su ɗauketa su kai mashi,   Bayan sun fito daga motar kaitsaye suka shiga cikin gidan tare da wucewa bedroom ɗinsu don rage gajiyar da suka kwaso,
Sehrish
Tasha kuka kamar kamar me,har sai da zazza6i da ciwon kai mai tsanani suka rufar mata sannan ta lalla6a ta haye saman gadonta ta kwanta,ta jima tana roƙon Allah akan yasa mafarki ne ba gaske ba,abunda ya faru tsakaninta da Aunty azmeenta,gaba ɗaya jikinta baya mata daɗi saboda dama can akwai fargar haroon dake damunta ga kuma wani ciwon kan ya taso mata na Azmee,duk ita kaɗae😢  ta jima tana juyi asaman gadon amma bacci yaƙi ɗaukarta sai ma ciwon nata dake ƙara gaba,fuskarta harta fara kumbura saboda kukan da tasha,dakyar ta lalla6a ta tashi jikinta na kerma ta wuce toilet jin an fara kiran sallar la'asar,bayan wasu ƴan mintina tafito daga ciki tana faman ƙanƙame jikinta saboda sanyin daya rufar mata gashi ta ta6a ruwa,   wurin wardrobe ɗinta ta wuce tare da buɗeta, ta zura hannu ta ɗauki hijab ɗinta ta zurata ajikinta sannan ta ɗauko carpet ta shimfiɗa,sam babu natsuwa ajikinta haka ta kabbara sallar tana karanta fatiha hawaye na wanko mata a fuskarta a haka ta kammala sallar tare da zama saman dardumar ta ɗaga hannayenta sama cikin shessheƙar kuka tashiga cewa"Ya Allah kasa aunty azmee tadawo cikin hayyacinta ta gane cewa ni ba ƙarya nake mata ba,bansan ya zanyi ba in ta juyamin baya,Ya Allah ka yayemun damuwar da nake ciki,ka kawomin sauƙi acikin rayuwata.........' sosai sehrish tashiga jera addu'o'i tana roƙon Allah akan abubuwan dake damunta,
Karanta>>>Â Kishi Da Aljan Complete Novel Document
  ta jima zaune saman dardumar tana tunanin maganganun aunty azmee,har lokacin tana kokwantan cewa anya Aunty azmee tana a cikin hayyacinta kuwa,   Har kusan Æ™arfe biyar sehrish bata motsa ba tana zaune zugudun,sai da biyar da rabi ta buga,sannan ta tashi jiki a mace ta cire hijabin tare da naÉ—e carpet É—in duka ta haÉ—a ta jefa asaman gadonta,cikin toilet tashiga ta wanko fuskarta sannan ta fito ta É—auki mayafi acikin wardrobe É—inta ta yafa shi asaman kanta, sannan ta buÉ—e Æ™opar É—akin ta fito,  Kitchen ta wuce saboda sanin cewa suna da aikin dinner,lokacin da ta Æ™arasa kitchen É—in tuni Azmee har tayi nisa a aikin nata,shiga ciki sehrish tayi tare da tsayawa tana kallon azmee dake tsaye agaban kitchen sink tana wanke naman da ta É—ebo acikin roba, Gabanta na faÉ—uwa tace"Sannu da aiki aunty azmee," tamkar bata ji taba haka ta shareta, kusan sau uku sehrish na maimaita maganar amma taÆ™i amsawa,   Jiki asanyaye sehrish ta Æ™arasa gaban chopping board ganin ta jera vegetables É—in da zata yayyanka, hannu takai zata É—auki wuÆ™a,muryar azmee ce ta katse ta da cewa"kada ki ta6amun komai! Zanyi aikina ni kaÉ—ai kamar yadda nasaba yi lokacin da baki nan,don haka ki fuce kibarmun kitchen É—in....' fuska aÉ—aure tayi maganar batare da ta juyo ta kalli. sehrish ba, . cikin tashin hankali sehrish tace"meyasa kika ce haka aunty azmee?tare muka saba yin aiki amma yau ke da kanki kike korata!?   rai a6ace azmee ta É—ago tare da nuna mata hanyar fita tace"dan Allah sehrish ki fuce kiban wuri!aikine nace bana so ni zanyi kayana,bana buÆ™atar taimakon ki,   ganin yarda azmee ke kwatsa mata tsawa yasata fashe wa da matsanancin kuka tana cewa"aunty azmee dan Allah kada kiyimun haka, nasaba dake na É—auke ki tamkar mahaifiyata,wlh bazan iya yi maki Æ™arya ba,ni bansan akan me kike magana ba,dan Allah kada kiyi fushi dani akan abunda banda masaniya akanshi,"!  tunda tasoma magana azmee ta zuba mata ido tana kallon ikon Allah,tamarasa me zatayi ma Sehrish ta huce,Æ™iri Æ™iri tana neman raina mata wayau,   "Sehrish in har kinason na kuma yarda dake to ki faÉ—amun gaskiya waye kika bani acct number dinsa na tura kuÉ—in dana baki naira dubu É—ari tara da kikayi mun Æ™aryar cewa Æ´an uwankine basa lafiya!!?  Jinkirtawa sehrish tayi daga kukan da takeyi tana tunanin wai ma ina takai kuÉ—in?bama wannan ba yaushe ta amshi kuÉ—in?   "Ina sauraronki"! Muryar azmee ce ta katse ta daga tunanin da ta tafi,   girgiza kai tashiga yi tana cewa"aunty azmee kiyi haÆ™uri amma ni bansan me kike magana akai ba,"   tabbas in taci gaba da sauraron Sehrish ranta zai cigaba da 6aci ne don haka tace"ki wuce kiban wuri banasan sake jin wata magana daga bakin ki," jiki asanyaye sehrish ta juya tare da barin kitchen É—in,   a hankali take tafiya jikinta ba kwari,  "Sehrish"! Muryar junaid ce ta katse ta,a hankali ta É—ago ta kalli gefen hagunta ta inda yake tunkarota,shigowar shi kenann cikin babban falon,   tunkan ya Æ™arasa ya lura da yanyinta,tsayawa yayi kusa da ita yana kallon fuskarta da tayi suntum saboda kukan data sha,   Cikin sanyin murya yace"reeeesh! Meya faru ne kike kuka?   ganin cewa bata da wanda zata faÉ—awa mawa face junaid tunda shine abokin shawararta, don haka ta sanar dashi dukkan abunda ya faru da ita, tsakaninta da aunty azmee   Cike da mamaki junaid ke kallonta tamkar mai nazarin wani abu can dae yace"sehrish saboda me za kiyima aunty azmee Æ™arya?meyasa zaki ce mata baki da wasu Æ´an uwa?   gaba É—aya sehrish tagama ruÉ—ewa cikin tashin hankali tace"junaid wlh bani da Æ´an uwa,ni bani da kowa ba Æ™arya nayi mata ba,'   harara yaÉ—an watsa mata kafin yace"idan har dagaske baki da Æ´an uwa,to su wanene kike kira a wayata? Lokacin da kike É—aukar mun phone É—ina batare da sani na ba?kin manta last time har na nuna maki message É—in da Æ´ar uwarki ta turo a wayata?sannan har kika roÆ™eni akan na kaiki ki gansu? A lokacin nace maki ki bari sai babban yayanmu sun koma Us ni da kaina zan kaiki ki gansu ko shi ma duk kin manta? Ya Æ™arasa maganar cike da tuhuma,   wani irin jiri sehrish tadinga gani a indonta,a hankali tashiga furta "innalallahi wa'inna ilaihirraji'un!!!" ganin tana Æ™oÆ™arin zubewa yasa shi yin saurin ruÆ™o shoulders É—inta yana cewa"ko baki da lafiya ne"? Ya tambaya yana kallon eyes É—inta dake a rufe, .....daÆ™yar ta iya furta cewa"junaid inaso nashiga bedroom É—ina,inaso na kwanta,"   gaba É—aya sehrish tayi confusing É—inshi lamarin ya É—aure mashi kai,ruÆ™o hannunta yayi ya taimaka mata suka nufi bedroom É—inta,buÉ—e mata yayi tashiga ciki, sai da yaga ta kwanta saman gadon sannan ya rufo mata É—akin,  Cikin sauri ya wuce kitchen wurin Azmee,da sallama yashiga kitchen É—in a lokacin tana tsaye agaban gass tana motsa farfesun data É—aura,jin muryarshi yasa ta juyo wa fuskarta babu fara saboda ruÉ—in da sehrish ta jefa ta aciki, Amsa mashi sallamar tayi sannan tace"junaid kana buÆ™atar wani abune"?   girgiza kai yayi alamar a'a Sannan yace"dama kan maganar sehrish ne,ta faÉ—amun duk abunda ya faru,bansan meke damunta ba,ni kaina tayi confusing É—ina,"   "Junaid sehrish tayimun Æ™arya,ban ta6a tunanin haka daga wurinta ba,meyasa za tayimun Æ™aryar cewa tana da Æ´an uwa,bayan ba haka bane saboda kawai ta cimma wani buri nata shine ta shiryamun plan,"!Â
Karanta>>>Â Shakuwa Ce Complete Novel Document
  "Aunty azmee bana tunanin sehrish tana cikin hayyacinta ne!saboda nima nasan da maganar ƴan uwan nata,da wayata takeyin amfani wurin kiransu tun a lokacin baya,akwai ma last message da sister ɗinta ta turo mata a wayana,nacewa suna buƙatar taimakonta har a lokacin naso na tura masu kuɗi amma lokaci guda wayarsu tadaina shiga kwata kwata,sehrish da kanta ta nemi na kaita garinsu tagansu,nace mata Sai babban yayanmu ya koma Us sannan zan kaita amma yanzu kuma ace ta manta komai? Yyi tmbyar yana kallon azmee itama kallon nashi takeyi,  Cikin mamaki tace"junaid naji kace tana amfani da wayarka wurin kiransu,kuma har message sun tura maka dan Allah idan wayar na'a kusa inason gani,'   cikin sauri junaid ya zura hannu acikin aljihun wandon jeans ɗinshi ya curo wayar,dannata yashiga yi can cikin messages ɗin shi yashiga sai ga saƙon da Jahad ta tura mata,  Ƙarasawa yayi dab da azmee ya miƙa matar wayar yana cewa"kin ganshi nan,"  Hannu tasa ta kar6i wayar tashi ta zuba ma screen ɗin wayar ido tana karanta saƙon, Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"Tabbas ƴan uwanta ne,idan bazan mantaba ta ta6a ambaton sunan JAHAD da HOSSANA amatsayin ƴan uwanta na jini,amma meyasa sehrish take ƙoƙarin mantawa dasu?ko don saboda tana cikin wannan daular ne......'  Junaid ne yayi hanzarin katse ta da cewa"i don't think so!rishi bazata ta6a mantawa da ƴan uwanta ba saboda abun duniya,na yarda da sehrish sosai kuma nayi imanin cewa rishi bazata ta6a yi maki ƙaryaba!tabbas akwai wani abu dake faruwa ne!!amma rishi bata cikin hayyacinta!!, .. azmee ta gamsu da bayanin shi amma har lokacin tana mamakin yarda akai hakan ta faru,   jinjina kai kawai tayi tace"yanzu ya zamuyi da ita junaid?inaso ni nasan awane hali ƴan uwan nata suke ciki ne,saboda inaso na haɗata dasu tun a lokacin naci burin hakan,nayi alƙawarin zan haɗata da ƴan uwanta,saboda yarda naga tana shiga damuwa akansu,   "Aunty azmee,yanzu babu halin yin wannan,in ma muka ce zamu cigaba dayi mata magana akansu to fa za'a samu matsala saboda zata iya samun ta6in hankali,amma in muka bi komai a hankali insha Allah dakanta zata dawo cikin hayyacinta wata rana,addu'armu kawai take buƙata,   Ajiyar zuciya azmee tayi maganganun junaid sun sa ta fara saukowa daga fushin da tayi da ita,   amsar wayarshi yayi daga hannunta sannan ya kuma cewa"pls aunty azmee karki ce zaki juya mata,ko kice zaki canza mata hakan zai iya haifar mata da damuwa,saboda ta saba dake sosai ta ɗauke ki tamkar mahaifiyarta,"  murmushi azmee tayi tare da cewa"shikenan junaid romeo insha Allah hakan ma bazata ta6a faruwa ba,kana da hankali sosai junaid shiyasa kake shiga ran mutane,ni nagaza fahimtar rishi,amma kai gashinan ka fahimce ta,"   murmushi shima yayi tare dasa kai ya fuce daga kitchen ɗin,
*************
Agalabaice Amal ta kammala wanke uban kayan da suka tula mata,kaf sai da ta wankesu,ba ita ta kammala wankin ba sai wuraren la'asar,da zazza6i taÆ™arasa shi,gaba É—aya ga66an jikinta ciwo suke yi mata,   ɗakinsu tashiga ganin babu kowa aciki saboda duk suna can É—akin mamynsu hayaam da abra wadda bata jima da dawowa ba,tana jiyosu acikin É—akin suna ta faman ciye ciyen kayan daÉ—in da abra tadawo masu dashi,babu wanda ya tuna da ita duk wannan uban aikin da tayi masu,shiga ciki tayi jikinta na kerma ta faÉ—a saman lumbutsetsiyar katifarsu,bargo taja ta lullu6e jikinta dashi,dakyar take numfashi,da wani irin hucin masassara numfashin ke fita,rayuwarta gwanin ban tausayi tun safe ko wanka batayi ba,saboda babu lokacin yin wanka,koda tayi niyyar yin wankan,sun riga da sun hanata amfani da sosonsu ko sabulun wankansu,wani lokacin in jikinta ya soma yi mata tsami,ruwa kawai take É—iba tashiga ta watsa,daga bayane tayi dabarar yankar buhu tayi amfani dashi amatsayin soso, ba sabulu haka take gurje jikinta dashi,ðŸ˜
 Cike take da tsoran karsu shigo su same ta acikin É—akinsu,saboda sun hana ta shiga ko'ina na gidan in ba kitchen ba,shima É—in in zatayi masu girki ne, tana acikin wannan yanayin tajiyo murya abra tana cewa"ke!uban mi ya kawo ki cikin É—akin mu?ba mamynmu ta hanaki shigar mana É—aki ba!! A fadace tayi maganar,tana a tsaye bakin Æ™opar É—akin,yarda kasan photocopy É—in aunty babba haka kamanninta suke,  Shiru Amal tayi batace komai ba zuciyarta ce kawai ke ta faman bugawa,  Rai a6ace abra tace"ko ki tashi kona zonan inyi wurgi dake Æ™azama kawai,"   har lokacin Amal tagaza motsawa saboda nauyin da jikinta yayi mata,jinjina kai abra tayi tare da shiga ciki azafafe don tayi wurgi da ita,har takai hannu zata fisgi bargon da ta lullu6e dashi,jin muryar hayaam yasa ta dakata daga Æ™oÆ™arin cire mata bargon da take yi,  Shigowa cikin É—akin tayi tare da cewa"meya haÉ—aki da ita ne,naji kina ta faÉ—a,"?   turo baki abra tayi tare da nuna Amal É—in da hannu tana cewa"baki ga yarda ta haye mana katifarmu ba da wannan baÆ™in jikin nata duk dauda,"  Sai lokacin Amal tasamu damar buÉ—e bakinta daÆ™yar murya na rawa tace"dan Allah kuyi haÆ™uri bani da lafiya,banjin daÉ—in jikina,"ðŸ˜ï¿? dakatar da abra hayaam tayi tare da cewa"ki rabu da ita,wahalar tayi yawa just for to day ta huta,tunda bata da lafiya," sam ba haka taso ba,bata ji daÉ—i da Hayaam ta hanata hukunta amal ba,a fusace ta fuce daga É—akin tana huci Shiga ciki hayaam tayi tare da samun wuri daga gefen katifar ta zauna,jin muryar Amal tana sambatu na raÉ—aÉ—in ciwo yasa ta kasa kunne tana sauraronta,
ï¿?
  "Ina jin cewa bazan rayu ba,dan Allah ku kaini wurin auntyna,inaso naganta kafin na bar duniya,"   dariya Hayaam tayi tare da cewa"aikuwa dae ba zaki ta6a ganinta ba adae nan duniyar, ae kin ɗaura aure da wahala tunda kika bari aka haifoki acikin gidan nan," tayi maganar tana ƙarashe dariyarta,  Amal kuwa fashewa tayi da kuka mai cin rai,  tsawa hayaam ta daka mata tare da cewa"yi mun shiru, kuka baya maganin komai sai ma ya ƙara jaza maki wani ciwon," shiru Amal tayi tana shassheƙar kuka ƙasa ƙasa Shigowa abra ta sake yi hannun ta ɗauke da wayar amani iphone 13 sai faman ruri take yi,miƙa mata wayar tayi tare da cewa"Sofwan ne ke kiranki,"  "ɗan wahala," ta fadi tare da kai hannu ta amshi wayar,juyawa abra tayi ta kalli Amal dake ƙumshe cikin bargo,guntun tsoki taja tare da cewa"salon ki sakarwa mutane miyan bacci asaman katifarsu,sai kin shanye shi don ubanki," ta ƙarasa maganar tare da kama hanya ta fuce daga ɗakin, Kara wayar tayi a kunnanta bayan tayi picking call ɗin,magana suka shiga yi dashi akan tafiyarta,duk wulaƙancin da tayi mashi hakan baisa ya rabu da ita ba, sai ma kiranta da yayi akan cewa gobe yanaso su tafi tare yakaita abujan, Sun jima suna waya kafin daga bisa ni su kayi sallama, tana ƙoƙarin ajiye wayar wani kiran ya sake shigowa,tsoki ta ɗanja tare da cewa"wani jarababben ne kuma yake kira na"!?   Duba screen ɗin wayar tayi Sunan AMANI ne ya bayyana,ɗan juyawa tayi ta saci kallon Amal dake ƙumshe cikin bargo alamu sun nuna cewa bacci yayi awon gaba da ita,hakan ne yasa ta ɗaga kiran tare da karawa a kunnanta tare da yin sallama,  On the other hand amani tace"wa'alaikum salam,hayam y kk ya gida yasu mammy"?   yatsina fuska tayi tare da cewa"duk suna lafiya,"   Amani tace"labarine ya same ni daga wurin aunty laila nacewa zaki koma gidansu Abbas da zama,sam abun bai dace ba wannan abun kunyar har ina?menene alaƙarmu dasu da har zaki koma gidan surukan mu da zama?amatsayin ƙanwar matar yayansu! Jin wannan maganar ta Amani yasa ran hayaam 6aci,miƙewa tayi daga zaunen da take saboda tsiwa tamkar zata fasa screen ɗin wayar haka tashiga cewa"Ki tsaya iya matsayinki AMANI!!babu ruwanki dani, iya sa idone kawai naki kada kice zakiyi mun shisshigi acikin lamarina! Ni ba kamar Aunty laila bace data saba jan ki ajiki har tayi maki sanadin auren Abbas,kina magana ne da HAYAAM!!!yakama ki iya bakin ki!!!!
ï¿?
 jin yarda hayaam ke zazzaga mata rashin mutunci yasa tayi rejecting kiran,  tsoki hayaam ta saki tare da cewa"matsoraciyar banza!!ae banso kika kashe kiran ba,so nayi na sauke maki kwandon rashin mutunci shashasha kawai," rai a6ace ta ƙarasa yin maganar tare da yin wurgi da wayar saman katifar,kama hanyar fita ɗakin tayi domin taje ta sanarwa mamaynsu yarda su kayi da Amanin,  fitarta ke da wuya, Amal ta buɗe idanunta waɗanda suka kumbura jawur saboda raɗaɗin ciwo, ta samu bacci amma tsiwar hayaam ce tafarkar da ita, gaba ɗaya duk wayar da su kayi da amani tana ji a kunnanta,saboda taji lokacin da hayaam ta ambaci sunan Amani,
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �
  A hankali ta sanya hannunta tare da yaye bargon,a galabaice ta ɗan tashi zaune, hannu takai tare da ɗaukar wayar hayaam wadda tayi wurgi da ita asaman katifar kuma cikin sa'a wayar bata kai ga shiga security ba,   jiki na kerma ta shiga wurin kiran,sai ga sunan amani ya bayyana a list ɗin farko da tayi waya dasu,cikin sauri Amal ta buɗo numbarta, zuba ma numbar ido tayi tana tunanin yarda zata ɗauki numbar,babu wurin da zatayi copying dinta,tuni hawaye sun soma zarya a fuskanta, wannan shi ake ce ma ga ƙoshi ga kwannan yunwa,  runtse idonta tayi tare da buɗe su akan screen ɗin wayar,nan take taji cewa zata iya haddace numbar akanta,muddin taci gaba da bitarta akanta, a hankali take ƙarewa numbers ɗin kallo tana naɗarsu akanta,motsin mutun taji alamar an tunkaro ɗakin cikin sauri Amal ta fita daga wurin numbar amanin ta danna power ɗin wayar tayi duhu sannan ta ajiyeta,da hanzari tashige cikin bargon ta lullu6e dukkan jikinta, Hayaam ce tashigo kai tsaye ta ƙarasa inda wayar take tasanya hannu ta ɗauka tare da fucewa daga ɗakin,  ajiyar zuciya Amal tashiga saukewa,har lokacin tana cigaba da bitar numbar amani akanta,
*******************
Bacci sosai sehrish tasha, har wuraren Æ™arfe biyar da wani abu babu alamun zata farka kamar matatta, kusan sau huÉ—u azmee na leÆ™owa don taga kota farka saboda ta lallashe ta akan abunda ya faru amma duk in tashigo sai ta same ta tana ta faman shan bacci,Â
Ƙarar jiniyar motocinsu ce tasa sehrish farkawa a gigice, fuskar nan tayi jaga-jaga da ita saboda kukan da tasha,ko da ta farka zuciyarta nata faman bugawa, a kasalance ta tashi zaune saman gadon tana faman sauke ajiyar zuciya, idonta takai kan agogon bangon dake manne, hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba ganin cewa har lokacin sallar magrib yayi, gashi ba tayi la'asar ba, cikin sauri ta sauko daga saman gadon ta wuce cikin toilet donta ɗaura alwala,
ï¿?
Yau da wuri suka dawo, Abbansu tare da marshal Omar da kuma Sgr sai kanal Yousouf, a nan main palour ɗin suka rarrabu, Abbansu tare da kanal yousouf suka wuce bedroom ɗinsu dake a nan down stairs, Omar da Rafayet atare suka haye upstairs, Tuni azmee ta kammala jera masu dinner ɗinsu a dining, duk anan suka hallara suka ci abincin, banda sgr da bai fito ba, bayan sun kammala ita tashiga kwashe warmers din da sauran tarkacen da sukayi amfani dashi tana kaiwa kitchen, ganin tana ta faman ɗawainiya ita kaɗae ba sehrish yasa junaid kama mata kayan suna kaiwa kitchen atare ba ƙaramin daɗin hakan taji ba,barin shi tayi a cikin kitchen ɗin ita kuma ta wuce don ta gyara masu dining area ɗin, kafin ta dawo har junaid ya kammala yin wanke wanken kayan da sukayi amfani dashi, tare da gyara kitchen ɗin tsaf tamkar ba'ayi amfani dashi ba,   tsayawa tayi tana kallon shi yana ƙoƙarin haɗama sehrish cornflakes acikin kofi,  Juyowa yayi ya kalle ta tare da cewa"aunty azmee irin wannan kallo haka"?  Murmushi tayi tare da cewa"junaid kai na musamman ne,kana bani mamaki yanzu kai da kanka kayi wanke wanken nan?kuma ka gyara kitchen ɗin nan?  Murmushi yayi tare da cewa "menene aciki aunty azmee?nifa ba aikin da bazan iya yi ba,kuma aiyukan mata suna burge ni sosai, naji ma ina shawa'ar inga ina wanke wanke girki da shara,"   dariya sosai azmee tayi tana girgiza kai tace"gsky baka da dama junaid, koda yake abune mai kyau ka koya,yana da amfani hakan saboda wata rana zaka taimaki matarka ne da wasu aiyukan cikin gidan,Ko ba haka ba?" ta tambaya tana kallon shi,.   ɗaga mata kai yayi alamar eh, sannan yace"aunty azmee ki tayani da addu'a Allah ya cikamin burina,inaso nayi aure very soon insha Allah end of this year.....' kasa ƙarasa maganar yayi ganin yarda Azmee ta saki baki galala tana kallon shi,  fashewa da dariya yayi a lokacin har ya kammala haɗa ma sehrish cornflakes ɗin,  "Joking aside pls faɗamun gaskiya amma dae wasa kake mun ko"?  girgiza mata kai yayi alamar a'a sannan yace"just keep praying for me, insha Allah soon i wll get marriage," yana faɗin hakan ya kama hanyar fucewa daga kitchen ɗin hannun shi ɗauke da Cup sai faman tiriri yake,
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �
 shiru azmee tayi tana kallon bayanshi har ya 6ace mata, lamarin ya É—aure mata kai tabbas tasan halin junaid tunda harya iya furta mata aure yakeso to kuwa fa auren zaiyi dagaske, kuma duk abunda ya nuna yanaso sai abbansu ya mara mashi baya,  "Ashe zamu sha biki," ta faÉ—i da dariya a fuskarta,Â
  Knocking kopar ɗakin sehrish ya shiga yi, a lokacin har wani baccin ya soma ƙoƙarin ɗaukarta asaman sallayar,tana jin bugun ƙopar a firgice ta tashi tana faɗin "Waye"!   daga waje junaid yace"Mijinki ne insha Allah," ita kanta batasan lokacin da tasaki murmushi ba,
ï¿?
 "Ka shigo ciki," ta bashi amsa, tura kopar yayi tare da sa kai yashiga ciki yana faman zabga mata murmushin nan nashi, wuri yasamu kusa da ita anan ƙasa ya lankwashe ƙafarsa ya zauna tare da miƙa mata cup ɗin yace"nasan zaki buƙaci wannan,haɗine na musamman daga mijinki insha Allah,"  fashewa da dariya tayi tana kallon shi, kafin ta zuro hannayenta daga cikin hijabin jikinta ta kar6a, jikinta har rawa yake yi wurin ɗaukar spoon ɗin dake aciki tashiga ɗebowa tana kaiwa bakinta, ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,  Tun tana sha da cokali har ta tsame cokalin daga cikin kofin ta miƙa mashi tare da cewa"ruƙe mun," hannu yasa ya kar6a, kafa cup ɗin tayi abakinta tashiga kwankwaɗarshi harta shanye duka,  tausayi ta bashi saboda ya lura ba ƙaramar yunwa take ji ba, cikin sanyin murya yace"nasan kina jin yunwa sosai,bari naje na kawo maki dinner ɗinki," yayi maganar tare da yunkurawa zai miƙe cikin sauri tace"a'a nagode da wannan ma,ba yunwa bace damuwata ba, abunda ke damu na shine Har yanzu aunty azmee fushi take dani"? fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar,   "Kada kisa damuwa aranki, nayi ma aunty azmee magana kuma ta fahimce ki,tun ɗazu ma take ta son tayi magana dake,"  Cike da farin ciki tace"dagaske Aunty azmee bata fushi dani kuma nema na take"?   jinjina mata kai yayi alamar eh, cikin sauri ta miƙe tana naɗe dardumar don taje ta ganta,   ɗaukar cup din da ta ajiye yayi sannan yayi mata sallama ya fuce daga ɗakin,
  cire hajib ɗin tayi, sannan ta ɗauko mayafi mai girma ta rufe jikinta dashi, buɗe ƙopan tayi sannan ta fito tare da wuce wa ɗakin azmeen, kwankwasa mata ƙopa tayi, a lokacin azmee bata jima da kammala salla ba,  tasowa tayi tare da sanya hannu ta buɗe mata ƙopan, jikinta na sanye da dogon hijabi hannunta na ruƙe da cazbaha,   Zuba ma sehrish ido tayi tana kallonta, cikin en ina tace"Aunty azmee dama junaid ne yace kina son gani na," ta ƙarasa maganar tana sunnar dakai cike da fargabar amsar da Azmeen zata bata,  murmushi azmee tayi tare da cewa"hakane tun ɗazun nake ta son in yi maki magana amma duk in nazo saina same ki kina bacci," jinjina kai sehrish tayi sannan tace"nasan na 6ata maki rai aunty azmee, ki yafe mun,"  hannu azmee tasa tare da shafa gefen fuskarta tace"just forget about the past komai ya wuce ki manta kawai, yanzu ma nake shirin zuwa in shirya maki abinci don nasan kina jin yunwa sosai,  Murmushi sehrish tayi ba ƙaramin kwanciyar hankali tasamu ba,    Sannan tace"bari na barki ki huta nasan kinyi aiki sosai kin gaji,banji daɗi ba ɗazun da kika hanani tayaki aiki," cikin sanyin murya ta ƙarasa maganar,   Azmee tace"ki manta da wannan, yanzu kije ki haɗa abincin ki ci," amsa mata tayi da toh,sannan ta juya zata fita, Muryar azmee ce ta sake katse ta da cewa"Au na manta ban sanar dake ba, babban yayan ku fa ya dawo, yau da wuri suka shigo, shi kaɗae ne ma ya rage bai ci abincin shi ba, ki fara kai mashi pls,"  Amsa mata tayi da toh sannan tasa kai ta fuce daga ɗakin nata,
 *SGR*
gaba ɗaya hankalin shi na akan Laptop dinsa da yake dannawa, yana a hakimce saman royal sofa mai mazaunin mutun biyu, jikin shi na sanye da kimono robe ta cotton,green colour jikinta akwai zane zane masu kyan gaske, rigar bata rufe faffaɗan ƙijinshi ba,hakan ba ƙaramin kyau ya ƙara mashi ba,ya ɗaure igiyar rigar adai dae saitin shafafen cikin sa, a natse yake danna laptop din da zira ziran yatsun hannun shi, ƙamshi ta ko'ina  da sallama sehrish ta shiga falon nashi, batare da ya ɗago ba ya amsa mata sallamar,
ï¿?
  Shiga ciki tayi hannunta na É—auke da Æ™aramin tray mai É—auke da fruits tare da coffee,  koda ta Æ™arasa dab dashi murya na rawa tace"sannu da aiki,fatan kana lafiya,"  "Alhmdllh," ya amsa mata har time É—in bai É—ago ba, ajiye mashi tray É—in tayi daga gefen laptop É—insa, sannan tace"kana buÆ™atar wani abu"? hannu yasa ya É—auki cup of coffee É—in yakai bakinsa ya É—an kur6a, janye shi yayi daga bakin shi sannan anatse yace"na manta phone É—ina asaman pillow a É—aukomin ita," juyawa sehrish tayi da sauri zata kama hanyar zuwa bedroom É—in nashi kamar daga sama taji gaba É—aya mayafin jikinta ya sulale Æ™asa daga jikinta, cikin sauri ta juya tare da kai hannu zata É—auki mayafin daya faÉ—i Æ™asa, ganin Æ™afar sgr tayi asaman mayafin ya take shi da farar Æ™afarshi, kasa É—aukar mayafin tayi saboda fargabar da tashi ga, ranta ne ya bata cewa ba dagangan yayi hakan ba, da alama baisan ya take mata mayafin ba,  A É—an tsorace tace"mayafi na" batare da ya É—ago ya kalle ta ba yace "ina Sane," jiki asanyaye ta juya tare da nufar É—akin nashi, tsoranta kar ace alluran nan ta jiya bata sake shi ba,  faÉ—awa cikin É—akin nashi tayi tare da nufar saman pillow É—insa wayar na ajiye asama,hannu takai zata É—auki wayar kwatsam taji motsin mutun abayanta hakan ya sanyata juyowa a firgice gaba É—aya sumar kanta ta watso harta gaban fuskarta, tsananin tsoro ne yakamata ganin mutumin da tabaro yana shan coffee tsaye agabanta, a wani irin yanayi yake bin jikinta da kallo tundaga kan Æ™afarta har izuwa saman Æ™irjinta, ganin haka yasa sehrish ta soma ja da baya a tsananin tsorace saboda tunawa da abunda ya faru jiya atsakaninsu hakan na nufin cewa Allurar bata sake shi bane, har yanzu akwai saura ajikin shi,Â
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �
  tuni zufa tasoma tsatstsafo mata a fuskarta, takawa sgr yayi yana matsawa kusa da ita, ja da bayan da zata ƙara yi ke da wuya , gaba ɗaya ta faɗa asaman gadon shi, bin ta saman gadon yayi gadan gadan ya tunkareta, hakan yasa ta fashe da matsanancin kuka atsorace ta dinga girgiza mashi kai tana cewa"wlh bani bace na ɗauko allurar ba ! Bani ita akayi....ba zan iya cutar dakai ba.......!!" sai faman sambatu takeyi ita kanta batasan me take cewa ba saboda ya ƙureta sosai ta runtse idanunta zuciyarta nata faman harbawa, sam batasan cewa sgr yana cikin hayyacin shi ba,da gangan yayi mata haka saboda akwai abunda yakeson ganowa game da daren jiya da kuma abubuwan da ya gani na canji a bedroom ɗinshi da kuma body ɗinshi, yasan cewa itace last person daya kasance tare da ita,    jin shiru baice komai ba yasa ta ɗan buɗe idonta, ba komai yake kallo ba face doguwar sumar kanta, sai yanzu ya gane inda ya samu siraran gashi guda uku masu tsayi, hakan na nufin gashin kan Yarinyar ne ya tsinta asaman gadon shi ɗazu da safe, acikin sambatun da tayi mashi ta ambaci cewa ba ita bace ta ɗauko allurar ba, ba ta ita akayi, nan ma ya gane cewa kwa6a tayi mashi jiya har ya ɗirka ma kanshi allura, that's why omar ya tambaye shi akan cewa shi ya dauko allurar, natsuwa yayi a hankali yana ƙare ma fuskar sehrish kallo, ita kuwa sai faman haɗiyar yawu take yi saboda tsoro ga zufa dake gangarowa ta cikin gashin kanta kamar mara gaskiya, duk da sanyin A.c dake gudana aciki,   rufe idanuwanta tayi tana faman karanta addu'oi' acikin bakinta,   for the first time daya ƙarewa wata ƴa mace kallo irin wannan aduniyar nan, yana kallon kyakkyawar fuskarta ne aƙoƙarin shi na ya tuna abunda ya faru jiya,amma yarda take motsi da siraran la66anta tana karanta addu'oi'n neman tsari hakan ba ƙaramin burge shi yayi ba, sai ya samu kan shi da shagala wurin kallon bakinta, tunanowa yayi da ranar daya turketa amatsayin mace yarda ta tsorata har ta sume mashi, shi kuma rayuwarshi mace mai shegen tsoro ba ƙaramin burgeshi takeyi ba,ba don komai ba sai don ya ruƙa tsorata ta don ya samu nishaɗi,   ɗan gyara muryarshi yayi tare da cewa"jiya kin ban allura nayi ma kaina har nayi ƙoƙarin yin raping ɗinki, ko ba haka akayi ba? ya tambaya fuskarshi a ɗaure,.   hankali tashe sehrish ta shiga furta"innalallahi wa'inna ilaihirraji'un. Nashiga uku, kasan Allah ni bani bace na ɗauko allurar ba bansan komai akai ba,.   shiru sgr yayi yana kallonta har lokacin taƙi buɗe idanunta, abunda bata sani ba shi guessing yayi bai tuna komai ba, amma yayi mata rijiya ta faɗa,   cigaba da magana yayi anatse"then tell me who brought it to u"?   shiru tayi lamo saboda tasan ba zata iya furta sunan haroon ba, ganin taƙi magana yasa shi daka mata tsawa tare da cewa"ba magana nake maki ba!!," wannan tsawar da yayi mata ne yasa ta sume mashi, dama sai da ranshi ya bashi,  Saukowa daga saman gadon yayi tare da fucewa izuwa palour dinshi, kai tsaye ya wuce wurin fridge ɗinsa tare da buɗewa ya ɗauko bottle water mai sanyi, sannan ya koma cikin bedroom ɗin nashi,zama yayi daga gefen gadon tare da sanya hannu ya buɗe roban rubar saida ya fara sha sannan ya ɗebo a hannun shi ya yayyafa mata a fuskarta, a gigice ta ware idanunta kai tsaye suka shiga cikin nashi a lokacin ya mayar da bottle din abakin shi yana ƙara shan ruwan, tamkar a mafarki take ganin abun har lokacin jikinta bai daina kerma ba, cire roban ruwan yayi daga bakin shi sannan ya mayar da murfin ya rufeta tare da ajiyewa saman side drawer ɗinshi,   sannan yayi mata nuni da hanyar fita yace"zaki iya tafiya," cikin sauri ta sauko daga saman gadon nashi, hanyar fita ta nufa da sauri da sauri, jinkirtawa tayi tare da ɗan juyawa don ta saci kallon shi, samun shi tayi a kashingiɗe saman gadon ya aza head dinsa asaman pillow, eyes dinshi a lumshe tamkat zasu rufe amma hasken kwayar idonshi blue ya ɗan fito alamar bai runtse idanun duka ba,   Muryarshi ce ta ratsa kunnanta da cewa"akwai wani abu ne"? Cikin sauri ta girgiza kai alamar a'a sannan ta fuce daga ɗakin, sai da tafara ɗaukar mayafinta dake zube a ƙasa, ta yafa shi akanta sannan ta fuce daga part ɗin nashi, tafiya take anatse fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi tayi mamakin yarda akai Sgr bai tuhumeta ba,bayan ya tuna duk abunda ya faru atsakaninsu jiya, tayi tunanin zata sha mari ne a wurin shi amma sai gashi abun yazo mata da sauƙi, har yau tana mamakin sauƙin kai irin nashi da ba kowa zai fahimta ba, amma tabbas bai da girman kai ko kaɗan, jan ajine kawai dake gare shi ko jinin sarauta bazai nuna mashi wannan ba, Domin kuwa shi kanshi Sarki ne mai cike da ƙarfin iko👑
 a hankali take taka steps ɗin down stairs zata sauko, jin alamar shigowar mutun cikin babban falon yasa ta tsagaitawa da tafiyar tana kallon shi, jahan ne ya shigo cikin falon hannun shi ruƙe da jakar kuɗin da zasu ba haroon, ganin yarda yake tafiya cikin sanɗa yasa ta gane cewa bai son wani ya ganshi cikin sauri ta ja da baya tare da samun wuri ta la6e,   sai faman ƴan waige waige yake yi yaga ko akwai mutun amma wayaam ba kowa hakan yasa cikin sauri ya wuce bedroom ɗinsu, ajiyar zuciya sehrish ta sauke tare da lalla6awa ta fito kai tsaye ta nufi kitchen tana zullumin ko menene Jahan ya ɗauko acikin jakar hannunshi, da alama dae wani mugun abunne tunda har yake sanɗa don kar aganshi, ta faɗi acikin ranta a lokacin da take ƙarasawa cikin kitchen ɗin don ta zuba ma kanta abincin da zata ci,
  turo Æ™opar yayi a hankali yashiga daga cikin É—akin nasu, jin alamar shigowar mutun yasa ayaan dakatawa daga zirga zirgan da yake yi acikin É—akin,  Cikin sauri ya nufe shi yana cewa"Jahan ka tabbata babu wanda ya ganka"? Amsa mashi yayi da cewa"eh babu da alama duk sunyi bacci, kazo yanzu mu hanzarta mu kai mashi kuÉ—in,"  Atare suka fito daga bedroom É—in nasu, duka suna sanye cikin jallabiya, É—akin haroon suka nufa, koda suka Æ™araso Æ™opar É—akin a rufe take, kwankwasawa Jahan yashiga yi a hankali,  "Su waye ne"? Ya tambaya daga ciki, Har suna haÉ—a baki wurin cewa "twins ne ",   kwance yake daga saman gadonshi,daga shi sai shorts ajikinshi ba riga, tasowa yayi tare da nufar kofan yasa hannu ya buÉ—e masu tare da cewa"ku shigo daga ciki," kallon juna su kayi kafin daga bisani suka shiga daga ciki,  tunda haroon yayi arba da jakar kuÉ—in dake hannun jahan yashiga sakin murmushin nan na shu'umanci yana cewa"ince dae kuÉ—ina ne acikin jakar nan ko"? yayi maganar tare da miÆ™a hannu zai kar6i jakar,janye ta jahan yayi tare da cewa"ka fara goge video É—in tukunna mu damÆ™a maka su,"  ta6e baki yayi yana kallon su,kafin ya juya ya nufi saman gadonshi inda wayar shi ke ajiye ya É—aukota, yatsan shi yasa ta buÉ—e sannan ya shiga wurin videos É—inshi ya lalubo nasu daya É—auka sannan ya miÆ™a masu tare da cewa"Gashi nan ku goge da kan ku,ina ga hakan zai fi ko"? Kallon juna suka sake yi duk jikinsu yayi sanyin, tsoransu karya cuce su,ayaan ne ya kar6i wayar tashi yayi deleting É—insa gaba É—aya, sannan ya kalli haroon É—in dake ta faman sakin murmushi yace"ka tabbata babu wani videon namu dake gare ka bayan wannan!?  ɗaga mashi gira yayi alamar eh, jahan yace'laptop É—inka fa babu wani aciki"? nan ma ya sake cewa"babu wannan ne kawai gare ni,"  ajiyar zuciya suka saki gaba É—ayansu,  MiÆ™a mashi wayar Ayaan yayi, sannan jahan ya damÆ™a mashi jakar kuÉ—in, kar6a yayi yana cewa"kun tabbatar cewa miliyan 80 É—inne"?  ayaan yace"ka Æ™irga su mana sai kaga in sun cika,"Â
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �
ZuÆ™unnawa haroon yayi tare da zuge zeep É—in jakar, sai ga bandir bandir É—in Æ´an dubu dubu, dami dami shaÆ™e acikinta, hannu yasa tare da curo bandir guÉ—a É—aya yakai a saitin hancin shi yana shinshinasu yace"Anya wannan ba kuÉ—in ganye bane?harara suka watsa mashi jahan yace"a'a na bishiya ne," dariya haroon yayi yana faman shaÆ™a kuÉ—in a hancin shi,  gaba É—aya ransu ya gama 6aci burinsu ya Æ™irga kuÉ—in yaga in sun cika, amma ya tsaya yi masu shegantaka,   tass ya fiddo da kuÉ—in ya Æ™irga su, duk dami É—aya na dubu É—ari ne, a haka yayi counting É—insu 80 millions ne bayan ya kammala Æ™irgasu, ya shiga cusa su acikin jakar kaf ya kwashe su, sai da ya zuge zeep É—in sannan ya É—ago ya kalle s u cike da shaÆ™iyanci yace"Au na manta ban baku la'ada ba,"  atare suka haÉ—a baki wurin cewa"mun fi Æ™arfinsu,kai ke buÆ™atarsu kai daga ganin mu kasancewa ba matsiyata bane,"  "Wow," ya furta yana tafa hannunshi "abu yayi kyau Æ´a'Æ´an billionaire,karfa kuce zaku gayamin magana!ku fuce mun daga É—aki cikin salama,"  Jahan yace"ba sai ka kore mu ba, mukan mu aÆ™agare muke da mu fita mubar maka wannan Æ™azamin É—akin naka wanda ko numfashi mutun daÆ™yar yake iya fitarwa!!kuma inaso ka sani Haroon baka ci bulus ba, zamu rama duk wani wulaÆ™ancin da kayi mana!!  yana kai Æ™arshen maganar tashi ya ruÆ™e hannun ayaan suka juya zasu fita daga É—akin karaf idonsu ya sauka akan mutumin dake shigowa cikin É—akin, A wani irin firgice suka ja da baya gaba É—ayansu, shi kanshi Haroon ya sha jinin jikin shi saboda basu son da mutun ba, gaba É—aya duk abunda suka tattauna acikin kunnanshi kaf ya gama naÉ—ar komai,  hankali tashe suke kallon shi,kamar yarda shima hankali atashe yake kallon suÂ
Follow my tiktok acct 👇 https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
Atare suka sauke ajiyar zuciya lokacin da suka shaida cewa junaid ne,sai faman murza idanunshi yake yi da hannunshi,da alama magagin bacci ne ya shigo dashi,hakan ya basu tabbacin ba lallai in ya fahimci komae ba,   cikin sauri Jahan yace"junaid tun yaushe kake anan?me kake yi har yanzu baka yi bacci ba"?  Cikin shagwa6a yace"nima bansan ya akai na shigo ba,dan Allah kutaimaka mun ku kaini ɗakin abbanmu in kwanta,wurin shi nake son zuwa,"  Shu'umin Murmushi haroon yasaki yana kallon shi,  ganin yarda yake binshi da kallo yasa su twins saurin ruƙe hannun junaid suka fuce dashi daga ɗakin,   "Ayaan kaje kawai ka kwanta,ni bari nakai shi ɗakin Abban namu," Amsa mashi yayi da toh,sannan ya wuce bedroom ɗinsu,  Shi kuma jahan zuƙunnawa yayi tare da ce mashi"ka hau na goya ka karka faɗi,"   daddagewa junaid yayi ya haye bayanshi tare da ƙanƙame shi,sannan jahan ya miƙe ɗauke dashi abayansa ya wuce bedroom ɗin Abban nasu,   A hankali ya tura ƙopar bedroom ɗin Abban nasu,yana kwance sai faman sharar bacci yake yi asaman royal bed ɗinshi,shiga da junaid ciki yayi a hankali ya sauke junaid saman gadon daga gefen abban nasu,    gyara kwanciya junaid yayi tare da rungumo Abban nasu da hannunshi sannan yace ma Jahan"thank u,"  murmushi jahan yayi ba ƙaramin burge shi yayi ba,sam junaid bashi da wata damuwa,sai yaji dama shine ke irin rayuwar shi,   "Sleep well," ya furta tare da juyawa ya fuce daga bedroom ɗin yana sauke ajiyar zuciya,ɗakinsu ya koma lokacin daya shiga a kwance ya samu Ayaan har bacci yayi awon gaba da shi,shima wucewa yayi tare da haurawa saman gadon ya kwanta daga gefenshi, Yaushe rabon da suyi bacci irin na daren nan harsun manta,saboda fargabar haroon kullum da damuwarshi suke kwana,yau dae sun huta ma rayuwarsu tunda sun sallame shi,
A 6angaren haroon kuwa tun bayan da suka fita ranshi ya raya mashi cewa tabbas akwai alamar tambaya game da zuwan junaid bedroom É—inshi,saboda tun da yake junaid bai ta6a faÉ—owa É—akinshi ba irin haka,duk irin magagin baccin da junaid yake yi bai ta6a zuwa É—akin shi ba,amma sai yau kwatsam zai faÉ—o mashi É—akin shi adai² lokacin da suke tattaunawa dasu twins kuma? Anya ba turo shi akayi baâ?   zama yayi daga gefen gadon nashi yana tunani,dakyar ya iya tashi yakai hannu ya kinkimi jibgegiyar jakar kuÉ—in,wuri yayi mata acan cikin É—akin nashi ya 6oyeta,   Sannan ya koma tare da hayewa saman gadonshi ya kwanta,
   ********************* Washe gariÂ
A hankali ya buɗe idanunshi da su kayi mashi nauyi saboda bacci,hannu yasa tare da yaye blanket ɗin daya lullu6a dashi,miƙa hannu yayi tare da ɗaukar wayarshi dake ajiye saman bedside drawer dinshi,missed calls ya gani nasu hossana da jahad,tashi yayi daga zaune yana kallon screen ɗin wayar tashi,jiya yaso yaje ya duba su amma bai samu time ba,   danna musu kira yayi tuni tashi ga ringing,  A lokacin Jahad ce acikin falon zaune saman 2 seater tana ta jiran kiranshi,hossana kuwa tana can tana sharar bacci,   har ta fidda ran cewa zai kirasu saiga kiran nashi ya shigo,cikin sauri ta miƙe ta nufi telephone ɗin tasa hannu ta dauka tare da karata a kunnanta,   Cikin sanyin murya tace"Assalamu Alaikum ya Omar an tashi lafiya,"  murmushi yasaki tamkar yana agabanta yace"lafiya lou Alhmdlh,nayi laifi ko?jiya banzo na duba ku ba,ayi mun afwa ina busy sosai,amma kuna araina,"   "Babu komai ya Omar,dama mun damune akan rashin zuwan naka,kuma mun kira wayarka jiya da safe,baka a kusa sai dai matarka Aunty zainab ta ɗaga kiran,"   "What!matata kuma? Wacece kuma aunty zainab?pls explain to me ni bangane me kike cewa ba,"   murmushi jahad tayi tare da cewa"Ya omar meyasa ba ka sanar damu cewa kana da aure ba?baka so mu sani ne?  Sam Omar baisan inda zanjen nata ya dosa ba,   "Jahad nifa bansan me kike cewa ba! Wacece kuma matata?  kafin jahad tace wani abu,sai ga hossana ta fito da saurin gaske jikinta sanye da kayan bacci,tana ƙarasowa tasa hannu ta kar6i telephone ɗin tare da karata a kunnanta cikin shagwa6a tace"eh mana ya omar ashe kana da aure,jiya da safe mun kira wayarka,mace ta ɗaga kiran tace mana kai mijinta ne kuma baka a kusa,sannan kuma tace mana tana ɗauke da juna biyu,kuma sunanta zainab amma kana kiranta da Hayaty,"   tunkan ta ƙarasa maganar Omar yashiga 6a66aka dariya,natsuwa su kayi gaba dayansu suna sauraron sautin dariyarshi,  "Ya omar kayi shiru baka ce komai ba," muryar hossana ce ta katse mashi dariyar tashi,daƙyar ya tsagaita tare da cewa"Am sorry na fahimci abunda kuke cewa,bazan iya yi maku bayani anan ba,insha Allah bayan na kammala breakfast dina zan shigo sai muyi magana ta fahimta ko?  Atare suka haɗa baki wurin cewa"Eh muna jiran zuwanka,sannan in ka tashi zuwa kazo mana tare da Hayati ɗinka muganta,"   murmushi kawai yayi tare da rejecting call ɗin,sai lokacin ya duba kiran nasu da sukayi mashi jiya acikin wayarshi,cike da mamaki yaga kiran da sukayi mashi jiyan da safen kuma already an ɗaga kiran,natsuwa yayi yana tunanin wanene ya daga mashi kira harya tsara wannan ƙaryar,tabbas junaid zai iya yi mashi wannan aikin,.   Miƙewa yayi tare da saukowa daga saman gadon nashi,ya wuce cikin toilet dinshi,within 15 mins ya fito ya wuce wurin closet ɗinshi,tsaf ya kammala shiryawa cikin shadda purple colour ba ƙaramin kyau tayi mashi ba yabi jikinshi duka ya feshe shi da turare,  Bayan ya ɗauki wayar shi ya fito tare da wuce wa part ɗin Rafayet,da sallama ya shiga ciki,baya acikin falon shi don haka ya wuce cikin bedroom ɗin shi,  Yayi mamakin ganin shi a kwance saman shimfiɗeɗen gadonshi,jikin shi na'a sanye da bathrobe da alama bai jima da fitowa daga wanka ba,   Shiga ciki omar yayi tare da samun wuri daga gefen gadon ya zauna sannan ya ambaci sunan shi a hankali"Rafayet wai haryanzu bacci kake yi?   Yamutsa fuska yayi alamar idonshi biyu sannan yace"Omar,yau lalaci nake ji ajikina,duba fa ka gani tun ɗazu nayi wanka amma nagaza tashi in shirya kaina,"   sakin baki Omar yayi yana kallon shi tare da jinjina kai yace"nasan meye matsalarka,wato har yanzu abun nan bai bar jikinka ba ko?
Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �
  "Mekenan"? Sgr ya tambaya yana kallon shi daga kwancen da yake,   Murmushi Omar yasaki batare da yace komai ba,   Miƙewa Sgr yayi tare da tashi daga zaune suna fuskantar juna shi da Omar yace"Na fa tuna duk abunda ya faru jiya a tsakanina da yarinyar nan,"!  "dagaske"? Omar ya faɗi da ɗan mamaki a fuskarshi,  "yeah,amma bakomai na tuna ba,so nake ka faɗamun gaskiyar abunda ya faru,time ɗin da ka tarar damu asaman gadon nan,shin na cire shorts ɗin jikina ko ban cire ba"?   tunkan ya ƙarasa maganar omar ya soma sakin dariya,  Ɗaure fuska sgr yayi tare da cewa"pls Omar banason wasa,just tell me the truth,cos banaso yarinya ta raina ni,"   tsagaitawa omar yayi sannan ya zayyana mashi dukkan abunda ya faru tsakanin shi da Sehrish,
  hannu sgr yasa tare da dafe forehead ɗinshi yace"OMG!Omar ashe kaine ka katse mun jin daɗina a wannan lokacin!meyasa baka bari na ƙarasa aikina ba"? ya ƙarasa maganar yana jifar shi da harara,   dariya omar ya kuma yi kafin yace"nifa taimakonka nayi,kisan kai fa zakayi,"   tsuke fuska yayi tare da cewa"babu wani nan,ni narasa meyasa kake mun haka,"  Yayi maganar tare da kai hannu ya dauki pillow ya wurga mashi shi a fuskarshi,tarbe pillow ɗin Omar yayi a hannunshi tare da cewa"Am sorry bro,bansan abun yayi hurting ɗinka ba,amma ae ko yanzu bata 6aci ba,kasan inason farin cikin ka,bari natashi naje na kira maka yarinyar sai ka ƙarasa aikin naka,"  Yana kai ƙarshen maganar tashi ya mike tare da nufar hanyar fita daga bedroom ɗin yana karashe dariyar shi,yana jiyo muryar sgr cike da zolaya yana cewa"Am waiting,"
Kai tsaye bayan Omar ya fito daga sashen sgr down stairs ya sauko tare da fuce wa daga main palour din,ko breakfast din bai tsaya yayi ba ya wuce wurinsu hossana,
Wuraren ƙarfe tara kiran Amrish ya tashe ta daga dogon baccin daya ɗauke ta tun bayan sallar asuba,dakyar ta iya buɗe idanunta da sukayi nauyi saboda bacci,hannu takai tare da daukar wayar dake ajiye asaman side drawer ɗinta,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta a kasalance tace"Assalamu alaikum Amrish irin wannan kira haka tunda sanyin safiya"?   daga can 6angaren Amrish tace"Sleeping sickness wai kina nufin har zuwa yanzu baki tashi daga bacci ba?duba time ki gani kusan 9 fa yanzu,"  Jin haka yasa sehrish sa hannu tare da janye blanket ɗin jikinta ta tashi daga zaune tana kallon clock, ɗan xaro ido tayi tare da cewa"subhanallahi wai har 9 tayi?meyasa aunty azmee bata tashe ni ba,ya ilahi,"  dariya amrish tayi tare da cewa"kin cika bacci reeshi yakama kije kiga psychiatric doctor ya duba brain ɗinki,"   ɗaure fuska sehrish tayi kamar tana agabanta tace"oh ashe dama kallon da kike mun kenan ko?    muryarta cike da dariya tace"no ba haka bane inason lafiyarki ne shiyasa na baki shawarar kije aduba ki,"   "Okey thanks for ur advise amma fa ni ba inda zanje,da raina da lafiyata bazan kwasa na tafi asibiti ba,salon su ja man bala'e," ƙarasa maganar tayi tare da cewa"pls inason zan shiga kitchen yanzu,i wll call u later bye,"   sallama su kayi da amrish sannan ta mayar da wayar saman side drawer ta ajiyeta, saukowa tayi daga saman gadon cikin sauri ta wuce cikin toilet, brush tayi tare da wanko fuskarta sannan ta fito ta wuce wurin wardrobe ɗinta,buɗewa tayi tare da ɗauko mayafi ta daure shi akanta kamar ɗan kwali,
Lokacin da fito har azmee ta kammala jera masu breakfast ɗin asaman dining,junaid ta samu tare da fawan zaune suna yin breakfast dinsu,kamar waɗanda yunwa ta koro sai faman turawa suke yi abakinsu suna ci,   dagowa junaid yayi tare da kallonta nan take ya sakar mata murmushi tare da kiran sunanta"sehrish,"  Juyowa fawan yayi tare da kallonta yace"ke zo nan,"  nan da nan taji gabanta ya faɗi dama basu ta6a magana dashi ba,  jiki asanyaye ta ƙarasa inda suke dai dai kusa dashi sannan ta tsaya tana faman ƴan kame kame,   cikin sanyin murya yace"jira kike na fara gaishe ki ne"?  cikin sauri sehrish tace"ina kwana,ka tashi lafiya,"  fashewa da dariya junaid yayi yana kallonsu,harara fawan ya watsa mashi tare da mayar da idonshi kan sehrish yace"lafiya lou,haka yadace daga yanxu basai nace ki gaishe ni ba,daga zarar kin ganni kiyi hanzarin gaidani amatsayina na yayanki,"  Murmushi sehrish tayi tare da amsa mashi da"toh,"   junaid yace"bismillah ki zauna muyi breakfast atare mana," girgiza kai tayi tare da cewa"a'a inaso zan shiga kitchen ne wurin aunty azmee,"  Amsa mata yayi da"okey,"  Sannan cikin sauri ta juya tare da nufar kitchen din,   time din da taƙarasa kitchen ɗin azmee ta kammala gyare kitchen din tsaf, dakyar ta iya cewa"ina kwana aunty azmee,"   sai lokacin ta lura da ita,murmushi tasakar mata tare da cewa"lafiya lou babyn junaid,sai yanzu kika tashi daga baccin naki?dazu nashiga ɗakin naki na sameki kina bacci,   ciki sehrish ta shiga tana cewa"Aunty azmee ae da kinsani kin tashe ni,nikaina banasan yawan baccin nan da nake yawan yi,"  Azmee tace"ai baida amfani atlease yakamata ace duk in kika kammala sallar asuba ki daure kina karanta al'qur'ani, sannan ki dinga yawaita yin azhkar,insha Allah duk wani abu dake damunki Allah zai yaye maki shi,"  "Insha Allah zan yawaita yinsu kamar yarda kikace,yanzu inaso in kaima babban yaya breakfast ɗinshi,bansani ba ko kin kai mashi,   Azmee tace"a'a ban kai mashi ba,bari na haɗa maki sai ki kai mashi,"   Tsayawa sehrish tayi tana jiranta,  Bayan azmee ta kammala shirya mata breakfast din nashi acikin tray ta miƙa mata,hannu biyu tasa ta kar6a tare da kama hanya ta fuce daga kitchen ɗin,  Da sallama abakinta tashiga part din nashi,   har time din bai fito ba,yana acikin bedroom ɗinshi,ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi tray din asaman table,sannan ta wuce izuwa bedroom ɗinshi daga bakin kopar ta tsaya tare da maimaita sallamar,   daga cikin bedroom ɗin tajiyo muryarshi yana cewa"wanene nan"  tuni tasha jinin jikinta,musamman data tuna abunda ya faru jiya ba ƙaramin tsoro ya bata ba,   murya na rawa tace"Ni ce,breakfast nakawo maka,"   "Okey,come in," a hankali tasa ƙafa tare da shiga ciki zuciyarta nata faman ɗar ɗar,  tsayawa tayi daga bakin ƙopan tana kallon shi,har lokacin yana kishingiɗe kamar yarda Omar ya barshi,   ganin ta tsaya abakin ƙopar yasa shi cewa"lafiya?   cikin sauri tace"bakomai," "Okey shigo ciki,ki fara gyara min toilet ɗina,"  ƙarasawa ciki tayi a hankali take tafiya tana satar kallon shi,eyes ɗinshi na'a rufe tamkar mai jin bacci,duk wani motsinta acikin kunnanshi yake jinshi,tura ƙopar toilet ɗin tayi tare da shigewa ciki,   Sai bayan da ta shiga ciki sannan ya buɗe idanun shi tare da bin ƙopar toilet ɗin da kallo,tunawa da abunda ya faru jiya tsakaninsu yayi,mayar da idonshi yayi tare da lumshe su,   ba da jimawa ba sehrish tafito daga cikin toilet tare da cewa"na kammala gyarawa,saura bedroom din,"   buɗe idanunshi yayi ba tare da ya kalleta ba yace "okey,ki duba cikin closet ɗina,ki ciro mun kayan da zan sanya,"  Cike da mamaki ido waje sehrish tace"dani kake"?  "Ni da waye" ya tambaya a ataƙaice,d'an murmushi tayi tare da wuce wa can ciki wurin wardrobe ɗinshi,mai girma da faɗin gaske gaba ɗaya glass ne ta gabanta,daga waje kana iya hango kayan sawarshi dake aciki gasunan abun kamar a company jeri jeri komai a tsare,tana ɗauke da sliding doors ajikinta,  Hannu sehrish takai ajikin wardrobe ɗin nan take ƙopar ta zuge da kanta,abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,ruwan ido ta tsaya yi tama rasa wanne zata ɗauko mashi,saboda kowanne acikin kayan sawar nashi kyau suke yi mata,wata ƙopar ta zuge anan taga jerin kayan hausawa ta jima tana mamakin ashe yana dasu amma bai ta6a sanyawa ba,hannu tasa tare da ɗauko mashi haɗaɗɗiyar shadda gezna sky blue mai ɗaukar ido,   ruƙowa tayi a hannunta tare da dawowa wurin gadon Shi a lokacin harya gaji da jiranta ya sauko da ƙafafunshi ƙasa yana ƙoƙarin tashi,jin takon tafiyarta yasa shi ɗagowa yana kallon kayan data ruƙo a hannunta,  tsayawa tayi dab dashi sannan ta miƙa mashi,   ƙin kar6a yayi saima nuna mata hanya da yayi tare da cewa"basu nakeso ba,ki canza mun wasu bana sa kalar wannan,"    Jiki asanyaye sehrish ta koma ta maida shaddar sannan ta ɗauko mashi jeans da t shirt baƙa,    Komawa tayi tare da miƙa mashi,hannu yasa ya kar6a tare da furta"thanks" a gefen shi ya ajiye kayan sannan ya miƙe tare da kai hannu ya zame bathrobe ɗin jikin shi,cikin sauri sehrish tayi hanzarin barin bedroom ɗin takoma daga waje tana faman sauke ajiyar zuciya,ƙiris ya rage sgr ya saki murmushi don ba ƙaramin dariya ta bashi ba,ita duk atunaninta babu shorts ajikinshi shiyasa tayi saurin guduwa daga ɗakin nashi,  Tsaf ya kammala zura kayan ajikinshi bayan ya gama ya koma gaban dressing mirror ɗinshi tare da kai hannu ya ɗauki kwalbar turarennan nashi shumukh yabi ko'ina na jikinshi ya feshe shi da shi,sannan ya koma wurin shoe rack ɗin shi tare da zaro takalma ya zura a ƙafarshi,   tana atsaye tana jiran fitowarshi muryarshi ta ratsa kunnanta da cewa"ki shiga ciki ki gyara mun,"  Sannan ya wuce ta izuwa cikin falon nashi,   Shiga ciki sehrish tayi anatse ta soma gyara mashi bedroom ɗin nashi,
  ************** A hankali motarsu tashiga cikin gidan abusufyan major ne ke driving ɗinshi yayin da yake zaune a back seat na motar,  Bayan yayi parking ɗin motar omar ya fito tare da wuce wa ciki,  Koda yashiga cikin falon samun su yayi azune saman 3seater sun haɗa kai sun kurawa plasma tv ɗin dake manne abango suna kallon tashar bollywood,   ba ƙaramin burgeshi su kayi ba,gyara muryar yayi tare da yi masu sallama,atare suka dago tare da kallon shi,hossana na ganin shi ta miƙe da gudun gaske ta tunkare shi,dakatar da ita yashiga yi da hannun shi amma ina sai da ta faɗa mashi,sosai ta rumgume shi tare da kwantar da kanta a saman wide chest ɗinshi,lokaci guda yaji wani irin yanayi atattare dashi,  Jahad kuwa a fusace tace"hossana menene haka wai?ba zaki bari ya ƙaraso ciki ba?   tamkar bata jita ba,haka ta ƙara ƙanƙame shi tana cewa"ya Omar nayi missing ɗinka sosai,jiya ko isasshen bacci bansamu ba saboda ban saka a idona ba,  hannu omar yasa tare da janyeta daga jikinshi suna kallon juna ido cikin ido yace"Am sorry pls,amma yanzu ae gashi nan nazo ko?  daga mashi kai tayi alamar eh,sannan tasanya hannunta cikin nashi suka ƙarasa ciki atare suka zauna kusa da Jahad saman 3 seater ɗin da take,  Cikin sanyin murya tace"sannu da zuwa ya omar,yasu abba da sauran mutanen gidan,  Fuskarshi dauke da murmushi yace"yawwa jahad,duk suna lafiya,ina fata kuma nasame ku cikin ƙoshin lafiya,"  Amsa mashi tayi da eh,sannan tace"namanta ban tambayeka ba,yasu Aunty zainab,"?   kafin yace wani abu hossana tace"ya Omar wai dagaske kana da aure"?a shagawa6e tayi maganar tamkar zatayi kuka,   cikin natsuwa ya soma kora masu jawabi"Ni banta6a aure ba,saurayi ne ni,ko budurwa ban ta6a ajiyewa ba,"  Jahad tace"amma ya Omar wacece ta ɗaga kiran wayarka da mukayi a lokacin?   shiru ya danyi kafin yace"ina tunanin younger brother ɗina ne Junaid,ya cika zolaya sosai," Domin Sauke Littafin Sai Ku Dannan inda aka saka Download Now! �
 maimaita sunan Jahad tayi "JUNAID!ya omar ƙaninka ne shima?  kallonta yayi tare da cewa"eh ƙanina ne,yana da kyau sosai ga kyan hali sannan ya iya kyakkyawan murmushi kuma shagwa6a66e,"  Murmushi su kayi jin yadda Omar ke zayyana musu ƙanin nashi da alama dae ba ƙaramin sonshi yake ba,   "Ya omar ka nuna mana hotonshi mu gani mana," acewar hossana,  Batare da 6ata lokaci ba Omar ya zura hannu a ajihun wandonshi ya ciro wayarshi tare da shiga gallery ɗinshi,hoton junaid ya buɗo tare da miƙa ma Hossana,hannu tasa ta kar6a tana kallon hoton cike da mamaki tace"wow! yaya Omar wai dagaske ƙaninka ne?wlh yana da kyau sosai dan Allah ka kaimu gidanku wata rana mu ganshi,"  Jin yarda hossana keta santin hoton junaid yasa Jahad sa hannu tare da kar6ar wayar,  Lokaci guda taji gabanta yayi wani irin bugu,tunda ta aza idonta akan kyakkyawar fuskar junaid bata ƙara cewa uffan ba,sam tagaza janye idanunta akan fuskarshi,bakomai take furtawa acikin zuciyarta ba face"Tabarakallahu Ahsanul khaliqin,"   Muryar omar ce ta katse ta da cewa"jahad naji kinyi shiru"?  jiki asanyaye ta ɗago tare da kallon shi tace"ya omar pls zan iya tafiya da wayarka cikin ɗakinmu?yanzu zan dawo,"  murmushi ya saki tare da cewa"ba damuwa zaki iya zuwa,"  cikin sauri ta miƙe tare da nufar bedroom ɗin nasu ta shige ciki,    "Ya omar bari nakawo maka breakfast nasan baka ci komai ba," hossana ce tayi maganar yayin da take miƙewa daga saman kujerar," Ruƙo hannunta yayi tare da cewa"dawo ki zauna,idan kika tafi wa zai tayani fira,"   ƙayataccen murmushi tasaki tare da komawa ta zauna daga gefenshi sannan tace"Ya Omar yaushe zakayi aure ne?  "Ranar dana samu maisona," ya bata amsa yayin da idonshi ke akan agogon hannunshi,  cikin shagwa6a tace"ya omar ni nasan cewa kana da ƴan mata dayawa da suke sonka,kawai dae kaine baka shirya yin auren ba,"  "haryanzu bansamu kalar wadda nakeso ba hossana," ɗan turo baki tayi tare da cewa"ka faɗamun kalar matar da kakeso ka aura,zan tayaka da addu'a insha Allah,"  murmushi ya ɗanyi tare da kwantar da bayanshi ajikin sofa ɗin yadda zai samu damar kallonta sosai sannan yace"Inason mace natsastsiya kamila,miskila mai ilmin addini dana zamani,mai ladabi da biyayya,idan Allah ya bani mace mai irin wannan suffar tuni zanyi wuff da ita,"  tunkan ya ƙarasa maganar hossana ta ɗaure mashi fuska,sunnar dakai ƙasa tayi tamkar zata zubar da hawaye,  "Meya faru ne"? Ya tambaya yana kallon ta,  Cikin shessheƙar kuka tace"ya omar ba dole sai mace nutsastsiya ba,ko miskila,in dai tana sonka tsakani Allah kawai ka aureta,"   kawar da fuskarshi gefe guda yayi yana murmushi,  Sanya hannunta tayi acikin nashi tare da kwantar da kanta asaman kafaɗarshi, ...sun jima a haka batare da wani yace ƙala ba,kusan 30 mins sai ga jahad tafito hannunta ɗauke da wayarshi,tsayawa tayi tana kallonsu shi ya lumshe ido,hossana kuma har ta fara bacci,  murmushi ta saki tare da samun wuri ta zauna daga gefen shi sannan ta ambaci sunan shi "ya Omar,"  Buɗe donshi yayi a hankali yana kallonta,miƙa mashi wayar tayi tare da cewa"thanks,"hannu yasa ya kar6i Wayar sannan ya mayar da idonshi tare da rufe su,.   Ajiyar zuciya tasaki tare da miƙewa ta koma cikin bedroom ɗinsu,saman gadonsu ta haye a inda ta ajiye drawing book ɗinta,ashe lokacin da ta kar6i wayar omar ta shigo dashi bedroom ɗin nasu,zama tayi tare da ɗauko kayan zanen ta acikin school bag ɗinta,a natse ta zauna tare da zana fuskar,ba ƙaramin kyau zanen yayi ba,fuskar ta fito raɗau dauke da wannan murmushin nashi,zuba ma zanen ido tayi tana kallon shi,lokaci guda taji tana son taganshi face to face~~~~   ************************ Yau tunda ta farka da kewarsu jahad ta tashi saboda mafarkinsu da tayi,fitowa tayi daga cikin bedroom ɗinta jikinta na sanye da riga bubu ta material,  tsayawa tayi daga tsaye tana sauraron wayar da Aunty babba keyi,da alama da hayaam suke magana saboda taji ta ambaci sunanta sai faman 6a66aka dariya take yi,   "wlh ba kiji irin farin cikin da nake ji ba,yau burina zai cika na ganin kin koma gidan da zama,hayaam bana so ki raga ma yarinyar nan!so nake acikin one week ki ƙuntata ma rayuwarta har taji ta tsani zama acikin gidan,maƙirci kawai zaki cigaba da haɗa mata ae nasan kin ƙware a wannan 6angaren shiyasa nake yin ki,"   girgiza kai hafsat tayi tare da ƙarasawa ciki ta samu wuri saman 2 seater ta zauna tana sauraronta,sun jima suna wayar kafin daga bisa ni su kayi sallamar,mayar da wayar tayi tare da ajiyewa agefenta,sannan ta ɗago tare da kallon hafsat tace"gulmawuya halan kin fito don kiji abunda muke tattaunawa ne?  Murmushi hafsat tayi tace"mommy kenan ashe haryanzu kina akan bakanki na ganin cewa hayaam ta koma gidansu Abbana da zama hmmmm whatever ni wannan ba damuwa ta bane,kawai akwai shawarar da nakeso na baki in ba damuwa,"  zuba mata ido aunty babba tayi tana sauraronta,.  Ci gaba da magana hafsat tayi"Mommy aunty hayam zata koma gidan da zama wannan ba laifi bane Amma zai iya zama abun kunya,amma maganar a ƙuntata ma rayuwar yarinyar dake acikin gidan sam wannan bai taso ba,in ba haka ba wlh zaku yi danasanin yin hakan,"  wata uwar harara aunty babba ta watsa mata kafin tace"ke tashi ki ban wuri!tun kafin ranki ya 6aci,"  Maƙe kafaɗa hafsat tayi tare da cewa"mommy dama ita gaskiya ɗaci gare ta,kullum ina faɗa maki kiji tsoran Allah,ki daina biye ma ruɗin duniya.....'  Katse ta aunty babba tayi tare da cewa"karfa kice zakiyi mun nasiha,ko iyayen da suka tsugunna suka haife ni ban ta6a sauraran nasiharsu ba balle ke ƴar cikina dana haifa,  tana kai ƙarshen maganarta,takai hannu tare da ɗaukar wayarta sannan ta miƙe tare da wuce wa ciki,  "Mommy ae da alama basu yi maki nasihar ma,don da ace suna yi maki da duk ba haka ba,nibansan ma ya akai abba ya auroki ba anya ba rufa ido kukayi mashi ba,"   "Hafsat! Me kike cewa"? A ɗan firgice hafsat ta juya tana kallonta duk a tunaninta ta jima da barin falon ashe bata ƙarasa fita ba,  Cikin sauri tace "haka nace ni dae na gode ma Allah daya bani uwa tagari kamar ki,"   ba don ta yarda da maganarta ba ta juya tare da wuce wa upstairs,  Ajiyar zuciya hafsat ta saki tana faman tiƙar dariya, � � _💋Boss Bature💋_
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
Lokaci guda Amal ta sauke nauyayyar ajiyar zuciya,ashe magen hayam ce ta faɗo ɗakin,sai faman kuka takeyi miyauu miyauu,da alama yunwa take ji ne,Batare da 6ata lokaci ba Amal ta zuƙunna ta shiga tattara kuɗin da sauri da sauri jikinta na kerma,don a matuƙar firgice take saboda magen nan data tsorata ta,  Miƙewa tayi hannunta ɗauke da kuɗin cikin sauri ta fice daga ɗakin,komawa tayi cikin ɗakinsu hayamm,jiki na rawa ta buɗe wardrobe ɗin kayansu,doguwar riga ta ɗauko ta Abra tare da mayafinta, A hanzarce ta shiga zura rigar ajikinta,ba ƙaramin yawa rigar tayi mata ba har ƙasa take ja,ga wuyar rigar da yayi mata yawa,yafa mayafin tayi,  Sannan cikin sauri ta fito daga cikin ɗakin,a nan waje ƙopar ɗakin ta ɗauki slippers tare da zura wa aƙafarta,   Jiki na kerma AMAL ta kama hanyar fucewa daga cikin gidan,sai da takai baƙin ƙopar fita sannan ta ɗan tsaya tare da juyawa tana kallon cikin gidan yayin da hawaye ke shararowa daga idonunta,bazata ta6a mantawa da irin uƙubar da tasha acikin gidan ba, ta dan jima a haka,daga bisani tasa kai cikin sauri tabar gidan,   Kamar walk'iya haka Amal tabar santar gidan gaba ɗaya,duk da bata jin kwarin jikinta,haka ta jure ta kama hanyar sauri sauri gudu gudu,ita kanta batasan ina zata dosa ba,amma tana da tabbacin cewa tasha zata nema domin ta hau motar zuwa Abuja, ...(Finally Amal taci nasarar barin gidan,saura fatan sauka lafiya)
***************** Sosai jahan ke ta faman sakin dariya cike da nishaɗi,bakomai yasa shi dariya ba face Ayaan dake zayyana mashi irin halin daya shiga na barazanar da haroon ke masu,hankalin su kwance basu da wani sauran damuwa,suna a kwance cikin hotel room ɗinsu,basu jima da fitowa daga wanka ba,kowannansu na sanye da white shorts ajikinshi,suna rungume da juna cikin lallausan bargo,  "Wlh jahan naji jiki sosai,wai ashe haka abun yake?sai gani a sume,gaskiya haroon ba ƙaramin shaiɗani bane,nasha Wahala a ranar nan,"     "dama kai rago ne Ayaaan,nafi ka juriya shiyasa abun yazo maka ahaka,ranar naji kishi da baƙin ciki sosai,har yanxu in na tuna abun ba ƙaramin ƙuna zuciyata ke yi mun ba,"acewar jahan,   "Pls ni banaso muna tuna abunda ya wuce,hakan zai iya sanya mana damuwa acikin zuciyoyin mu,mubar maganar kawai,"  Jahan yace"shikenan mu bar maganar amma inaso na tambayeka pls,yanzu kwatsam a lokacin nan da ace bamu ba haroon kuɗin nan ba,ya saki videon mu a social media har Abba da babban yayanmu suka gani,me kake tunanin zai biyo baya,"  Da wasa jahan yayi maganar amma har sai da zuciyar Ayaan ta ɗan buga,   "Abunda zai faru shine,zuciyar Abban mu zata buga anan take ya yanke jiki ya faɗi,babban yayan mu kuma zai yi mana bugun mutuwa,abunda ba'a fata kenan,"Ayaan ya ƙarasa maganar yana dariya,    Shima jahan dariyar yayi yana cigaba da sauraron shi kafin daga bisani suka ɗaura daga inda suka tsaya,"   **************Sehrish
Tun bayan da tadawo cikin bedroom ɗinta,wanka tayi tare da ɗauro alwala,bayan ta kammala sallar,ta koma wurin wardrobe ɗinta,ta ciro kayan da zata sanya,dogon wando ne na roba,Army trouser tun lokacin da suka je siyayya,ta ɗauke shi saboda ba ƙaramin burgeta kayan sojoji suke yi ba,tare da farar shirt off shoulder ta zura ajikinta,ba ƙaramin kyau tayi ba,komawa tayi gaban dressing mirror ta ɗauki turarenta tabi ko'ina na jikinta ta feshe shi,wuri ta samu saman chair ɗin da ke a front ɗin madubin,ribbom ɗinta ta ɗauko tare da zura shi a hannunta,yau taci alwashin saita ɗaure gashin kanta, da iya ƙarfinta na ƙarshe ta tattare gashin ta haɗo shi wuri guda,tare da zura ribbom ɗin ta ɗaure shi sosai,ya sauko a gadon bayanta,
  Murmushi ta saki tana kallon kanta acikin mirror ɗin kafin daga bisani ta miƙe tare da wuce wa gaban gadonta,within 15 mins ta kammala gyara bedroom ɗinta,komawa tayi tare da hayewa saman gadon,takai hannu ta ɗauko wayarta dake ajiye saman side drawer,   Wi-fi ta kunna nan take messages ɗin whatsapp dinta suka soma shigowa acikin wayarta,shiga whatsapp grp tayi na school ɗinsu,new student ne ke ta introducing ɗin kansu tare da pics ɗinsu,tunani ta soma yi bata da hoto ko ɗaya,gashi tana buƙatar pictures saboda ita ma tayi nata introduction din,   tana cikin wannan tunanin kiran junaid ya shigo wayarta,cikin sauri tayi picking tare da karawa a kunnanta,  Tun kafin tayi sallama yace"yunwa nake ji,"yana faɗin hakan ya katse kira,murmushi Sehrish tayi tare da cewa"shagwa6a66e kawai"  Ajiye wayar tayi saman pillow sannan ta miƙe tare da saukowa daga saman gadon,sam ta manta bata yafa mayafi ba,saboda saurin da take yi nata kai mashi tadawo don tayi pictures din,takalmi kawai ta zura a ƙafarta,sannan ta buɗe ƙopar ta fita,  A natse take tafiya hanyar kitchen ta nufa,wayam babu kowa a main palour ɗin da alama duk suna cikin bedroom ɗinsu wasu kuma sun fita,   Batare da 6ata lokaci ba ta haɗo mashi cornflakes tare da snacks acikin tray,kai tsaye ta wuce upstairs bedroom ɗinshi,  Tsayawa tayi tare da yin knocking ƙopar bedroom ɗin nashi,  daga ciki tajiyo muryarshi yana cewa"a buɗe take fa,just come in,"  a hankali ta tura door din tare da shiga cikin ɗakin nashi,  yana tsaye agaban mirror waist ɗinshi na ɗaure da farin towel da alama fitowarshi kenan daga wanka,   ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table din dake kusa da gadon shi,   Juyowa junaid yayi daga gaban mirror ɗin da yake,zuba mata ido yayi yana kallon bayanta,wandon jikinta ba ƙaramin fidda mata shape ɗin jikinta yayi ba,  takawa yayi a hankali ta bayanta ya tsaya sannan yakai hannunshi tare da ruƙo lallausan sumar kanta,a firgice Sehrish ta juya tana kallon shi,sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi yayi,  A hankali ta ambaci sunan shi"junaid"!  bai amsa mata kiran sunan shi da tayi ba,sai cewa yayi"reesh ina mayafin ki yake ne"?   Sai lokacin ta tuna cewa bata yafa komai ba ajikinta ta fito,   "Mantawa nayi ban sanya ba,"ta bashi amsa tana kallon fuskarshi,  "Kinyi kyau sosai,but pls kada ki ƙara fitowa haka batare da mayafinki atare da ke ba,"ya ƙarasa maganar cikin sanyin murya,  Har lokacin bai saki wutsiyar gashinta ba daga hannun shi,sai faman murza gashin yake acikin hannun shi,  Sakin gashin yayi tare da zagayawa da hannun shi ta bayanta,ya zame ribbom ɗin dake akanta,nan take sumar kan ta tarwatse abayanta,duk tana tsaye tana kallon shi batare da ta hana shi ba,   tura hannunshi yayi acikin lallausan gashin kan nata,wasa ya shiga yi mata dashi,ganin abun nashi ba mai ƙarewa bane yasa tace"junaid wai menene haka?kamar wata ƴar baby ka kama mun sumar kai sai murzawa kake yi,"   Murmushi yayi tare da cewa"kwarkwata nake son cire maki,don nasan baza a rasa su acikin kan nan naki ba,abunda baki sani ba su suke saki yawan mantuwa,"  Buge hannun shi tayi tana dariya tace"wlh ka 6aci da ƙarya junaid,bansan waya koya maka ƙarya ba,"  tayi maganar tare da wuce wa tana nufar hanyar fita daga ɗakin,cikin sauri yakai hannu tare da ruƙo nata acikin nashi yace"pls kada ki tafi,ki tsaya na kammala lunch ɗin mana,inyaso sai mu fita atare,    Batare da musu ba tace"bazan tafi ba amma zan fita daga waje,idan ka kammala sanya kayan saina shigo,"    ƙarasa maganar tayi tare da fucewa ta tsaya daga waje tana jiran shi, Shaf shaf ya kammala shirya wa cikin jeans da t shirt,sannan ya samu wuri daga gefen gadon ya zauna tare da kwala mata kira,   dawowa ciki tayi tare da takawa zuwa gefenshi ta zauna,
  "Sehrish inason magana dake,"
Yanayin yarda junaid yayi mata maganar da wata irin kasalalliyar murya yasa ta jin faɗuwar gaba batare da sanin dalilin hakan ba,     Cikin sauri ta juyar da fuskarta tana kallon cikin idanunshi tace"menene junaid"  ƙara matsawa yayi kusa da ita,fuskarsu ta kasance a kusa data juna,numfashinsu har harhaɗewa yake dana juna don ƙiris ya rage tsinin hancin shi ya ta6a nata,hakan ba ƙaramin tsorata sehrish yayi ba,tun da take arayuwarta bata ta6a ganin fuskar junaid da irin wannan yanayin ba batare da Murmushi ba,sam babu murmushin nan a fuskarshi,  Cikin en ina sehrish tace"..junaid wai menene haka?me yake faruwa ne"?  Lumshe kyawawan idanuwanshi yayi tare da sake buɗesu a hankali ya furta"I LOVE U REESH,I wanna be with u,for the rest of my life," in serious matter junaid yayi maganar,amma sai Sehrish ta fashe.da dariya kamar kamar me,   Mamakine ya kamashi ganin tana yi mashi dariya,  Miƙewa tayi daga saman gadon nashi tana ci gaba da yin dariyar,dakyar ta tsagaita tare da kallon shi tace"gaskiya junaid ka iya wasan kwaikwayo,wlh ni har gabana ya faɗi duk atunanina wani abun kirki ne ashe zolayar taka ce ta motsa,"  Hankali atashe junaid ya miƙe tsaye yana kallonta yace"reesh nifa ba wasa nake maki ba,inason bayyana maki irin tsananin son da nake maki ne,"   Muryarta ƙumshe da dariya tace"wlh junaid da ace kai actor ne acikin film ba ƙaramin ƙayatarwa zaka yi ba,saboda ka iya tsara wasan kwaikwayo,"   Tana kai ƙarshen maganarta,ta kama hanya da sauri ta fuce daga cikin ɗakin nashi tana ƙarashe dariyarta,  Jiki a mace junaid ya koma tare da zaunawa saman gadon,   jinjina kai yayi tare da cewa"tashin hankali!ashe irin kallon da sehrish keyi mun kenan!yanzu taya za'ae na bayyana mata irin yarda nake ji a game da ita?  Ya jima yana wannan tunnanin aranshi kafin daga bisani ya mayar da idanunshi akan cornflakes ɗin da ta haɗo mashi,.  A sanyaye yakai hannu tare da ɗaukar spoon ɗin dake acikin cup din,ya fara ɗebowa yana kaiwa bakin shi,
adai dai lokacin da Sehrish ke gabda shiga Corridorn da ɗakinta yake Sgr ya fito waya kare a kunnan shi,da alama waya yake yi,karaf idonshi ya sauka akan bayanta wanda lallausar gashin kanta ke baje har wurin ƙugunta,don bata maida ribbom din da junaid ya cire mata ba dama dakyar ta ɗaure shi ɗaxu,ƙarasa fitowa yayi slowly ya dafa handrail da hannunsa guda har lokacin yana amsa wayan da yake yi, yayin da blue eyes dinsa ke bin bayanta da kallo, ba komae ne ya ja hankalin shi ba face Army trouser din dake jikinta don ba ƙaramin kyau yayi mata ba dama kuma favorite color dinsa ne......
_💋Boss Bature💋_
Wuraren biyu na rana hossana tafarka daga dogon baccin daya ɗauketa,miƙewa tayi daga kwancen da take asaman sofa,sai faman hamma takeyi tana murza idanunta, a hankali ta ware idanunta tana neman Omar da bacci yayi awon gaba dasu,wayam tagani babu shi alamar ya tafi bataso hakan ba, dakyar ta iya tashi daga saman sofa din,tana tafiya a hankali saboda jirin da take ji,ga wata irin Yunwa dake cin ta,
Bedroom ɗinsu ta shiga,a nan ta samu jahad zaune saman darduma ta jima da kammala sallar Azhar,amma bata bar saman sallayar ba,tana zaune zugum tana tunanin duniya, Jin alamar tafiyar mutum yasa ta juyowa tana kallon hossana dake tunkarato, Ƙarasawa tayi wurin jahad tare da zuƙunnawa kusa da ita tace"jahad ashe ya omar ya tafi bai tashe ni ba,ko sallama ba muyi ba,"murya a kasalance ta ƙarasa maganar, murmushi jahad tayi tana kallon fuskarta tace"kada ki damu,in dae ya Omar ne zaki iya ganin shi da anjima ko da daddare ma," Ta ƙarasa maganar tare da cewa"ko kina jin yunwa ne?naga kina ta hamma" "E inaji sosai,'ta bata amsa, Jahad tace"Okey,yanzu nake shirin tashi na shiga kitchen in girka mana abunda zamu ci,amma kafin nan ki fara ɗaukar fresh milk a fridge sai ki haɗa da wani abu kisha,sannan in kin kammala kiyi sallah,gashi har time ma ya wuce,' amsa mata tayi da toh,sannan ta miƙe tare da fucewa daga bedroom ɗin, Murmushi jahad tayi tare da cewa"nan ba da jimawa ba zamu sha bikin Amarya hossana tare da bride ɗinta ya Omar,"
Yunƙurawa tayi tare da miƙewa daga saman sallayar, hannu takai zata cire hijabin jikinta, nan take ta tunano da maganar da mahaifiyarsu ta ta6a yi masu a lokacin da suke tare da ita, "Burin da nake dashi kafin nabar duniya Allah ya nuna mun ranar Aurenku,kamar yarda na haife ku arana ɗaya haka nakeso na aurar daku ku duka ukun arana ɗaya kuma a lokaci ɗaya,zan cigaba da yi maku addu'a Allah ya baku mazaje nagari,"
Cikin sauri jahad ta ƙarasa cire hijabin tare da ajiyeta nan saman gadonsu,sannan cikin sauri ta fito cikin falon anan tasamu hossana zaune saman 3 seater hannunta ɗauke da sinkin bread tare da fresh milk sai cusawa abaki takeyi tana haɗawa da madarar, jin alamar tafiyar mutum yasa ta ɗagowa tana kallon jahad dake tunkarota, Ganin yanayinta yasa hossana cewa"jahad meya faru naga kamar kina cikin damuwa"? jiki asanyaye jahad tace"hossana mun manta ba muyi ma Ya Omar maganar SEHRISH ba!banji daɗi da muka manta da batun nemanta ba,baiwar Allah bamusan wani hali take ciki ba," cike da damuwa Jahad ta ƙarasa maganar tare da samun wuri saman hannun kujera ta zauna, Nan take yanayin hossana ya canza,lokaci guda taji komai ya fita ranta, ba don komai ba sai don tunawa da Sehrish, murya na rawa ta soma cewa"inason ganin sehrish sosai jahad, zan sanarwa ya Omar ya nemo mana ita,bazan ƙara mantawa ba insha Allah," "Nima bazan manta ba, da zarar yazo zamu sanar dashi,". a cewar jahad, Daga haka ta miƙe tare da wucewa kitchen, ********************** Wuraren ƙarfe biyar na yamma,motar sofwan ta shigo layin gidan,tun a bakin Gate security guards suka tsayar da motar tasu,kamar wasu zakuna haka sojojin suka tunkari motar shi,hankali tashe ya juya tare da kallon hayaam dake manne ajikinshi tana bacci ta aza kanta asaman kafaɗarshi,jikinta na sanye da dogon hijabi har ƙasa ta sanya niƙab a fuskarta,kamar wata Malamar Addini,  da ƙarfi ya ambaci sunanta"Hayaam!!Hayaam!!"har cikin kanta ta dinga jin kiran nashi,daƙyar ta iya buɗe baki tare da cewa"wai menene"?   "Mun ƙaraso gidan fa,dan Allah ki tashi kiyi ma waɗannan dakarun bayani,nifa a tsorace nake dasu,".  guntun tsoki taja ta janye jikinta daga nashi,sannan tace"haba sofwan bafa yau ka fara zuwa gidan nan ba,menene abun tsoro aciki,sai kace ba namiji ba,"   wani irin kallo yayi mata tare da cewa"ba yau na fara zuwa gidan ba,amma ae ko lokacin da na ta6a zuwa ɗaukarki a iya bakin babban gate ɗin nan nake tsaya......' Bai ƙarasa maganar ba,saboda bugun glass ɗin motar daya ji anyi daga waje,muryar wani basamudan soja ce ta karaɗe kunnansu da cewa"Oya wind down ur glass,"  A hanzarce Sofwan ya sauke glass ɗin motar,yana ta faman mazurai kamar wani mara gaskiya,   tambayarsu yashiga yi"Su wanene ku!kuma wurin wa kuka zo,?   Murya na rawa sofwan yashiga nuna hayaam yana cewa"am..yalla6ai..itace zatayi jawabi,bani ba,"   girgiza kai hayaam tayi tare da kai hannu ta ɗauko purse ɗinta dake ajiye saman laps ɗinta,cikin sauri ta ciro wayarta tare da ruƙe ta a hannunta,nan fa tashiga tunanin wa zata kira acikinsu don yayi masu magana subarsu su shiga,  "Madam ke muke jira,bama son 6ata lokaci and remove dat thing u covered ur face with" muryar sojan ce ta sake katse ta,yana nuna nikab din da yatsansa.  Tuni taji zufa ta soma karto mata a fuskarta da sauri tasa hannu ta cire nikab din,contact ɗinta tashiga tare da dialing numbar Kanal Yousof,cikin rashin sa'a wayar tashiga ringing amma ba'a ɗaga ba almost 3 times,cikin sauri ta kuma lalubo numbar Junaid,har ta gama ringing junaid bai ɗaga kiran ba,da alama shima baya kusa da wayar tashi,  Hankalin Hayaam ba ƙaramin tashi yayi ba,dama su biyu kawai take da numbarsu a wayarta gashi duk sunƙi ɗaga kiran,    ganin zata 6ata masu lokaci yasa sojoji bashi umarnin yaja motar shi yabar wurin,     Wani irin ƙululun baƙin ciki ne ya tokare mata maƙoshinta,ba ƙaramin 6acin rai tashiga ba,amma babu yarda zatayi dolenta su koma,  Sofwan na ƙoƙarin tashin motar su bar wurin,sai ga motar Sgr ta kunno kai daga cikin babban gate ɗin gidan, Zuba ma motar ido sukayi gaba ɗayansu musamman hayaam da take jin cewa sauƙi yazo mata,don tasan kowanene zai bada Umarnin abarsu su shiga ciki ne, "Sir I think something is wrong here," Amstrong ne yayi mashi magana, Don haka sgr ya bashi command ɗin ya tsayar da motar tasu don jin meke wakana, A daidai saitin motarsu Hayaam Amstrong ya dakatar da tasu motar,sannan a hankali a wani irin slow glass ɗin motar suka soma saukewa atare, Waro ido waje hayaam tayi nan take zuciyarta tayi wani irin bugun bazata,ba don komai ba sai don ganin mutumin da tajima bata sashi a idonta ba,wato abun harinta, A hakimce yake zaune a back seat ɗin motar,ba ƙaramin kyau yayi ba yayi wani fresh dashi,musamman wankan daya ɗauka,Red shirt ce ajikinshi,tare da black trouser,
launin rigar ya ƙara fito da wannan hasken fatar nashi sosai fari sol kamar ka ta6a jini ya zuba,sumar kan nan kuwa tana ɗaure abayanshi,yayin da idanunshi ke lumshe tamkar mai jin bacci, Cikin sauri sojan ya ƙarasa inda yake tare da buga ƙafa ya sara mashi sannan yace"Sir,wasu baƙin fuska ne ke son shiga cikin gidan,kuma basu da shaidar da zamu iya barinsu su shiga cikin gidan,shiyasa muka dakatar dasu, kusan 5 mins bai buɗe bakin shi ba,babu alamar cewa zaiyi magana ma,kowa yayi tsit yana jiran jin ta bakin shi,kai har sai da sojan ya fidda rai da zaiyi magana sannan Calmly yace"What about asking their details? Sojan yace"ban tambaye su wannan ba,amma bari naje na tambaye su," juyawa yayi tare da ɗan matsawa kusa da motar Sofwan yace"yana buƙatar bayani a wurinku,ku gabatar da kanku don yasan su wanene ku," jin shiru hayaam bata ce komai ba yasa sofwan juyawa zaiyi mata magana,sakin baki yayi yana kallon ikon Allah,gaba ɗaya hankalinta ya tafi kan Sgr,ba ƙaramin tafiya da imaninta yayi ba, Nan take yaji wani irin kishi ya rufe shi,acikin ranshi yace"haba no wonder,sai yanzu na gane dalilin dayasa hayaam ta haukace mun akan wannan Namijin,mutum kullum ƙara kyau yake yi,kamar shi yayi kanshi don kyau,muddin irin wannan na yawo agari tofa bazamu ta6a yin kasuwa ba," "Don't waste our time"! muryar sojan ce ta katse mashi tunanin nashi, Cikin sauri yace"Hayaam!magana fa ake maki,kiyi masu bayanin alaƙarki da mutanen gidan," Ajiyar zuciya hayaam tasaki,sannan anatse ta soma magana"ka sanar dashi cewa ƙanwar matar yayansu ce hayaam," Juyawa sojan yayi tare da komawa wurin motarsu Sgr yace"yalla6ai tace ita ƙanwar matar yayanku ce kuma sunanta Hayaam," a hankali sgr ya ɗan buɗe idanun shi, Hakan yasa Hayaam dake hangen shi ta soma washe baki,ba don komai ba sai don ita atunainta sgr ya gane jawabin da Sojan yayi mashi, Cike da ƙasaita yace"sam wannan bayanin bai kwantamin araina ba!infact,I don't know any person wit dat name hayaam or what...,ban ta6a jin sunan ba,Sergeant!!a sallamesu su koma,nd add more security!!" Yana ƙarasa maganar tashi,glass ɗin motar ya ɗaga sama sannan a hankali Amstrong ya tashi motar,anatse yake driving ɗinshi har suka bar wurin gaba ɗaya, dariya ce ƙumshe abakin sofwan amma ya gaza fitar da ita saboda tsoran 6acin ran hayaam,sam yaƙi yarda su haɗa ido da ita,saboda tsoran karta huce akanshi, Kamar ta aza hannu akai ta fasa ihu haka taji,zuciyarta har wani boiling take tana burning saboda tsantsar 6acin rai da baƙin ciki,ashe duk haukan nata ma abanxa ne Sgr baisanta ba,baisan wacece ita ba duk zuwan da takeyi gidan a lokacin baya, daƙyar sofwan ya daure ya cije tare da ce mata"mu juya ko"? A tsiwace tace"bansani ba!!mtswww" ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki, Can kuma tace"babu inda zanje wlh,kota tsiya kota arziƙi wlh saina shiga cikin gidan koda kuwa zamu kwana anan ne,don bazanyi tafiyar banza ba," Cikin sanyin murya sofwan yace"Hayam ki bi komai a hankali!su fa waɗannan mutanen da kika gani ba kamar sofwan ɗin da kika raina bane,muddin kikace zakiyi masu rashin kunya wlh dukan tsiya zaki sha,kakkarya ƙasusuwan jikinki zasu yi,kuma kada kiyi tunanin cewa zakiyi masu kwarkwasa ko kija hankalinsu da kyanki,don wlh babu ruwansu da mace,su ba mayin mata bane irina,so u ave to be very careful," ya ƙarasa maganar fuskarshi ɗauke da dariya,don yau ba ƙaramin nishaɗi yasamu a wurin Sgr ba,ba ƙaramin burge shi yayi ba yanayin acting ɗinsa babu wasa aciki,Namijin ne dae na gaske, Tsuke fuska hayaam tayi,harara ta watsa mashi tare da jan dogon tsoki batare da tace komai ba, tunani tashiga yi akan yadda za'ae su shiga cikin gidan,nan take zuciyarta ta bata shawarar ta kira Aunty babba ta sanar mata,tana ƙoƙarin kiran nata sai ga Motar Haroon ta shararo da gudun gaske cikin layin, tunkan ya ƙaraso wurinsu ya rage gudun motar tashi,sai da yazo dai dai bakin gate ɗin gidan sannan yayi parking ɗin motar tare da sauke glass ɗinta,da alama yasha ya bugu har takai mashi karo,saboda yarda idanunshi ke ta faman rurrufewa sunyi luhu luhu dasu, dakyar ya iya tsayar da idanunshi akan Motar sofwan,nan take suka hango mashi kyakkyawar fuskar hayaam,ɗaga murya yayi tare da kwala ma sojojin kira,cikin sauri suka tunkari motar tashi tare da sara mashi, Yatsina fuska yayi ya kallesu a wulaƙance yace"Meke faruwa anan ne?su wanene acikin motar can"? ɗaya daga cikinsu ne yace "Yalla6ai,ba mu san ko su wanene ba,mun hana su shiga ciki ne saboda basu da shaidar da zamu iya barinsu shiga cikin......' Tunkan ya ƙarasa maganar haroon ya katse shi da cewa"Saboda gidan na ubanku ne!wai ma uban wanene ya kafa wannan dokar ta hana mutane shiga cikin gidan nan ne!"?ni banga amfanin takurawa mutane ba,idan tsaro ne ba Allah ke tsarewa ba mtswwww, Shiru sojojin sukayi suna sauraron faɗan nashi kamar ubansu,hayaam kuwa tunda taji yana zazzaga masifa yasata ɗagowa tana kallonsu,ganin yarda yake banbamin bala'e akan an hanasu shiga yasa ta soma sakin murmushin jin daɗi, Sofwan kuwa jinjina kai yayi tare da cewa"ikon Allah,kowanene wancan jarababben da yake ta faman tada jijiyoyin wuya,da alama ba ƙaramin hatsabibi bane,' Cikin lallashi sojojin suka haɗa baki wurin cewa"Sorry sir!Allah ya huci zuciyarka!" Hura hanci haroon ya shiga yi kafin daga bisani yace"Ban amince abarsu su shiga da motar da suka zo da ita ba!shi namijin yaja motar ya koma gidan ubansa,ita kuma budurwar kuce mata tashigo daga cikin motata na sauke ta cikin gidan,idan har bata amince ba to su tattara su koma inda suka fito,". "An gama yalla6ai,"atare suka amsa mashi,sannan suka juya tare da tunkarar motar sofwan,tun kafin su ƙaraso hayaam ta buɗe motar jiki na rawa ta fito saboda taji duk bayaninshi acikin kunnanta, Hankali tashe sofwan yace"Hayaam ni kuma awani matsayi kika ajiye ni ne"? Batare da ta waigo ta kalleshi ba tace"Zan kiraka a waya,in nasamu lokaci,ta bude back door ta dau jakanta" Jiki asanyaye Sofwan yaja motar,yayin da zuciyarshi ke cike da 6acin ran abunda tayi mashi,yasha wahalar kawota,amma ko godiya babu balle yayi tunanin sake samun wani abu awurinta,tuni yaji hawaye sun cika mashi idanunshi,tabbas hayam ta cuce shi sosai ba ƙaramar wahala yasha akanta ba,duk don ya mallake ta amma gashi nan ya tashi a tutar babu!dashi da Zero basu da bambanci ƙwara ma zero yana da amfani wurin yin lissafi,
Shu'umin murmushi haroon ya saki lokacin da hayaam ta Æ™araso jikin motar tashi,hannu tasa tare da buÉ—e gaban motar tashiga ta zauna tare da rufe motar,sannan ta mayar da idonta akan haroon daya zuba mata ido ko kyaftawa baiyi, ita kanta saida tasha jinin jikinta da ganin irin zubin shi,cikin sanyin murya tace"Sannu ko," É—an ta6e la66ansa yayi tare da cewa"Yawwa,amma naga baÆ™uwar fuska ina buÆ™atar Æ™arin haske," Cike da kwarkwasa tace"Sunana Hayaaam,ni Æ™anwar Aunty laila ce da kuma Aunty Amani," murmushin gefen fuska haroon yasaki kafin yace"Wow,no wonder that's why naga kamanceceniyar ki da Aunty laila,ashe ke Æ™anwarsu ce,amma fa am really sorry game da abunda ya faru,securities É—in gidan nan basu son ciwon kansu ba,in ba haka ba taya zasu ga mace kamila irinki sanye cikin dogon hijab kuma su hanaki shiga? Sunnar dakai Hayaam tayi tana faman sakin shu'umin murmushi,aranta tace"dalilin dayasa na sanya dogon hijabi kenan saboda nasan cewa kowa zaiyi tunanin ni mutuniyar kirki ce,hmmmmm basu san cewa da fuska biyu nazo masu ba," (Rashin sani yafi dare duhu!hayaam batasan da wa take magana ba," "Kada na cika ki da surutu,bari nashiga dake cikin gidan," Ya faÉ—i tare da jan motar da gudun gaske ya shige cikin babban gate din gidan (Finally hayaam ta samu nasarar shiga cikin gidan)Â
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
Abban sojoji part 2 â? Bayan Haroon yayi parking É—in motar,hayaam tayi mashi godiya tare da É—aukar bag É—inta,ta fito daga cikin motar sannan ta nufi cikin gidan,  Shu'umin murmushin nan nashi ya saki yabi ta da kallo tare da cewa"Nifa bana abu don Allah,kowani tsautsayin ne da Æ™addara suka kawo ta cikin gidan nan!Allah yasa ta kwanan mana biyu...." ya jinjina kai tare da cewa "tsuntsu daga sama gasasshee!"ya Æ™arashe maganar tashi tare da zura hannun shi cikin aljihun jeans É—in dake a jikinshi,wayar shi ya ciro tare da duba screen É—in, missed calls aka mashi da wata hidden number,    shiru yayi yana tunanin taya zai bi kiran saboda kira ne mai mahimmanci a wurin shi gashi dole sai in shi mai 6oyayyiyar numbar ne ya kira ka,  Yana cikin wannan tunanin sai ga kiran ya sake shigowa,cikin sauri yayi picking call É—in tare da kara wayar a kunnan yana jiran jin me za'a sanar dashi  Wata irin muryace ta irin hamshaqan matan nan waÉ—anda suka ji duniya ta soma magana"Haroon!kana shirin jamin bala'e ko?meyasa ka fiye shiririta ne?ko kamanta plan É—in mu ne"?   nan take haroon yashiga en ina murya na rawa yace"ban manta ba,inaso nabi komai a hankali......'bata bari ya Æ™arasa maganar ba ta kwatsa mashi tsawa"Ya isa Haka! kasani wlh akanka bazan bari nayi gangancin rasa damar da nake da ita ba!haroon zaka iya rasa ranka muddin kace zaka kawomin wasa acikin lamarina!kai kasan wacece NI!bani da imani,"  Wata irin zufa ce ta soma gangaro mashi daga cikin sumar kanshi,lokaci guda duk yabi ya rikice yashiga zazzare idanu,   sautin dariyarta ce ta karaÉ—e kunnan shi,tsagaitawa tayi da yin dariyar sannan ta sassauto da muryarta wurin cewa"Am sorry fa,na tsorata ka ko? Nannauyar ajiyar zuciya haroon ya saki tare da cewa"Yanzu me kike so ayi ne,just command me zanyi maki koma menene,"!   "So nake ka kashe JUNAID!saboda shikaÉ—ai ne hanyar da zanbi wurin Æ™untata masu,banaso junaid ya rayu,muddin yana araye toh farin cikin gidan zai cigaba da wanzuwa ne,ni kuma abunda bana so kenan!,"     girgiza kai haroon yashiga yi tare da cewa"Kiyi haÆ™uri wannan ne karo na farko da kika ban umarni na musa maki tunda na fara maki aiki!junaid is innocent I can't kill him,zan iya kawar maki da duk wanda kikeso acikin gidan nan,Amma banda junaid!banda Abbana,Rafayet kuma yafi Æ™arfina banda wata hanyar da zan iya cutar dashi,sai ma in jefa kaina cikin matsala!"   fashewa da dariya tayi tamkar zata fasa screen É—in wayar,bayan ta tsagaita da yin dariyar taci gaba da magana"kasan koni wacece,kasan kuma abunda zan iya!idan har bazaka iya kawar mun dasu ba,to ni zan iya kawar dasu ta cikin ruwan sanyi,Haroon u must do what i command you!if not i wll expose ur secrets,kai kasan me zai biyo baya,ko ka kashe junaid ko kuma ni in kashe maka rayuwa gaba É—aya...!!!!   Waro ido waje Haroon yayi yana sauraronta,  Cigaba da magana tayi"Maganar videon su Twins daka É—auka,nasan ka goge na wurinka,amma akwai wani a hannuna,zanyi amfani dashi wurin tarwatsa zuciyar mahaifin nan nasu,da kuma masoyina Rafayet!inason ganin tashin hankalin shi sosai...."  A tsorace haroon yace"Kada ki kuskura ki saki bidiyon nan!in ba haka ba asirina zai tonu ne!kuma kina sane da cewa,muddin asirina ya tonu to ke ma kin gama yawo!!atare zamu fuskanci sakamakon mu,zasu kamo ki ne aduk inda kika 6uya!!"    ya Æ™arasa maganar yana faman sakin huci yayin da idanun shi sukayi jawur saboda tsananin 6acin rai,   fashewa ta kuma yi da wata irin mahaukaciyar dariya kafin ta tsagaita da yin dariyar tace"Haroon!Iska bata ruÆ™uwa!domin ni tamkar iskar nake,kada kamanta ina amfani da baÆ™aÆ™en aljanu wurin gudanar da aiki na,kuma zanyi amfani dasu ne wurin ganin na tarwatsa dukkan zuri'ar Salahuddeen Hussein!wannan alwashi ne na É—auka,rai uku masu mahimmanci suka kashe mun,ni kuma rayuka zan É—auka!don bana yafiya arayuwata!"  Shiru yayi bai ce komai ba kusan minti biyar, sam baison wani abu ya samu abbanshi shi kaÉ—ae yafi ji sannan yace"Maganar yaran nan fa?su kuma ya zakiyi dasu?   "Inaso saina fara sanya soyayyarsu acikin zukatan Æ´an uwansu sosai,saboda inaso inyi amfani da wannan damar ne wurin Æ™untatawa dukkan wani jin daÉ—i na zuri'arsu,kamar yarda suka Æ™untata ma tawa zuri'ar,"    Jinjina kai haroon yayi kafin ya kuma cewa"Yanzu menene plan É—inki"?   Wannan karan anatse ta soma magana"plan É—ina shine kawar da junaid,dalilin dayasa nakeson kawar da junaid shine!sihirina bazai ta6a tasiri akan Rafayet ba har sai an samu lagwanshi,kuma ba kowa bane lagwanshi ba fa ce Junaid,da zarar ya rasa junaid zaiyi sakaci da ibadarshi hakan zai bani damar yin aiki akanshi,kuma shi ya kasance Bugun zuciyar family É—insu inaso na É—anÉ—ana masu raÉ—aÉ—in rasa mutumin daka kwallafa rai akansa!sannan maganar bidiyon nan zan sake shi a social media kowa ya gani,daga zarar hakan ta faru nasan cewa Martabar family É—insu da kuma Æ™imar da suke dashi a duniya gaba É—aya zasu zube,kowa zai tsani zuriyarsu duk wata daraja da suke dashi a idon duniya zata tashi abanza ne!ni kuma hakan nakeso,kafin na saki bidiyon inaso kayi amfani da kuÉ—in da suka baka wurin barin Æ™asar,ka koma malaysia da zama,na shirya maka komai najin daÉ—in rayuwa acan,giya da mata har saika gaji dasu,"   shu'umin murmushin nan nashi ya saki aranshi yana ayyana irin rayuwar da zaiyi acan cikin daular da aka shirya mashi,nan take yaji cewa zai iya aikata komai takeso,  Sam yama manta da waya yake yi saboda tsabar farincikin da ya ziyarce shi,mayar da bayanshi yayi a jikin seat na motar yana cigaba da sakin murmushi,   "Kana jina kuwa,"muryarta ce ta ratsa kunnan shi,hakan yasa ya dawo daga dogon tunanin daya tafi,   Sai da ya samu natsuwa sannan yace"Naji duk abunda kika ce,hakan yayi mun sosai,musamman da kika ambaci giya da mata,sai naji wani nishaÉ—i araina dama irin rayuwar da nakeson yi kenan,amma akwai wata shawara da nakeson baki,in ba damuwa,"  Tace"ina sauraronka haroon," "Ga me da bidiyon tsaraicinsu twins,kada ki sake shi a social media pls,sun riga sun biyani kuÉ—i kamar yarda na buÆ™ata,shiyasa nakeso ayi masu sassauci,mutun biyu kawai nakeson suga bidiyon nan Abban su da kuma wannan ifiritun sarkin jin kan nan,sannan maganar kashe junaid nasan ban isa na hanaki aikata abunda kika yi niyya ba,amma abunda nakeso ki bar komai a hannuna,ni ko ke babu wanda zai kawar dashi!kiyi amfani da sihirin ki kawai ta cikin ruwan sanyi yarda babu wanda zai zarge ni!!"     Dariya sosai tayi da alama shawarar Haroon tayi mata,   Sannan tace"daga yau komai zai fara"!!! murmushi haroon ya saki tare da cewa"Allah yaba mai rabo sa'a"  daga haka su kayi sallama ya kashe kiran,kasa fitowa daga cikin motar yayi ba don komai ba sai don kasalar da yaji ta baibaye shi,fuskar junaid kawai yake gani acikin idanun shi,😢
  ****************** Lokacin da Hayaam ta shiga cikin gidan da sallama abakinta tashiga main palour ɗin,tsayawa tayi da tafiya ganin babu kowa acikin babban falon,takun tafiyar da taji ne yasa ta juyawa ta gefen hagunta tana kallon mai tafiyar,bakowa bace face Sehrish sai faman sauri take yi don ta shiga kitchen,har yanzu shigar ɗazu ce a jikinta,amma ta yafa mayafi ajikinta tayi rolling ɗinshi,   ta wutsiyar idonta ta hangi mutum hakan yasa ta dakata da yin tafiyar ta ɗan juya don taga wanene,karaf idonta suka haɗu akan na Hayaam,cike da mamaki take kallonta,batasan ko wacece ita ba,amma ganin hasken fatarta yasa tayi tunanin ko ƴar uwarsu Junaid ce,   tunkararta sehrish tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta ƙarasa inda hayaam take,tunkan sehrish ta ƙaraso zuciyar Hayaam ta shiga bugu,don ta gane cewa itace Ƴar aikin da Aunty laila take bata labarin cewa tana rayuwa acikin gidan,yarinyar da Abbansu ya mayar da ita ɗiyar shi,   fuska ɗauke da murmushi sehrish tace"Sannu da zuwa,"   hayaam tace"yawwa,ina mutanen gidan nan?naji shiru ko ba kowa ne"?  sehrish tace"duk sun fita,amma junaid da Fawan suna acikin bedroom ɗinsu,sai Aunty azmee tana acan cikin kitchen,   Jinjina kai Hayaam tayi har ta buɗe baki zata kuma cewa wani abu,sai ga Azmee ta fito daga cikin kitchen ɗin,ganin Hayaam yasa ta soma Sakin fara'a kamar gonar auduga,cikin sauri ta tunkaro wurinsu tana cewa"Wata sabon gani!Anya ba idona ne ke nuna min badaidai ba?  dariya hayaam tayi tare da wuce sehrish ta tunkari wurin Azmeen suka rungume juna,  ɗago da ita azmee tayi daga jikinta tana cewa"Oh ni Hayaam!ashe dama zan sake ganinki a duniyar nan?gaskiya kun yada zumunci!ina ji tun bikin Amani yaushe rabon ki da gidan nan!   Sai faman washe baki Hayaam takeyi ba don komai ba sai don sanin cewa Azmee zata kar6eta hannu bibbiyu kuma zata goya mata bayan zama acikin gidan,     "Kai Aunty azmee,nafa zo bayan bikin Amani kin dai manta ne,gaskiya nayi missing ɗinku sosai,shiyasa ma nace dole nazo naganku,"  Magana takeyi amma hankalinta na akan Sehrish,dake tsaye tana sauraronsu,   Azmee tace"mu ma munyi kewarki sosai,amma dai bada wuri zaki koma ba ko?don bazan bari ki tafi batare da kin zauna mana ba,".   Anzo wajen da tafiso nan fa tashiga washe baki tana cewa"ae Aunty azmee har sai kun gaji dani,in dae ba ku kuka kore ni ba,amma ni ina nan ba inda zanje,"  murmushi Azmee tayi tare da cewa"Ae bama wanda zai kore ki hayaam,".  taƙarasa maganar tare da mayar da idonta kan sehrish tace"wannan Hayam kenan!ƙanwar matar yayansu ishaq,da kuma Amani wadda tazo ran nan harna gabatar maki da ita"?  wani irin bugu taji zuciyarta tayi mata ba don komai ba,sai don tuna kalaman Amani da tayi in har wannan takasance ƙanwarta ce,lallaikam akwai matsala,  da ƙyar sehrish ta ƙaƙalo murmushin yaƙe sannan tace"Allah sarki,ashe kanwarsu ce,naga suna yanayi da Aunty amanin,"   ta6e baki hayaam tayi jin abunda sehrish tace,   ruƙo hannunta Azmee tayi tare da cewa"Kada na cika ki da surutu,mu shiga ciki ki huta don nasan ba ƙaramar gajiya kika kwaso ba,"  atare suka wuce ciki da Azmeee,zuru sehrish tayi ita dai tun da tayi arba da Hayaam taji sam bata kwanta mata arai ba,kama hanyar shiga kitchen ɗin tayi tana cikin tafiya taji muryar junaid ya ambaci sunanta,   dakatawa tayi da tafiyar sannan ta ɗan juya tana kallon shi,fuskar nan tashi a yamutse alamar daga bacci ya tashi,sai faman sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi yake,   acikin ranta tace"Shagwa6a66e halan yunwa yake ji ne,"   ƙarasa saukowa yayi daga saman stairs ɗin kai tsaye wurinta ya nufa,     Lokacin da ya ƙaraso inda take tsaye muryar shi cike da kasala yace"Reesh har yanzu Abbanmu bai dawo ba"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh,tamkar zaiyi kuka yace"dama nasani,tunda wannan abokin nashi yazo mai farin gemu,nasan cewa ba zai barshi ya shigo ciki ba,yana can yaja shi sun tafi yawo gidan abokanansu,"  maganar shi ba ƙaramin dariya taba Sehrish ba,   "Amma dae baka da mutunci junaid,abokin abban naku ne kake ce ma mai farin gemu"?   turo baki yayi cike da shagwa6a yace"eh mana,farin gemu gare shi,ae ba ƙarya nayi ba, Ya ƙarasa maganar da cewa"nidai yanzu ki taimakamin bana jin daɗin bakina farfesu nakeson sha,"   bin lips dinshi tayi da kallo yarda yake magana ashagwa6e,sunyi dark red dasu kamar wanda yashafa jan baki,      Tunanowa tayi da maganar shi ta ɗazu da ya furta mata kalmar so,acikin ranta tace"yanzu ace dagaske junaid sona yake yi,tabbas zan iya haƙura da wanda nakeso don na aure shi,saboda ba ƙaramin tausayi yake bani ba,komai nashi kuma yana burgeni,sai dai bansan ya rayuwar auren mu zata kasance ba,yarda yake shagwa6a66en nan ba ƙaramar wahalar shi mace zata ci ba,wannan rainon shi ma zanyi kenan?kullum sai ya tashi tsakar dare da kukan rigima,don haka sai in tanadi feeder da zan rinƙa haɗa mashi madara yana sha.......' Kasa ƙarasa zancen zucin nata tayi saboda dariyar data zo mata,tafin hannunta tasa tare da rufe bakinta,ta ƙumshe dariyar don karta fito da ita,junaid ya gani ranshi ba ƙaramin 6aci zaiyi ba,  Harara ya watsa mata tare da cewa"meyasa kike kallona ne?kuma kinsa hannu kin rufe mouth ɗinki da alama baki da gaskiya sehrish,"   kafin tace wani abu,sai ga haroon ya faɗo cikin main palour ɗin,jin takon tafiyar shine,yasa gaba daya suka juya suna kallon shi,adaidai lokacin shima ya ɗago da idanunshi kai tsaye suka sauka akansu, Nan take sehrish taji gabanta ya faɗi rass,saboda ta tsani ganin shi acikin idanunta,  da alama wurinsu yake tunkarowa,murmushi junaid ya shiga sakar mashi yana cewa"Ya haroon sannu da dawowa,"    "Yawwa baby junaid,me kuke yi anan ne"? .  yayi maganar yayin da yake ƙarasawa wurinsu,   sunnar dakai sehrish tayi batare da ta ɗago sun haɗa ido dashi ba,  Junaid yace"muna magana ne da sehrish,"  ɗan ta6e bakin shi yayi kafin yace"okey,ka wuce ciki inason magana da ita,"   batare da musu ba junaid ya wuce cikin palourn tare da samun wuri saman 3 seater ya zauna,    ja da baya sehrish tayi aɗan tsorace tana jiran jin mai zai ce,   "Kinyi kyau sosai,shigar jikin ki tayi mun,"ya fadi yana faman bin wandon jikinta da kallo,   Shiru tayi mashi batace komai ba,jira kawai take yayi ƙoƙarin ƙure mata ta watsa a guje,   "dama nasan ba zaki ce komai ba,hakan yayi mun sosai,bakomai ne yasa nace inason magana dake ba face don in baki wata shawara mai kyau,sai dai bansan ko zaki ɗauka ba  Sai lokacin ta ɗago da idanunta tare da kallon shi tace"wata irin shawara kenan?kada kayi tunanin cewa zan ɗauki shawarar ka,saboda kai ba abun yarda bane!nagama yarda da duk wani abu da zai fito daga wurinka,burinka kawai ka cutar dani!"   hannunshi ya zura acikin aljihun shi tare da ƙara matsawa dab da ita yace"shawarar ba akanki bane!akan junaid ce!   daram!!taji gabanta ya faɗi a ɗan rikice take kallon shi,   "Nasan tunda na ambaci sunan junaid,yanzu zaki so ki saurari me zance,don na lura ba ƙaramin jinshi kike yi ba,"  Murya na rawa sehrish tace"me...me..kake son cewa ne agame da junaid?me junaid yayi ne?    Maimakon ya bata amsar tambayarta sai cewa yayi"ran nan nayi maki ƙarya na cewa ni shaiɗanin aljani ne,wannan maganar ba gaskiya bace,abunda ya faru shine akan idona Omar yashigo cikin falon nan kai tsaye naga ya wuce upstairs sai raina ya bani cewa dole zai ji sautin kukan ki,kasancewar part ɗinshi dana sgr basu da tazara sosai a tsakaninsu,maganar cewa ni na shaƙe maki maƙoshinki alokacin da kika zo ambaton sunana agaban Marshal Omar shima duk ƙaryace,bani nayi maki hakan ba,kawai nayi guessing ne kuma da alama na canka dai dai,nasan kin tsorata alokacin kuma kinyi tunanin cewa ni ba Mutum bane,don haka inaso kisa aranki cewa Ni haroon cikakken mutum ne kamar kowa,"yana ƙarasa maganar tashi yasa ƙafa zai wuce part ɗinsu, ..cikin sauri sehrish tace"ka manta baka ban shawarar da kace zaka bani ba,"   dakatawa yayi da tafiyar batare da ya juyo ba yace"ku dage da addu'a," yana fadin hakan yasa kai ya wuce ciki,   Tsayawa tayi cike da zullumin maganar haroon nacewa su dage da addu'a,tana cikin wannan yanayin muryar Azmee ta katse ta da cewa"Sehrish!tsayuwar me kikeyi anan ne?nayi tunanin zan zo na same ki a cikin kitchen,'  cikin sauri sehrish ta nufe ta,tana cewa"yanzu nake ƙoƙarin shiga kitchen ɗin,wani abune ya ɗauke mun hankalina,"   Atare suka shiga kitchen ɗin,batare da 6ata lokaci ba suka soma aikace aikacen girke girken nasu kamar yarda suka saba,     Tun bayan da azmee takai hayaam ɗaya daga cikin bedroom ɗin da suka saba ajiye baƙi insun zo,zame hijab ɗin jikinta tayi,wata ƴar short gown ce ajikinta daidai guiwarta,kai tsaye toilet ta faɗa,bayan wasu ƴan mintina sai gata ta fito waist ɗinta ɗaure da towel,sai lokacin ta tuna cewa ashe tabar trolley ɗin kayanta acikin boot ɗin motar Sofwan,yanzu dole ta neme shi ko don ya kawo mata abunta,   ƙarasawa tayi tare da hayewa saman gadon ta zauna,sannan takai hannu tare da ɗauko purse ɗinta da ta ajiye asaman gadon tun shigowarta tare da Hand bag ɗinta,    wayarta ta ciro anan taga missed calls na Aunty babba har kusan uku,  Murmushi ta saki tare da bin kiran nata,wayar na fara ringing Aunty babba ta ɗaga,.   kara wayar a kunnanta tayi tare da cewa"Auntyna takaina!yanzun nan naga missed calls ɗinki,banji ma da fitowa daga toilet ba,  on the other hand aunty babba tace"kin isa gidan ne!"?  Hayaam tace"eh,yanzu hakama gani asaman gadona inaso nayi bacci don na rage gajiyar dake ajikina,amma fa aunty nasha wahala kafin nasamu shiga cikin gidan nan!"   Aunty babba tace"wahala?kamarya kenan?    Nan hayaam ta kwashe duk abunda ya faru a wurin shigowarsu cikin gidan ta sanar mata,   uban tsoki aunty babba ta saki tare da cewa"Ke kika ban haushe wlh!taya zaki tsaya yi masu kwatance cewa ke ƙanwa tace?to menene alaƙar dake tsakani na dasu ne da har zasu shaidaki!tun a lokacin yakamata ki kirani awaya sai inyi ma wani magana daga cikin gidan akan yayi masu magana su barki ki shiga,amma don kince hayaam ƙanwar matar yayansu,to koni nan da kike gani Sgr baisan sunana ba,bare har yasan naki sunan hayaam,wannan mutumin ma bana tunanin yasan kamannin fuska ta nikaina,"   yatsina fuska hayaam tayi tare da cewa"aunty inaso in kwanta bacci nake ji," . Aunty babba tace"to shikenan!kardae ki manta da abunda yakai ki cikin gidan,so nake kafin sati mai zuwa naji ana zancen bikinki da Sgr,kafin shekara mai zuwa kuma inji kukan jariri,"  Fashewa da dariya hayaam tayi jin abunda Aunty babba ke cewa,   Sun jima suna waya kafin daga bisani sukayi sallama,wurgi da wayar tayi gefe guda sannan ta kwanta asaman lallausan bedmattress ɗin,nan take bacci yayi awon gaba da ita,
********************** Abun da ya faru bayan barin Amal gidan,wuraren bayan sallar la'asar mammy da Abra suka shigo cikin gidan,jikinta na sanye da hijabi abra kuwa atampa ce ajikinta ta aza mayafin asaman kafaɗarta,sai faman fira suke yi atsakaninsu,   "Mammy yanzu me zakiyi da kuɗin nan da sofwan ya baki?naga kamar suna da yawa,dama akwai ankon bikin wata ƙawata da nakeson yi,kinga sai ki aramun dubu takwas aciki inyi amfani dasu," .  tsuke fuska mammyn tayi tare da cewa"matsalarki kenan!daga kinga wani ya bani kuɗi sai ki bijiro da maganar anko,tun wuri ma ki fidda rai don ko sisi bazan baki acikinsu ba,malam zan kaima cikon kuɗin shi sannan sauran ni zanyi amfani dasu,ko ɗan farfesu naman nan an samu ayi,dama na kwana biyu ban sha ba,  ta ƙarasa maganar a lokacin da suka ƙarasa tsakiyar filin gidan,.  Rai a6ace abra tace"mammy kalli kiga fa har yanzu yarinyar nan bata fito daga ɗakin ba,ko ubanwa takeso ya ɗaura mana girki?gidan ma ko share shi ba tayi ba!   cike da masifa mammy ta shiga kwaɗa mata kira"Amal!!Amall!!don ubanki kina ina ne?bazaki fito kiyi mana aikin cikin gida ba!  Jin shiru bata amsa masu ba,yasa mammy ce ma Abra"maza kije ki tashe ta,ta fito tayi mana aiki,ko tasha na jaki,"  Kama hanyar ɗakin nasu abra tayi har ta kusa shiga ɗakin,ta tuna wata mugunta,cikin sauri ta juya tare da nufar fanfon cikin gidan,ƙaramin bokiti ta ɗauka na plastic ta ciko shi da ruwa sannan ta wuce dashi ɗakin a hannunta,   Murmushi mammy tasaki tare da cewa"haka nakeso,ƴa'ƴana su dinga koyi dani,"ta faɗi hakan tare da sa ƙafa ta wuce cikin ɗakinta,   ae tana shiga cikin ɗakin ta aza idonta akan gadonta inda tabar kuɗin da sofwan ya bata nan taga wayaam babu komai a wurin,hannu tasa tare da murza idanunta don ta tabbatar da abunda idanunta ke nuna mata,again ta kuma ganin wayaam babu komai asaman gadon,  Cike da mamaki tace"wai ba nan na jiye kuɗin da sofwan ya bani ba?kodai na jefa su wani wuri ne bansani ba!  ta faɗi hakan tare da sanya hannu ta zame zanin gadon tana kakka6e shi wai koda zata ga kuɗin a ƙasan shi,nan ma babu,  Cikin sauri ta zuƙunna tare da zoƙa kanta tana leƙen ƙasan gadon koda sun faɗo sun shige ƙarƙashin gadon,nan ma wayaam babu su,   Hankali atashe ta miƙe tana tafa hannu ranta ajagule tace"To wai kodai kuɗin nan ƙafafu ke gare su ne?in ba haka ba taya akai suka bar saman gadon nan!nifa nan na ajiyesu ban canza masu wuri ba,"  Lokaci guda tabi ta rikice ta rasa natsuwarta,saboda mace ce mai shegen son kuɗin tsiya,har faɗi take da naira biyar ɗinta ta faɗi kwara haƙorinta guda ya cire,   Acan kuwa bayan Abra tashiga cikin ɗakin da Amal take,sam bata lura babu mutun asaman katifar ba,saboda yarda shape din bargon ya bada kamar akwai mutun acikin shi,  Ciza le6anta tayi tare da cewa"ƴar jakar uba,yau zaki gane kuranki,wato banza tasamu tun jiya kike ja mana na rago asaman katifarmu duk kin 6ata mana katifarmu da yawun bacci,yanzu zanyi maganinki,ƙazama kawai  ta ƙarasa maganar tare da ɗaga bokitin ta kwarara ruwan asaman bargon tana faman 6a66aka dariyar mugunta,abun mamaki shiru babu alamar Amal zata saki ihun jin saukar ruwa ajikinta,.   Hakan yasa dariyar abra ta soma komawa ciki,ganin yarda bargon ya lafe ajikin katifar,yasa ta gane cewa babu mutum asaman katifar,  Hankali atashe ta saki bokitin ƙasa tana faman kwala ma Amal kira, Shiru bata amsa ba,cikin sauri ta fito tana nemanta a tsakar gidan,babu inda bata duba ba daga kitchen har cikin toilet ɗinsu duk bata nan,  da gudun gaske ta koma ɗakin mamynsu a firgice mammyn ta ɗago tana kallonta ganin yarda ta faɗo mata yasa tace"Abra lafiya meke faruwa ne"!   Muryarta har wani shakewa takeyi wurin fadin"Mammy!babu Amal acikin gidan nan!Amal ta gudu!dama saida raina ya bani cewa zata iya guduwa,'   jin hakan yasa mammy cewa"hakan na nufin itace ta kwashe kuɗin da Sofwan ya bani?   "Mammy dagaske baki ga kuɗin ba!aiko indae hakane toh Amal itace ta kwashe kuɗin,innalallahi bansan ya akai wannan daƙiƙiyar yarinyar har tayi tunanin guduwa ba,ina mata kallon shashasha....'    Katse ta mammy tayi da cewa"amma shegiyar yarinyar nan ta gama dani wlh!naci buri akan kuɗin nan,maimakon ta gudu tabarmin kuɗin shine ta haɗa dasu ta gudu,insha Allah a wulaƙance rayuwarta zata ƙare,Allah ma yasa kidnappers su ɗauketa su kwace kuɗin,sannan su lalata rayuwarta....."   "Subhanallahi!!me nake ji haka!"  Muryar Abbansu Abra ce ta karaɗe kunnansu,shigowarshi kenan cikin gidan ya same su suna ta tsinar Amal,   wani koɗaɗɗen mutum ne,tamkar baya a cikin hayyacinshi haka zubin shi yake,tsohon yadi ne ajikinshi duk yayi uban squeezing,kamar kanshi farau talauci,   ƙarasawa bakin kofar dakin yayi yana tambayar lafiya menene ya faru,    Tsawa mammy ta daka mashi tamkar ba mijinta ba haka tashiga ɗura mashi zagi   "Munafukin banza,munafukin wofi kazo kaji abunda muke tattaunawa ne!Anya bakaine kayi ma Amal hanyar guduwa daga cikin gidan nan ba!wlh ban yarda dakai ba!ka faɗamin gaskiya taya akai Amal tabar cikin gidan nan!?don nasan hakanan banza Amal baza tayi tunanin barin gidan nan ba!dole da taimakon wani,   Tuni yasha jinin jikinshi,saboda mugun tsoranta yake ji,gaba daya ta gama asirce shi,shiyasa baida ikon yin komai sai da Umarnin ta,   tsawa ta daka mashi tare da cewa"ba zaka faɗamun gaskiya ba!taya akai amal tabar gidan nan!   Zuru yayi da ido sai faman kyafta ido yakeyi yana mazurai kamar mara gaskiya,   tsoki abra taja tare da cewa"mammy dama kin daina wahalar da kanki,Abba bai ma da cikakken hankalin da zai iya taimakon Amal wurin barin gidan nan!6ata mana lokaci kawai zaiyi,ni ina ganin ki fito kawai muje mu nemo ta acikin gari,   harara Mammy ta watsa mashi tare da fitowa daga ɗakin ita da Abra suka kama hanyar fita daga gidan,  Bayan sun fuce daga cikin gidan,matsawa abi yayi tare da kai hannu ya ɗauki kujera ƴar tsugunno ya zauna asamanta,   Muryar Amal ya tuna acikin kunnan shi,ashe sun haɗu da ita akan hanya sai faman sauri take yi tamkar zata tashi sama,kamar daga sama taji an ruƙo mata rigar jikinta a firgice ta juya tana kallon shi,ganin Abbansu ne yasa ta fashe da kuka don tasan cewa zai iya mayar da ita gida,cikin shessheƙar kuka tace"Abie nasan inda Aunty amani take,bazan cigaba da zama acikin gidan nan ba,kana gani zasu kashe ni,amma ba ka iya tsawatar masu akan su daina cutar dani,dan Allah Abie kabarni in tafi,kada ka sanar ma mammy cewa ka ganni akan hanya,ka nuna cewa bakasan komai ba,"  tsananin tausayinta ne ya kama shi,nan take yaji cewa zai iya taimakonta gudun karta faɗa hannun mutanen banza,tun da ƙaramar yarinyace mai ƙananun shekaru tsaf za'a iya yi mata wayau,   "Kiyi haƙuri Amal akan dukkan abunda ke faruwa,nima bada son raina bane,bani da yarda zanyi ne gaba daya mammy ta addabi rayuwata,ta hanani dukkan wani farin ciki na rayuwata,tun bayan da Allah yayi ma mahaifiyarku rasuwa ban ƙarasamun kwanciyar hankali ba,komai na duniyar nan ya fita raina Amal,mammy ta jima tana cutar da rayuwata da kuma rayuwarki,yanzu ina da kwarin guiwar iya taimaka maki!dama abunda yasa tuntuni banyi hakan ba saboda bani da ikon yin magana dake acikin gidan,inaji ina gani an rabani da ƴata kuma ana cutar da ita akan idona,babu komai akwai ranar sakayya,"  Yana kai karshen maganar tashi ya ruƙo hannun Amal tare da janta suka tafi,da kanshi yakaita tasha sannan ya damƙa ma drivern amanarta,kasancewar drivern ɗaya daga cikin abokanshi ne ana mutunci sosai,agaban motar drivern yayi mata wuri ta zauna kusa dashi,  Sai lokacin drivern yake tambayarshi inda zasu sauke ta a abujan,shi kanshi abie baisan inda amani ke zaune ba acan,   Cikin sauri Amal tace"ina da numbar wayar Aunty amanin,idan mun isa sai ya kira mun ita awaya,nasan zata zo,"   Murmushi abie yasaki yana tsaye daga waje yashiga tofa mata addu'o'i tare da yi masu fatan sauka lafiya,   tuni Amal taji hawaye sun wanke mata fuskarta,ji take kamar ta fito daga cikin motar tabi mahaifinta,haƙiƙa ta tausaya mashi sosai,haka ta dinga jin raɗaɗi azuciyarta har motar tasu ta kusa barin tashar,ya jiyo muryar Amal tana kwala mashi kira,  "Abie!!Abie!!" da saurin gaske ya ƙarasa inda motar take,kowa na cikin motar tsayawa yayi yana sauraron muryar yarinyar,   murmushi ta sakar mashi,tare da zura hannu cikin aljihun rigar Abra dake ajikinta,zaro kuɗin nan tayi kusan dubu arba'en,sannan ta zura hannunta ta saman glass ɗin murfin motar ta miƙa mashi su,   ganin ya tsaya yana kallon kuɗin yasa tayi saurin cewa"Abie dan Allah kada ka tambaye ni ina nasamu kuɗin,in dai ka yarda dani to ka kar6a kawai nasan kana buƙatarsu,"    Murmushi yayi tare da sanya hannu ya kar6i kuɗin,sannan a hankali glass ɗin ya soma dagawa sama,   Tana jiyo muryarshi yana cewa"ki kula mun da kanki,sannan in Allah ya haɗaki da ƴar uwarki Amani,ki gaishe mun da ita,kice Abbanta yana gaishe da ita sosai,    har motar tabar tashar Amal bata daina leƙenshi ba ta glass ɗin motar,haka zalika shima yana atsaye yana kallon motar tasu,har sai da ta 6ace ma ganin shi,sannan ya haƙura ya juya tare da kama hanya ya soma tafiya yayin da idanunshi ke akan hannunshi yana kallon kuɗin da Amal ta bashi,  Ba ƙaramin daɗin kuɗin nan ya ji ba,yaushe rabon daya ruƙe naira dubu tashi ta kanshi harya manta,ba damar ya samu kuɗi yashiga gidan shi,da zarar mammy ta gani zata amshe kuɗin,ko sisi bata son taga ya ruƙe a hannun shi,tafi son taganshi a matsiyacin shi yana yawo,wannan ba damuwarta bace,   Sanin cewa zata iya ganin kuɗin a hannunshi ta kwace mashi su hakan yasa baiyi gangancin zuwa gidan dasu ba,kai tsaye ya wuce wurin wani abokin shi mai siyar da nama abakin hanya,wuri yasamu ya zauna bayan sun gaisa ya bashi ajiyar kuɗin duka,sannan yace ya zuba mashi naman na dubu uku yaci,bai bar wurin ba sai da yaci ya ƙoshi sannan sukayi sallama da mai naman ya wuce gaba,
  Murmushi abie ya saki bayan ya kammala tunanin nashi yace"Allah sarki Amal!kin taimaki mahaifinki,ba don ta bani kuɗin nan ba,da yau haka zan kwana da yunwa,"    Mammy da abrah tamkar zasu yi hauka wurin neman Amal,gida gida haka suka dinga bi suna nemanta,saƙo da lungu ba inda basu duba ba,har bayan sallar magrib suna waje wurin nemanta,a ƙarshe dasuka gaji agalabaice suka koma gidan suna faman haki kamar waɗanda suka sha gudu,tun acikin zauren gidan mammy ta yanke jiki ta faɗi a sume,saboda tsabar baƙin cikin Amal data gudar mata da kuɗinta, . hankali atashe abra tashiga zabga ihu tana kuka tana ambaton sunan mammy,  Da alama dae mammy sai anyi jinya,
****************************
Around 11pm,
fitowa tayi daga cikin toilet jikinta na sanye da sleeping dress riga da wando,white colour,da alama tayi shirin kwanciya,tun acikin toilet take jin wayarta na ringing,hakan ne ma yasa tayi hanzarin fitowa,ƙarasawa tayi cikin sauri tare da kai hannu ta ɗauki wayar dake ajiye asaman mirror,duba sunan mai kiran tayi,ganin baƙuwar number yasa taƙi ɗaga kiran,sai tayi rejecting ɗin kiran,kafin ta ajiye wayar sai ga wani kiran ya ƙara shigowa na baƙuwar numbar, Cike da mamaki tace"Wai wanene ke kirana a irin wannan lokacin,kuma da bakuwar number,salon ajamun bala'e,bari dae in ɗaga inji,picking call ɗin tayi tare da karawa a kunnanta,muryar namiji ce taji ya zabga mata sallama,aikuwa cikin sauri ta katse kiran tana faman dafe saitin zuciyarta,ta tsorata da jin muryar me kiran nata,koma wanene ba ƙaramin mutum bane,  tsayawa tayi tana tunanin wa tasani da wannan muryar,bata ta6a jin mai irinta ba,   tana cikin wannan yanayin sai ga message ya shigo cikin wayarta,cikin sauri takai hannu tare da janyo saƙon daya shigo daga saman screen din wayar tashiga karantawa kamar haka   _baiwar Allah,ina ta kiran wayarki kin ƙi ɗagawa,dama ƙanwarki Amal ce ta ban numbarki don na kira na sanar dake cewa kizo ki ɗauke ta,ni ne drivern daya kawota abuja,idan ba damuwa ki kira kuyi magana da ita,don kiji muryarta_  Wani irin bugu zuciyarta tayi,cikin tsananin mamaki tashiga maimaita sunan Amal,muryarta na kerma tashiga cewa'Amal!wata Amal yake nufi!ko dai Amal ƙanwata!!!   Cikin sauri ta danna ma numbar kira,yatsun hannunta har kerma sukeyi don aƙagare take da taji bayanin mutumin daya turo mata saƙon...........
Pls read this👇👇👇
*Assalamu Alaikum,barkanmu da juma'a fatan kowa na lpy,yauwa inaso indan yi wani karin haskene,aduk lokacin da bansamu yin update ba har ranar ta wuce ina kokarin ganin nayi long page don yayi covering da wanda bansamu yi ba,nasan wasu sun fahimci hakan,yayin da wasu kuma basu fahimci hakan ba sai suyi ta maganar page kaza yakamata inyi tunda banyi na rana kaza ba,duk page da nake saki yafi Æ™arfin page guda a Æ™a'idar page,ina haÉ—e 2 pages ne sometimes ma yana haura 2 pages, Shiyasa in na sanya short page wasu ke complain saboda sun saba ganin long page,sannan ban kin yin typing sai don uzurin da ba yadda zanyi,da fatan zaku fahimce ni,sannan akwai masu maganata abayan idona nacewa wai ina jan littafi? Allah sarki rashin sani yafi dare duhu,bani da wani burin daya wuce inga na kammala littafin nan ayanzu saboda abubuwa da sukayi mun yawa,bani ke jan littafin nan ba!bada son raina ba kuma hakana ke faruwa ba!yanayi ne dake nake ciki,yakamata mutane su dinga yi mun uziri bai kamata arinÆ™a yi mun irin waÉ—annan maganganun ba,duk wanda kuma yake yi Alhakina na akanshi, wai wasu ma har cewa suke yi don naga littafinna yasamu kar6uwa mutane naso. shiyasa nake jan labarin,wlh dana ji wannan maganar kamar na fasa ihu don takaici, hmmmm babu komai akwai Allah,to my real fans nagode kwarae da hadin kai da kaunar littafi na da kuke,godiya mara adadi kuci gaba da yi mun uziru kuma acigaba da yi mun addu'a,shine kawai insha Allah komai mai wuce wane,Littafin nan inaji araina cewa kammaluwarsu tazo zanyi Æ™oÆ™arin tabbatar da hakan!insha Allah*â?
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
ðŸ¤â¤ðŸ’?
Kiran na shiga drivern ya ɗaga,cikin sauri ta kara wayar a kunnanta tare da yi mashi sallama tace"kayi haƙuri bawan Allah,ban fahimci zancen ka bane,dan Allah ka ƙara yi mun bayani yarda zan gane,"   drivern yace"ƙanwarki ce Amal na kawota Abuja,yanzu haka ita kaɗai ta rage acikin tashar nan,kiyi hanzari kizo ki ɗauke ta saboda dare yana yi kuma ni yanzu nakeson na juya,"  Cikin sauri tace"ka turomin da address ɗin wurin gani nan zuwa,"     Amsa mata yayi da toh,sannan ya kashe kiran,ba da jimawa ba sai ga message ya shigo wayarta na address ɗin inda suke,  Da sauri Amani ta ƙarasa wurin wardrobe ɗinta tare da buɗewa ta ɗauko mayafi tayi rolling ɗinshi akanta,sannan ta dawo ta dauki purse ɗinta dake ajiye asaman bedside drawer ɗinta,        gaba ɗaya duk tabi ta dabarbarce ko escort bata nema ba, da kanta ta shige motarta,ta fisgeta da gudun gaske ta fice daga cikin gidan,driving take tana ta faman sambatu"Ya Allah ka tabbatar mun da abunda nake tunani,Allah yasa Amal ce ƙanwata,Ya Allah kasa itace,wayyo Allah da naji daɗi,      ji take kamar motar bata sauri,tamkar tayi fiffike ta tashi sama don ta ƙarasa da wuri,
tun bayan da Drivern ya turama Amani adireshin wurin inda suke shiru bata ƙaraso ba,gashi dare sai ƙarayi yake,kuma babu wani passenger daya rage acikin station ɗin sai ita kaɗai kwallin kwal,sai kuma wasu daga cikin mazauna station ɗin,tana zaune acikin motar baiwar Allah ba ƙaramin galabaita tayi ba,ga gajiyar tafiya ga kuma ciwo da take fama dashi,don har yanzu zazza6in nan bai bar jikinta ba,ganin cewa zasu 6ata mashi lokaci gashi yana da wani uzuri mai mahimmancin da yake so yaje yayi,hakan yasa yace ma Amal ta fito daga cikin motar,daƙyar ta iya miƙewa tare da saukowa daga cikin motar ta fito waje tare da tsayawa tana jiran jin me zaice, Ruƙo hannunta direban yayi sannan yajata izuwa wurin wani benci yace ta zauna anan ta jira ƴar uwarta tazo,kada taje ko'ina,shi zai wuce don yana da uzuri,  Hankalin Amal ba ƙaramin tashi yayi ba ganin direban zai tafi yabarta acikin station ɗin gashi babu wata ƴa mace aciki sai ita kaɗae,  Shi kanshi baiso hakan ba,saboda amanace aka bashi,amma ba yarda zaiyi,ya zamar mashi dole ya juya ya koma da motar,   tana ji tana gani direban nan ya shige motarshi tare da janta yabar cikin tashar da ita,  Lokaci guda wani irin sanyi ya lullu6eta,nan da nan jikinta ya shiga rawar ɗari,hatta haƙoranta sai faman kakarwa suke yi suna fidda sauti kaf kaf suna game wa da juna,ƙanƙame jikinta tayi tana ta faman ambaton sunan Allah abakinta,  Tana cikin wannan yanayin tajiyo takun tafiyar mutane daga gefen hagunta,cikin sauri ta juya don taga su wanene,gabanta ne yayi wani irin faɗuwa ganin wasu giggan tantirai su uku suna tunkaro wurin da take,sai faman nunata sukeyi da hannu da alama ma abuge suke,sun sha takai masu karo suna tafiya suna tangal tangal kamar zasu faɗi,   ganin hakan yasa Amal ta miƙe cikin sauri ta soma tafiya tana waiwayonsu,muryar wani daga cikinsu ne tajiyo yana cewa"kai karfa ta kufce mana,naga kamar tana so ta tsere mana," haba ina ae Amal na jin wannan maganar ta manta da yanayin da take ciki,takai hannu tare da tattare rigar jikinta ta watsa aguje kamar zata tashi sama,suma ganin ta fara gudu yasa suka bi ta aguje don su taddota,   Gaba ɗaya duk tabi ta rikice tana gudu tana waiwayonsu hakan yasa ta hau saman titi batare da saninta ba,kafin tayi wani aune tuni wata mota tayi awon gaba da ita,wata irin razananniyar ƙara Amal ta saki yayin da ta baje asaman titin idonta na kallan sama,jini na zuba ta saman goshinta da kuma hancinta,da la66anta duka sun raunata,   Waro ido waje tantiran nan sukayi ganin abunda ya faru,aikuwa a gaggauce suka zura da gudu don kar ace sune suka kashe ta,    Hankali tashe suka tsayar da motar,sannan atare suka fito daga cikinta da hanzari suka tunkari wurin da yarinyar take kwance,gaba ɗayansu suna sanye da kakin sojoji ajikinsu,    Zuƙunnawa daya daga cikinsu yayi yana kallon fuskar yarinyar dake ta faman faɗin"innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"   "bata mutu ba,har yanzu tana numfashi amma tana bleeding ya kamata muyi saurin kaita asibiti,"   Na zuƙunnan ne yayi magana,sannan batare da 6ata lokaci ba,yasa hannunshi tare da sungumarta asaman kafaɗarshi cikin sauri suka wuce da ita cikin motarsu,a back seat ɗin motar ya zaunar da ita,sannan shima ya shiga daga gefenta ya zauna tare da ruƙota jikinshi,  Shi kuma ɗayan ya shiga gaban motar tare da yi mata key,yaja ta aguje suka juya domin zuwa kai yarinyar asibiti,   Adai dai lokacin da Motar tasu take ƙoƙarin shiga shantalelen titin dake a left hand dinsu,Motar Amani ta kunno kai ta titin dake a right-hand ɗinsu, a wani slow Amani ta zuge glass ɗin motarta tana bin tasu motar da kallo saboda kukan mutum da tajiyo acikin motar ba ƙaramin ɗaga mata hankali yayi ba,aranta tana cewa"Allah yasa dae ba wani mummunan abunne ke faruwa acikin motarcan ba,"  Tana ƙarasa maganar taja motarta da gudun gaske ta ƙarasa cikin tashar motocin,wuri ta samu tare da yin parking ɗin motar,cikin sauri ta fito tana faman gyara mayafin dake ajikinta,hannu tasa tare da ciro wayarta dake acikin purse ɗinta,sannan ta dannawa direban kira,cikin rashin sa'a aka sanar da ita cewa numbar da take kira a kashe take,   hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,  A ruɗe ta soma cewa"kodai ƙarya mutumin nan yayi mani ne?amma meyasa zai kirani a waya ya sanar dani cewa ƙanwata Amal ya kawo Abuja,kuma sannan yanzu na kira wayar shi a switch off,Ya ilahi amma dae bai kyautamun ba wlh,"   tana cikin wannan zancen zucin sai ga waɗannan tantiran guda uku da suka biyo Amal,ganin su yasa Amani tayi tunanin ko ta tambayesu may be a dace,  da hanzari ta tunkare su tare da yi masu sallama,   a firgice ɗaya daga cikinsu ya shiga cewa"wlh ba mu muka kashe ta ba,kawai mun ganta ne acikin tashar nan zaune ita kaɗae,shine muka biyota don mu tambayeta ina iyayenta suke ne...."tun kafin yakai ƙarshen maganar tashi wani daga cikinsu ya buge mashi baki tare da cewa"Ƙarya Haramun!Aunty bari na faɗi maki gaskiyar lamari,mu ɗinnan da kika ganmu 6arayi ne masu yankar aljihu,mun biyota ne domin mu kwamushe ƴan kuɗaɗen dake hannunta tana ganin mu sai ta watsa aguje,tana ta faman gudu kamar zata tashi sama kawai sai ga wata mota tayi Wuff ta ɗauke ta sama........'  gaba daya basu acikin hayyacinsu da alama giyar ce takai masu karo,sai faman kora mata bayanin abunda bata tambayesu ba suke,  Murya na rawa Amani tace"dan...Allahh ban gane akan me kuke magana ba?wacece kuma kuka bi aguje har mota ta buge ta?wace yarinya ce,!kuyi mun bayani,ni ina neman ƙanwata ne Amal,ɗazu wani driver ya kirani a waya ya sanar dani cewa ya kawota inzo in ɗauke ta kuma shine ma yaban addreshin wurin nan,"  Har haɗa baki suke yi wurin cewa"ae itace yarinyar da muke yi maki magana akai Aunty,ae yanzu haka ma yarinyar tana acikin motar waɗanda suka banketa,yanzun nan suka bar wurin nan da ita,  Tun kafin ya ƙarasa maganar Amani ta juya da saurin gaske ta nufi motarta saboda tunawa da tayi da Motar da tagani ta gifta ɗazu da kukan yarinya acikinta,  buɗe motar tayi tare da shigewa ciki taja ta da gudun gaske,tana jiyo muryar waɗannan matasan suna cewa"Aunty Allah tsare hanya,"      *************************** SEHRISH
Sam ta hana idanunta bacci saboda jiran dawowar babban yaya,yau harya haura lokacin daya saba dawowa hakan ba ƙaramar damuwa ya jefata ba,harta sauya kayan jikinta izuwa na bacci riga da wando masu laushin gaske orange colour,tun wuraren ƙarfe sha biyu daidai takai mashi fruit a ɗakinshi,Coffee ne kawai bata kai mashi ba saboda tasan cewa bazai shaba idan ya salafce,don ta lura cewa yafi buƙatar shi da zafi zafinshi,don wani sa'en har yana tururi yake shan shi,   sai faman safa da marwa takeyi acikin ɗakin har sai da ƙafafunta suka soma yi mata raɗaɗi sannan ta koma tare da samun wuri gefen gadonta ta zauna,lokaci guda kuma ta soma sakin hammar bacci,duk yarda sehrish taso ta hana kanta bacci amma abun yaci tura,sai gata kwance abaje tana ta faman sharar bacci asaman gadonta,  da yake ta sama ranta abun sai gashi ta farka wuraren ƙarfe daya na dare,daƙyar ta iya mikewa tsaye tana kallon clock ganin ɗaya ta buga yasa taji gabanta ya faɗi rasss,tsoranta kar ace ya dawo tana cikin sharar baccin nan,  Cikin sauri ta taka izuwa wurin window ɗinta,hannu tasa tare da janye curtains din sannan ta zuge glass ɗin tana hangen wajen harabar ajiye motocinsu,anan ta hangi motarshi ajiye alamar ya dawo kenan,    dafe saitin zuciyarta tayi gabanta na faduwa a fili tace"Nashiga uku ashe ya dawo,yanzu ya zanyi kenan nasan ranshi zai iya 6aci akan ban kai mashi coffee ɗin ba,"  cike da takaici taja guntun tsoki tare da cewa"duk wannan baccin ne daya ɗauke ni,da hakan bata faru ba,yanzu ya zanyi kenan gashi dare ma yayi sosai,in naƙi kai mashi matsala, in nakai mashi ma hakan zai iya jamin wani abun kuma,"  taƙarasa maganar tare da yanke shawarar takai mashi kawai,hannu takai tare da daukar mayafinta,ta rufe kanta dashi,sannan ta zura silifa aƙafarta,a hankali ta buɗe ƙopar ɗakin kamar mara gaskiya haka ta dinga tafiya har ta isa kitchen,shiga ciki tayi tare da wuce wa kai tsaye wurin cupboard,hannu tasa tare da curo cup ɗin data ware mashi nashan coffee ɗinshi,batare da 6ata lokaci ba ta zuba mashi coffee ɗin da zafin shi aciki cup,asaman plate ta aza mashi kofin sannan ta nufi hanyar fita,tana ƙoƙarin fita daga cikin kitchen ɗin sai ga Hayaam ta faɗo ciki,ba ƙaramin tsorata Sehrish tayi ba don har saida takusa zubar da coffeen dake hannunta,ido azare take kallonta don bata tsammaci mutum ba adai dai irin wannan lokacin,  tun da tazo gidan take ƙumshe aɗakinta tana baccin lalaci,koda ta farka bata fito waje ba,sai yanzu Allah yayi ta samu ta fito,short gown ɗin nan ce ta ɗazu ajikinta,kan nan nata ko arziƙin dankwali babu balle mayafi,sai dai gashin kanta data ɗaure abayanta,   Murya a sanyaye sehrish tace"Sannu da fitowa,ya gajiyar tafiya,"  Ƙayataccen murmushi hayaam ta saki tare da cewa"yawwa ƴan mata,gajiya tabi jiki yanzu ina jina normal,"  Ta ƙarasa maganar tare da kallon cup din dake ruke a hannun sehrish tace"Wannan fa?ke zaki sha ne"?  girgiza kai sehrish tayi tace"a'a banawa bane,babban yaya zan kaimawa ne,"  yamutsa fuska amani tayi tare da cewa"Oh ashe ya dawo cikin gidan kenan,"  Sehrish tace"eh,ya dawo," "ra'ayin kanki ne kai mashi coffeen ko kuma shi ya buƙata ne"?ta kuma jifarta da tambaya,    "Ai shi ba'a yi masa katsalandan,shi yace na rinƙa kai mashi a kullum wuraren ƙarfe sha biyu idan sun dawo daga aiki," ta bata amsa tare da kama hanya zata wuce,  Cikin sauri hayaam ta sake shan gabanta tare da cewa"gaskiya bai kamata ace ƙaramar yarinya kamarki tana kai mashi abunsha adai dai irin wannan lokacin ba,sam wannan tsarin baiyi ba,yakamata ace yanzu kina kwance kina bacci ko don saboda zuwa school yana da kyau ki rinƙa yin bacci da wuri," ..murmushin yaƙe sehrish tayi sannan tace"nagode da shawararki,amma wannan aikina ne kula dashi,kuma nasaba da yin hakan"   ganin hayaam zata 6ata mata lokaci yasa tayi saurin wuce wa batare da ta saurari sauran abunda zata ce mata ba,  jinjina kai hayaam tayi tare da cewa"yarinya dani kike magana,wato har wani faɗamun take itace mai kula dashi,shisshigi kawai da kutsi," ta faɗi hakan tare da jan dogon tsoki ta wuce bedroom ɗinta,   lokacin data ƙarasa part ɗinshi baya acikin falon hakan yasa kai tsaye ta wuce bedroom ɗinshi,sallama tayi mashi amma shiru ba'a amsa mata ba,almost 4 times tana zabga mashi sallama amma tsit babu alamar za'a amsa mata,  saurarawa tayi don taji ko zata ji motsin shi aciki,nan ma shiru ranta ne ya bata cewa kawai tashiga cikin bedroom ɗin nashi,   ƙafa tasa tare da shigewa ciki,nan take ƙamshin turaren nan nashi ya daki hancinta har saida ta ɗan ja da baya saboda yarda ƙamshin ya shigeta kai tsaye,sauke ajiyar zuciya tayi tare da ware idanunta tana bin bedroom ɗin nashi da kallo,wayamm tagani babu shi acikin ɗakin,tsayawa tayi tana tunanin ko'ina ya shiga ne,kodai bai dawo bane?amma kuma ae ga motarsu can awaje alamar sun dawo,har ta yanke shawarar barin ɗakin,zata juya kenan eyes ɗinta suka sauka akan fruits ɗin da takai mashi,wanda ta ajiye mashi asaman table din dake kusa da gadonshi,a rufe takai mashi kayan marmarin amma sai taga an cire plate din data rufe su dashi,alamar ya fara shan fruits ɗin kuma ya dakata,ranta ne ya bata cewa may be yana acikin toilet ne,   murmushi ta ɗanyi sannan ta ƙarasa wurin table ɗin tare da ajiye mashi cup of coffee din agefen kayan marmarin,  tsayawa tayi tana tunanin ko dae ta tsaya ya fito daga cikin toilet ɗin wata'ƙil zai buƙaci wani abun bayan wannan,wata zuciyar kuma ta bata shawarar cewa ta tafi kawai tabar dakin saboda dare yayi sosai,   tana cikin wannan tunanin,sgr ya fito daga cikin toilet,waist ɗinshi na ɗaure da short towel wanda bai kai guiwar ƙafafunshi ba da alama wanka yayi aciki,
sam bai lura da mutum a cikin bedroom ɗin nashi ba,gadan gadan ya tunkari wurin dressing mirror ɗinshi,cikin rashin sani tafin ƙafarshi ya hau saman 6awon ayabar daya ci ɗazu,ya maƙale masa a jikin shirt ɗinsa saida zai shiga wanka ne ya lura dashi yasa hannu ya ka6e shi ya faɗi anan ƙasa,aikuwa nan take wani irin mugun sul6i ya kwashe shi bazato ba tsammani gaba ɗaya ya tafi a burkice zai faɗi,a firgice sehrish ta juya tare da yin ƙoƙarin taimaka mashi cikin sauri ta ruƙo shi nan take ƙarfin shi ya rinjayi nata gaba daya suka faɗa saman shimfiɗeɗen gadonshi a manne da juna,tashin hankali da ba'a sama shi date,  wata irin nauyayyiyar azuciyar zuciya Sgr yashiga saukewa,tabbas ya ɗan firgita saboda bai tsammaci hakan ba,bai ta6a yin irin wannan gangancin ba,hada ƙarin sam ya manta da 6awon ayabar a wurin bai jefa shi dustbin ba,da ace sehrish bata ruƙo shi ba awannan lokacin da ba ƙaramin buguwa zaiyi ba yanda yake dogon nan,   atare zuciyoyinsu suka shiga bugawa da ƙarfi da ƙarfi,gaba ɗaya sehrish ta gama tsorata abun tamkar a amafarki take ganin shi,ta gaza yarda cewa itace tare da Surgeon general Rafayet kwance asaman gado ɗaya kuma amanne da juna,   gaba ɗaya jikinshi ya rufe nata hatta face ɗinta tana a saitin wide chest ɗinshi,tana jin yarda yake ta faman sauke ajiyar zuciya,da kuma yarda heart ɗinshi ke beating very fast,   tsit kake ji daga ita harshi an rasa mai wani kwakkwaran motsi,danshin ruwan dake ajikinshi ba ƙaramin sanyaya mata jikinta yayi ba,daƙyar take iya breathing saboda hancinta daya manne da fatar ƙirjinsa,haka la66anta ma suna manne da fatarshi,  Boss man ɗin fa ya gaza ɗago da jikinshi daga nata,ba don komai ba sai don yarda abun yazo mashi unexpected,ba ƙaramin jinjinawa lamarin yayi ba shi kanshi,   Jin yarda yarinyar keta kokawa wurin fitar da numfashinta,yasa ya daure tare da yunkurawa zai tashi daga jikinta,baiyi wani aune ba towel din dake ɗaure a qugunshi ya shiga warwarewa gaba daya dama daurin ya saki,  Shi kanshi baisan lokacin daya mayar da jikinshi asaman nata ba ya kwantar da kanshi a saman left shoulder dinta,bakomai ne yasa yayi hakan ba face gudun kar towel din jikinshi ya saki agabanta,don muddin hakan ta faru tofa wannan karon ba sume mashi zatayi ba,zuciyarta ce zata buga tabar duniyar saboda tsabar firgici don ya lura yarinyar ba ƙaramar matsoraciya ba ce,    wani irin yanayi mara misaltuwa taji atattare da ita,jikinta yayi wani irin sanyi sanyi kasala kasala haka,sam bata jin nauyin jikinshi akan nata sai ma yanayin da hakan ya jefa ta,    idanunta na'a rufe sam tagaza buɗesu ba don komai ba sai don tsoran abunda zai biyo baya,a matuƙar tsorace take hakan yasa ko kwakkwaran motsi tagaza yi,lumshe idanunshi yayi yayin da hancinshi ke gogar fatar wuyanta,fragrance ɗin turarenta ne yake kaimashi ziyara acikin hancinshi,ƙamshin ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,har lokacin tana jin yarda numfashinshi ke fita afatar jikinta,  almost 15mins suna cikin wannan yanayin,tajiyo hannunshi a hankali ya zura shi adai dai saitin waist ɗinshi don ya gyara ɗaurin towel dinshi,wannan moving ɗin da ya runka yi da hannunshi awurin yana gogar jikinta ba ƙaramin kashe mata jiki yayi ba,amace ta mace gaba ɗaya tashiga wani irin yanayi na daban....,   sai da ya samu ya ɗaure towel ɗin sannan a ƙaro na biyu ya ɗago da kanshi don ya raba jikinshi daga nata,nan take sehrish ta saki wata irin razananniyar ƙara gaba ɗaya ta gigita shi,ashe raɗaɗin Earring ɗinta ne daya sargafo gashin kanshi ya harɗe acikin ɗan kunnan,wannan ɗagawar da zaiyi ajikinta shine sumar kanshi taja ɗan kunnan nata da ƙarfi wannan ne dalilin dayasa ta fasa ƙara,cikin sauri Sgr ya mayar da kanshi tare da kwantar dashi agafen fuskarta,fashewa da kuka sehrish tayi sosai saboda ba ƙaramin zafi taji ba,don wurin harya fara fidda ɗigon jini,a hankali ya buɗe blue eyes ɗinshi tare da bin kunnan nata da kallo yarda sumar kan nashi ta harɗe acikin earring ɗin shine yafi komai bashi mamaki,tunani ya soma yi taya za'ai ya cire gashin nashi acikin ɗan kunnan nata?dole akwai buƙatar yabi a hankali wurin zagayo da hannun na dama don ya cire shi,   A hankali ya ɗago da fuskarshi daga gefen fuskarta,ya kasance cewa suna facing ɗin juna sosai,hatta numfashinsu yana haɗewa dana juna,wannan shessheƙar kukan da takeyi ne yaja hankalinshi wurin kallon fuskarta,la66anta har kerma sukeyi yayin da idanunta ke arufe,  Muryar shi ce ta katseta da cewa"I don't wanna hear that sound again,"  Cikin sauri sehrish ta tsagaita dayin kukan gaba daya,ta koma tana faman sauke ajiyar zuciya,  buɗe idanunta tashiga yi waɗanda ke cike tab da ruwan hawaye,tun kafin ta ƙarasa ware idanun nata take hangen hasken blue ɗin kwayar idanun shi,a hankali ta ƙarasa buɗe idanun sosai akan kyakkyawar fuskarshi dake fuskantar tata,duk da irin bugun zuciyar da take ji amma hakan baisa ta mayar da idanunta ba ta rufe su,   A natse ta soma bin pink lips ɗinshi da kallo shape ɗinsu ba ƙaramin kyau ne dasu ba,tausasan gaske,mayar da eyes ɗinta tayi akan dogon hancin shi da tsinin ke dab da nata hancin,ta jima tana kallon hancin nashi daga bisani kuma a hankali ta aza idanunta acikin nashi nan take taji wani irin bugun zuciya,    sai faman lumshe idanunshi yake yana kuma opening ɗinsu saboda baccin da yake ji,dama agajiye ya dawo cikin gidan,a hankali yake ɗan waresu akan idanunta,anatse yake bin long eyes lashes din idonta da kallo,har yanzu akwai sauran tears dake dripping a cikin idonta,sun jiƙa eyes lashes ɗin nata sharkaf,   Eyes balls ɗinta yabi da kallo a lokacin itama nata na'a kan kwayar idon tashi tana ƙarewa launin idon nashi kallo,kasa janye idanunshi yayi acikin nata,kamar yarda itama tagaza janye nata acikin nashi duk da tsoran kwayar idon nashi da take ji,   Suna cikin wannan yanayin a hankali ya zagayo da right hand ɗinshi ta saman kanta,ya ƙaraso dashi wurin ɗan kunnan nata sannan ya haɗa da hannun shi na hagu ya shiga ƙoƙarin cire gashin nashi daga jikin earring ɗin nata,        runste ido sehrish tayi saboda zafin da take ɗan ji a wurin,ganin hakan yasa ya haɗe fuskokinsu awuri guda,jin yarda lips ɗinsa suka manne da nata tamkar zaiyi kissing ɗinta hakan ba ƙaramin rikitar da ita yayi ba,   duk yarda yaso ya cire gashin daga jikin ɗan kunnan abun ya gagara ganin hakan zai 6ata mashi lokaci yasa yayi deciding tsinka gashin kan nashi daya sargaho earring ɗinta,   Cikin sa'a ya katse gashin nashi yabar mata sauran siraran da suka ruƙo dan kunnan nata,   Sai da ya raba ɗan kunnan sannan yaji wata irin kasala ta baibaye shi,lokaci guda ya rasa karfin janye jikinshi daga nata,ya dai samu ya ɗan janye face ɗin shi daga nata,sai kan head ɗinshi ya koma asaman boobs ɗinta,lamo yayi yana jin wani irin yanayin da bai ta6a ji ba arayuwarshi har wani bacci sosai ya dinga fisgarshi,sehrish kuwa tuni bacci yayi awon gaba da ita don bazata iya jurewa wannan yanayin ba,hannunta na asaman waist ɗinshi ta ƙankame shi sosai ajikinta,hada ƙarin hakan ya ƙara kashe mashi nashi jikin,
 Mamakine ya kama hayaam ganin cewa har yanzu Yarinyar bata fito daga part ɗin sgr ba,ashe tun bayan da sukayi magana da sehrish ta koma bedroom ɗinta sam tagaza samun natsuwa shine ta dinga leƙowa don taga ko yarinyar ta fito daga part ɗin nashi,amma shiru babu alamar cewa ma zata fito,hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,nan tashiga zargi kala kala acikin zuciyarta tana cewa"ko uban mi ya tsayar da ita ɗakin shi a irin wannan lokacin,ni dama banyarda da yarinyar can ba,daga ganinta irin sumu-sumu kasau ɗinnan ne,wlh saina yi maganinta bazan bari taci gaba da shiga sashen shi ba,
   tun tana sa ran fitowar sehrish harta haƙura ta koma bedroom ɗin data sauka,shiga ciki tayi tana ta faman sambatu kamar wata zararra duk akan sehrish ne take wannan 6acin ran,    ****************** *Junaid Romeo*
Bacci yake yi amma gaba ɗaya jikin shi kerma yake yi sosai da sosai,sai faman mutsu mutsu yake yi da alama baijin daɗin jikin shi,wata irin Zufa ce take tsattsafowa daga jikin shi saƙo da lungu na jikinshi gaba ɗaya ya kasance ajiƙe yake sharkaf,a wani irin firgice Junaid ya farka arazane yana faman zazzare manyan idanunshi da suke cike tab da kwalla,  Yana ƙoƙarin kai hannu ya tashi Abbansu dake kwance a gefen shi,sai ga wani baƙin hayaƙi ya fito daga Cikin mirror ɗin ɗaƙin mai yawan gaske baƙi wulik,bin hayaƙin junaid yayi da idonshi yana kallon shi a matuƙar tsorace,tattarewa hayaƙin yayi wuri guda kai tsaye ya nufi wurin shi,gaba ɗaya ya tunkare shi,ganin hakan yasa junaid faɗawa jikin abban nasu tare da ƙanƙame shi gaba ɗaya duk yabi ya firgice,kafin Abban nasu ya farka tuni wannan baƙin hayaƙin ya mamaye jikin junaid ta ƙofar hancin shi yabi ya dinga kurɗaɗawa cikin jikinshi,fashewa da matsanancin kuka junaid yayi yana ambaton sunan abban nasu,"Abba ka tashi dan Allah,abba pls ka tashi,bansan meke shirin faruwa dani ba,Abba ka tashi kaga halin da baby junaid ɗinka yake ciki",  duk wannan koke koken da junaid keyi abun mamaki ko motsi Abban nasu baiyi ba,sosai junaid ya dinga jijjiga jikinshi yana ambaton sunan shi amma shuru bai farka ba,babu alamar cewa zai farkama,   Allah sarki,sun sangartar da junaid sosai wanda hakan yasa bai iya ambaton wata addu'a acikin bakin shi ba,sai ihu da yake yi yana koke koke,ko addu'ar bacci wannan junaid bai ta6a yi ma kanshi ba,saboda ya saba kullum in Abbansu na nan shike yi masu addu'ar su kwanta atare,in kuwa abbansu bai nan anyhow yake baccin shi batare da tunanin yin addu'a ba,tsantsar son da suke yi mashi ne yasa basu son ya wahala ko kaɗan,junaid bai ta6a zuwa islamiyya ba don koyon wani abu na addini,amma Abbansu da kuma ƴan uwanshi suna zaunar dashi su koyar dashi wasu abubuwan sosai,a kwanakin baya har malami abbansu ya samo wanda zai dinga koya mashi karatu,tun rana ta farko da malamin yazo zai koya mashi karatu basu ƙara ganinshi ba,6at aka neme shi aka rasa,kusan sau huɗu hakan na faru duk in Abbansu ya samo malamin da zai koyar dashi addini daga yazo sau ɗaya sai a neme shi arasa,hakan yasa daga baya ya haƙura da neman malaman da zasu koyar dashi,musamman da yaga ƴan uwanshi na koyar dashi acikin gidan sai hankalinshi ya kwanta da hakan,abun da baisani ba kosu da suke koya mashi agabansu yake nuna ya fahimta kuma ya gane karatun amma da zarar yabar wurin karatun tofa komai ya zube acikin kanshi,yadawo zero 0
  Wani irin sanyine ya gauraye ko'ina na sassan jikinshi,lamo yayi abayan abban nasu yana faman sauke ajiyar zuciya,a wannan yanayin kuma bacci yayi awon gaba dashi,🥺   Meke shirin faruwa ne!?
A hankali ta soma buɗe idanunta dake ɗauke da bacci biji biji ta soma gani kafin daga bisani suka washe ta dinga ganin komai normal,jin babu nauyin mutum akanta yasa ta gane cewa sgr ya bar jikinta,cikin sauri ta miƙe zaune tare da kai idanunta inda yake kwance yana bacci,zuba mashi ido tayi tana kallon shi,yanayin yarda yake baccin zai tabbatar maka da cewa yana cikin kwanciyar hankali da natsuwa,   A hankali takai hannu tare da jan blanket ɗinshi ta rufe mashi jikin shi har wurin wuyan shi sannan ta saki bargon,   tamkar karta tafi tabarshi haka ta dinga ji,hannu takai tare da ruƙo sumar kanshi mai laushin gaske,ta tattare mashi ita tare da yin gefe guda da Ita,hakan ne ya bata damar kallon kyakkyawar fuskarshi sosai,  Cikin sanyin murya tace"inason farin ciki ya cigaba da wanzuwa a wannan kyakkyawar fuskar taka,kuma insha Allah zan tabbatar da hakan,zan cigaba da addu'a akan Allah ya mallakamin kai amatsayin abokin rayuwata,duk da nasan cewa zaiyi wuya hakan tafaru saboda kafi ƙarfina sosai nesa ba kusa ba"   Jiki asanyaye taƙarasa maganar yayin da ta juya tare da saukowa daga saman gadon nashi,sai da tafara kashe mashi hasken ɗakin sannan ta fuce daga part ɗin nashi,  A 6angaren Amani kuwa tunda tabi bayan motarsu da gudun gaske,bata ci nasarar taddo tasu motar ba saboda suma gudun sukeyi tuni sun 6ace ma ganinta,jiki asanyaye tayi parking ɗin motarta agafen titi,tamkar zata fashe da kuka haka ta dinga ji,hannu takai tare da ɗaukar wayarta dake ajiye asaman laps dinta,missed calls ta gani na Abbas har kusan shida,duk bata ji ringing ɗin da wayar keyi ba,saboda bata cikin natsuwarta hankali atashe tace"nashiga uku!Ashe abbas ya kira ni bansani ba,yanzu mai zan faɗa mashi,gashi ban hadu da wadda akace Amal ce..."   fuskarta a yamutse tayi maganar,yatsun hannunta har kerma sukeyi wurin dialing ɗin numbarshi tabi kiran da yayi mata,tana fara ringing ya ɗaga kiran,cikin sauri takara wayar a kunnanta,saurarawa tayi tana jiran jin me zaice,   "Ki dawo gida inason ganinki," Yana faɗin hakan yayi rejecting ɗin kiran nata,  Nan fa ido ya raina fata,a kasalance ta tashi motar tare da karya kwana ta miƙi hanyar komawa gida,
************************* Sosai Amal ke kuka tana ambaton sunan Allah abakinta duk tabi ta zauce,  Rai a6ace JAHAN yace"yarinyar nan tayi mun shiru!nagaji da jin tsiwarta,duk tabi tayi confusing ɗina,Ayaan kodai ka toshe mata baki ko kuma in dakatar da driving ɗin nan don ni bazan juri tsiwarta ba,"   cikin sanyin murya Ayaan yace"pls take it easy Jahan,yarinyar nan fa ba ƙaramin jiki take ji ba,ita kanta bazata iya control ɗin kanta ba saboda raɗaɗin ciwon da take ji,"  Uban tsoki jahan yaja yana faman hura hanci,adai dai lokacin suka ƙaraso da Amal katafaren asibitin sgr,shiga da motar ciki yayi tare da samun wuri yayi parking ɗinta,fitowa Ayaan yayi kafaɗar shi ɗauke da Amal kai tsaye ya wuce da ita cikin asibitin,  Jahan kuwa zaman shi yayi acikin motar yana jiran ƙarasowar ayaan ɗin,don yace bazai shiga cikin asibitin ba,ya miƙata kawai ya fito su juya,   Ayaan na shiga ciki da sauri reception nurses suka kar6e ta,tare da wuce wa da ita medical room don a kwantar da ita,   tsayawa yayi yana faman zarya a wurin,kiran jahan ne ya shigo wayarshi cikin sauri ya ɗaga kiran tare da karata a kunnan shi,   tunkafin yayi magana jahan yace "what are u waiting for Ayaan!tun da ka miƙa ta awurinsu ka fito kawai mu juya gida,"   amsa mashi yayi da okey,sannan ya kashe kiran,  harya juya zai fita daga corridor ɗin,yajiyo muryar wata nurse tana dakatar dashi,tsayawa yayi tare da juyawa yana kallonta,ƙarasowa tayi da sauri cikin harshen turanci ta soma yi mashi magana"sir yarinyar taƙi bari mu dubata,da alama tana da damuwa sosai,akwai wani suna da take ta ambato abakinta,in badamuwa muna so ka shigo daga ciki kayi mata magana,may be ta samu natsuwa,"   batare da musu ba,Ayaan yabi bayanta har cikin ɗakin da suka kwantar da Amal,sai faman kuka takeyi tana kiran Sunan Aunty amani,tana cewa dan Allah su kira mata ƴar uwarta karta mutu bata sata a idonta ba,   ganin shi yasa sauran nurses ɗin dake aciki suka ja da baya tare da bashi wuri don ya wuce,  Ƙarasawa ayaan yayi tare da samun wuri daga gefen gadon da take kwance,yama rasa ta yarda zai shawo kan yarinyar don tayi nisa bata jin kira sai faman sharara kuka takeyi ta cika ko'ina da kukan nata,   tsawa ya daka mata,aikuwa a firgice ta mayar da idanunta akanshi yayin da jikinta yashiga yin kerma saboda tsoran da taji,  Yarda ya zare mata idanunshi ba ƙaramin tsoro taji ba musamman launin kwayar idonshi da takasance ash colour,  Lokaci guda tayi tsit tana faman zazzare idanu,  dama yayi mata hakan ne don tayi shiru,sassauto da murya yayi tare da cewa"faɗamun menene damuwar?bakyaso ne ayi treating wounds ɗin dake ajikin ki?ko so kike ki mutu ne?  Cikin shesshekar kuka tace"banso na mutu,inason ganin Auntyna ne,dan Allah ku kira mun ita tazo naganta kafin na mutu,inason ganinta,"   tsananin tausayinta ne ya kama shi,bin idanunta yayi da kallo ganin yarda hawaye ke kwaranyo daga cikinsu,yarinyar dae ba ƙaramin jiki taji ba da alama,   ajiyar zuciya ya sauke tare da cewa"yanzu baki da lafiya,ki bari su duba jikinki,in yaso zuwa gobe ni dakaina zan kira maki auntynki a waya,kin amince da hakan"?   amsa mashi tayi da eh,sannan ya miƙe tare da yi masu sallama,ya fuce daga asibitin,   shaf shaf suka bar Asibitin da motarsu,
Koda Amani ta koma gida,abbas baiyi mata faɗan komai ba,ko tambayarta inda taje baiyi ba,hakan ba ƙaramin daɗin yayi mata ba,dama fargabarta kenan karya tuhumeta akan ina taje acikin daren nan,
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
_💋Boss Bature💋_
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Amalil Islam
Kwance take saman gadon asibitin hankalinta kwance sai faman sharar bacci take,tasamu kulawa sosai wurin nurses ɗin nan gaba daya duk wani rauni da taji anyi mata dressing ɗin wurin,a daren jiyan nan har ƙarin ruwa su kayi mata fiye da leda ɗaya don taji jiki,da safe kuwa kyakkyawan breakfast tasamu na kyauta da suke rabawa asibitin,sai da taci tayi hani'an sannan tafara wannan baccin,har farkawa tayi tana neman waɗanda suka kawota asibitin don su kira mata Auntynta kamar yarda ɗaya daga cikinsu yayi mata alƙawarin cewa zai kira mata ita, nurse ɗin dake kula da itace ta sanar da ita cewa basu zo ba,sam hankalinta bai tashi ba,don ita ji take koda basu zo ba,ba inda zataje ita fa tayi gida acikin asibitin don ba ƙaramin daɗinshi take ji ba,
Wuraren ƙarfe 12,Motarsu Jahan ta shigo cikin katafaren asibitin,a hankali sukayi mata gurbi a parking space ɗinsu,ɗagowa jahan yayi tare da kallon ayaan dake a gefenshi yace"zan jiraka anan and don't keep me waiting"   Wurga mashi kallo Ayaan yayi tare da cewa"bro kai fa baka da imani na lura,jiya kaine kayi causing accident ɗin nan,yarinyar ta raunata amma ko zuwa ciki ka leƙata bakayi ba,atlease ya kamata kaje ka dubata yau,"   ɗaure fuska Jahan yayi yace"bani ne Sila ba!yarinyarce ta fado mana agaban moto dinmu all of a sudden,har nagaza cin burki,so am not guilty,'   Cikin lallashi ayaan yace"pls mu shiga atare mana,"yarda yayi maganar da ƴar shagwa6a afuskarshi yasa Jahan cewa"taci albarkacin wannan shagwa6ar da kayimun da ba don haka ba,ba inda zanje,"   Murmushi Ayaan yayi tare dasa hannu ya buɗe motar ya fito waje,shima Jahan ya fito daga cikin motar,atare suka jera tare da nufar interior din asibitin,   Ayaan ne ya fara shiga room ɗin da aka kwantar da Amal sannan jahan yabi bayansa suka shiga ciki atare,  Lokacin da jahan ya aza idonshi akan Amal dake baje saman gadon tana sharar bacci,a wani irin firgice yaja da baya yana faman zare ido,  Kallonshi ayaan yayi tare da cewa"meya faru ne bro?naga kamar ka tsorata da wani abu,  Nuna amal yayi da yatsan shi tare da cewa"Ayaan dama wannan halittar muka kwaso acikin motar mu jiya?shiyasa akace rashin sani yafi dare duhu Ya ilahi da nasan hakane da ban sha wahalar ɗaukota ba Allah,dole ayi mana wankin mota yau,"   baki asake ayaan ke kallonshi,duk wani wulakanci da anzo kan Jahan to an ƙare,don shi kankat ne dama yana ɗaya daga cikin waɗanda suka ɗauko ɗabi'un mahaifiyarsu da halayyarta kaf bai bar komai ba,"   girgiza kai kawai Ayaan yayi tare da wucewa wurin gadon da Amal take,wuri yasamu asaman chair ɗin dake fuskantar gadon nata ya zauna yana kallonta gwanin ban tausayi,  Jahan kuwa koda ya matso wurin bed din nata,goya hannun shi yayi asaman ƙirjin shi yana binta da kallo a ƙyamace yace"Anya Ayaan yarinyar nan ma tana numfashi kuwa?karfa mu ƙarasa gawar da ba tamu ba"  Murmushi kawai Ayaan yayi tare da kai hannu ya dan bubbugi pillown da Amal ta kwantar da kanta sama,  Firgigit ta ware idanunta tana faman binsu da kallo ganin mutum biyu iri ɗaya,hannu tasa tare da ɗan murza idanunta tana ƙare masu kallo, lokaci guda ta gane cewa identical twins ne,   "Barka da safiya,ya jikin naki,"?ayaan ne ke tambayarta fuskarshi asake,hakan ne yasa ta gane cewa shine na jiyan nan da yayi mata alƙawarin kiran Auntynta,  Ƙoƙarin tashi Amal tashiga yi,cikin sauri Ayaan ya taimaka mata ta zauna tare da dan tada bayanta a jikin pillown,   Cikin sanyin murya tace"Alhmdllh,naji sauƙi sosai,"   "Kinyi breakfast"? Ya kuma tambayarta,ɗaga mashi kai tayi alamar eh,  Lumshe idonshi yayi tare da cewa"Masha Allah,so now tell me, how can i help u? Zuba mashi ido tayi tana kallonshi,hakan ya tabbatar mashi da cewa bata gane me yake nufi ba,don haka yace"ina nufin taya zan iya taimaka maki ne?wurin haɗuwa da Auntyn naki"?  Cikin sauri tace"ina da numbarta akaina," Amsa mata yayi da okey,sannan ya zura hannunshi acikin trouser pocket dinshi ya ciro wayarshi,karanto mashi numbar Amal tashiga yi shi kuma yana dialling numbers ɗin acikin wayarshi,bayan ya kammala rubuta numbar ya buga call ɗin nan take Sunan Matar yaya ya bayyana akan wayarshi,tsananin mamaki ne ya kama shi aranshi yace wannan ae numbar Amani ne matar Yaya Abbas,kanshi ya gama ɗaurewa a lamarin,har kiran ya katse amani bata ɗaga ba,almost 6 times yana kiran numbarta amma ba'a daga ba,hakan yasa ya ɗan dakata tare da kallon Amal yace"idan ba damuwa inason jin yaya kuke da Auntyn nan taki da kika ban numbarta....'tunkan ayaan ya ƙarasa maganar jahan ya buga tsoki tare da cewa"Ayaan am tired ka tashi kawai mu tafi,bansan menene amfanin tambayarta ba,   mayar da idonshi yayi akan na Jahan yace"pls ka bani time,zan faɗa ma dalilin dayasa nake tambayarta,"  tsuke fuska jahan yayi yana faman hura hanci,   "Ina sauraronki," muryar ayaan ce ta katse mata tunanin data tafi,  Murya asanyaye tace"ƴar uwatace ita,na jima ina nemanta bamu ta6a haɗuwa da ita ba,ita ma kuma nema na takeyi,tunda tayi aure na rabu da ita,shine yanzu nasamu sunan garin da take nazo,amma bansan a ina zan sameta ba,abu ɗaya kawai nake dashi numbar wayarta,drivern daya kawoni ya kirata a waya ya sanar da ita cewa tazo ta ɗauke ni,batazo ba shine wasu mutane suka biyoni acikin tashar,wannan ne dalilin dayasa nayi gudu harna faɗa saman titi Motarku ta buge ni.........'   jinjina kai Ayaan yayi tare da cewa"Yanzu idan na kaiki gidan Auntynki,Ni kuma wani tukuici zaki bani,"   cike da mamaki tace"kasan inda take ne"?  Lumshe idonshi yayi tare da cewa"a'a bansan inda take ba,amma inaso zan kaiki wani wuri in ba damuwa,bari nasa doctor ya sallame ki,sai mu tafi atare,Zaki bini?   shiru ta danyi tana tunanin karfa tayi gangancin binsu wani abu ya faru da ita,tunda ita dae batasan ko su wanene ba,amma ta wani 6angaren taji cewar zata iya binsu saboda ta yarda dashi sosai,ba don komai ba sai don yarda yake yi mata magana cikin lallami,"   amsa mashi tayi da eh,miƙewa ayaan yayi daga saman chair din,ruƙo hannun jahan yayi tare da janshi gefe guda yace"ko kasan cewa numbar da yarinyar can ta bani na kira mata auntynta,ta matar Ya Abbas ce Amani!"  Fuska ɗauke da mamaki Jahan yace"Really?kenan ƙanwarta ce ita,amma indai hakane ya akai ita yarinyar ta kasance haka?  Ayaan yace"abunda nake tunani kenan nima,"   jahan yace"Ba shakka,dama na jima ina tunanin taya akai Ya ishaq da Ya Abbas suka auri waɗannan matayan nasu,Nidae raina ya jima yana bani cewa matsiyatan talakawa ne,saboda koda mu kaje ɗaurin aure fa a maid,bakaga tsohonsu ba wani zararre dashi,yadin jikinshi duk ya koɗe,zariyar wandonshi fa har ƙasa take ja,abun kunya...'  Rufe mashi baki Ayaan yayi cikin sauri saboda yarda yake magana yana ɗaga Voice ɗinshi,yarinyar zata iya ji,   "Pls jahan its okey,mubar wannan zancen nidae yanzu so nake mu ɗauki yarinyar mukaita gidan Auntyn nata...'tunkan Ayaan ya ƙarasa maganar Jahan yace"Wai a motar wa kake nufin za'a kaita?ae wlh waccan sauran ramin bazata ƙara zauna mana a motar mu ba,sai dai ka tsaida taxi ta kai ku atare,ni kaga tafiyata"yana kai ƙarshen maganar tashi ya juya tare da fucewa daga cikin room ɗin,   girgiza kai kawai Ayaan yayi tare da cewa"sai yanzu nasan da wa nake tare,Jahan sam baka da mutunci,haihuwarmu kawai akai atare amma zuciyoyinmu ba iri ɗaya bane,ni ta 6angaren Abba nake kai kuma ta 6angaren Mommynmu kake da kuma Ammi dama sune masu zafi,'
Batare da 6ata lokaci ba,Ayaan yasa aka sallami Amal ba don komai ba sai don yayi suprising É—inta,kamar yarda jahan yace sai dai su hau taxi hakan ce tafaru,a bakin Hospital ya tsayar masu da taxi suka shiga ciki atare,
**********************Reeshi
Zaune suke acikin class sun natsu suna sauraron karatun da akeyi masu,malaminsu ne mai koyar dasu islamic studies,tun da ya fara karatun ya lura da yarinyar dake kwance tana yi mashi bacci acikin class,shiru kawai yayi baice komai ba,sai da ya kammala karatun sannan yace"wacece waccan yarinyar dake yi mun bacci acikin class"?ya tambaya yana nuna sehrish da maker ɗin hannunshi,  kamar jira ƴan class ɗin sukeyi ya tambayesu nan fa kowa yashiga bada bayani,   "Uncle ae wannan yarinyar da kake gani sleeping sickness gare ta,ba'a ta6a yin darasi ba idonta biyu,kullum cikin bacci take kamar mai tsohon ciki," fashewa da dariya ƴan class din sukayi,  Wani kuma yace"sir,da zarar tearcher ya shigo cikin class shikenan zaka ga ta fara hamma,daga nan sai bacci,"   Bayan ya gama sauraron bayanansu,ya taka ya ƙarasa inda seat din sehrish yake,hannu yasa tare da ɗan bugun desk din,a firgice sehrish tafarka tare da ɗago da kanta daga saman desk ɗin tana kallonshi,   jallabiya ce ajikinshi fara,ya tara dogon gemu,kana ganinshi zaka san cewa ba ƙaramin malamin addini bane,fuskarshi na manne da farin glass yayin da kanshi ke anaɗe da rawani,    hankali tashe sehrish ke kallonshi tayi wuƙi wuƙi da ido saboda tsoran karya hukunta ta akan baccin da take yi mashi a class,   Cikin harshen larabci yace mata ta miƙe tsaye,jiki na rawa sehrish ta miƙe tana faman zazzare ido,   "Kalli cikin idona,"ya bata umarni,sunnar dakai sehrish tayi tana faman jin wani irin bugun zuciya,maimaita mata ya sake yi da cewa"bakiji me nace ba!ki kalli cikin idona!"   ƙin ɗagowa tayi da idonta ta kalleshi,kuma nan take jikinta ya shiga yin kerma,  Ƴan class ɗin duk sun zuba ido suna kallonsu,musamman amrish da tashiga damuwa ganin kamar malamin nason takurawa ƙawarta,  Cikin sauri tace"pls uncle ayi mata afwa,bazata ƙara ba,'  Batare da ya kalleta ba yace"Amrish ba laifi tayi mun ba,in fact nikeson taimakonta,shin wannan yarinyar ƴar wani gida ce"?ya tambaya yana jiran amsarsu,har lokacin sehrish na tsaye kanta na kallon kasa a matuƙar tsorace take,   amsa mashi su kayi da cewa"bamu san a wani gida take ba,lokacin da aka kawota class ɗinnan tayi introducing ɗin kanta amman bata faɗa mana family status ɗinta ba,,'  Amrish tace"nima bansan taƙamaimai daga inda take ba,amma akwai wani elder bro dinta dana sani sunan Shi Junaid romeo,muna shiri sosai dashi,'  mayar da idonshi yayi kan fuskar sehrish yace"Ke!a wani gida kike?su wanene iyayenki?  murya na rawa tace"Ni....ni..daga family din SALAHUDDEEN HUSSEIN nake Abban sojoji....'tunkan ta ƙarasa maganar malamin ya waro ido waje yana kallonta,bama shi ba hatta sauran student ɗin cike da mamaki suke kallonta,sun jinjinawa gidan da tafito bakomai yafi ɗaure masu kai ba face yarda ta kasance ba ruwanta da kowa haka,bayan duniya tasan da zamansu,  "Kina nufin ke ƙanwar Surgeon genaral rafayet ce!da marshal Omar!"? Amsa mashi tayi da cewa"eh,"kuma har lokacin bata ɗago da ido ta kalleshi ba,  Jinjina kanshi yayi yana tuna wani abu daya ta6a faruwa dashi wanda ke da alaƙa da gidan,"    gajiya da tsayuwa sehrish tayi nan take idonta suka soma shararo da kwalla,don bata da juriyar wahala irin hakan,tun lokacin data fara rayuwar hutu da jin daɗi,   "Insha Allah bazan fasa ba,kamar yarda nayi kyakkyawar niyyar taimakawa tun a lokacin baya,don haka zan taimaka maki tunda Allah ya haɗani dake," malamin ne yayi wannan maganar,sannan ya mayar da idonshi kan amrish dake zaune a seat ɗinta tana kallonsu yace"Amrish idan na kammala yi maku karatu ki same ni a office ɗina zan baki ruwan addu'a kiba wannan yarinyar tayi amfani dashi," Amsa mashi tayi da toh sir,sannan yaja da baya tare da juyawa ya koma wurin board,   Jiki asanyaye sehrish ta koma tare da zaunawa tana faman sauke ajiyar zuciya,aranta tana mamakin ruwan addu'ar mi zai bama amrish ta bata,gaskiya ni bazanyi amfani dashi ba,lafiya ta lou,koya ban zubarwa zanyi.......'  Sai faman sambatu takeyi ƙasa ƙasa sam takasa samun natsuwa har sai da Malamin yabar Class ɗin,tashi amrish tayi tare da binshi don ta amso mata ruwan addu'ar dayace zai bata.
bayan mai taxi ɗin ya sauke su,hannunshi ruke dana Amal suka shiga cikin gidan,gaba ɗaya duk tabi ta susuce tana kallon katafaren gidan duk a tunaninta kodai gidansu ne ya kawo ta? Lokacin da suka shiga katafaren palourn babu kowa acikin shi,tsayawa yayi tare da ita atsaye yana jiran ganin ko wani zai fito,ita kuwa Amal wuyanta kamar zai tsinke saboda kalle kalle muryar Ayaan ce ta katse ta da cewa"har yanzu ciwon na maki zafi?girgiza kai tayi tare da cewa"a'a babu zafi ina lafiya,"  "Okey,ki ɗan ƙara jira nasan matar gidan zata fito ne,bari na sake kiran layinta,"  Hannu yasa tare da ciro wayarsa yana ƙoƙarin danna ma Amani kira,kunnan shi suka jiyo mashi takun takalmanta kwas kwas,ɗagowa su kayi gaba ɗaya suna kallonta,hannunta na ɗauke da tray da alama kayan breakfast ɗinsu da suka ci na safen nan ta fito dashi daga bedroom ɗinta dake a upstairs,jallabiya ce fara ajikinta ta yafa mayafin akanta,  A hankali take saukowa down stairs sam bata lura da mutane ba,ƙura ido Amal tayi tana kallonta sam takasa gane wacece,juyawa ta danyi tare da kallon Ayaan tana neman ƙarin bayani,a lokacin shima idonshi na akanta yace"baki gane ta ba ko"?  ɗaga mashi kai tayi alamar eh,murmushi yayi tare da cewa"Bari ta matso kusa,"  Gyaran murya Ayaan yayi wanda hakan yasa Amani tayi firgit tana kallonsu,murmushi ta saki ganin Ayaan cikin sauri taƙarasa saukowa daga saman stairs ɗin ta tunkaresu,zuba mata ido Amal tayi tana kallonta tabbas taso ta shaidata amma abunda yayi confusing ɗinta shine,taya zata kasance wadda take tunani tunda saurayin ya kawota gidan tafi tunanin ko Auntynshi ce,  Tunkan Amani ta ƙarasa inda suke,hankalinta yakai ga Amal binta da kallo ta dinga yi cike da mamakin ina Ayaan ya samo wannan yarinyar haka,duk taji jiki kodai ya fara taimakon marayu ne,  tsayawa tayi kusa dasu idonta na akan Amal ita ma kallonta takeyi,ji tayi gabanta na faɗuwa rasss rassss,cikin sauri ta mayar da idonta akan Ayaan murya na rawa tace"who...who is she pls?   Murmushi ayaan yayi yace"i don't even know,ni dai ta bani numbar auntynta ne tace na kira mata ita,shine dana sa numbar Auntyn nata sai sunanki ya bayyana akai,that's why nayi deciding kawota wurinki,maybe adace.........'tunkan ya ƙarasa maganar a firgice Amani ta saki tray ɗin hannunta ya tarwatse ƙasa,zube wa tayi saman guiwowinta kusa da Amal ɗin ta ruƙo hannunta tana cewa"Amal kece dagaske nake gani,ko idona ne Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"!!!  Tuni hawaye sun cicciko acikin idonta,  Itama Amal ɗin tuni ta fara shararo hawaye saboda ta ganeta yanzu musamman data ambaci sunanta,  Cikin shessheƙar kuka tace"Ni...Ni ce aunty Amani,ashe dama zan sake ganinki arayuwata.........'kukane yaci ƙarfinta hakan ne yasa takasa ƙarasa maganar,atare suka fashe da kuka suna yi kamar kamar me,   Muryar Ayaan ce ta katse su da cewa"pls Aunty amani,ki lallasheta akwai wounds ajikinta idan tana kuka hakan zai ƙara mata raɗaɗin ciwon,"dakyar Amani ta tsagaita da kukan nata kallon fuskarta har izuwa jikinta,tayi matuƙar tsorata da ganin yarda yarinyar ta tsotse ta rame ta ƙanjame kamar kwarangwal,ƙashin wuyanta kamar zai ballo waje,komai na yarinyar da zai nuna cewa ita macece babu shi,sai dai ta hanyar shigarta ta mata da kuma muryarta,   Janyota tayi ajikinta tare da rungumeta sosai tana ci gaba da ambaton sunanta"Amal amal ɗita ce ta koma haka?meya faru dake Amal ya akai kika 6ata,ki ka tafi kika barni inata nemanki Amal,"  Ganin halin da suka shiga yasa Ayaan yanke shawarar tafiya yabarsu,juyawa yayi kawai tare da kama hanya ya fuce daga falon dama jahan sai doko mashi calling yake,
 Anan ƙasa Amani da Amal suka zauna atare suna fuskantar juna,  "Amal kina jin yunwa"? Jin wannan tambayar yasa hawaye suka ƙara cika mata ido,yaushe rabon da wani ya tambayeta tana jin yunwa harta manta Allah sarki ɗan uwa mai ɗaɗi,musamman in ya kasance shaƙiƙin kane kuma kuna son junanku,   Murya asanyaye tace"bana jin yunwa naci abinci a asibiti,"   Jinjina kai Amani tayi tare da cewa"inason jin Ya akai kika 6ata Amal kika barni?mammy ta sanar dani cewa bakyajin magana wai kina zuwa yawo sun hanaki kin ƙiya shine kika 6ace aka neme ki aka rasa....'   Girgiza kai tashiga yi yayin da hawaye ke cigaba da sharara a idonta tace"Aunty amani wannan duk ƙaryace suke yi maki!nagode ma Allah da ya haɗani dake,a yau inaso zan sanar dake komai game da irin cin zalin dasu Mammy sukayimun na raba ni dake,   Hankali tashe Amani ke kallonta murya na kerma tace"faɗamun meya faru dake!wani irin cin zalin su kayi maki,"  Batare da 6ata lokaci ba,Amal ta zayyana mata duk irin ƙarairayin da sukeyi mata akan cewa ta 6ace,da kuma irin wahalar da takesha a hannunsu da kuma kaita da sukeyi gidan makwabtansu ana kulleta,babu abunda Amal ta 6oye mata kaf takwashe ta sanar da ita,  A kiɗime Amani ta miƙe tsaye cikin tsananin 6acin rai,jikinta har kerma yake yi,wasu irin zafafan hawaye ne suka shiga shararowa a idonta,   Sai faman cizon yatsa take yi tana danasani,kai aƙarshe data rasa abunyi sai ta sake fashewa da wani matsanancin kukan tana girgiza kai tana cewa"Wlh bazan ta6a raga masu ba!mugaye azzalumai kawai,banta6a ganin mutane masu zuciyar kafirai ba irin tasu,Sun cutar dake Amal kuma sun cutar dani sun yaudareni sunyi mun ƙarya suna samun kuɗi awurina na cewa za'a ba malamai suyi addu'ar neman sa'a akanki ashe duk ƙarya ne!!!!basu tsaya a iya kanmu ba sun cutar da mahaifiyarmu har saida tabar duniya ga mahaifinmu da suke ta gana ma azaba,nayi tunanin soyyaya suke nuna min ta ƴan uwantaka shiyasa na saki jiki dasu har nake ƙoƙarin taimaka musu wurin cimma wannan mummunan ƙudirin nasu,ashe cutata suke suna can suna gana ma ƙanwata azaba,na cuci kaina!tun yanzu Allah ya fara nunamin irin kuskuren da nake ƙoƙarin yi na taimakama waɗancan bijimayen.......'tsagaitawa tayi da maganar tana faman shessheƙar kuka,daga bisani ta ɗaura da cewa"wlh saina tarwatsa duk wani plan ɗinsu uban kowa ya rasa don bazan kyalesu ba,muddin ina numfashi hayaam ko abra ɗaya daga cikinsu bazai ta6a auran jinin salahuddeen hussein ba!!!!, abun ba ƙaramin ƙona ma Amani rai yayi ba,ta fusata ainin zuciyarta har wani tafarfasa take yi saboda 6acin rai, Hannu tasa tare da matse kwallarta sannan ta juya tare da takawa takai hannu ta ruƙo hannun Amal ta miƙar da ita tsaye,sannan ta wuce da ita cikin bedroom ɗinta gado ta nuna mata tare da cewa"Amal ki kwanta ki huta kin raunata sosai,amma karki samu damuwa tunda Allah ya haɗaki dani ƙarshen wahalar ki tazo insha Allah,zakiyi rayuwa tare da Auntynki zan baki kyakkyawar kulawa,kuma zan kira doctor domin ya ƙara dubamin lafiyarki da kyau har kiji sauƙi, Ba ƙaramin daɗi Amal taji ba farin ciki har bakinta ya gaza rufuwa,sai da amani ta tabbatar cewa Amal ta kwanta sosae saman gadon sannan ta zauna daga gefen gadon tana kallonta har bacci yayi awon gaba da ita,amani bata bar wurin ba,kallonta take hawaye na zuba a idonta haƙiƙa su Mammy da Aunty babba ba ƙaramin cutarta su kayi ba, Jinjina kai tayi tare da cewa"rama cuta ga macuci ibada ne,Aunty laila kin shiga uku dani,zanbi duk hanyar da zanbi don ganin na tarwatsa plan ɗinki,dama ke jani talau ce sai yarda akai dake sannan kike bi,zanyi amfani da wannan damar wurin lalata shirinki" Haka Amani ta dinga tufka da warwara a ƙarshe ta shirya nata plan ɗin. **************** Hayaam na zaune saman gadonta hannunta ruƙe da wayarta tana jiran shigowar kiran Sofwan,harta fidda rai da zai kawo mata trolley ɗin sai ga message ɗinshi ya shigo wayarta,cikin sauri ta buɗe tana karantawa, _hi beb ya kike ya kwanan gidan surukai ina fata kina lfy,nafa zo gidan ki turo wani ya amsar maki trolley ɗin kayan,don bazasu bar ni nashigo ba_ Jin hakan yasa tayi saurin saukowa daga saman gadon tare da ɗaukar dogon hijabinta dake ajiye saman gadon,zurawa tayi ajikinta sannan tafito daga cikin bedroom ɗin,kama hanya tayi ta fito main palour ɗin tana wurga ido don tasamu wanda zai kar6ar mata kayanta,tana cikin wannan tunanin sai ga Fawan ya fito daga part ɗinsu, kwala mashi kira tayi cike da kisisina tace"Fawan"! ɗagowa yayi yana kallonta da wannan kallon nashi na rainin wayau, cikin sauri hayaam ta nufe shi sai da tazo kusa dashi sannan tace"dan Allah taimako nakeso kayimun,wani brother ɗina ne ya kawo mun trolley ɗin kayana,an hanashi shigowa ciki shine nace ko zaka taimaka ka amso mun," Yatsina fuska fawan yayi tare da cewa"Am sorry ni bazan iya wannan wahalar ba,zan dai kira ɗaya daga cikin security guards ɗin na basu umarnin su barshi ya shigo abokina ne inyaso sai kije ki kar6o kayanki," washe baki hayaam tashiga yi tana cewa"thank u so much fawan,kana da mutunci sosai naji daɗin taimakonnan da kayimun,' ɗan ta6e baki fawan yayi tare da kai hannu ya ciro wayarshi a aljihun rigarshi,call ya buga tare da kara wayar a kunnanshi,ɗaga kiran akayi sannan ya sanar dasu cewa subarshi ya shigo abokinshi ne,amsa mashi sukayi sannan ya kashe kiran, batare da ya kalleta ba yace"kije ki amso kayanki," da hanzari Hayaam ta juya tare da kama hanyar fucewa daga falon sai faman sauri take yi kamar zata tashi sama, Ruƙe ƙugu fawan yayi tare da cewa"Ikon Allah,nifa bangane ma Yarinyar can ba,Naji tana cewa zata amshi trolley ɗin kayanta me hakan ke nufi"?ya jefa ma kanshi tambaya,cizon la66ansa yayi tare da cewa"zaki gane kuranki ne,"yana faɗin hakan ya kama gabansa
*💋Boss Bature💋*
Wuraren ƙarfe 1:30 junaid ya ɗauko sehrish daga school,tun acikin mota ya lura da yanayinta duk a yamutse babu natsuwa a tattare da ita,har tambayarta yayi ko bata jin daɗine,sai ta sanar dashi cewa bacci ne kawai take ji,jin haka yasa ya ƙara gudun motar har suka ƙaraso cikin gidan, Fitowa tayi daga cikin motar tare da komawa ta buɗe back seat ɗin ta curo school bag ɗinta sannan ta wuce cikin gidan da sauri, Abun ya ɗaure ma junaid kai,ganin ta tafi batare da ta jirashi ba kamar yarda suka saba shiga cikin gidan hannunsu ruƙe dana juna, hannu yakai tare da buɗe motar ya fito bayan ya rufeta,ya kama hanyar shiga interior ɗin gidan,koda ya shiga main palour ɗin kai tsaye ya wuce upstairs bedroom ɗinshi don shima a gajiye yake, wani irin zazza6ine ya rufar mata,dama tun lokacin da suka haɗa ido da wannan malamin taji gaba ɗaya yanayinta ya sauya,tana shiga bedroom ɗinta tayi wurgi da school bag ɗin ƙasa,sannan ta faɗa saman gadonta tare da kwantawa tana faman juyi asaman shi, A wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita, Turo ƙopar bedroom ɗin nata junaid yayi anan ya same ta tana ta faman sharar bacci ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa zai fuce daga ɗakin karaf idonshi suka sauka akan Bottle water ɗin da malamin nan yaba Amrish takai mata,ashe lokacin da ta shigo ɗakin tayi wurgi da jakar nan take robar ruwan ta gangaro daga cikin jakar,saboda ta manta bata rufe zeep ɗin wurin data sanyata ba, Murmushi junaid yayi yace"Oh ni reeshi kamar wata ƙaramar yarinya,wai yawo da robar ruwa acikin school bag hmmm,"yayi maganar tare da ƙarasawa yakai hannu ya sungumi robar ruwan, Jin salaf babu sanyi ajikin robar ruwan yasa shi cewa"bari naje na sanya mata shi a fridge,zai fi daɗin sha," Yana ƙarasa maganar ya juya tare da fucewa daga ɗakin nata,kai tsaye ya wuce wurin fridge ɗinsu,hannu yakai tare da buɗewa ya sanya robar ruwan aciki,sannan ya mayar ya rufe ya kama hanya yabar wurin,
After some minutes sai ga su twins sun faɗo cikin main palour ɗin dawowarsu kenan daga masallaci,raba hanya su kayi Jahan ya wuce bedroom ɗinsu,shi kuma Ayaan ya wuce wurin fridge saboda wani irin ƙishin ruwa da ta zo mashi,hannu yasa tare da buɗe fridge ɗin,ya ɗauko bottle water ɗin da Junaid ya ajiye, Buɗe murfin yayi tare da kafawa abakinshi ya shiga ɗaɗɗakar ruwan,sai da yayi rabin robar ruwan sannan ya mayar da ita cikin fridge ɗin ya ajiye, Shafa ƙirjinshi yayi tare da cewa"Alhamdulillalh yanzu naji wani sanyi ya ratsa maƙoshi na," Yana faɗin hakan ya nufi bedroom ɗinsu,lokacin daya shiga samun Jahan yayi kwance yana jiranshi ya ƙaraso, ɗaga kafar da zaiyi kenan yaji gaba ɗaya jikinshi ya shiga jijjiga ta ko'ina,ganin hakan yasa jahan tashi daga zaune yana cewa"lafiya Ayaan meke faruwa ne!! A wani irin galabaice Ayaan ya zube saman guiwowinshi yana ambaton sunan Allah abakinshi,kafin Jahan yayi wani yunƙurin durowa daga saman gadon tuni ayaan ya yanke jiki ya faɗi kasa abaje idonshi na kallon ceilling yayin da launin idanunshi suka 6ace 6aat sai farar kwayar idon, "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un," jahan ne ya ambaci hakan a lokacin da ya ƙarasa durowa daga saman gadon ya ƙaraso a hanzarce inda Ayaan yake, ya zube saman guiwowinsa agabanshi,hankali atashe yake ambaton sunan shi "Ayyaaan!!!Ayaan dan Allah ka tashi!meke faruwa dakai ne rabin raina!!.,....' ganin bai da wata mafita yasa ya miƙe da gudun gaske ya fuce daga ɗakin nasu don yaje ya sanar ma wani, Fitar Jahan ke da wuya,wani siririn hayaƙi baƙi wulik ya dinga fitowa daga ƙofofin hancinshi da kuma bakin shi,da yawan gaske hayaƙin ke kurɗaɗowa ya mamaye ko ina,kafin wani lokaci ya disashe tare da 6ace wa 😳😳😳
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727. Â
  _💋Boss Bature💋_
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Am really sorry 4 the late post👌
Wata irin zufa ce ta soma tsastsafo mashi a jikinshi kamar wanda aka tsamo daga cikin ruwa,lokaci guda yashiga Sakin atishawa yafi talatin a jere suke fitowa daga bakinshi,daga bisani kuma a hankali launin kwayar idonshi ya bayyana,komai nashi ya dawo yarda yake,ganin shi kwance a ƙasa yasa shi yin hanzarin miƙewa tsaye yana tunanin wai menene yakai shi ƙasa kwance?me ya faru dashi ne?hannu yasa yana shafo zufar dake a gefen fuskarshi har lokacin bata daina zuba ba,hakan yasa ya nufi toilet tare da shigewa ciki don yayi wanka,
Bai jima da shiga ba sai ga Jahan ya faɗo ɗakin yana atare da kanal yousouf,tsayawa su kayi abakin ƙopar ɗakin,Jahan na mamakin Ina ayyan daya bari cikin wani hali yashe a ƙasa Kallon shi kanal yousouf yayi tare da cewa"Kace mun Ayaan ya faɗi ƙasa jikinshi na kerma,gashi kuma ni banga Ayaan ba,"  Fuskarshi aruɗe yace"Ya yousouf nikaina abun ya ɗaure mun kai,nan fa nabarshi kwance cikin wani yanayi yanzu kuma babu shi a wurin," jin hakan yasa hankalinsu tashi su duka biyun,  tsayawa su kayi kowa da abunda ranshi ke bashi,suna cikin tsayuwar nan sai ga Ayaan ya buɗe ƙopar toilet tare da fitowa jikinshi ɗaure da towel,ga danshin ruwan dake ajikinshi alamar wanka yayi,abun ba ƙaramin ɗaurewa jahan kai yayi ba hatta kanal yousof ɗin,shi kuwa hankalinshi kwance har zai gifta ya hangesu tsaye ta wutsiyar idonshi,hakan yasa ya ɗan ja da baya tare da juyawo yana kallon su,cike da mamaki yace"Ya yousouf!Jahan!meya faru naganku a tsaitsaye kunyi curko curko?ko lafiya,"?   ajiyar zuciya jahan ya sauke tare da tunkarar shi kai tsaye ya rungumo shi ajikinshi yana ɗan bubbuga bayanshi yace"babu komai ayaan,nashiga damuwa ne ɗazu dana ga ka yanke jiki ka faɗi nayi tunanin kowani mummunan abune zai faru dakai that's why nayi deciding kiran ya yousouf don yazo ya duba min kai," ya ƙarasa maganar tare da raba jikinshi daga na Ayaan,   "Nifa lafiyata lou,babu abunda ya faru dani,kawai jiri ne ya ɗan ɗebe ni but now Alhamdulillah har wani ƙarfi nake ji ajiki na,ko in gwada maka ka gani," yarda yayi maganar tare da ɗaga masu damtsen hannunshi ba ƙaramin dariya ya basu ba,girgiza kai kawai kanal yousouf yayi tare da juyawa ya fuce daga ɗakin,   wucewa Ayaan yayi ya nufi mirror,cikin sauri Jahan ya bishi tare da hugging ɗinshi ta baya ya kwantar da kanshi a saman kafaɗar Ayaan,   Shiru Ayaan yayi yana tunanin mai jahan ke ƙoƙarin yi mashi ne,menene dalilin rungumar da yayi mashi ne hada wani kwantar da kanshi a saman shoulder ɗinshi,bai ƙarasa zancen zucin nashi ba,yaji hannun Jahan agabanshi yana ƙoƙarin zame towel ɗin jikinshi,aikuwa a wani irin firgice ya ka6e mashi hannunshi tare da yin wurgi dashi gefe guda,sannan ya juyo fuskarshi a ɗaure yace"Jahan bana son iskanci!menene haka?bakasan me ka kama mun bane?so kake ka ciremun towel ɗin jikina ne!"  Murmushi Jahan ya saki tare da cewa"Ayaan banason irin wannan wasan pls,ka riga da kasan abinda nake buƙata a wurinka,"   Fuska ayamutse Ayaan ke kallonshi,ganin hakan yasa jahan tunanin cewa kodai bai jin daɗine duba da abunda ya faru dashi ɗazu,bai ƙara yi mashi magana akan abun ba saboda yasan cewa jarabar tashi zata motsa ne kuma zaizo ya sameshi ne,komawa yayi saman gadon tare da kishingiɗawa yana kallon Ayaan daga kwancen da yake, Ganin yarda jahan ke zuba mashi ido ko kawar dakai baiyi,hakan yasa shi tsuke fuska tare da barin gaban mirrorn ya shige can cikin ɗakin don ya sanya sutura,sa6anin da basa jin kunyar wannan bawani abu bane awurinsu in ɗaya ya tu6e kaya agaban ɗayansu.
â¤ðŸ¤ðŸ’?
Around 3:30,sehrish ta farka tana faman murza idanu,ba ƙaramin bacci tasha ba,sai hamma take saboda wata irin yunwa dake cinta,dama ko a school bata wani ci abun kirki ba,hannu tasa tare da yakice hijabin dake jikinta tayi wurgi da ita gefe guda,sannan ta zuro ƙafafunta tare da saukowa daga saman gadon,tsayawa tayi tana kallon school bag ɗinta da tayi wurgi da ita ƙasa bakomai ya faɗo mata a rai ba face Ruwan addu'ar da Malamin nan mai farin glass ya bata,ƙarasawa tayi tare da zuƙunnawa ta janyo bag ɗin,tana dudduba cikinta sam babu roban ruwan aciki,abun ya ɗaure mata kai,hannu tasa tare da zazzage kayan cikin jakar duka amman babu robar ruwan,  Tunanowa tayi da abunda Amrish ta faɗa mata"Ga ruwan addu'ar da malaman yace na baki,kuma yace indai bakiyi amfani dashi ba,ƙusumbi zai fito maki abayanki,"waro ido waje sehrish tayi tuna wannan maganar ta amrish nan take yatsun hannunta suka shiga kerma hatta la66anta,gaba ɗaya duk tabi ta rikice ba don komai ba sai don tsoran ƙusumbin da akace zai fito mata,mugun tsoran ƙumbin take yi saboda taji ana cewa aljanune ke ajiya a cikin ƙusumbin,ƙyamar abun take ji,   Hawaye ne suka soma wanke mata fuskarta murya na rawa tashiga furta"innalillahi wa'inna ilaihir rajiun, nashiga ukuna!wayyo Allah na,yanzu ya zanyi?nan fa na ajiye robar ruwan nan amma yanzu na duba babu ita.....yanzu shikenan ƙusumbi zai fito min ya suffata zata koma tare da ƙoƙo abayana............'fashewa tayi da matsanancin kuka,anan wurin ta tsugunna tana matse kwalla duk tabi ta rikita kanta,sai da tayi mai isarta sannan ta miƙe tana faman shasshekar kuka takai hannu tare da tattara books ɗinta tana mayar dasu cikin school bag din,bayan ta kammala ta ɗauke jakar taje ta ajiyeta,   Rage kayan jikinta tayi,ya rage daga ita sai white short da half vest,sannan ta shige cikin toilet cike da kasala,  Ta jima acikin toilet din kafin ta fito jikinta ɗaure da towel,har lokacin idanunta na cike tab da hawaye,zulluminta ƙusumbin da akace zai fito mata,saboda tasan in hakan ta faru hatta Junaid sai ya guje ta,shi da yafi kusa da ita,da wannan yanayin ta kammala shirya kanta cikin wando palazzo maroon colour tare da halter shirt black colour,just imagine it ba ƙaramin kyau rigar tayi mata ba,ta ɗame jikinta sam rigar bata da hannu amma ta rufe ƙirjinta har neck ɗinta ta zagaye shi,komawa tayi gaban mirror tana feshe jikinta da turaren nan nata mai ƙamshin gaske,kafin daga bisani ta ɗauko ribbom launin wandonta maroon colour,tattare gashin tashiga yi zata ɗaure shi amma ina duk yadda taso ta haɗe shi wuri guda ta ɗaure abun yaci tura,har wani huci takeyi saboda 6acin ran yaƙi ɗauruwa,tana cikin dambe da gashin,taji ana kwankwasa mata ƙopa,dakatawa tayi da ɗaure gashin tace"Wanene,"  "Auntynki ce,"muryar azmee ce ta bata amsa daga waje,   ƙarasowa Sehrish tayi tare dasa hannu ta buɗe mata kopan,sanye take cikin hijabi hannunta ruƙe da cazbaha fuskar nan ɗauke da murmushi tace"irin wannan kyau haka? . sunnar dakai sehrish tayi tare da cewa"Ina yini aunty azmee,"  "Lafiyalou,tun ɗazu naso nazo na dubaki amma bansamu hali ba,ya school ɗin"?  "Alhamdulillah Aunty azmee," "ina fata kina lafiya,naga kamar akwai damuwa a fuskarki"?  girgiza kai sehrish tayi tace"a'a lafiyata lou,dana dawo ne bana ɗan jin daɗin jikina shine na kwanta nayi bacci sosai banjima da tashi ba,shiyasa fuskata take a haka,"  Jinjina kai azmee tayi tare da cewa"okey,nagane ina fata kinyi sallah,  "A'a yanzu nake shirin yi," Azmee tace"okey ya kamata ki hanzarta yi time har zai wuce,"  Ta ƙarasa maganar tare da juya zata fita,tsayawa ta ɗanyi tare da jiyowa tana cewa"Oh namanta ban faɗa maki ba,ɗazu da safe da kika tafi school,hayaam ce taje kaima Sgr breakfast ɗinshi,'  Jikin sehrish ne yayi sanyi tunkan ta ƙarasa jin abunda takeson faɗa mata tasoma jin jealous a zuciyarta,  "Yanzu kenan itace zata cigaba da kula da part ɗinshi tana kai mashi abinci"?yarda sehrish tayi maganar taba azmee dariya,saboda a wani irin yanayi na tashin hankali tayi tambayar,   "Kin tari numfashi na baki bari na ƙarasa maganar ba ai,Hayaam takai mashi abinci amma baici ba yace ta mayar dashi saboda shi ba'a sharing a aikinsa,yafison mutum ɗaya daya fara yi mashi aiki yaci gaba da yi batare da an canza mashi wani ba,ko kuma mutum biyu na mashi aiki at thesame time bayaso,"   Wani irin ƙayataccen murmushi sehrish ta saki,farin ciki kamar anyi mata albishir da gidan Aljanna,tama rasa bakin magana sai faman zabga murmushi take,   Azmee taci gaba da cewa"yanzu haka tun safe ba'a gyara mashi bedroom ɗinshi ba,na dai kai mashi breakfast ɗinsa,amma ban gyara ba saboda ba aikina bane,aikinki ne don haka da zarar kin kammala salla ki hanzarta zuwa ki gyara mashi part ɗinshi before ya dawo,"   Dakyar Sehrish ta iya amsa mata da toh,kamar jira take azmee tabar ɗakin tana fita tashiga daka uban tsalle tana rawa don murna,   Sam ta manta da maganar roban ruwanta da take nema,   Sai da tayi salla sannan ta koma gaban dressing mirror ta shafa jan baki launin wandonta maroon colour ba ƙaramin kyau yayi mata ba,bayan ta gama ta kara feshe jikinta da turare sannan ta koma wurin wardrobe ɗinta tare da ɗauko mayafinta,ta yafa shi ajikinta,ta ɗauko takalmi baƙi ta zura a ƙafarta Open toe mai ɗan tsini,sai gashi ta fito ɗass da ita,   hannu tasa tare da buɗe door din ɗakin ta fito tare da kama hanyar fita daga corridor din,  Adaidai lokacin Hayamm ta fito daga masaukinta,itama ta ɗauki wankan lace mai ɗan karan kyau,riga da skirt ash colour,kayan sun matseta sosai,daga saman rigar kamar boobs ɗinta zasu fito waje gaba ɗaga,skirt ɗin kuwa wata tsaga gare shi tun daga guiwar ƙafarta tafara har wurin ƙafarta kana hangen fatar ƙafafunta,high heels ne a ƙafarta tana tafiya sautin na fita kwas kwas,ta cuge ɗaurin ɗan kwali abunta yarda kasan wadda zata gasar miss world   jin takun tafiya yasa sehrish jiyuwa bayanta,har sai da gabanta ya faɗi da tayi arba da hayaam saboda wankan data ɗauka tayi uban makeup kamar wata aljana,bakin nan yasha jan janbaki ta wani cuno shi irin na masifaffu, Tuni sehrish tasha jinin jikinta ganin irin wankan da Hayaam ta ɗauka,ba ƙaramin kyau tayi ba kuma zata ja hankali sosai, kawar da kai sehrish tayi tare da juyawa zata tafi,muryar hayaam ce ta katse ta dacewa"Wait inason magana dake ƴan mata," tsayawa sehrish tayi tana jiran jin me zata ce mata, Koda Hayaam ta ƙaraso,bin sehrish tayi da wani irin matsiyacin kallo tun daga ƙasa har sama sannan tace"nasan gabanki ya faɗi kuma kin tsorata da ganin irin kyau da kuma kyawun sura da Allah yayi mun," ɗaure fuska sehrish tayi batace komai, Hayamm taci gaba da cewa"so nake ki fahimci cewa ni ba sa'ar yinki bace!bansan wani irin shisshigi kike ma Sg rafayet ba da har kika samu matsayi a wurinshi,inaso na gargaɗeki ne, kuma naja kunnanki akan ki fita daga sabgarshi saboda yafi ƙarfinki nesa ba kusa ba,don na lura abunda kike hari kenan,in ma banda haɗama irin taki ina zaki kai mutum kamarsa?dan Allah jibarki fa ƴar ƙarama dake amma sai kankanbar tsiya,wai ma menene connection ɗinki da mutanen gidan nan ne? tayi tambayar tana kallon sehrish yayin da fuskarta ke ɗauke da shu'umin murmushin nan nata, jikin sehrish ba ƙaramin sanyi yayi ba don tuni idanunta sun cicciko da kwalla,daƙyar ta iya shanyesu sannan ta dake tare da cewa"Bansan meyasa kike gayamun waɗannan maganganun ba,da alama dae baƙin cikin ɗazu ne da sgr ya ƙumsa maki shine kikeson ki huce akaina,sannan kuma yaushe nace maki inason shi ne da har kike cewa yafi ƙarfi na?bama wannan ba,Naji kina magana akan cewa menene alaƙata da mutanen gidan to bari na baki amsa," matsawa sehrish tayi dab da Hayaam sannan tace"Ni yar aikinsu ce,biya na suke ina masu aiki kuma suna jin dadin aikina shiyasa nasamu kar6uwa a wurinsu,kuma ina alfahari da hakan,wannan shine alaƙata dasu,ke kuma fa?ƙanwar matar yayansu ce fa?ina alaƙa take anan? Lokacin da sehrish takai ƙarshen maganarta,waro ido waje Hayaam tayi tana kallonta,bata ta6a tunanin cewa yarinyar zata iya mayar mata da martani ba ashe itama ba kanwar lasa bace,ranta ba ƙaramin 6aci yayi ba,tuni idonta sun canza launi saboda fusatar da tayi, Sehrish kuwa murmushi ta saki tare da juyawa ta kama hanyar tabar wurin, Wani irin tafarfasa zuciyarta keyi mata,tama rasa mai zatayi ma sehrish ta huce don tsabar takaicin maganar da ta yada mata, "Da ace ban mayar mata da martani ba,dani zan kwana da baƙin ciki," sehrish ce tayi maganar a lokacin da take ƙarasa shiga part ɗin sgr, Sai faman murmushi take saki abunta,wucewa tayi cikin bedroom ɗinshi,wannan daddaɗan ƙamshin turaren nasa ne yayi mata maraba da zuwa,duk da baya cikin ɗakin amma ƙamshinsa ya gauraye ko'ina, Lumshe idonta tayi tare da buɗesu a hankali suka sauka akan shimfiɗeɗen gadonshi,tunawa tayi da abunda ya faru jiya atsakaninsu nan take taji wani irin yanayi atattare da ita,nan take tashiga tariyo dukkan abunda ya faru jiya a tsakaninsu,musamman lokacin daya kwantar da kanshi asaman chest ɗinta sai taji shi tamkar babynta,hmmmmmm shiga ciki sehrish tayi batare da 6ata lokaci ba,tashiga gyara mashi bedroom ɗin nashi,tamkar sabo haka ta Canza mashi kamanni,bayan ta kammala da bedroom ɗin,ta cire mayafinta tare da ajiye shi daga gefen gadon sannan ta koma cikin toilet ɗinsa don ta gyara mashi,
Bata jima da shiga ciki ba,sgr ya dawo cikin gidan,har yanzu wankan ɗazu ne ajikinshi,na warp shirt da black trouser,da alama a ɗan gajiye yake,kai tsaye ya nufi upstairs part ɗinshi,hankalin Hayaam ba ƙaramin tashi yayi ba lokacin data ga gifcinshi yana ƙarasa hawa upstairs ɗin,taso ta tarbe shi tayi mashi sannu da zuwa kota samu yasan ya idonshi acikin nata,amma bata samu damar yin hakan ba,saboda fargabarshi da take ji,
A wani irin gajiye ya shiga bedroom ɗinshi yana faman lumshe blue eyes dinshi saboda baccin da yake ji,yana ƙarasawa ciki yasanya hannayenshi tare da ɗebe rigar jikin shi gaba ɗaya,ya azata asaman laundry basket dinshi,zame belt ɗin wandonshi yayi sannan ya zame shi daga jikinshi ya ajiye shi asaman rigar,ya rage daga shi sai shorts ajikinshi, Komawa yayi tare da hayewa saman royal bed dinshi ya kwanta don ya ɗan runtsa,sosai ya miƙe saman gadon yana faman sauke ajiyar zuciya har bacci yayi awon gaba dashi,almost 6 mins sai ga sehrish ta fito daga cikin toilet ɗinshi,tunkarar gadon tayi saboda ta ɗauki mayafinta sai da ta kusa dab da gadon sannan idonta suka hango mata Boss Man ɗin nata kwance yana bacci,wani irin bugu taji zuciyarta tayi mata har sai da taɗan ja da baya tana kallonshi,hannu tasa tare da ɗan murza idanunta donta tabbatarwa idonta abunda take gani wai ko gizau ne,amma zahiran taƙara shaida cewa sgr ne da kanshi ya dawo, Hankali kwance yake baccin shi,ya zagayo da left hand dinshi ta saman sumar kanshi,yayin da hannun damanshi ke asaman shafaffen cikinshi, Ji tayi bazata juri kallon surar jikinshi ahaka ba saboda gudun jefa kanta cikin matsala,don ba ƙaramin fisgarta yake yi ba,kamar irin magnet din nan, Har ta kama hanyar fita daga bedroom din nashi cikin sauri taji jelar gashinta na gogar hannunta,tsayawa tayi Cak tunawa da Mayafinta data ajiye asaman gadon nashi kafin tashiga gyara mashi toilet ɗinshi,a hanzarce ta juya tana kallon inda ta ajiye mayafin,waro ido waje tayi cike da fargaba ganin yarda sgr ya mamaye mayafin nata gaba ɗaya,ya kwanta asaman shi,tabɗijan can Tunani tashiga yi kodai ta tafi tabar mashi mayafin tunda ba iya ɗaga shi zatayi ba,wata zuciyar kuma tace,idan ya farka ya samu mayafin naki asaman gadonshi bakya tunanin cewa zai iya zargin wani abu akanki?dole ya tuhume ki akan miya kawo mayafinki saman shimfiɗarshi,haka in kika fita ba mayafin wani ya ganki kin fito daga part dinshi haka fa,kiyi tunani sehrish barin mayafin risky ne,haka zalika daukarshi ma zai iya zama risky, Runtse idanunta tayi tamkar ta fasa ihu saboda tsabar takaici,taji haushin cire mayafinta da tayi tun farko da bata jefa kanta cikin matsala ba, Nan fa tashiga tunanin yarda za'ae ta dauke mayafinta batare da Sgr ya farka daga baccin shi ba, cikin sanɗa sehrish ta soma tafiya a hankali tana tunkararshi a tsorace batare da sautin takon tafiyarta na fita ba, Sai da tazo dai dai kusa dashi sannan tashiga cizon yatsa tana tunanin wai ma taya zata janyo mayafin daga jikinshi,Sehrish da kasada, Hannu tasa tare da ɗan kamo mayafin daya leƙo daga bayanshi tana janshi a hankali don ya sulalo daga bayanshi,amma ko motsi wannan baiyi ba don ba ƙaramar danna sgr yayi mashi ba,gaba ɗaya nauyin jikinshi na akan mayafin taya zata iya janye shi!? tun tana jan mayafin a hankali yana turjewa har takai ga hasala tashiga janshi da ɗan ƙarfi har sai da sehrish tashiga fitar da wani irin gumi a fuskarta,sakin mayafin tayi tana faman huci,duk da haka bata daddaraba,sai tasa hannu tare da dafa mattress ɗin ta haye saman gadon kaɗan daga gefenshi,hannu takai zata ruƙo mayafin karaf idonta suka sauka akan farar fatar ƙirjinshi,mayar da idonta tayi akan damtsen hannunshi,haryanzu akwai sauran zanen nan nashi na tattoo bai ƙarasa gogewa ba gaba ɗaya,tun farkon zuwanshi 9ja tare da zanen ajikinshi ya dawo kamar tambari ne na mukaminshi ba ƙaramin kyau yayi mashi ba, Gaba daya sehrish ta shagala da kallon surar jikinshi,kafin tayi wani aune,Sgr yayi wani irin kwakkwaran juyi zai gyara kwanciyarshi,aikuwa gaba ɗaya ya haɗa da sehrish yayi juyin tare da sanya hannunshi yayi hugging ɗinta tighly a faffaɗan kirjinshi,duk a tunaninshi pillow ne ya rungumo hakanne yasa ya matseta sosai a ƙirjinshi kamar yarda ya saba rungume pillow in zaiyi bacci wani sa'in,tashin hankali da ba'a sama shi date, Tabɗijancan,ƙiris ya rage sehrish ta saki fitsari saboda tsabar tsoran da taji,hankalinta yayi matuƙar tashi,saboda tasan mai zai biyo ba in sgr ya farka yaganta manne ajikinshi,yasan na jiya taimakon shi tayi gudun karya faɗi,na yau kuma mai zai kira shi!?meya kawota saman gadonshi da har ta faɗa jikinshi!? yarda ya matseta a ƙirjinshi ko kwakkwaran motsi sehrish ba ta iya yi,ba ƙaramin ruƙo yayi mata ba,tunkan ya farka taga irin hukuncin da zai yi mata harta fara zubar da hawaye,kai tsaye kuma hawayen suke shafar fatar jikinshi, sai faman shessheƙar kuka takeyi ƙasa ƙasa yayin da la66anta ke gogar fatar breast dinshi,gaba ɗaya Wannan jan bakin data shafa ya koma a fatarshi,sosai zanen lips ɗin sehrish ya fito raɗau tare da kalar jan bakinta maroon colour,duk bata lura da hakan ba,saboda la66an nata amanne suke a wurin, Tana cikin wannan yanayin tajiyo takun tafiyar mutum a falonsa alamar ana tunkaro bedroom ɗinshi,hakan ba ƙaramin firgita sehrish yayi ba,nan take tashiga haɗiyar yawu a tsananin tsorace, Muryar Abbansu tajiyo yana cewa"Wai har yanzu rafayet bai dawo bane?inaso naji ko sunyi waya da Mommynshi ne game da zuwanta Nigeria,' "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,"sehrish ce ta ambaci hakan acikin zuciyarta,"Shikenan na mutu wayyo Allah na,ya Allah ka kawomun ɗauki,daga wannan sai wannan......'bata ƙarasa zancen zucin nata ba tajiyo muryar Marshal Omar yana bashi amsa da cewa"Abba ashe muna da manyan baƙi cikin watan nan,don munyi waya da goggon katsina ma ta sanar dani cewa mu shirya ma zuwanta don in ta tashi zuwan bazata zata yi kuma ba zata tafi ba har sai taga An shafa fatihar kowannan mu.....' ya ƙarasa maganar da dariya a fuskarshi, Suna tafiya suna nufar bedroom ɗin sgr yayin da suke fira a tsakaninsu, Abban nasu yace"Albishirinka," Cike da zumuɗi Omar yace"Goro," "Fari ko ja"? Abban nasu ya tambaya fuskarshi ɗauke da murmushi, Omar yace"Fari," ƙayataccen murmushi Abban nasu ya saki kafin yace"Uncle ɗinku Abusufyan shima yana nan tafe insha Allah,sannan Auntynku azeema tana nan tafe,uwa uba kuma Ammynku itama tana nan tafe,don haka ku shirya don ta sanar dani cewa muddin tazo sai an ɗaura auran kowannanku,da alama zata zo tayi yaƙi da tazuranci ne acikin gidan nan.....'ƙarasa maganar yayi muryarshi ɗauke da dariya,shima Omar dariyar yayi yana girgiza kai yace"Abba Allah yaso ni,ina da wadda nakeso,don haka ni bani da matsalar komai wlh,Alhamdulillah Allah ya kawota Lafiya musha biki,' Cike da mamaki Abban nasu yace"wai dagaske Omar kana da wadda kakeso?hakan na nufin kayi budurwa baka sanar dani ba"? ɗaga kai Omar yayi alamar eh,wani irin farin cikine ya cika abban nasu har ya gaza magana sai faman sakin murmushi yake yi yana cewa"Ikon Allah,"
A ƙopar shiga bedroom ɗin sgr suka tsaya suna cigaba da tattaunawa cike da nishaɗi atsakaninsu,
Saboda tsabar tashin hankali har wani zazza6i ya lullu6e sehrish tuni temperature ɗin jikinta yayi wani irin zafi,zuciyarta har wani bugu takeyi daram!daram!!fargabarta karsu shigo su same su a wannan yanayin ita da sgr, Hayaniyar da suke yi ce,ta fara disturbing ɗin baccin nashi,hakan yasa ya fara motsi alamar zai farka,waro ido waje sehrish tayi cike da fargaba jin alamar zai farka, Hannunshi ya janye daga ruƙon da yayi ma sehrish,hakan ne ya bata damar kufcewa daga jikinshi,kamar walƙiya haka ta mirgina tare da faɗawa ƙasan gadon,sam bata ji zafin buguwar da tayi ba,tana faɗowar nan ta yunkura tare da miƙewa tayi wuff ta faɗa bayan labulan ɗakin shi, Shigarta ke da wuya,Abba da marshal suka shigo cikin ɗakin nashi atare bakunansu ɗauke da sallama, A hankali sgr ya soma buɗe idanunshi dake cike da bacci ga wata irin kasala data mamaye shi don baccin bai ishe saba,daƙyar ya iya sa hannunshi tare da dafa mattress ɗin ya tashi daga zaune tare da jingina back ɗinsa asaman pillow yana kallon Abban nasu tare da Omar sai faman lumshe ido yake yi, Zama Abban yayi daga gefen gadon nashi yana kallon fuskar kyakkywan yaron nashi yace"Rafayet bacci kuma a irin wannan lokacin?ko baka ga time bane? Sai lokacin sgr yakai idonshi akan diamond clock ɗin dake manne a bangon ɗakinshi ƙarfe 6:30 na yamma, lumshe idonshi yayi kafin ya waresu akan Abban nasu yace"Abba bansan time ɗin da baccin ya ɗauke ni ba" jinjina kai abban nasu yayi kafin yayi yunƙurin cewa wani abu karaf idonshi suka sauka akan jan bakin sehrish dake zane asaman breast ɗinshi, waro ido waje abban nasu yayi tare da cewa"Kai me nake gani haka kodai idona ne"?yarda yayi maganar a ruɗe yasa marshal Omar ɗan matsowa daga tsayen da yake ya russina yana ƙare ma Ƙirjinshi kallo,cike da mamaki Omar yace"ba shakka Abba,ba idonka bane wannan alamar sumbata ce,ga zanen la66an mace nan raɗau asaman fatar kirjinshi, Gaba daya sun gama confusing ɗin Sgr,sam bai gane inda zancen nasu ya dosa ba," Hankali atashe Abbansu yace"Rafayet tell me the truth!wa kayi feeding haka har ta goga maka jan baki asaman breast dinka!!!" Saboda tsabar kiɗima tuni jikin sehrish ya soma tsastsafo da wata irin zufa,duk da sanyin ac dake gauraye da ko'ina, Ganin yarda sgr ya dabarbarce kamar bai gane kan me suke magana ba,hakan yasa omar ƙarasawa gaban dressing mirror ɗinshi,yasa hannu tare da ɗauko ƙaramin madubin dake ajiye asaman shi, Ƙarasowa yayi wurinshi tare da saita mashi madubin yarda zai gani da kyau, Ware manyan idanunshi yayi yana kallon zanen la66an dake asaman chest ɗinshi cike da tsananin mamakin a ina ya same shi.......
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.*💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Ansamu long page🥱
________________________Zuba mashi ido su kayi suna jiran amsa,Omar yace"pls ka faÉ—a mana gaskiya kawai,wacece wani abu ya shiga tsakaninka da ita har akasha wannan Love haka?kaga dai daga ni sai Abba babu wanda zaiji abun da ya faru,"wani irin kallo sgr ya wurga yana mashi Æ´ar harara yace"Omar bana so, ka fara ko"?  Murmushi Abban nasu yayi kafin yace"abunda Omar ya faÉ—a gaskiya ne,Son bai kamata ka 6oye mana komai ba tunda Allah dai yasa yau asirikinka ya tonu munga komai,ashe kana kula mata har romance kake dasu asaman gado ko?faÉ—amun Æ´arwa ka kwamushe acikin É—akinka har akai abun arziÆ™in nan bansani ba,"cike da zolaya Abban nasu ke magana,  ɗaure fuska Sgr yayi tare da haÉ—e girarsa wuri guda ya tsuke small lips É—inshi yana kallonsu,yarda suka tasa shi gaba suna tuhumarshi kamar wani Æ™aramin yaro ba Æ™aramin hasala shi yayi ba,gashi sam ya rasa amsar da zai basu tunda bai isa ya Æ™aryata abunda suka gani ba asaman Æ™irjinshi,don shi kanshi a ruÉ—e yake da lamarin abun ya É—aure mashi kai,taya aka samu jan bakin mace raÉ—au haka asaman Æ™irjinshi!?bai gama zancen zucin nashi ba muryar Omar ta katse mashi tunani,  "Abba zargi fa ya tabbata,kalli ka gani,"Omar ne yayi maganar yayin da yake ruÆ™o mayafin sehrish dake a Æ™asan laps É—in Sgr ya danne shi,   dafe kirji abban nasu yayi cike da razana yace"Æ™alu innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Rafayet!wannan fa?ya akai yazo wurinka"?ya tambaya hankali tashe yana kallonshi, Runtse ido sehrish tayi daga 6oyen da take bayan labulen É—akin,hada Æ´an matan hawayenta saboda tsoran hukuncin da zata kar6a,  Cikin sauri sgr ya aza eyes É—inshi akan mayafin da Omar ya ruÆ™o a hannunshi just speechless,amace bakin shi ya mutu yama rasa bakin magana abun ya zarce tunaninshi,  Omar ne yace"Abba tunda kaga yayi tsit ya gaza magana,to ya aikata É—inne kasan mara gaskiya,ni fatan da nakeyi ma Allah yasa iya mayafi ya cire mata bai........'kasa Æ™arasa maganar yayi saboda saukar pillow daya ji a saman fuskarshi,hannu yakai zai Æ™ara rarumar wani pillow abban nasu ya dakatar dashi da cewa"Wannan fa alamar rashin gaskiya ce,tun É—azu kaÆ™i buÉ—e baki ka ce uffan,sai faman Æ´an kame kame kakeyi mana,kaji tsoran Allah ka faÉ—a mana gaskiya,Rafayet yin hakan kuskure ne bai kamata don kana ra'ayin mace ka runÆ™a kawota har bedroom É—inka ba asaman gadonka don ka rage zafi da ita ba,in kaga yarinya kanaso Ni zakayi ma magana sai aje masallaci ashafa fatiha kaga shikenan sai a kawo maka ita É—akinka babu mai jin kanku,taka ce halak malak.....'  Zare blue eyes É—inshi yayi yana kallon Abban nashi,rai a6ace ya ciji la66ansa tare da É—ago pillown hannunshi ya É—aga sama zai jefa ma Abban nasu a saman fuskarshi,sai kuma ya saki filon a saman katifar,   Ganin ya dakata yasa Abban nasu cewa"ae fa kai yanzu komai ma zaka iya,saurayin da zai iya kawo mace É—akinshi har saman gadonshi acikin gidan ubansa meke bazai iya ba Omar? Ya Æ™arasa maganar yana kallon Omar dake Æ™umshe da dariya yace"of course Abba,ina goyon bayan maganar ka,yanzu sai dai mu bishi da addu'a don na lura yarinyar ba Æ™aramin zautar dashi tayi ba tunda gashi har ya gaza buÉ—e bakinshi yayi mana magana,rashin gaskiya dai baiyi ba,"  gaba É—aya sun gama hasala Sgr,yama rasa amsar da zai basu su dukansu,a Æ™arshe ma daya rasa abunyi kawai sai ya fashe da dariya unexpected,tsananin mamaki ne ya kamasu ganin Sgr yana 6a66aka dariya yau shi da kanshi,yaushe rabon da suga sgr yayi dariya irin haka,white teeth É—insa sun fito rairasss,da wuya kaga yana dariya sai dai wannan murmushin nashi na gefen fuska shima kuma in kaga yayi wannan murmushin tofa zai bada horo ne,don ya iya murmushin mugunta,   Hannu sehrish tasa a hankali ta É—an yaye labulen tana leÆ™ensu,ba Æ™aramin bugun zuciya taji ba,kasa janye idonta tayi daga kallon kyakkyawar fuskar sgr da yake ta faman dariya kamar zautacce,gaba É—aya dimples É—in fuskarshi sun lotsa sosai abun ba'a magana sai wanda ya gani,suman tsaye sehrish tayi amace ta mace wurin kallon fuskarshi,aranta tana maimaita kalmar nan"tabarakallahu ahsanun khaliqin,"   Har wani duÆ™ar da kanshi yake yi Æ™asa yana dariyar hakan yasa sumar kanshi ta É—an yarfo ta gaban fuskarshi,  Atare Omar da Abbansu suka haÉ—a baki wurin cewa"ikon Allah,abun mamaki abun al'ajabi,"   Tsagaitawa yayi da dariyar lokaci guda ya É—aure fuskarshi tamkar dariya bata ta6a wanzuwa a fuskarshi ba,takaici ne dama ya ishe shi shiyasa ya fashe da dariyar,  Cikin sanyin murya yace"joking aside pls,abba nikaina bansan ya akai nasamu zanen lips É—in nan asaman chest É—ina ba,sannan bansan ya akai mayafin nan yazo bedroom É—ina ba,na rasa ta yarda zansa kuyi understanding É—ina,gaba É—aya kunyi confusing É—ina,kun tsareni da tambaya kamar wasu lauyoyi,that's why nayi shiru bance komai ba,"ya Æ™arasa maganar a kasalance,   Murmushi Abban su ya saki yana kallon face É—inshi,bakomai ya faÉ—o mashi araiba face Mommynsu,komai na fuskarshi irin na mahaifiyarshi ne,yafi kama da ita amma akwai wasu abubuwan daya É—auko na Abbansu,   "Zan shiga toilet,"ya faÉ—i tare da saukowa daga saman gadon ya kama hanyar shiga toilet É—in,   Bin bayanshi su kayi da kallo har ya shige cikin toilet É—in, Sannan Suka janye idanunsu,cikin sauri Omar ya samu wuri tare da zaunawa yana fuskantar abbansu ya ruÆ™o hannunshi tare da cewa"Abba,dan Allah ka aurar damu tare, nida Rafayet,kayi mun wannan alfarmar"  Murmushi Abbansu ya É—anyi kafin yace"Omar bangane me kake nufi ba,har yanzu É—an uwanka bai janye ra'ayin shi akan mace ba,ni kuma banson na takura mashi,duk da banda burin daya wuce wannan nima,inaso naga auran kowanne daga cikinku,musamman auran shi saboda ina tunanin cewa in soyayya ta shiga zuciyarshi zai rage wannan zafin kan nashi,zai sassauto ya zama tamkar kowa,idan har rafayet baiyi aure ba ya tsaya akan bakanshi,tabbas za'ayi asarar namiji har namiji Omar,bansan ya zanyi dashi ba,"yanayin da abban nasu yayi maganar zai tabbatar maka da cewa abun ba Æ™aramin ciwo yake masa ba,  "Abba kadaina cewa bakasan yarda zaka yi dashi ba,shifa É—anka ne halak malak Allah ya mallaka maka,kuma kana da iko Akanshi,idan yau kaso Abba gaba É—ayanmu zaka iya yi mana aure batare da son ranmu ba ko batare da saninmu ba kuma dole muyi maka biyayya,"   zuba mashi ido Abban yayi yana sauraran bayanin shi, Ƙasa Æ™asa da murya Omar yayi gudun kada Sgr yafito daga cikin toilet É—in yaji abunda suke tattaunawa,  Yasa shi yin hakan sannan yaci gaba da cewa"Abba,namiji irin rafayet,aure akeyi masu batare da saninsu ba,sai dai kawai suji an É—aura auran... "  Katse shi abban nasu yayi da cewa"baka tunanin cewa zai iya sakin matar anan take,kasan shifa ba'ayi mashi dole,"?    Murmushi Omar yayi tare da cewa"Abba ka fahimta mana,kaifa kake iko dashi,ka sama mashi mace ta gari wadda kasan cewa bazaiyi dana sanin zama da ita ba,ko kuma ni kaban za6i zan sama mashi macen data dace da rayuwarshi,ka aura mashi ita batare da sanin shi ba,sai bayan an É—aura auran ka ware rana É—aya ka sanar dashi cewa Umarnine ka bashi amatsayinka na mahaifinshi,in ya kuskure kuma yasan sauran,"  dariya sosai Abbansu yayi yana sauraron omar dakyar ya tsagaita da dariyar yace"Omar ka iya zolaya Allah kamar mahaifiyarku,yanzu rafayet kakeso nayima auren dole?so kake ya tashi bomb acikin gidan nan"?  "Abba baka fahimce ni ba,tunda muka taso tare da É—an uwana,komai namu iri É—aya muke yinshi tamkar twins haka muke,duk abunda nayi rafayet sai yayi shi,haka shima duk abunda yayi nima saina yi shi,yanzu abba aure ne zai banbanta ni da É—an uwana"?  In serious matter Omar ke magana,wannan yasa Abban nasu ya gane cewa ba zolaya bace yake mashi,har cikin ranshi yake maganar kuma ba Æ™aramin jin abun yake ba acikin zuciyarshi,bai gama zancen zucin nashi ba omar yaci gaba da cewa"Abba tuntuni ban ta6a sanar dakai ba,amma yau zan sanar dakai komai,najima inason na cika maka burinka na ganin cewa munyi aure, ba don komai ba sai don saboda farin cikinka,bakomai ne yasa nayi jinkirin yin aure ba face Rafayet!inason aure bawai banaso ba,rafayet shine dalilin dayasa naÆ™i yin aure,saboda ina ganin cewa kamar banyi mashi adalci ba,inna riga shi yin aure,saboda mun saba komai atare duk wani cigaban da zamu samu atare muke samun shi abba,taya zanso na samu wannan babban cigaban batare da É—an uwana ba"? Ya Æ™arasa maganar muryarshi asanyaye yana kallon Abban nasu, Gaba É—aya Omar ya gama kashe ma Abban nasu jiki,ba Æ™aramin tausaya mashi yayi ba,lalle ba Æ™aramar shaÆ™uwa bace a tsakanin shi da É—an uwanshi ba,tun da har zai iya hana kanshi wani jin daÉ—i na rayuwarshi saboda ganin cewa tamkar baiyi mashi adalci bane,   "Abba,na jima ina jiran ganin cewa É—an uwana ya fara soyayya koya fara maganar aure,amma har yanzu ba wani sauyi abun ba Æ™aramin ta6amin zuciyata yake ba,bana faÉ—i ne kawai saboda nasan faÉ—in bashi da amfani zan 6ata bakina ne kawae,sau da yawa ina janshi da fira akan mace don na bugi cikinshi naji koya fara ra'ayin yin aure amma kullum babu wani cigaba game da haka,Abba rafayet shine yasa Omar É—inka Æ™in yin soyayya tun da jimawa kuma shine ya hana nayi aure,wanda bani da burin daya wuce wannan arayuwata....,.......'  Kasa Æ™arasa maganar yayi saboda siririn hawayen daya zubo mashi a idonshi na hannun dama,  Cikin sauri abban nasu ya sanya hannunshi tare da yin saurin goge masu shi yace"Omar ban ta6a tunanin haka ba,meyasa tuntuni baka sanar dani wannan maganar ba?meyasa nagaza fahimtarku amatsayina na mahaifinku?ashe shaÆ™uwar dake tsakaninku har takai haka?nagode ma Allah sosai da kuka kasance masu son junanku,ina matuÆ™ar alfahari daku Æ´a'Æ´ana," magana yakeyi yayin da idanunshi suke cike tab da kwalla,  Sehrish kuwa dake la6e bayan labule sai faman shessheÆ™ar kuka takeyi ta rufe bakinta da tafukan dukkan hannuwanta,tsananin tausayinsu ne ya kamata,tunda take a rayuwarta bata ta6a ganin Æ´an uwa masu matuÆ™ar Æ™aunar junansu ba irin ahalin salahuddeen hussein,akwai soyayya da shaÆ™uwa tsakaninsu,zumuncin dake tsakaninsu mai Æ™arfi ne sosai,da ace kowane ahali zasu kasance haka da ba Æ™aramin cigaba za'asamu ba,amma yanzu zamanin da muke ciki,babu wannan soyayyar atsakanin shaÆ™iÆ™ai ma,sai kaga na waje ma wani can yafika kusanci da É—an uwanka shaÆ™iÆ™inka,idan kuwa akazo kan shiga matsala ko damuwa tofa zaka ga mutum indai bashi ta shafa ba,babu ruwanshi da damuwa akan halin da É—an uwanshi yake ciki,sai ma ya kasance É—an uwanka yana cikin Æ™unci da matsanancin damuwa,amma kai kuma hankalinka kwance sai ma ajika kana ta faman tiÆ™ar dariya,mai makon arunÆ™a jajantawa juna,shiyasa dayawa zaka ga na waje ma wani yafika kusanci dashi saboda yafi damuwa da É—an uwan naka,wanda dayawa hakan ke jefa rayuwar É—an uwan cikin hatsari,ba'a janshi ajiki cikin gida tun daga iyayen har Æ´an uwan,bakamar salahuddeen hussein ba, ya É—auki Æ´a'Æ´anshi tamkar abokanan shi,Æ™aramin É—anshi ma tamkar amininshi ya mayar dashi,kuma hakan yasa basa jin shakkar sanar da mahaifinsu abu in ya same su,ko neman shawara awurinshi,wanda a yanzu zaka ga cewa wani a gidansu tsoro ma yake ji ya sanar cewa wani na cutar dashi awaje,saboda wasu iyaye basa tsayawa su fahimci Æ´a'Æ´ansu daga sun ji abu sai afara hantarar mutum in Æ™arami ne kaga an haÉ—a mashi da bugu ma,babu wannan shaÆ™uwar ta iyaye,da Æ´an uwantaka da har mutum zai iya faÉ—in damuwarshi acikin gidansu,sai dae ya nemi abokinshi ya sanar dashi halin da yake ciki instead of wani nashi nakusa dashi,daga nan kuma awajen in Allah yasa abokin ba nagari bane shine zaka ga anzo ana danasani, don mafi akasarin mutane na fadawa mugun hali ne ta sanadiyyar abokai,ku yi koyi da wannan ahalin wurin nuna ma junanku soyayya,ku zama naku ku kaÉ—ai babu mai jin kanku👌ðŸ‘
Sehrish bata bar bedroom ɗin sgr ba,har sai da aka kira sallar magrib suka fita tare da abbansu domin zuwa yin sallar magrib sannan ta samu cikin sauri ta ɗage curtains ɗin,da hanzarin gaske ta sungumi mayafinta sannan da sauri hadda gudu ta haɗa wurin barin part ɗinsa, Saukowa downstairs tayi a lokacin duk sun tafi salla masallaci,kai tsaye kitchen ta nufa tunkan ta ƙarasa ta hangi Azmee da hayaam suna ta haramar kammala dinner ɗin ranar,duk sai taji babu daɗi taso ace tare da ita suka fara,jiki asanyaye ta shiga kitchen ɗin da sallama a bakinta, Juyowa sukayi suna kallonta atare,da alama ma sun kammala aikin nasu,Azmee ce ke haɗawa Hayaam warmers acikin tray tana kaiwa dining, "Kin kammala gyara mashi part ɗin nasa ne?azmee ce ta jefa mata tambaya, "Eh,nagama," "Ya akai kika daɗe acan ne"? Sunnar da kai tayi tana wasa da yatsun hannunta saboda ta rasa amsar da zata bata, Hayaam kuwa sai faman wurga mata harara take yi kamar kwayar idonta zata faɗo ƙasa, Murmushi azmee tayi tare da cewa"ki wuce kije kiyi sallah,kada ki samu damuwa,nasan cewa wani abunne ya tsayar dake," Ajiyar zuciya sehrish ta sauke kafin ta juya tasa kai tabar cikin kitchen ɗin,bedroom ɗinta ta nufa domin tayi sallah,
A 6angaren su hossana kuwa,tun bayan da suka dawo daga school suke ta faman saran zuwan Omar amma baizo ba,burin jahad ta sanar dashi cewa taga ƙaninshi a school ɗinsu,gaba ɗaya yinin ranar sunyi shi ne cike da kewar Ya omar ɗinsu musamman hossana ko lunch bata ci ba tunda suka dawo gashi ko'a school ma bataci komai ba,saboda tayi alƙawarin cewa tare da ya omar zasu ci abinci zai bata abaki,hakan yasa taƙi cin komai,duk yarda jahad taso ta fahimtar da hossana akan ta zauna taci abinci sam taƙi,har dai tagaji ta ƙyaleta, sai faman zagaye takeyi acikin bedroom ɗinsu,fuskar nan ɗauke da murmushi ae tunda tayi arba da Romeo sam tagaza samun natsuwa wani irin tsantsar son shi da ƙaunarshi takeji kamar kamar me,fiye da yarda take jin ya omar ma lokacin da taso shi,saboda shi son da tayi mashi hada ƙarin don ta kyautata mashi ne akan irin ɗawainiyar da yake yi dasu,shi kuma kalar son da take yi ma junaid kallo ɗaya tayi ma kyakkyawar fuskarshi tabi ta rikice,kuma tunda Omar ya furta cewa ƙaninshi ne nan take taji ya kwanta mata aranta,sai dai abunda jahad bata sani ba shine,junaid ba babba bane kamar yarda take tunani,
**********haroon Gaba ɗaya ya rikita ɗakin nashi wurin neman kuɗin da su Twins suka bashi,sam hankalin shi ya gaza kwanciya yama rasa inda zaisa kanshi,wata irin zufa ce ke gangaro mashi a fuskarshi saboda tsabar 6acin rai,yafi ƙarfin awa 2 yana neman jakar kuɗin amma babu ita ƙasa ko sama,an ɗauke ta daga ɗakinshi babu ita babu alamarta,yayi ma bedroom ɗin nashi kaca kaca wurin binciken inda jakar kuɗin take,kamar zaiyi hauka saboda yarda ya zauce,sun rigada sun gama tsara plan ɗinsu, shirin tafiya kawai ya rage mashi daga zuwa ya ɗauki jakar kuɗin an ɗauketa daga ɗakinshi,gashi ya rasa wanda ya shigo har cikin bedroom ɗinshi ya ɗaukar mashi ita,komawa yayi gefen gadonshi ya zauna yana faman huci kamar wani zaki,tunani ya shiga yi wanene zai iya shigowa ɗakinshi ya ɗaukar mashi jakar kuɗin shi?kodai su twins ne suka yi mashi wayau,don sunsan cewa ya goge videon shine suka ɗauke jakar kuɗin,tabbas kuwa sune saboda su kaɗai ne suka san da kuɗin acikin bedroom ɗinshi, Jinjina kanshi yayi yana huci yace"yara kenan harni zakuyiwa wayau,ƙananun ƴan iska kawai masu kwana da wando,saboda sun mayar dani shashasha shine suka zagayo ta bayan idona suka ɗauki jakar kuɗin,wlh sai kunyi danasani saina illata rayuwarku gaba ɗaya muddin baku maido mun da kuɗina ba,"ya faɗi a lokacin da ya miƙe tsaye zumbur yana faman naushin tafin hannunshi na dama da hannunshi na hagu,tashin hankali da ba'a sama shi date,
**********************Amani Zaune take saman 3 seater,yayin da Amal ke zaune kusa da ita,ta fito fess abunta tayi wanka ta bata kaya ta canza duk da rigar tayi mata yawa saboda kayanta ne taba ma amal ɗin ta sanya kafin zuwa gobe zata je da ita shopping mall ta zabi abunda take so,ta kuma yi mata siyayyar kayan sawa da sauran abubuwa na rayuwa wanda zata buƙata, Hannunta na ruƙe da wayarta,shiga contact ɗinta tayi tare da nemo numbar Aunty babba ta buga mata call,nan take wayar tashiga ringing,
Hafsat na faman zarya acikin parlourn nasu taji shigowar kira a wayar mommynta dake ajiye saman hannun kujera,cikin sauri takai hannu tare da ɗaukar wayar,ganin sunan Amani ya bayyana ne yasa ta juya tare da tunkarar kitchen ɗin,tunkan taƙarasa aunty babba tafito daga kitchen din jin ringing ɗin wayarta,miƙa mata wayarta tayi tare da cewa"Amani ce ke kira," Yatsina fuska tayi tare dasa hannu ta kar6i wayar bayan tayi picking ta kara wayar a kunnanta tana cewa"Sai yau kika tuna dani"?_ on the other hand Amani tace"Am really sorry auntyna takaina,kullum kina araina,kawai abubuwane sunyi mun yawa," tsoki aunty babba taja tare da cewa"Abubuwa su kayi maki yawa,ciki gare ki ko goyo"?_ Amani tace"ko ɗaya daga cikinsu babu,pls mubar zancen ae nabaki haƙuri,yanzu akwai maganar da nakeso nayi maki pls," Aunty babba tace"kunne ke ji," "dama maganar Amal ne!wai har yanzu ba labarinta?ba'asan inda take ba?nagaza samun kwanciyar hankaline saboda mafarkin da nayi jiya agame da ita," Shu'umin murmushi Aunty babba tasaki tare da cewa"Yawwa dama inaso nayi maki magana game da Zancen neman Amal,munyi waya da mammy ta sanar dani cewa an samu wasu malaman da zasuyi mata sauka,manyan malamai ne na addini kuma da zarar sunyi saukar nan ake cin sa'a buƙata ta biya," Ƙiriss ya rage Amani ta saki dariya,don tsabar takaici da ban haushi,aranta tace wai sai yaushe matar nan,zata daina ƙarya ne? Juyawa tayi ta ɗan kalli Amal dake zaune hankalinta kwance idonta na kallon plasma tv ɗin dake facing dinsu,tana kallon tashar mbc 3, gyara murya Amani tayi tare da cewa"Masha Allah,gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba auntyna takaina,ashe ansamu wasu malaman ae ni indai akan Amal ne ko nawa ne zan iya badawa,ko bani dasu zan nemo ne,'_ Jin haka yasa aunty babba,janye wayar daga kunnanta tana faman 6a66aka dariyar mugunta,duk hafsat na tsaye tana kallonta baki asake saboda tasan da zancen neman Amal ɗin,kuma a gabanta Jiya abra ta kira mommyn nata tana sanar da ita cewa Amal ta gudu,sarai tasan cewa yarinyar ta gudu shine kuma takeson ƙara cutar da Amani saboda tsabar son abun duniya? "Yanzu nawa zan tura kenan"?acewar Amani, Aunty babba tace"ba wasu kuɗine masu yawa ba,dubu ɗari takwas ne,ae ni nayi mamakin ma yarda suka faɗi kuɗin da sauƙi har haka," murmushin takaici amani ta saki kafin tace"okey,zanyi maki magana indae na samu kuɗin,yanzu dae mu koma zancen Hayaam,shin har yanzu tana maid ne ko tazo Abujan nan"? "Tun jiya fa ta ƙaraso,yanzu ae ta jima da zama ƴar gida,"ta ƙarasa maganar tana washe baki,anzo inda tafi auki, ɗan ta6e baki amani tayi tace"Okey yayi kyau,yanzu komai zai fara tafiya dai dai,akwai wani albishir da zanyi maki," Natsuwa Aunty babba tayi tare da cewa"ina sauraronki ƙanwata,faɗamun albishir ɗin," Shu'umin murmushi Amani tasaki tare da miƙewa daga saman sofa ɗin tabar Amal zaune tana kallo,takawa tayi nesa da falon,sannan tace"Nasan inna faɗa maki albishirin nan ko bacci ba zaki iya yi ba saboda tsabar farin ciki," A ƙagare Aunty babba tace"dan Allah shaƙamun mana kanwata wane irin albishir ne wannan, Murmushi Amani ta kuma yi sannan tace"nasamo ma Hayaam maganin mallaka a wurin wani hamshaƙin boka,aikin shi tamkar yankan wuƙa yake,saboda Ni shaidace akan idona aka ta6a amfani da maganin kuma yaci," Cike da farin ciki Aunty babba tace"Wai dagaske"? dariya amani tayi tare da cewa"dagaske mana!,wata neigbour ɗinace keson ƙanwarta ta auri ƙanin mijinta,sun rasa yarda zasu jawo hankalinshi acikin gidannan saboda mutunne mai matuƙar ji dakai,kamar dai sgr,ina baki labari kwatsam sai ga wata ƙawarmu ta bamu labari akan wani shu'umin boka,agabana aka shirya zuwa wurin bokan suka amso maganin,a yanzu dai labarin da nake baki,yarinyar na nan ta aure shi hada ciki ma sai faman shan soyayya suke abun gwanin burgewa,"_ Saboda tsabar Murna Aunty babba ta gaza rufe bakinta dakyar ta iya cewa"Yanzu ya za'ae kenan asama ma Hayaam maganin?nawa zamu nema"? "Ko sisi basai kin bada ba Auntyna,fisabilillah na amso ma hayaam maganin da kuɗina ai nima kanwata ce ko,nidae burina shine inga ta auri sgr Abra kuma ta auri marshal Omar," washe baki Aunty babba tashiga yi tana cewa"Allah sarki Amani,ashe haka kika damu da ƙannen namu?gaskiya ba ƙaramin daɗi naji ba,yanzu kenan Hayaam zatazo ta kar6i maganin gidanki kenan"? Amani tace"eh,in ma batasamu zuwa ba ni zanje nakai mata shi,babu damuwa,"_ Sun jima suna waya kafin daga bisani firar tasu ta ƙare anan, Tuntsirewa da dariya Aunty babba tayi tana tafa hannu tashiga cewa"ban ta6a ganin ƴar wahala ba irin Amani,duk irin abunda nakeyi mata amma ita burinta ta taimakamun wurin ganin na cimma burina,gaskiya na tausaya mata,abun tausayi, girgiza kai kawai hafsat tayi tare da wucewa ciki tabar mommyn nata tana ta faman sambatu, A can 6angaren kuwa fashewa da dariya Amani tayi tare da cewa"Aunty laila kenan!ke atunaninki kinyi mun wayau bakisan cewa Amanin da kika sani ada ba ita bace ayanzu ba,ashirye nake dana kwance dukkan wasu notikan kanki,zan mayar dake kamar wata zararra,ita kuma hayaam zanyi amfani da wannan damar wurin ganin na canza mata halittar jikinta,kamar yarda kuka canzawa Amal kamanni ta tsotse ta rame ta ƙanjame haka itama nakeson ta koma,dama ance ramuwar gayya tafi ta gayyar zafi,that's my plan!
Tana faɗin hakan ta juya tare da komawa wurin Amal ta zauna,kallonta Amal tayi tare da cewa"Aunty amani,dan Allah kiyi haƙuri da abunda zan faɗa maki,bansan ko zai 6ata maki rai ba,nasan cewa su mammy sun cutar damu sosai,amma kada kice zaki ɗauki fansa,mubarsu da Allah kawai shi zai saka mana,sannan in zamu iya mu taimaki mahaifinmu don yana cikin mawuyacin hali" Shuru kawai amani tayi batace mata komai ba,amma fa har yanzu tana akan bakanta,maganar mahaifinsu kuwa tasan matukar mammy na numfashi bazata barshi ya sarara ba,don ba karamar shedaniyar mata bace,ita kanta yanzu tana shakkun in don Allah aka hadata da Abbas.
_💋Boss Bature💋_
______________________tunda yadawo daga masallaci yake jin jikinshi wani irin yanayi mara daɗi,bedroom dinshi ya shiga tare da nufan saman gadonshi ya haye yana faman sauke ajiyar zuciya,pillow ya jawo tare da aza kanshi a saman shi yana faman lumshe ido,yana cikin wannan yanayin yaji fitar wani abu daga hancinshi mai ruwa ruwa,cikin sauri junaid ya tashi daga zaune yana kallon pillown nashi,zuba ido yayi yana kallon jinin daya ɗigo daga hancinsa,abun yayi matuƙar ɗaure mashi kai,kafin yayi wani yunƙuri sai ga wani ɗigon jinin ya sake fitowa daga ƙopan hancinshi,abu kamar wasa jinin ya dinga ɗiɗɗigowa saman bedsheet ɗinshi,  Hankali tashe junaid ya sauko daga saman gadon da saurin gaske ya faɗa cikin toilet ɗinsa,kai tsaye ya nufi wash basin,dafa shi yayi yana kallon fuskarshi acikin mirror ɗin,hancin shi yabi da kallo ganin yarda hancinshi ke cigaba da bleeding,sam bai damu ba saboda yasan cewa yana yawan yin nose bleeding,don haka tunaninshi ha6o ne kawai,  Hannu yakai tare da kunna tap ɗin,ruwa ya soma shararowa da gudun gaske,tarba hannunshi yayi tare da ɗebo ruwan ya watsa a fuskarshi yana wanke blood ɗin,murzar wurin ya shiga yi don jinin ya tsaya amma yaƙi daina zuba,ya kusan 15mins a haka sannan jinin ya dakata da ɗigowa,ajiyar zuciya ya saki tare da kai hannu ya kashe tap din,  Sannan ya fito daga cikin toilet ɗin,yana ƙoƙarin ɗaga ƙafarshi ya nufi gadonshi,wani irin jiri ya kwashe shi,hannu ya aza asaman kanshi tare da ambaton sunan Allah,yayin da idanunshi ke ganin mashi biji biji,  Yana cikin wannan yanayin Sehrish ta faɗo cikin ɗakin ambaton sunanshi ta shiga yi "junaid, junaid.....,"  ganin shi atsaye abakin ƙopar toilet ya sata tsayawa tana kallonshi tare da cewa"baby junaid meya faru ne naganka haka?baka jin daɗine,"   Jin muryarta yadinga yi acikin kanshi tamkar ana buga ganga,hakan yasa ya yanke jiki zai faɗi gadan gadan,  A wani irin slow sehrish ta ƙarasa wurin da sauri ta ruƙo shi suka faɗi ƙasa atare,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba jin yarda yake kokowar fitar da numfashinsa,hankali a matuƙar tashe take faɗin"Innalillahi_!junaid!meke faruwa dakaine!me yake damunka ne?ka faɗamun dan Allah,   Ko iya ɗaga la66ansa ba yayi bare ya iya furta mata wata kalma,hannunshi dake kerma yasa tare da ƙara ƙanƙameta sosai ya kwantar da kanshi asaman ƙirjinta yana cigaba da ƙoƙarin fitar da numfashinsa,hankalin sehrish ba ƙaramin tashi yayi ba,tuni ta soma fitar da ƴan matan hawaye,yanke shawarar zuwa ta sanar ma wani tayi don a hanzarta zuwa aga halin da yake ciki,ƙoƙarin janye jikinta tayi daga nashi,tamkar zata rabashi da ranshi haka yaji,ƙanƙameta ya kuma yi sosai da sosai sai lokacin ya iya furta"rishi kada ki tafi ki barni a yanayin da nake ji zan iya mutuwa," Cikin shessheƙar kuka take cewa"junaid ka bari inje in sanar dasu,idan wani abu ya same ka fa"?   "A'a nidai kada ki tafi kibarni,"ya ambaci hakan da wata irin kasalalliyar murya,tsananin tausayinshi ne ya kamata,mayar da hannunta tayi abayanshi tare da ƙara rungumo shi ajikinta tana tofa masa addu'a,lamo yayi ajikinta yana faman sauke ajiyar zuciya,lokaci guda kuma numfashin ya daidaita kamar yarda yake ada,komai nashi yadawo normal,wani irin sanyine ya ratsa zuciyarshi,idonshi na arufe yake shaƙar ƙamshin turaren rishi ɗinsa,gaba ɗaya ya shiga yanayin da bai ta6a shigar irinsa ba, Muryarta ce ta katse shi da cewa"junaid kana lafiya kuwa?naji ka tsit"?   shiru yayi mata,saboda bayason tasan cewa ya dawo cikin hayyacinsa,baison ta raba jikinta da nashi,ɗumin jikinta ba ƙaramin daɗi yayi mashi ba,yaushe rabon da yaji ɗumin mace haka akusa dashi tun yana da kananun shekaru,tunda mommynshi tabarshi,Aunty azmee ta ɗaura da shayar dashi,shima ɗin da zarar ta kammala bashi nono ƴan uwanshi ke ɗauke shi daga wurinta,don basu son rabuwa dashi kona minti ɗaya,ya saba da jikin abban shi,dana ƴan uwanshi yayi missing wannan feeling ɗin,   Jin yarda junaid ya lafe mata ajikinta kamar jinjiri,yasa tayi tunanin cewa kodai ya cika ne,cikin sauri takai hannu tare da ɗago da kanshi tana kallon fuskarshi,waro ido waje tayi ganin yarda yake ta faman sakin murmushin nan nashi,ranta ne ya bata cewa Dama duk plan ne ya tsara mata don ya tsoratar da ita,ɗaure fuska tayi tare da cewa"janaid wannan duk shirinka ne ko? don ka tsoratar dani," Buɗe idanunshi yayi a hankali yana kallon fuskarta data zuba mashi ido,tana mashi kallon Tuhuma,  Murmushi ya kuma saki tare da cewa"dan Allah rishi ki mayar dani a jikinki na kwanta,ba kiji wani irin daɗi dana ji ba,daɗi kamar nayi bacci,"ya ƙarasa maganar yana lumshe mata ido,tsuke fuska sehrish tayi tare da cewa"amma ka rainamin wayau junaid!wai meyasa ka fiye shiririta ne,kalli fa, ka gani hada hawaye na soma zubarma saboda halin da na sameka aciki,ashe duk plan ne ko"?   girgiza mata kai yayi tare da cewa"ba haka bane reesh,kona faɗa maki gaskiya ba zaki yarda ba,"  A hankali ta kwantar mashi da kanshi ƙasa,sannan ta matsa tare da saita fuskarta akan tashi tana kallon shi,shima binta yayi da kallo yarda ta duƙo da fuskarta asaman tashi sumar kanta kuma tayi masu rumfa,tunda ta faɗo bedroom ɗin nashi tashigo da gudu don ta tarbe shi mayafinta ya sulale ƙasa daga jikinta,   "Junaid waye uncle Abusufyan?naji abbanku na cewa zaizo nigeria,kodai shima ɗin yayanku ne"?  girgiza mata kai yayi alamar a'a yace"uncle ɗinmu ne,ƙanin mahaifinmu dake zaune a ƙasar turkey"   jinjina kanta ta ɗanyi kafin ta kuma cewa"bayan shi kuma naji Abbanku yana cewa,Mommynku zata zo itama,tare da wata goggonku ta katsina da kuma Ammi da Aunty azeema,duk zasu zo,"   Sai da ya bari takai ƙarshen maganarta sannan ya ɗan harareta tare da cewa"Ashe dama jin gulma ne ya kawoki ɗakin"?   Murmushi tayi tace"no ba haka bane junaid,inason nasansu ne saboda na koyi zama da kowannansu,bana so na samu matsala da kowa acikin family ɗinku,"   "Zan faɗa maki halin kowannansu amma bisa sharaɗi ɗaya'?ya jefa mata tambaya,  Tace"ina sauraronka wane sharaɗine wannan"?_  murmushi ya saki tare da kai hannunshi ya nuna mata red lips ɗinsa yace"kiss on lips,if u agree then saina faɗa maki,"   hannu tasa tare da ɗan buge bakinshi tace"pls junaid banason wasa fa,in zaka faɗamun ka faɗamun kawai,in ba haka ba zan tashi inyi tafiyata,"  tayi maganar tare da yunƙurawa zata miƙe cikin sauri ya ruƙo hannunta tare da cewa"rishi mommyn mu bata da sauƙi,nima haka naji ana faɗa,amma in har zaki iya zama da babban yayanmu to wannan bazai maki wuya ba,bambancin ita mace ce kinsan ku mata da tsiwa kuke,  Dariya tayi tana sauraronshi "Uncle ɗinmu kuma Abusufyan,wayayyen mutun ne,idan yazo zakiji daɗin zama dashi,bafa wani babba bane autansu daddynmu ne,yana da sauƙin kai sosai amma idan mutun bai kwanta mashi araiba hmmmmm bazasu ta6a jituwa ba,Aunty azeema kuma kamar abbanmu take wurin faran faran da mutane ga son ƴa'ƴa,zakisha mamaki idan tazo ta ganki sosai zata jaki ajikinta,goggon katsina kuwa......"bai ƙarasa ba ya kama dariya,  Murmushi ta saki tare da cewa"me tayi ita?ko batasan mutane"?   Girgiza kai yayi tare da cewa"a'a tanason mutane sosai,matsalarta ɗaya tana da mental illness.......'  Tunda junaid ya ambaci mental illness taji gabanta ya ɗan faɗi kaɗan kamar maison tuna wani abu acikin brain ɗinta,  "tana da ban dariya sosai,tana fa iya ganinki tace ke ɗiyar wani ce acikin family ɗinmu kuma dole ki yarda da hakan in ba haka ba ta sanya rigima hada kuka ma,'  Sai faman zuba junaid yake yi yana korama sehrish jawabi,ita kuwa tuni tayi nisa cikin tunaninta,kalmar da ya faɗi na cutar ta6in hankali ta tsaya imata arai,so take ta tuna waye ta ta6a sani da irin wannan lallurar amma sam tagaza tuna hakan,  Ganin ta tafi duniyar tunani yasa junaid kai hannu ya janyo sumar kanta yana cewa"wai menene haka reeeshi,kin barni ina ta zuba kamar rediyon da bata da saiti,"  Firgita ta ɗanyi tare da kallon shi har lokacin yana daga kwance tace"junaid thanks for the information,zan koma bedroom ɗina naji ana kiran sallar isha,kaima ka tashi kaje kayi sallar,'   Ba musu ya amsa mata da cewa"bari nayi alwala sai mu fita atare,"  Amsa mashi tayi da toh sannan ta miƙe tare da juyawa ta ɗauko mayafinta daya faɗi kasa ta rufe kanta dashi,toilet junaid ya shiga shaf shaf yayi alwala,bayan ya fito atare da ita suka saukko downstairs,   Anan ya haɗu dasu Irfan zasu masallacin suma yabi bayansu suka tafi,   Komawa bedroom ɗinta tayi kai tsaye ta fada toilet ta ɗauro alwala,bayan ta fito ta ƙarasa wurin wardrobe dinta tare da ɗaukar hijabinta da sallaya ta shimfiɗa tare da kabbara salla,anatse ta kammala sallar,fitowa tayi daga dakin nata sannan ta wuce kitchen don ta shirya ma kanta abincin da zata ci saboda yunwar data taso mata,
_💋Boss Bature💋_
A hankali Motarsu tashiga babban gate din gidan Abusufyan,major ne ke driving dinshi yayin da Omar ke hakimce a seat ɗin baya,sai faman zullumin haɗuwarshi da hossana yake saboda yasan cewa ba ƙaramin fushi take dashi ba,saboda ƙin zuwan da yayi, Parking ɗin motar major yayi sannan ya fito tare da buɗe mashi motar,a hankali Omar yasa ƙafa tare da fitowa daga ciki,sannan cikin sauri batare da 6ata lokaci ba ya wuce cikin gidan, Tunkan yasa ƙafarshi cikin parlourn nasu yajiyo shessheƙar kukan hossana,tsayawa ya ɗanyi yana sauraron abunda suke cewa,   "Hossana wai ba zaki daina kukannan ba?salon ki 6ata kwalliyarki ko"?  "Jahad ba zaki gane bane,bakisan yarda nake ji bane,saboda ya omar nayi kwalliyar nan,amma ta tashi a banza,yau ma bazaizo wurin mu ba...'cikin shessheƙar kuka ta ƙarasa maganar, ƙayataccen murmushi Omar ya saki a fuskarshi,kafin yasa kai tare da shiga cikin palourn,samunsu yayi zaune asaman 3 seater,hossana ta kwantar da kanta asaman hannun sofa ɗin,yayin da jahad ke gefenta tana rarrashinta,gaba daya duk sunyi wanka sun canza kayan jikinsu,riga da skirt ne ajikin jahad,hossana kuma gown ce mai kyan gaske,   jin alamar motsin mutum yasa jahad ɗagowa tana kallon shi,cike da mamaki ta buɗe baki zatayi mashi magana,da hanzarin gaske ya dakatar da ita ta hanyar yi mata nuni da hannunshi alamar ta tashi ta tafi,murmushi jahad tayi tare da miƙewa cikin sanɗa tabar saman sofa ɗin ta koma saman 1 seater ta zauna tana kallon dramar da ya Omar ɗinsu zai shirya,cikin sanɗa ya lalla6a tare da komawa wurin da jahad ta tashi ya zauna,sannan yakai hannunshi tare da ɗan janyo wutsiyar gashinta, A fusace tace"dan Allah jahad ki rabu dani inji da abunda ke damuna,ki tashi kiban wuri," Murmushi Omar yayi tare da cewa"zan tafi amma ki fara faɗamun meyasa kika damu da yaya Omar ɗinki har haka"? Sam hossana bata gane voice ɗinshi ba saboda ranta a6ace yake, "Saboda inason shi sosai,jahad nasan ni kawai nake haukana,yana can wurin hayatyn shi,suna shan soyayya.....' Katse ta Omar yayi da cewa"kina kishi ne"? A faɗace tace"saboda me bazanyi kishi ba,nima ae zuciyata ce a ƙirjina ba dutse ba," Wannan maganar ta hossana ba ƙaramin dariya taba marshal Omar ba,hatta jahad sai da ta murmusa daga inda take, Kwantar da kanshi ya ɗanyi abayanta yana cewa"am really sorry babyn Omar,nayi missing ɗinki sosai,nasan nayi laifi ayimun afwa bazan ƙara ba..."jin muryar Omar raɗau a kunnanta yasa tayi hanzarin ɗagowa tana kallonshi da idanunta da suka cicciko da kwalla, Waro ido Omar yayi yana kallonta ba ƙaramin tsorata yayi ba da ganin makeup ɗin da ke a fuskarta,ta dambara Uwar foundation kamar wata aljana,Jan bakin da ta shafa ya 6ata fuskarta har wurin cheeks ɗinta saboda uban kukan da tasha,ga maskara ta zazzago mata a ƙasan idonta, Hankali tashe Omar yace"subhanallahi,kuke ganinmu bamu muke ganinku ba,Babyn Omar wannan kwalliyar fa?dama itace kwalliyar da ake cewa anyimun don inzo in gani,"cike da zolaya yayi maganar,amma tamkar ya tunzura hossana nan take ta 6are baki itare da fashewa da wani sabon kukan, Dariya jahad ta dinga tiƙa kamar kamar me har tagaza dakatar da kanta, Yama rasa ta inda zai fara shawo kanta don ya lallashe ta,hakan ya ƙara hasalata,kamar wata ƙaramar yarinya,ba ƙaramin tausayi ta bashi ba yasan duk don saboda rashin zuwan shi ne,hannu yasa tare da janyota jikinshi yayi hugging ɗinta sosai yana ɗan bubbuga bayanta,lokaci guda ta nemi kukan da takeyi ta rasa,sai gata tana faman sauke ajiyar zuciya, a hankali ya furta"am really sorry hossana,bazan ƙara 6ata maki rai ba,kullum zan dinga zuwa idan ma bansamu halin zuwa ba zan kira ku awaya mu gaisa," Ya ƙarasa maganar tare da cewa"kin yafe mun"? ƙasa ƙasa tace"na yafe maka,amma karka ƙara," murmushi yayi tare da ɗagota daga jikinshi yana kallon fuskarta,sai faman cin magani takeyi tana haɗe mashi fuska, "Kin ci abinci kuwa"? "A'a banci ba," "Why"? Ya tambaya yana kallon bakinta da take ta faman turowa irin na shagwa6a66u, "Kai nake jira kazo ka bani abaki," "Really"? ɗaga mashi kai tayi alamar eh, Juyawa ya ɗanyi tare da kallon jahad dake zaune tana kallonsu gwanin burgewa yace"dagaske hossana bata ci komai ba"?_ Amsa mashi tayi da eh,jinjina kai yayi sannan yace"ki kawo mata dinner ɗinta anan,sai na tabbatar da taci ta ƙoshi sannan zan tafi," Murmushi jahad tayi tare da miƙewa ta wuce downstairs don pta shiryo masu dinner din,"
_💋Boss Bature💋_
Yau da wuri suka dawo cikin gidan wuraren karfe goma dai dai,wani irin tsoro da fargaba sehrish taji,musamman da azmee ta sanar da ita cewa ga dinner É—in sgr can taje takai mashi,bakomai ya faÉ—o mata arai ba face abunda ya faru É—azu tasan cewa dole ya tuhumeta saboda ita kaÉ—ai ce macen da take shiga part É—insa,sai faman zarya takeyi acikin bedroom É—inta,tana tunanin yarda zata tunkare shi ayau É—innan,
Hayaaam
Tafiya takeyi cikin sanɗa tana waige waigen ko akwai wani a main palour din cikin sa'a taga babu kowa,murmushin mugunta ta saki tare da nufar kitchen din,tana shiga tayi arba da tray na abincin da Azmee ta shirya ma Sgr,asaman dogon table na kitchen ɗin ta ajiye mata,jinjina kai hayaam tayi tare da cewa"hmmmmm yarinya kenan yau zaki fara sanin koni wacece wurin iya makirci," Tana faɗin hakan ta shiga ciki kai tsaye ta tsaya wurin tray din,hannu tasa tare da buɗe warmer ɗin dake ɗauke da chicken ppr soup,sai faman ƙamshi yake yi,murmushi hayaam tasaki tare da kai hannu cikin sumar kanta,ta cinko gashin kanta sannan ta jefa acikin chicken ɗin hadasa hannu ta motsashi aciki,sannan ta rufe murfin,duk hakan bai mata ba sai da tabi komai na abincin ta sanya gashi aciki,sannan cikin sanɗa tabar kitchen ɗin,tana faman sakin dariya don tasan cewa da zarar sgr yaga gashin nan yarda yake da tsaftar nan ba ƙaramin ƙyamatar yarinyar zaiyi ba,kuma tasan dole ya koreta daga yi mashi aiki,bama wannan ba dole ya hukuntata, tashin hankali da ba'a sama shi date,
💋💋💋
Fitowa sehrish tayi bayan ta gama zullumin nata,kitchen ɗin ta nufa batare da 6ata lokaci ba ta ɗauko tray ɗin a hannunta tare da wuce wa upstairs,hakanan tadinga jin gabanta na faɗuwa kamar wani mummunan abu zai faru da ita,tsayawa tayi abakin ƙopar shiga falon nashi,sai da ta dai²ta natsuwarta sannan ta zabga sallama,tana jiran jin amsawar shi, Jin shiru yasa ta ƙara maimaita sallamar,har kusan sau uku ana huɗun ne tajiyo muryarshi yace"Come in,"
Ae tunda taji Voice ɗinsa jikinta ya shiga yin kerma,addu'o'in neman tsari tashiga karantowa abakinta,ta jima atsaye tana faman zullumin abun da zaibiyo baya kafin daga bisani ta daure tare da shiga cikin falon nashi,ƙamshin turaren nan nasa ne ya wanko mata hancinta har saida ta lumshe idanunta,tunkan taƙarasa ta hango shi kwance ya miƙe kafafunshi asaman 3 seater,jikinshi na sanye da pyjamas yellow,ba ƙaramin kyau su kayi mashi ba,kunnanshi na kare da wayarshi alamar waya yake yi,   Gabanta na faɗuwa haka ta nufe shi tare da ajiye mashi tray ɗin asaman table dinsa,saboda tsabar rashin gaskiya,tana ajiye tray ɗin ta juya cikin sauri zata bar parlourn nashi,kamar daga sama taji anyi ma mayafinta kwakkwaran ruƙo ta baya,nan take mayafin ya sulale daga jikinta,zazzare ido waje sehrish tayi jikinta na kerma,nan take tashiga haɗiyar yawu,tsayawa tayi tana jiran maizo biya baya,   Jin alamun motsin shi abayanta ya tabbatar mata da cewa shine yaja mayafinta daga jikinta,tsayawa tayi tana ambaton sunan Allah abakinta,ganin kusan minti biyar bata ji ya ƙara motsawa ba yasa tayi hanzarin juyawa a wani irin firgice sam bata tsammaci yana tsaye abayanta ba sai dai kawai taji ta kai mashi karo,ja da baya ta ɗanyi tana faman zare ido,tunkan ya tambayeta ta shiga cewa"dan Allah kayi haƙuri,nasan na 6ata maka rai,wlh nima bada son raina hakan ya faru ba,nashiga na gyara maka bedroom ɗinka ne,bayan na kammala shine na ɗan cire mayafina na ajiye asaman gadonka don naji daɗin yin aikin,ashe kafin na fito daga cikin toilet ɗin ka dawo,shine na same ka akwance kana bacci saman mayafina,saboda ina tsoran ka farka ka ganshi yasa nayi ƙoƙarin janshi daga jikinka,shine...cikin bacci batare da saninka ba ka...........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda jin yatsun hannunshi da tayi asaman lips ɗinta,alamar tayi mashi shiru,sannan ya hankali ya ɗan ware eyes ɗin nashi akan fuskarta............
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
💋BOSS BATURE💋
Follow this link to join my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Father of soldiers (takun ƙarshe)
A tsananin tsorace take kallon fuskarshi ganin ya ware idanunshi yana kallon fuskarta,a hankali ya zame finger ɗinshi daga saman tausasan la66anta dake ta faman kerma,sai faman haɗiyar yawu take yi tsoranta wane hukunci zaiyi mata,sau biyu yana ƙoƙarin buɗe mouth ɗinsa zaiyi magana amma ya kasa,saboda ya rasa me zaiyi ma yarinyar,tun da yake wata ƴa mace bata ta6a ƙetare iyakar da yarinyar ta ƙetare ba,a matsayinta na wadda ba muharramarsa ba kuma ƴar aikin gidansu,ƙara matsawa yayi kusa da ita,cikin sauri sehrish ta ƙara ja da baya,tana faman girgiza mashi kai Alamar yayi haƙuri karya hukunta ta,tuni ta soma fitar da ƴan matan hawaye a idonta,ba komai take kallo ba face damtsen hannunshi da kuma wannan faffaɗan ƙirjin nashi,uwa uba yarda ya tsaya agabanta tamkar wani zaki,
Hannunshi yakai tare da ruƙe waist ɗinshi yana kallon yatsun hannunta dake ta faman kerma,  A natse ya soma magana"I will punish you for the mistake you made in my bedroom on my bed,so that you know under whom you are working,cos u crossed your boundary," Gabanta ne taji yayi wani irin bugu jin abunda sgr yace,hankali tashe take kallonshi,muryarta har kerma take wurin cewa"bazan ƙara ba,"   girgiza kanshi yayi alamar bai amince ba sannan yace"You are going to start frog jumping around the chairs without stopping, if you do that I will let you go, but if you dare stop,I will punish you badly," yana ƙarasa maganar tashi ya juya tare da komawa saman sofa ɗin yana kallonta yace"Am watching u,"yayi maganar tare da nuna mata blue eyes ɗinshi da 2 fingers ɗinshi,alamar idonshi na akanta,   Tamkar ta fashe da kuka haka taji,ga matuƙar tsoranshi da take ji,ga punishment ɗin daya bata na tsallan kwaɗi abunda ta tsana arayuwarta saboda tasan wahalarshi,ba abune mai sauƙi ba bazata ta6a mantawa da lokacin da fawan ya sanyata frog jump ba har jini ya 6alle mata,saboda tsabar wuyar da tasha har suma tayi lokacin,   gyaran muryar da Sgr yayi mata ne yasa tayi saurin zuƙunnawa tare da kama kunnanta da hannayenta sannan a hankali ta soma yin tsallen kwaɗin,in da Allah yasota ma Wando ne ajikinta ba skirt ba da abun yafi muni,da sauri take yin tsallen har ta zagaya ta bayan sofas ɗin ta kuma dawowa ta gabansu duk yana kallonta,tun Sehrish tana yin tsallen kwaɗin cikin daɗin rai har ƙafafunta suka soma rurruƙewa,wani irin zogi suka shiga yi mata,nan take hawaye suka fara shararowa daga idanunta har da majina duka ta haɗa,  Yana jin shessheƙar kukanta amma ko ajikin shi,a ƙarshe ma sai ya ɗauki lemu mai sanyi ya tsiyaya acikin cup ya shiga kur6arshi a bakinsa yana sha,tun yana shan lemun daga zaune har ya ɗan kishingiɗa kafaɗarshi saman sofa hand ɗin,   A wani irin galabaice sehrish ke ɗaga kafafunta tana yin tsallen kwaɗin,a ƙalla ta zagaye kujerun kusan sau takwas amma sgr baice ta dakata ba,tun tana sa ran zai tsayar da ita harta fidda rai,saboda tsabar tsoro da firgicin da take ciki yasa ta gaza gane cewa sgr fa bacci ya kwashe shi asaman sofa ɗin,duk in ta zagayo ta wurinshi sai taga kamar idonshi biyu,batasan cewa tuni bacci yayi awon gaba dashi ba,har ya ajiye cup ɗin dayake shan lemun dashi,
Wani irin matsanancin ciwon kaine ya far mata,ga raɗaɗin da kafafunta keyi mata,lokacin da ta ƙara zagayo wa ta wurin shi,cikin shessheƙar kuka tace"...Am really sorry babban yaya,i ave realized my mistake,bazan ƙara ba nayi maka alƙwarin hakan," tabbas yajiyo muryarta acikin ears ɗinshi amma sam bazai iya buɗe idanunshi ba,saboda nauyin baccin da yayi,  Ganin bai tanka mata ba,yasa sehrish cigaba da yin tsallen kwaɗayin da takeyi dakyar dakyar,tana cikin wannan yanayin wani irin stomach pain ya taso mata haikam,nan take ta yanke jiki ta faɗi saboda galabaitar da tayi,taji jiki sosai,
Sai faman zagaye hayam takeyi a tsakanin upstairs da kuma down,ba don komai ba sai don taga a wani yanayi Sehrish zata fito daga sashen sgr,har wani murmushin mugunta take saki don tasan cewa muddin Sgr yaga siraran gashi a cikin abincinsa dole ya kikkifa Mata mari,sannan ya kore ta daga yi mashi aiki,daganan ita kuma zata samu shiga a wurin shi,gajiya ta fara yi da zagayen ganin cewa har ƙarfe sha biyu na dare tayi Sehrish bata fito daga part ɗinshi ba,hakan ba ƙaramin ƙona mata rai yayi ba,baƙin ciki kamar ya kashe ta,tsayawa tayi ruƙe da qugu tana cewa"Ko uban me yarinyar can takeyi a part ɗinsa har wannan lokacin bata fito ba!wlh na tsani yarinyar can,ko son ganinta bana yi,shisshiginta yayi yawa nasan yanzu haka tana can ta liƙe mashi tana kalle mun surar jikin mijina,Allah bazan ƙyaleta ba sai nayi maganinta mtssw,!"ta ƙarasa maganar tare da jan dogon tsoki sannan ta kama hanyar komawa bedroom ɗinta tana faman sambatu kamar wata zautacciya ,"
_💋Boss Bature💋_
Kwance yake asaman gadon Abbansu hannunshi rungume da pillow,yayin da idanunshi ke arufe tamkar mai bacci, Yana jin lokacin da abbansu ya fito daga cikin toilet jikin shi sanye da Jallabiya,ƙarasowa yayi wurin gadon tare da samun wuri daga ɗan gefe ya zauna,sannan ya ɗan juya tare da kallon fuskar junaid da yayi likimo kamar mai bacci,hannu yasa tare da shafa sumar kanshi yace"sarkin rigima yayi bacci,"ya faɗi da murmushi a fuskarshi,janye hannunshi yayi daga saman sumar kan junaid,sannan ya miƙa hannu tare da ɗaukar wayarshi dake ajiye a saman bedside drawer,contact ɗinshi ya shiga ya lalubo numbar mommynsu junaid ya danna mata kira,nan take kiran ya shiga,cikin sa'a ta ɗaga kiran nashi,murmushi yayi tare da kara wayar a kunnanshi yace"Noorul ƙalbina"  On the other hand alexandra tace"yau kuma soyayyarce ta motsa?ni zaka yaudara da kalamanka saboda kaji cewa zanzo nigeria ko?to ae ba saboda kai zanzo ba,zanzo ne don naga Yarona kuma da zarar nazo zan ɗauke abuna na dawo Australlia dashi,don bazan barshi a hannunku ba don ban yarda da irin rainon da kake mashi ba,"   girgiza kai abbansu yayi tare da cewa"Yaushe zaki canza ne?ke ko tausayina bakya ji ne?baki damu da halin da nake ciki ba,na rashinki a kusa dani,ina fa sonki har yanzu kuma ban rabu dake ba,kece kika rabu dani kika kama hanya kika bar ƙasar nan batare da sani na ba,yanzu kinyi mun adalci"? Cikin sanyin murya ya ƙarasa maganar yana sauraron Amsarta Junaid daya kasa kunne yana sauraransu sai faman murmushi yake yi idonshi a rufe,   Shiru Alexandra tayi yayin da idanunta ke kallon sararin samaniya ta cikin windown katafaren bedroom ɗinta,kunnanta na kare da wayarta tana sauraron shi,muryarshi ta kuma ji yana cewa"kinyi shiru baki ce komai ba"?  Ajiyar zuciya ta sauke tare da ɗan jinjina kai tace"me kake so yanzu"?    Runtse ido abbansu yayi saboda ya rasa yarda zai fahimtar da ita,wata irin bauɗaɗɗiyar mace ce,ko don tayi aikin soja ne yasa ta kasance haka,saboda a tsaye take ba irin raunin zuciyar nan na mata,   "Hossein in baka da abun cewa,Ni zan aje waya ne,"  Muryarta ce ta kuma katse shi,a lokacin ranshi ya gama 6aci a faɗace yace"Fatima na gaji da irin wulaƙancin da kikeyi mun,nayi danasanin haɗuwata dake tun farko,kuma nayi danasanin haɗa zuri'a dake,saboda kin cutar da rayuwata,sam baki respecting ɗina a matsayina na mijinki,kuma uban ya'yanki,idan kinsan zaki tafi kibarni meyasa tunfarko kika sanyamun soyayyarki acikin zuciyata?   Muryarshi araunace yayi maganar yanayin sautin kamar zai fashe mata da kuka,   Jin tayi shiru bata ce mashi uffan ba yasa shi cewa"banaso ki dawo ƙasar nan!ki cigaba da zama acan,saboda zuwan naki baida amfani awurina,kuma babu ruwanki da ƴa'ƴana dama can baki damu dasu ba,tun da har zaki iya tafiya kibarsu,batare da tunanin yaya rayuwarsu zata kasance ba"!  Jin wannan maganar ta Abban nasu yasa hawaye suka soma gangarowa a idanun junaid,sam baiji daɗin yarda mommynsu ke 6ata ma Abbanshi rai ba,   Bai jira Alexandra ta bashi amsa ba ya katse kiran nata tare da yin wurgi da wayar gefe guda,jiki amace ya kifa kanshi asaman gadon,idanunshi sunyi jawur sun cicciko da kwalla,   a hankali hawayen suka soma gangarowa,kamar daga sama yaji tafin hannu a fuskarshi,cikin sauri yakai idonshi akan junaid dake share mashi hawayen fuskarshi,  Cikin shessheƙar kuka yace"Abba don Allah kadaina zubar da hawayenka akan mommynmu,ba dole sai da ita zaka samu farin ciki ba Abba,Ni na isheka duk wani farin cikin duniyar nan,Abba ka ta6a faɗamun cewa ko kallona kayi kanajin sanyi aranka,why zaka Sanya ma kanka damuwa akan mommynmu?ka rabu da ita kawai Abba,akwai mata da yawa agari waɗanda suka fi ta hankali.........'   Murmushi Abban nasu yayi jin abunda junaid yace,   Miƙewa yayi daga zaune suna fuskantar juna yace"junaid bazaka gane ba!mommynku ba kamar sauran mata take ba,idon har tana raye ni bazan iya kula wata ƴa' mace ba,"   ɗaure fuska junaid yayi tare da zum6ura baki yace"Saboda me Abba?me tafi sauran matan?duk yarda take 6ata maka rai?    "Junaid she's special saboda ta bani babbar kyautar da har yau in na kalleta nake jin farin ciki araina,"   Cike da mamaki junaid yace"Wata irin babbar kyautace wannan? Ya tambaya yana kallon Abban nasu,   Murmushi Abbanshi yayi tare da nuna shi da yatsanshi yace"Am talking about u junaid!Matar da ta haifamun lu'u lu'u kamarka taya zan iya rabuwa da ita junaid?ta bani farin cikin da har na bar duniyar nan bazan ta6a samun makamancinshi ba,kyakkyawan yaron da kowa ke alfahari dashi,kowa yake so kuma yake ƙauna,Junaid bani da burin da ya wuce in farka in ganka akusa dani da ranka da lafiyarka...........'  Tsagaitawa yayi da maganar yana kallon junaid da bakinsa yaƙi rufuwa saboda tsabar farin ciki kamar ya zuba ruwa ƙasa yasha,sai faman washe baki yake yi,kamar wanda akayima albishir da gidan Aljanna,ya ma rasa mai zaiyi don tsabar farin ciki,a ƙarshe ya faɗa jikin Abban nasu tare da rungumeshi ya ƙankame shi sosai ajikinshi yana faman dariya,    Zagayo da hannunshi yayi yana ɗan bubbuga Bayan junaid yaci gaba da cewa"I love u so much my baby boy,Allah ya nuna mun ranar auranka kafin nabar duniya,koda ace shine abu na ƙarshe da zan gani kafin na koma ga mahalicci na,Ina rokon Allah ya nuna min wannan ranar,da shagwa6a66an yarona zaiyi aure,zanso naga yaron da matarka zata haifa mana,wanda zamu dinga kira da Babyn baby,"  Fashewa sukayi da dariya, suka dinga yi atare,har lokacin basu raba jikinsu ba,   Ƙarar shigowar message a wayar Abban nasu ce,yasa junaid janye jikinshi daga na abban nasu sannan ya rarrafa tare da kai hannu ya ɗauko mashi wayar,ya miƙa mashi,  Kar6a Abba yayi tare da duba message ɗin da aka turo mashi yana karantawa kamar haka   "Forgive me my love.......nasan na 6ata maka rai sosae,kayi haƙuri ka yafe mun kuma inaso kasan cewa nima ina sonka sosai har yanzu ba abunda ya sauya na sonka acikin zuciyata,zan dawo nigeria ne saboda na gyara alaƙata da uban ƴa'ƴana,da kuma ƴa'ƴan nawa,ka shirya tarbar amaryarka Alexandra...........'  gaba ɗaya ya rikice saboda tsabar farin cikin saƙon da ya shigo mashi,saboda ruɗu har hannu yasa yana goge idanunshi wai ko badaidai ya karanta bane,saboda tunda yake arayuwarshi alexandra bata ta6a bashi hakuri ba,bai ta6ajin kalmar sorry daga bakinta ba,koda ace tayi mashi laifi sai dai shiya bata haƙuri ya rarrashe ta amma badai ita ba ae tafi ƙarfin wannan,amma yau ita da kanta take bashi hakuri!?_  Ganin yarda Abban nasu ke ta sakin murmushi yasa junaid cewa"Abba menene naga kamar farin ciki a fuskarka,"  Miƙa mashi wayar abban nasu yayi dama tsakaninsu babu 6oye 6oye,  "Junaid dubamin ka gani,kodai idona ne ke nunamin ba daidai ba,wai mommynku ce ke ban haƙuri da kanta,"  hannu junaid yasa ya kar6i wayar daga hannun Abban nasu ya shiga karanta saƙon,nan take yaji wani irin sanyi aranshi,   "Junaid baka ji farin cikin dana ji ba wlh,naji daɗin saƙon nan na mommynku,da ace bataban haƙuri ba da bansan a wani yanayi zan kwana ba yau,"  Murmushi junaid yayi bayan ya kammala karanta saƙon cike da zolaya yace"Su Abba an kusa angwancewa,amarya mommyn junaid zata dawo,amma dai Abba idan tadawo nigeria ba zaka kore ni daga kwana bedroom ɗinka ba ko?   Wani irin kallo abban nasu ya jefa mashi tare da cewa"Ae aranar da tadawo,zaka tattara yanaka yanaka kabarmin ɗakina,dama nagaji da kwana tare da ƙato a ɗakina.....'kasa ƙarasa maganar yayi saboda dariyar daya kwashe da ita,junaid kuwa tsuke fuska yayi yace"Allah Abba ba inda zanje ko mommy ta dawo,sai dai mu rinka kwana tare daku,ku sanyani a tsakiyarku muyi bacci atare," ashagwa6e ya ƙarasa maganar tashi,   harara abba ya watsa mashi tare da cewa"Allah ya kiyaye mu kwana tare da kai,"   Da buɗar bakin junaid sai cewa yayi"Abba kaima ya haramta a musulunce ka kwana tare da mommynmu......'tunkan ya ƙarasa maganar tashi,Abban nasu ya wawuro pillow tare da buga mashi asaman kanshi yana cewa"gidan ubanwa ka ta6a jin haka junaid?waya koya maka wannan kalamin ƙabihin?   dariya junaid ya shiga yi yana tarbe pillown da yake bugun shi dashi,gaba daya suka shiga yin wasan bugu da pillow shi da abban nasu,yarda kasan wasu ƙananun yara,sun jima suna shiririta kafin daga bisani bacci ya kwashe su gaba ɗayansu kowa hannun shi ruke da pillow,
_💋Boss Bature💋_
Tun bayan da Jahad ta haɗo mashi abincin a tray,ta kawo mashi anan ƙasa ya sauko tare da hossana suka zauna,da kanshi ya dinga ɗebo abincin yana bata abaki tana ci,sai da ya tabbatar da taci ta ƙoshi sannan ya ƙyaleta,ya jima a wurinsu suna fira atare gwanin ban sha'awa kafin daga bisani wurin sallar isha'e yayi masu sallama da nufin zaije yayi sallah ya dawo kafin ya wuce gida,
Lokacin da Omar ya dawo,bai same su a palourn ba babu kowa aciki,hakan ya tabbatar mashi da cewa sunyi bacci don yadan jima daya fita masallacin,tsayawa yayi yana tunanin ya tafi ko ya tsaya,harya juya yaji cewa bazai iya tafiya batare daya ƙara sanya Hossana a idanunshi ba,   juyawa yayi tare da nufar bedroom ɗinsu,a hankali ya tura door ɗin ɗakin,sannan yasa kai ya shiga da sallama abakin shi,   Sunyi nisa acikin baccinsu,hankalinsu kwance sai faman sharara bacci suke yi,kowaccen su na sanye cikin kayan baccinsu,jahad riga da wando farare,hossana kuma ƴar riga ce dai dai guiwa pink colour,sharara rigar take,saboda daɗin bacci ta hankaɗe rigar tayi sama hakan ya bayyana santala santalan cinyoyinta da suka ji hutu,dama bata iya kwanciyar bacci ba,   tsayawa Omar yayi yana kallonsu ta hanyar hasken Bedside lamps ɗin da suka kunna,sun haskaka wurin gadon nasu,yarda suke bacci cikin kwanciyar hankali ba ƙaramin kyau su kayi mashi ba,har ya yanke shawarar ya juya yabar bedroom din idonshi suka sauka akan laps ɗin hossana dake dan kerma alamar sanyi ya kama kafafunta,kafin su kwanta sai da Jahad ta lullu6esu,cikin bacci hossana tayi wurgi da bargon gaba ɗaya,ya yi gefe guda can ƙasan ƙafafunsu,   ƙarasawa ciki omar yayi da nufin ya rufe su da bargon,amma tunda ya isa wurin gadon,ya gaza janye idanunshi daga kallon surar jikin hossana,abun da bai ta6a yi ba,tamkar ana ingiza shi zuwa gare ta haka ya dinga ji,nan take yaji wata irin ƙishirwar sha'awarta ta kama shi lokaci guda,gaba daya ya makance akanta har baisan lokacin da ya faɗa jikinta ba gaba ɗaya,ya shiga ƙoƙarin biyan buƙatarshi,tuni ya zame hannun rigar jikinta,ya sulale ta izuwa kasa har wurin stomach ɗinta,ba ƙaramin rikicewa yayi da gani booobs ɗinta ba,a cike fam suke tuni suka tsone mashi ido,gaba daya omar ya farmasu kyakkyawar damƙa yayi masu ya shiga murzasu a hannunshi,jikin shi har kerma yake yi,laushin su ba ƙaramin gigita shi su kayi ba hakan yasa yakai bakinsa gaba ɗaya,   A wani irin firgice hossana ta farka saboda raɗaɗin da taji kan nipples ɗinta,jin mutum asaman jikinta yasa ta fasa wata irin razananniyar ƙara mai sautin gaske tana faɗin"Jahad!!jahad!!nashiga uku!Abba zai cutar dani!dan Allah kadaina !ka bari!kada ka kashe ni mutuwa zanyi!dan Allah kabari Abba banso!!!!!gaba daya Omar baya a hayyacinsa ƙoƙarin zame belt ɗin wandonshi yake yi don ya cimma inda yake son zuwa,    Wannan ihun da hossana keyi ne ya farkar da jahad,a wani irin gigice ta yunƙura tare da miƙewa zaune tana kallon wannan tashin hankalin,kamar a mafarki haka take kallon Lamarin,saboda tsabar ruɗu bata gane fuskar waye ba,da hanzarin gaske ta dunƙule hannayenta tare da daddagewa ta ɗuma mashi dundu abayanshi,amma ko gizau Omar baiyi ba sai faman cigaba da abunda yake ƙoƙarin yi yake,   Fasa ihu jahad tayi tana faɗin"Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!"gaba daya ta rasa ta yarda zata iya ceton Hossana,ƙoƙarin ruƙo shi ta shiga yi,aikuwa gaba ɗaya Omar yayi wurgi da ita,gaba ɗaya jahad ta gangara ta faɗa ƙasan gadon,kanta ba ƙaramin buguwa yayi ba,kafin jahad ta yunkura ta taso daga faɗawar nan da tayi,hossana ta daddage ta gartsa mashi cizo asaman damtse hannunshi,kusan sau uku tana cizon shi amma ko gezau baiyi ba,gashi harta fasa mashi fatar jikinshi,shaidar jinin harya fara fitowa ajikin farar shirt ɗin dake ajikinshi,  Ganin yana ƙoƙarin zame pant ɗin jikinta daya rage mata,yasa Hossana fashewa da wani irin sabon kuka tana cewa"Jahad kizo ki taimakeni!zai kashe ni!Abba zai cutar da rayuwata!Ya Omar bazai barka ba sai ya kashe ka........"idanunta na arufe take ambaton hakan yayin da hawaye ke 6ulbulowa daga cikinsu kamar an kunna fanfo,   Lokaci guda tunaninshi yadawo cikin hayyacinshi ta dalilin sunan shi da hossana ta ambata,zaro ido Omar yayi hankalinshi a matukar tashe yake kallon hossana daya raba ta da kayan jikinta,innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,A uzubillahi minasshaiɗanin rajim!!!shine abunda ya shiga ambata abakinshi,gaba ɗaya yabi ya gigice kanshi yashiga sara mashi da wani irin matsanancin ciwon kai,kunyar duniya tabi ta baibaiye shi,a hanzarce ya miƙe da saurin gaske ya fuce yabar bedroom ɗin,cikin sa'a batare da Hossana ta buɗe idanunta ba,kuma batare da jahad taganshi ba,dukansu babu wanda ya shaida shi,ƙaramin kuskure kan iya jefa mutum faɗawa tarkon shaiɗan,omar yayi danasanin dawowarshi cikin gidan,yayi danasanin shiga bedroom ɗinsu,in banda tsautsai da ƙaddara bai ta6a gigin shiga ɗakinsu ba sai yau,     Fucewarshi ke da wuya,jahad ta ɗago da kanta daga buguwar da tayi a ƙasa wurin harya ɗan fashe kaɗan,da saurin gaske ta haye saman gadon tana faman shessheƙar kuka,tsayawa tayi tana faman wurga ido cike da mamaki ganin babu mutumin nan dake ƙoƙarin keta haddin hossana,abun ba ƙaramin ɗaure mata kai yayi ba,6aat babu shi babu alamar shi,  Cikin sauri ta ƙarasa wurin hossana dake a kwance babu kaya ajikinta,da alama suma tayi saboda tsabar firgicin data shiga,    Hannu jahad takai tare da janyo bargo ta lullu6e mata jikinta,sannan ta rungumota ajikinta tana faman ambaton sunanta"Hossana!!hossana!!!"ganin ko motsi taƙiyi yasa hankalin jahad tashi,jijjigata tashiga yi tana cewa"Hossana ki farka dan Allah!!ki tashi!Allah yasa bai kaiga cutar dake ba!nashiga ukuna ni yau!meyasa haka ke faruwa dake ne?burin kowa yaga ya lalata maki rayuwarki hossana!meyasa bazasu barki kiji da abunda ke damunki ba!meyasa bai tunkare ni ba sai ke........'kasa karasa maganar tayi saboda kukan daya ciyota,mai raɗaɗin gaske,gaba daya ta fashe da matsanancin kuka tana cewa"Ya Allah kasa mafarki nake ba gaske ba!!Allah karka nunamin wannan ranar da zan rasa ƴar uwata!!hossana dan Allah ki tashi kada ki mutu kibarni.......'  Ganin ko motsi hossana taƙiyi yasa jahad sakinta tare da yin saurin saukowa daga saman gadon,da gudun gaske ta fito cikin falon tare da nufar telephone don ta kira Ya omar ɗinsu ta sanar dashi abunda ke faruwa cewa wani ya shigo musu cikin gidansu,   Hannunta har kerma suke yi wurin daukar telephone ɗin tare da danna numbers ɗinsa ta buga mashi kira,Allah Allah take akan ya ɗaga kiran ta sanar mashi saboda tsoran Kada mutumin ya ƙara dawowa,ga kuma hossana dake kwance araye ko amace,   Lokacin da kiran Jahad ya shigo wayar Marshall Omar,yana acikin motar shi bawan Allah,duk yabi ya takure yaji ya tsani rayuwarshi gaba ɗaya,kamar ya binne kanshi haka yake ji,wasu irin zafafan hawaye ne ke gangarowa daga idanunshi sai faman cizon la66anshi yake yi,idanunshi sunyi jawur,   Jikin Major ba ƙaramin sanyi yayi ba,saboda ya gane halin da Ogan nashi yake ciki,ga wayarsa sai faman ringing takeyi amma yaƙi ɗaukota bare yayi picking call ɗin,  A hankali major yayi parking ɗin motar tasu agefen titi ba don komai ba sai don baijin zai iya cigaba da driving yayin da oganshi ke cikin wani yanayi,   Ganin ya tsayar da Motar yasa Omar cewa"major meyasa ka tsayar da motar"?   Cikin sanyin murya major yace"ka gafarce yalla6ai,bazan iya driving ɗin bane,saboda gaba daya jikina amace yake,guiwowina sun sage tamkar anzare lakar jikina haka nake ji,bansan me ya faru dakaiba amma ina da tabbacin cewa wani abu mara daɗi ne yasaka shiga wannan halin da kake ciki,"   Muryarshi tamkar zaiyi kuka yace"Major yau nayi abun kunya,naji kunya sosai kamar na binne kaine,ashe dama shaiɗan baida tabbas"?yayi tambayar yayin da zuciyarshi ke cigaba dayi mashi ƙuna,  Cigaba da magana yayi"major yau ni da kaina nayi attempting rape,kuma ba kowa nayi yunkurin aikata ma hakan ba face hossana.....'
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
    *💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Abban sojoji paid book ne,ga duk mai buÆ™atar karanta cigaban shi yayi mun magana kai tsaye ta number ta 08103884440 Whatsapp only banda phone calls, 300 ne only ðŸ¤
Cigaba da magana yayi"major yau ni da kaina nayi attempting rape,kuma ba kowa nayi yunkurin aikata ma hakan ba face hossana.....'   Jin abunda omar yace yasa major cikin tashin hankali yace"Subhanallahi!!yalla6ai garin yaya hakan ya faru!nidai nasan cewa bayin kanka bane,na yarda dakai sosai,Ni shaidane akanka yalla6ai,kai da kanka kake hukunta masu aikatawa,kana ɗaya daga cikin mutanan dake daraja ƴa mace,ba zaka ta6a yin hakan abisa son ranka ba,"   "Major naji haushi sosai,zuciyata batamun daɗi,duk nabi na tsani kaina,nayi abun kunyar da bazan ta6a mantawa ba,indama na godema Allah yaran basu shaidani ba,da idanunsu da ace sun gane ni ne da nasan cewa duk wani girma na da suke gani zai zube ne,kuma zasu fara tunanin cewa ba don Allah na taimaki rayuwarsu ba...."   tsananin tausayinshi ne ya kama major,da yana da halin da zai cire damuwar dake acikin zuciyar ogan nashi da tuni yayi exchanging heart ɗinsu,ba don komai ba sai don ya tsani yaga marshal acikin wani hali na ƙunci,   daƙyar major ya kwantar mashi da hankalinshi ta hanyar yi mashi tausasan kalamai masu daɗin gaske har sai daya ga ya shiga natsuwarshi sosai sannan ya tashi motar suka nufi gida,   kuka sosai jahad keyi ganin tana ta jaraba kiran layin Omar amma ba'a ɗagawa,a ƙarshe ma da ta ƙara kira sai ta samu wayar a switch off,jiki asanyaye ta mayar da telephone din ta ajiye asaman table ɗin,   dafe kanta tayi saboda wani irin raɗaɗi da taji yana yi mata,gaza tsayawa tayi da ƙafafunta nan take ta yanke jiki ta faɗi ƙasa asume,
Tashin hankalin da ba'a samashi date!a can 6angaren sehrish ta sume,anan 6angaren kuma hossana da jahad sun sume,ko mai zai biyo baya?
Wuraren ƙarfe 1:30 na dare,Ayaan na kwance cikin kayan baccinsa,yaji hannun mutun acikin wandonshi,a firgice ya farka tare da ware idanunshi akan wanda ke lalubar jikin nashi,ganin jahan asaman jikinshi yasa yayi hanzarin yin wurgi dashi gefe guda ya tashi zaune rai a6ace yace"Jahan!banason wannan wasan!karka kuskura ka ƙara ta6a jikina in ba......'bai ƙarasa maganar ba saboda haɗe bakinsu da jahan yayi wuri guda yashiga ƙoƙarin zura harshen shi acikin bakinsa,   Hankali tashe Ayaan ya rurruƙe shi yana kiciniyar kwace kanshi daga hannun jahan amma abun yaci tura,kamar wani zombie haka ya koma mashi, Muryarshi har shaƙewa takeyi wurin cewa"Ja...ja..jahan!ka rabu dani!wai meyake damunka ne!baka da hankaline kasan me kake ƙoƙarin yi mun ne,yayi maganar tare da janye jahan daga jikinshi yana kallon shi,   Wata irin zuface ke gangarowa daga cikin sumar kanshi saboda tsabar jarabar da yake ji,  A kasalance yace"ayaan kadaina mun wasan nan,kasan fa abunda nake buƙata awurinka,ka bani haɗin kai kamar yarda muka saba,baka ji yadda nake ji ba ajikina....'Ya ƙarasa maganar yana faman lumshe idanunshi,  Ayaan kuwa kallonshi yake yi gwanin ban tsoro,lokaci guda kuma ya tuna komai yace"Jahan kayi haƙuri bazan iya ba,na ƙyamaci abun acikin zuciyata,ya fita raina gaba ɗaya,bazan iya cigaba da aikata wannan mummunan zunubin ba,bayan Allah ya yaye mun,idan harna biye maka muka aikata hakan,hukunci zai hau kaina,Allah bazai......'kafin Ayaan ya ƙarasa maganar tuni Jahan yayi kukan kura ya afka mashi,don bazai juri sauraron kalamanshi ba,saboda a ƙagare yake daya kawar da muguwar sha'awar data taso mashi mai tare da wani irin raɗaɗi,  Dambe suka shiga yi atsakaninsu,jahan na ƙoƙarin zame ma Ayaan kayan jikinshi,yayin da Ayaan ke ƙoƙarin kufcewa daga hannunshi ya gudu,wani irin ƙarfi jahan ke ji gaba daya ya zauce ya fara fita hayyacinshi burinshi ya biya mashi buƙatarshi,kafin wani lokaci jahan ya yayyaga ma Ayaan rigar jikinshi,yayi mata kaca kaca,ruƙo wandon jikinshi yayi tare da janshi ya zame gaba ɗaya,ya rage daga shi sai short ajinshi,a lokacin ya tattara dukkan wani ƙarfin shi yayi wurgi da jahan gefe guda saman gadon,sannan da gudun gaske ayaan ya sauko daga saman gadon ya faɗa cikin toilet ɗinsu tare da rufe ƙopar,yana faman sauke ajiyar zuciya,a bakin kopar ya tsaya tare da kasa kunne yana sauraran gurnanin da Jahan keyi,  tsigar jikinshi ce ta soma tashi tsaitsaiye,nan take idanunshi sukayi wani irin ja tamkar garwashin wuta,saukar bulali ya dinga ji ta ko'ina abayanshi nan take yabi ya gigice ya dinga sakin ihu yana kuka mai cin ran,  Runtse ido Ayaan yayi wani irin tausayin shi ne ya kama shi,saboda yasan irin halin da suke shiga aduk lokacin da basu kusanci junansu ba,tabbas Jahan bazai rayu ba muddin bai bashi haɗin kai ba,fashewa da kuka Ayaan yayi tare da sulalewa ya zukunna abakin ƙopar toilet ɗin yana faman shassheƙar kuka,  Yana jiyo yarda jahan ke ta faman ihu yana kuka,akan kunnanshi yaji sautin faɗowar jahan daga saman gadon,ta hanyar sautin da yaji timmmmmm!  rarrafowa jahan yayi daƙyar yake jan jikinshi har ya isa bakin ƙopar toilet din,muryarshi na kerma yace"Ayaan yau kai da kanka kake guduna!bayan kasan irin halin da muke shiga aduk lokacin da bamu aikata hakan atsakanin junan mu ba!so kake na mutu ko"? daƙyar sautin maganarshi ke fita,maƙoshin shi tuni ya jima da bushewa ƙamas,numfashinshi daƙyar yake fita, Cikin muryar kuka Ayaan yace "am really sorry jahan,ina mai matukar takaicin gaza taimakonka a wannan lokacin,zanyi kuka sosai in na rasa ka jahan,bani da tamkarka aduniyar nan,ina tsananin kaunarka sosai ɗan uwana,kayi haƙuri ka yafe mun........"kasa ƙarasar maganar yayi saboda kukan daya ciyoshi,   tamkar zaiyi hauka haka ya dinga ji,gaba daya rayuwarshi tashiga cikin ƙunci,idonshi ya makance,makoshin shi ya bushe,ya rasa duk wani kuzarin jikinshi,lokaci guda ya zama zautacce yabi ya burkice sai faman magiya yake yi ma Ayaan ya taimaka ma rayuwarshi amma ina Ayaan sam yaƙi buɗewa bama alamar zai buɗe, Wani irin sauti Jahan ya shiga fitarwa tamkar ranshi ne ke fita,hakan ba ƙaramin gigita Ayaan yayi ba,muryar jahan yaji ƙasa ƙasa yana cewa"Ayaan maƙoshina ya bushe!mutuwa zanyi ka taimakamin da ruwa insha,"agalabaice yake maganar,  Da hanzarin gaske Ayaan ya buɗe ƙopar ɗakin,anan yayi arba da Jahan baje ƙasa rai hannun Allah jikinshi sai karkarwa yake,wasu irin sahun bulali ne a jikinshi ta ko'ina ga shaidarsu nan asaman farar fatar jikinshi,dama babu kaya ajikinshi iya gajeran wando ne ya bari,   ɗaga ƙafa ayaan yayi zaije ya ɗauko mashi ruwan,kamar daga sama yaji jahan ya ruƙo kafarshi da ƙarfin gaske nan take ya kife ƙasa timmmm,jan jiki Jahan yayi tare da hayewa saman jikin Ayaan ya ƙankame shi ruƙo bana wasa ba,sannan ya shiga biyan buƙatar shi,wa'iyazubillah!wannan wata irin masifa ce!
 Gaba ɗaya jahan ya gama kashe mashi jikinshi,ko hannunshi bai iya ɗagawa,babban abunda yake tsoro kada wani ya faɗo ya same su acikin wannan yanayin da suke,   kiciniyar kwace kanshi ya shiga yi da iya ƙarfinshi na karshe amma hakan ya gagara,a ƙarshe daya rasa yadda zaiyi saiya daddage ya garza ma jahan cizo asaman ƙirjinshi,ko gizau baiyi ba,   wani irin juyi Ayaan yayi anan ya samu nasarar hankaɗe jahan yayi gefe guda ƙasa,shi kuma ya tashi cikin sauri yana gyara short ɗin jikinshi,      Har yasa ƙafa zai bar ɗakin,yaji gabanshi yayi wani irin mugun bugu,cikin sauri ya juya tare da kallon jahan da idanunshi ke kallon sama,kwata kwata baya motsi komai nashi ya tsaya cak da yin aiki,waro ido waje yayi da hanzarin gaske ya koma wurinshi tare da zubewa saman guiwar ƙafafunshi yana ambaton sunanshi hankali a matukar tashe!  "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!Jahan!jahan!don Allah kayi magana!ɗan uwana kada ka mutu ka barni!bana fata ace ni nayi silar barinka duniya!na cuce ka jahan nagaza cetonka!ka yafe mun ba laifina bane!"   Kuka sosai Ayaan keyi yana jijjiga jikin Jahan,bai da wata mafita a halin yanzu,ji yake tamkar ya watsa aguje yaje ya sanar ma su Abbansu halin da ake ciki,amma fargabar kada ace jahan ba mutuwa yayi ba,in har hakan ta faru to tabbas zai iya farkawa agabansu ya cakume shi ya shiga ƙoƙarin biyan bukatar shi agabansu,tunda baya acikin hayyacinshi,   Yasha kuka sosai kamar kamar me,a ƙarshe ya yanke shawarar zuwa ya ɗauko ruwa don ya yayyafa mashi ajikinshi ya ga ko zai farka,  A hanzarce ya miƙe tare da kama hanya ya fuce daga cikin bedroom din,  Sauri yake yi tamkar zai tashi sama aranshi sai addu'a yake yi Allah yasa jahan ba mutuwa yayi ba,
Fitar shi ke da wuya daga cikin bedroom din nasu,Haroon ya faɗo cikin ɗakin afusace don yayi masu magana akan Money bag ɗinsa da yake zargin su suka ɗauke shi,koda yayi arba da jahan kwance aƙasa baya motsi,abun ba ƙaramin ɗaure mashi kai yayi ba,ta6e baki yayi tare da shigewa ciki,ya zukunna adaidai inda jahan ɗin yake kwance,yakai hannu tare da shafa ƙirjinshi,da yake shu'umine,nan take ya gane awane hali jahan yake,   sunnar da kanshi yayi tare da haɗe bakinshi wuri ɗaya dana jahan,zura tongue ɗinshi yayi acikin bakin jahan,aikuwa awani irin yanayi Jahan yayi motsi alamar yaji abunda yakeso,batare da 6ata lokaci ba Haroon ya shiga biya mashi buƙatar shi,    Ayaan na ƙarasawa wurin fridge ɗin yasa hannu tare da buɗewa cikin sauri,hannu yakai cikin jerin bottles water ɗin dake a jere cikin frigde ɗin,har zai ɗauki robar ruwan swan idon shi ya sauka akan Robar ruwan addu'ar nan da junaid ya ajiye ta sehrish,bakomai ne yaja hankalin shi akan robar ba,face rubutun Larabcin dake rubuce ajikinta,tunda akeyi masu order na abunsha,ba'a ta6a kawo masu kalar robar ruwan nan ba,mai rubutun labarabci ajikinta,zubama robar ido yayi yana kallonta nan take abunda ya faru ɗazu ya faɗo mashi aranshi,wasiwasi Ayaan yashiga yi acikin ranshi yana cewa"wannan roban ruwan kamar itace na ɗauka ɗazu nasha!kuma tunda nasha ta komai nawa ya canza,tabbas ina tunanin cewa tana tattare da wani abu ajikinta,amma kuma waye ya ajiyeta indai haka ne?don ina da tabbacin cewa ba'a kawo mana kalar wannan bottle water ɗin acikin gidan mu!bari na jaraba kaima Jahan ya sha,tanan zan gane abunda ke tattare da robar ruwan nan!"  Yana ƙarasa zancen zucin nashi batare da 6ata lokaci ba,ya sungumi robar ruwan a hannunshi,bayan ya rufe frigde ɗin,da saurin gaske ya wuce part ɗinsu,  Yana gab da shiga bedroom ɗin nasu,ya dinga jin wani irin gurnani mara daɗin ji,a wani irin tsorace ya afka cikin ɗakin,waro idonshi waje yayi saboda tsabar 6acin rai baisan sa'adda yayi wurgi da Robar ruwan dake a hannunshi ba,nan take ta faɗi ƙasa tana gangarawa murfinta ya cire,ruwan cikinta ya kwarare ƙasa gaba ɗaya,   A fusace ya ƙarasa tare da damƙar rigar haroon da iya ƙarfin shi na ƙarshe yayi wurgi dashi gefe guda,ɗagowa haroon yayi yana kallon Ayaan da idanunshi waɗanda suka canza launi izuwa jawur dasu,sai faman lashe bakinshi yake kamar wani tsohon maye,   Rai a6ace ayaan yace"wai kai wani irin daƙiƙin mutum ne dabba!kuma jahili wanda baisan ciwon kanshi ba!mugu azzalumi kawai,banta6a ganin fasiƙin mutum irinka ba!wanda baya tsoran Allah!"ran Ayaan ba ƙaramin 6aci yayi ba,yana magana hawaye na gangarowa daga idanunshi masu zafin gaske,   Duk a tunaninshi haroon zai ji haushin kalamanshi,amma abun mamaki fuskarshi ɗauke da wannan shu'umin murmushin nashi yace"Kwantar da hankalin ka mana!nifa ceton rai nike,duk irin son da kake ma Jahan ka gaza taimakon shi,kana ji kana gani zai mutu,ni kuma bazan so haka ba saboda inason ɗan uwana,shiyasa nayi hakan don na cetoshi daka halaka......'  Tunkan ya ƙarasa maganar Ayaan ya daka mashi tsawa tare da cewa"Karka kuskura ka ƙara ambaton sunan jahan a matsayin ɗan uwanka!kai ba jinin mu bane,mutun mai halin dabbobi irinka bazai ta6a zama jinin mu ba,yanzu bana doubting akan haka,Haruna kai ba ɗan uwanmu bane!ka wulaƙanta rayuwarmu,Allah ba zai ta6a barin ka ba,ƙarshen ka bazai yi kyau ba haroon!tun wuri ina baka shawarar ka tattara kayanka kabar gidan nan tun kafin lokaci ya ƙure maka!!!!"   fashewa da dariya haroon yayi,a yayin da yake miƙewa tsaye daga zaunen da yake a ƙasa,takawa yayi izuwa wurin da Ayaan yake sannan yace"naji duk bayananka akaina,kuma naji shawarar da ka bani,inaso ka sani cewa ko kaɗan banji tsoro akan kalaman da kayimun ba,ka ajiye wannan zamuyi magana akanshi,abun da ya kawoni ɗakinku shine Jakar kuɗin Da kuka kaimun ban ganta ba,an ɗauke ta daga ɗakina,kuma ba kowa nake zargi ba face ku,saboda ku kaɗae kukasan da zancen kuɗin,bayan ku babu wani da yasan da maganar!!ina jakar kuɗina take!!"    takaici ne yasa Ayaan kasa yin magana tabbas da ace yana da halin kawar da haroon da tuni yakai shi inda ya dace,   Cike da takaici Ayaan yace"maganar ɗauke jakar kuɗinka sam bata shafe mu ba,don haka tun wuri ka nemi wanda ya ɗauke maka kuɗinka!idan ma kanaso kayi amfani da wannan damar ne don kayi mana wayau ka ƙara samun wasu kuɗin awurinmu to inaso ka sani cewa ko sisi bazasu ƙara fitowa a wurin mu ba!bazamu baka ba!kaje kayi duk abunda kaga dama,'  Wani irin huci haroon ya runƙa fitarwa yana kallonshi yace"Kadaina yi mun magana A gadarance!taƙamarka kun goge videon dake a wurina to inaso ka sani cewa akwai wani videon a wurina!ni ba shashasha bane kamar yarda kukayi tunani!dama sai da raina ya bani cewa akwai wata ƙullalliyar da kuka shiryamun,don haka muddin baku dawomun da jakar kuɗina ba saina fallasa ku Uban kowa yaga abunda kuke aikata........'bai ƙarasa maganar ba saboda Ayaan daya kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya,nan take kan haroon ya ɗaure yashiga mamakin dalilin dariyar ta Ayaan,  Sosai Ayaan yake 6a66aka dariya kamar kamar me,hada dafe cikinshi,tashin hankalin da ba'a sama shi date,kwatsam yake zuwa,  duk wannan surutan da suke yi Jahan yana kwance a ƙasa sai faman juyi yakeyi saboda raɗaɗin da cikinshi ke yi mashi,sam baya acikin hayyacinshi,saboda he isn't satisfied,   "Me kake yi ma dariya"?haroon ya jefa mashi tambaya,  tsagaitawa da yin dariyar yayi yana Girgiza kai yace"Haroon ka gama yawo!wlh ka mutu!kai baka da tunani ne,bazan baka satar amsa ba,amma kaje kayi tunanin waye ya ɗauki jakar kuɗin nan!taya akai wani yasan da zancen jakar kuɗin nan har ya bi ɗakinka ya ɗauke ta!junaid kaɗae ne ya shigo cikin bedroom ɗinka a lokacin da muke tattaunawa,kuma kasan cewa junaid baya acikin sense dinshi ya shigo,koda ace yana cikin hayyacinshi bazai iya ɗaukar maka jakar kuɗin nan ba!to waye ya ɗauki jakar kuɗin?mu dai bamu bane!"?  shiru haroon yayi yana kallonshi gaba ɗaya ayaan ya burkita mashi tunaninshi,hakanan ya dinga jin gabanshi na faɗuwa,bai ƙara tanka ma Ayaan ba,cikin sauri ya kama hanya tare da fucewa daga ɗakin, Ajiyar zuciya Ayaan ya sauke,jin hannun mutum a ƙafarshi yasa yayi hanzarin kai idanunshi ƙasa yana kallon Jahan dake ta faman fitar da numfashi sama sama,hankali tashe ya shiga neman robar ruwan daya shigo da ita acikin ɗakin,can ya hangota ta gangara wurin shoe rack ɗinsu,murfinta ya cire ga ruwan ciki ya malale ƙasa,dafe kansa yayi da hannunshi na hagu cike da takaicin ruwan daya zube,   ƙokari jahan yake yayi mashi magana akan ya kira mashi Abbanshi karya mutu baisa shi a idanunshi ba,amma kwata kwata sounds ɗin bai fitowa abakinshi,ko idonshi bai iya budewa bare ya iya yin magana,gaba ɗaya Ayaan ya rasa yarda zaiyi,kanshi ya gama kwancewa,kamar yayi hauka haka yake ji,yana cikin wannan yanayin dubara tazo mashi,juyawa ya kuma yi yana kallon roban ruwan,Ruwan ya malale gaba ɗaya kasa ya tattaru a wuri guda,   Da saurin gaske ya ƙarasa wurin robar ruwan,tare da zubewa saman guiwowinshi,hannu yakai tare da ɗago da robar ruwan ya zaunar da ita ta tsaya tsaye,sannan cikin sauri ya sanya tafukan hannayenshi tare da kwalfo ruwan acikinsu,ya dinga zubasu acikin robar,yana ɗebowa wani na zubewa ahaka ya samu ya ɗan tara kaɗan wanda bai wuce ayi mashi kur6a uku ba ya ƙare,   ɗaukar robar ruwan yayi da sauri ya koma wurin jahan tare da zuƙunnawa agabansa,sannan yasa hannunshi na dama asaman lips ɗin jahan yana ƙoƙarin buɗe bakinshi,ya rufe bakin gam,hakan yasa Ayaan ya gaza samun damar buɗe mouth din nasa,  tsoranshi kar ace jahan ya mutu,saboda yayi delaying wurin kawo mashi taimakon gaggawa,  "Jahan pls,ka buɗe nasamo maka ruwan ka sha!banaso na rasaka ɗan uwana,"muryar shi tamkar zaiyi kuka haka ya dinga rokon shi akan ya buɗe bakin nashi ya sanya mashi ruwan,amma ko motsi wannan baiyi ba,  hannunshi har kerma yakeyi wurin ɗaga robar ruwan ya kaita saitin idanunshi yana duba rubutun dake ajikinta,larabci ne kuma shi baijin harshen larabci,balle ya gane me aka rubuta ajikinta,  Ganin zai rasa ɗan uwansa yasa ya ajiye robar ruwan ƙasa,sannan ya daddage da iya ƙarfinshi na ƙarshe ya sanya dukkan hannayenshi biyu ya shiga ƙoƙarin buɗe bakin Jahan,cikin sa'a bakin ya ɗan saki,da sauri Ayaan ya ɗauko robar ruwan tare da kafata a bakin Jahan nan take ruwan ya dinga shiga acikin bakinshi daƙyar daƙyar,wani na shiga wani na fita,ahaka yasamu ya bashi,bayan ya kammala yayi wurgi da robar ruwan gefe guda,sannan ya zauna tare da zabga tagumi yana jiran ganin sakamakon da zai biyo baya,hawaye sai shararo mashi suke a idanunshi,aranshi yana cewa"idan na rasa jahan bansan ya zanyi da rayuwata ba,nima zan bishi ne kawai,"   Yayi maganar tare da runtse idanunshi yana matse hawayen dake fita daga eyes ɗinshi,  Kafin Ayaan ya ankare,wannan baƙin hayakin ya soma kurɗaɗowa ta cikin ƙofofin hancin jahan,yarda kasan an koro shi daga cikinsa,haka ya dinga fitowa kafin kiftawar ido,hayaƙin yayi disappearing gaba ɗaya,tamkar bai ta6a existing ba,    Fitarsa ke da wuya,zufa ta soma tsastsafowa a jikin jahan,kamar an watsa mashi ruwa ajikinshi,haka zufar tashiga feso mashi,a hankali bakinsa ya buɗe ya shiga ambaton"La'ila ha'illallah!   A wani irin firgice Ayaan ya ware idanunshi sai lokacin ya kalli jahan dake kwance zufa ta gama wanke mashi jikinshi,wani irin farin ciki ne ya cika Ayaan la66ansa har rawa suke yi wurin ambaton sunan shi"ja..jahan"  Amsa mashi yayi da"Na'am," "Alhamdulillah!Alhamdulillah!Allah na gode maka!" Ayaan ne ke faɗin hakan yayin da yakai hannunshi yana tatta6a fuskar jahan dake ƙoƙarin buɗe idanunshi,    Tunani yazo ma Ayaan aranshi yace tabbas Ruwan cikin robar can ba normal ruwa bane da suka saba sha,akwai wani abu atattare dashi,tun da gashi Yaba jahan yasha kuma ya tashi da irin yanayin daya tashi dashi ɗazu da rana daya sha ruwan,ya tashi yana zufa kuma shima Jahan gashi zufar ce ke fita,hakan na nufin cewa shima Jahan ya warke kenan,  Ƙarasa tunanin nashi yayi tare da kai goshinsa ƙasa yayi sujjada yana ma Allah godiya,🥰   Bayan Jahan ya gama farfaɗowa,Ayaan ya taimaka mashi wurin kaishi toilet yayi wanka,nan take yaji wata irin natsuwa ajikin shi,basu 6ata lokaci ba wurin hayewa saman gadonsu,tare da lullu6ewa da bargo saboda baccin da kowannansu ke ji,yau gaba dayansu sunyi bacci cike da kwanciyar hankali,kuma Ayaan Yaci alwashin sai yayi investigation akan wannan robar ruwan da suka sha,
(Banji daɗi da ruwan addu'ar nan ya zube ba,wlh nima ina buƙatar shi don nasha)
Yanayi mara daÉ—i,a daren ranar Omar ya kwana yana kukan zuciya saboda abunda yayi Æ™oÆ™arin aikata ma Hosana, ya kwana da tunanin wane hali suke aciki?sunyi bacci kuwa?baida amsar tambayoyin shi dole sai inya gansu,gashi baya jin zai iya takawa yaje dubasu saboda fargabar karsu gane cewa shine yayi masu wannan abun kunyar,matsananciyar damuwar daya sa ma ranshi ne da tunane-tunane ya haifar mashi da wani irin severe headache na 6arin kai,yaji jiki adaren nan har magani yasha amma bai sauka ba,a haka ya kwana yana juyi asaman gadonsa,  Adaren ranar nan dai abubuwa dayawa sun faru masu daÉ—i da marasa daÉ—in ji,dama haka rayuwa take ba kullum ake jin daÉ—in ta ba,idan yau anyi farin ciki,gobe zai iya kasancewa baÆ™in cikine,idan yau anyi dariya gobe zai iya kasancewa kuka ne,haka rayuwar ke tafiya babu wani yanayi da yake kasancewa permanently,Allah yasa mu dace,yasa mu fi Æ™arfin zuciyoyinmu,kuma ya kare mu daga aikata aikin danasani,wasu sun É—auki rayuwar duniya wani abu,da har suka É—auke ta da zafi suna aikata abunda suka ga dama,sun manta da cewa acikin seconds za'a iya zare ransu su bar duniyar gaba É—aya suje su fuskanci abunda suka shuka,duka nawa ne jin daÉ—in duniyar?basa tuna donme aka halicce su,ta wace Æ™opa suka faÉ—o duniyar nan,taya zasu koma ga mahaliccinsu?daga kai fa sai likkafaninka za'a binne ka cikin Æ™abarinka,sai kuma halinka daka je dashi,na gari ne kona banza,😢Allah yasa mu cika da kyau da imaniðŸ™
Wuraren sallar Asuba Sgr ya farka daga dogon baccin daya ɗauke shi,a hankali ya buɗe eyes ɗinshi,yayin da bakinsa ke ambaton addu'ar tashi daga bacci,a kasalance ya miƙe daga kwancen da yake saman doguwar kujerar,mamaki ne ya kama shi ganinshi kwance a palour ɗinsa yana bacci instead of saman gadon shi,ya jima yana mamakin yarda bacci yayi awon gaba da shi adaren jiyan nan,sauko da ƙafafunsa yayi ƙasa,idanunshi suka sauka akan tray ɗin da sehrish ta kawo mashi na dinner ɗinsa da baici ba jiya,tsayawa yayi yana ƙoƙarin tuna abunda ya faru adaren jiya,yunƙurawa yayi tare da tashi tsaye daga saman sofa din ya soma takawa walking slowly,jin sul6in wani abu a ƙasan tafin kafarshi yasa shi yin saurin kai idonshi wurin yana kallo,mamaki ne ya kama shi ganin Mayafin yarinyar nan yashe a kasa,yasan cewa shiya cire mata mayafin amma abunda ya ɗaure mashi kai zaman me gyalenta keyi acikin part ɗinsa?   russunawa yayi tare da kai hannunshi ya ruƙo gyalen tare da ɗagowa dashi yana kallon shi,sai lokacin ya tuna abunda ya faru jiya tsakanin shi da ita,na commanding ɗinta da yayi akan tayi tsallen kwaɗi,to ina yarinyar take,tambayar daya jefa ma kanshi kenan,   Cikin sauri ya zagayo ta bayan sofas ɗin tunkan ya ƙarasa ya hangi yarinyar kwance magashiyyan a sume bata motsi,tasha wahala sosai sam baiyi tunanin cewa zata cigaba da yin frog jump ɗin ba,yasan ba komai ne yaja hakan ba face tsananin tsoronshi da take ji,shiyasa bata yi tunanin ta tafi ba,tunda taga bacci yayi awon gaba da shi,     A hankali ya ƙarasa takawa inda take sannan yaɗan zuƙunna agabanta yana kallon sumar kanta data rufe mata fuskarta,hannu yasa tare da ruƙo gashin kan nata,ya janye mata shi daga saman fuskarta ixuwa gefe guda,   Zuba ma kyakkyawar fuskarta ido yayi yana kallon yarda tayi jaga jaga da hawaye duk ta yamutse saboda kukan da tasha,idonta sun kumbura,haka la66anta ma sunyi suntum dasu,tsananin tausayinta ne ya kama shi,baiji daɗin baccin daya ɗauke shi ba,da baibari tasha wahalar nan ba,ba da nufin ya cutar da ita yayi hakan ba,kawai yaso ya ɗan hukuntata ne donta kiyaye shi sosai,    miƙewa yayi tare da nufar wurin fridge ɗinshi,ya buɗe ya ɗaukko bottle water daga ciki mai sanyi,sannan ya dawo inda sehrish take ya cire murfin tare da ɗebo ruwan a hannunshi ya yayyafa mata shi a fuskarta,ruwan na sauka asaman fuskarta,taja dogon numfashi tare da sauke nannauyar ajiyar zuciya,a hankali tashiga mutsu mutsu zata buɗe idanunta,   "Get up" yace,jin muryarshi yasa sehrish ware idanunta akan sgr dake zuƙunne agabanta,jikinta har kerma yake yi wurin yunƙurawa tare da tashi daga kwancen da take ta zauna,tun kafin taji me zaice ta shiga bashi haƙuri tana cewa"dan Allah ka yafe mun babban yaya,bazan ƙara maimaita kuskuran da nayi....,.'   Kasa ƙarasa maganar tayi,a firgice ta shiga girgiza mashi kai ganin yadda ya ɗago da hannunshi,duk a tunaninta marinta zaiyi amma sai taga akasin hakan,a hankali ya aza tafin hannunshi a saman lallausar fatar gefen fuskarta,ɗan zaro ido sehrish tayi tana kallon fuskarshi,yayin da shi kuma yake kallon brownish lips ɗinta dake ta faman kerma,   Almost 5 mins sannan yace"Tashi ki tafi,"ya ambaci hakan tare da zame hannunshi daga gefen fuskarta sannan ya miƙe tsaye hannunshi ruƙe da bottle water ɗin yana maida murfin robar,daddagewa sehrish tayi tare da yunƙurawa daƙyar ta miƙe,aikuwa nan take ƙafafunta suka bada wani irin sauti ƙasss!,a gigice ta saki wata irin razananniyar ƙara nan take ƙafafun suka gaza ɗaukarta,gaba ɗaya ta tafi zata kife ƙasa,sai dai ina kafin takaiga ƙasan tuni hannun sgr ya damƙi qugunta kwakkwaran ruƙo yayi mata da hannu ɗaya,gabanta ne taji yayi wani irin bugu daga bisani kuma ta shiga sauke ajiyar zuciya ba ƙaramin tsorata tayi ba,har lokacin hawaye ne ke zubowa daga cikin idanunta,janyota Sgr yayi ta faɗo saman jikin shi gaba ɗaya,sannan ya ɗan russinar da kanshi tare da ɗago da ita,ya sanyata a saman kafaɗarshi,yadda kasan ya ɗauki wannan ɗiyar robar ƴar tsana,haka ya sa6i sehrish asaman shoulder ɗinshi,tafiya ya soma yi ɗauke da ita,ya ƙarasa wurin fridge ɗinshi tare da ajiye roban ruwan dake hannunshi,sannan ya juyo tare da kama hanya ya fito daga part dinshi kai tsaye ya nufi downstairs,ajiyar zuciya sehrish ke ta faman saukewa tayi lamo abunta,yadda take jin daɗin kafaɗar tashi tamkar ta hau Jirgin sama,   A natse yake taka matattakalar benen ɗauke da ita har ya ƙarasa saukowa da ita cikin Main palour ɗin nasu,bin ko'ina yayi da kallo babu kowa da alama basu kammala shirin zuwa yin sallar asubahin ba,duk da dama lokaci bai ƙarasa yi ba,a lokacin ake ta haramar fara kiran sallan, Tunani ya shiga yi a ina zai sauke yarinyar,don shi bai ta6a sanin ma a ina yarinyar take rayuwa acikin gidan ba,har wani lumshe ido sehrish take yi saboda yanayin da ta shiga wata irin kasala ga baccin da take ji,ta gaza yarda cewa sgr ne da kanshi ya sa6ota asaman kafaɗarshi,jin abun take kamar a mafarki,duk da halin da take ciki amma har addu'a take yi cikin ranta Allah yasa dagaske ne ba mafarki bane,   Yana cikin wannan tsayuwar ɗauke da sehrish a kafaɗarshi,kwatsam Abbansu ya fito daga bedroom ɗinshi ya tunkaro main palour din,sai faman sauri yake yi don yaje ya tashi sauran su tashi su kimtsa lokacin sallah yayi,tunɗazu yake trying numbers ɗinsu don ya tashe su amma mutum ɗaya ne kawai yayi picking call ɗin,wato kanal yousouf,amma sauran babu wanda ya ɗaga alamar basu tashi daga bacci ba,   Da wa Allah ya haɗa shi?ae yana fadowa babban falon karaf idanunshi suka sauka akan Sgr dake ɗauke da Sehrish a kafaɗarshi,har sai da gabanshi ya faɗi,cikin sauri Abba ya ɗan ja da baya saboda kar Sg rafayet ya ganshi,har wani murza idonshi yake yi da hannayenshi don ya ƙara tabbatarwa da kanshi abunda yake gani,wai ko idanunshi ne ke nuna mashi ba dai-dai ba,lamarin ya ɗaure mashi kai,tsananin mamaki ne matuƙa ya kama shi,har ƙara leƙawa yake yi don ya tabbatar ma kanshi wanene acikin matasan nashi ya ɗauko mace a kafaɗarshi,   Hasken fatar sgr,da kuma wannan doguwar ƙirar tashi ne suka tona mashi asiri,uwa uba doguwar sumar kanshi,  Doubting ya shiga yi yana cewa"Anya kuwa shine?kodai idona ne ke nuna min ba dai dai ba,kodai tsufa ne yazo mun gadan gadan harya sa nake ganin hakan!kai wannan fa Rafayet ne ba wani ba,yarinyar daya ɗauko a kafaɗarshi kuma wannan yarinyar ce sehrish!ita kaɗae ce ƴar matashiya acikin gidan!idan har zargina ya tabbata toh me ya haɗa shi da yarinyar ne harya ɗaukko ta saman kafaɗarshi?Hakan na nufin a bedroom ɗinshi ta kwana"? Ya jefa ma kanshi tambaya,gaba ɗaya ya kuma ruɗewa,  Can dai yace"Ina yi mashi kyakkyawan zato,amma tabbas akwai alamar tambaya anan!"  Shiru ya ɗanyi yana ƙara leƙensu,abunne ya daure mashi kai sosai tunda yake bai ta6a ganin sgr da mace haka ba,aranshi ya shiga cewa kodai Ya fara kula mata ne?wata'ƙil akwai wata alaƙa atsakanin shi da yarinyar,'  Jinjina kanshi yayi tare da cewa"Biri yayi kama da mutum tabbas!sai yanzu na gane inda ya samu jan baki asaman ƙirjinshi,Oh ni hussein ina nan sake da baki ana mun aika aika acikin gidana!nagode ma Allah daya nunamin wannan abu akan idona,nasan me zanyi!"  Yana fadin hakan ya juya tare da komawa part ɗin nasu,don ya tashi sauran dama Upstairs ya nufa don ya tashi Omar,abunda yasa ya koma saboda baison sgr ya ganshi ya gane cewa ya ganshi ɗauke da Yarinyar a kafaɗarshi,   Jin takun tafiya yasa Sgr juyawa don yaga wanene,Azmee ce ta fito tana ta faman ƴan waige-waige,bakomai ne ya fito da ita ba face neman Sehrish, taje bedroom ɗinta donta tashe ta daga bacci taga babu kowa,hakan yasata fitowa don ta nemeta acikin gidan,   "Ke,zonan,"a ɗan firgice Azmee ta kallo inda yake,dama tunda taji an ambaci hakan tasan cewa Sgr ne,saboda shi kaɗai ke mata wannan kiran kai tsaye kamar wata ƙaramar yarinya,ko sunanta bai iya faɗi sai dae ke,don shi a yadda ya ɗauka duk wata mace ƙarama take awurinshi,
 Fargaba ta shiga yi,ganin Sehrish kwance a kafaɗarshi,zullumi ta shiga yi acikin ranta,tsoranta kar ace wani abu ta aikata masa,   ƙarasawa tayi kusa dashi murya na rawa tace"Gani yalla6ai," Ko uffan baice mata ba,a hankali ya saukko da sehrish daga saman kafaɗarshi ya tsayar da ita akan ƙafafunta dake ta faman kerma,cikin sauri Azmee ta ruƙo hannunta,hankali tashe take kallonta ganin yadda ko'ina na jikinta ke kerma,cike take da son jin me ya faru da ita,Me ya haɗata da sgr da har ya ɗaukkota haka asaman kafaɗarshi,   Juyawa sgr yayi cikin sauri ya haye saman stairs da sauri da sauri yake taka steps ɗin sai da yakai step na ƙarshe sannan ya ɗan tsaya kamar mai nazarin wani abu,
A lokacin azmee ta ruƙo sehrish tana taimaka mata wurin yin tafiya,a hankali a hankali suka nufi part dinsu,gaba ɗaya sehrish taji wani irin yanayi a tattare da ita,sam bataso sgr ya sauketa daga saman kafadarshi ba,don ba ƙaramin relief ta samu ba,ita kaɗae tasan yarda take ji aduk lokacin da takasance tare dashi,  Runtse idonta tayi yayin da hawaye ke cigaba da zubowa sun jiƙa mata fuskarta sharkaf,suna cikin tafiyar nan,ranta ya bata cewa ta ɗan jiyo ta kalle shi,taga yana nan ko ya tafi,  A hankali ta ɗan juyo da fuskarta, ta kalli upstairs din,adaidai lokacin shi ma Ya juyo da fuskarshi a wani slow,kai tsaye idanunshi suka sauka acikin nata dake kallon shi,gaza janye idanunshi yayi daga kallon hawayen dake shararowa a fuskarta,wani irin tausayinta ne yaji ya kama shi,saboda yasan cewa shine silar zuban hawayen nata,kamar yarda yake kallonta,itama haka take kallonshi duk da sunyi nisa da juna,a hankali ya lumshe idanunshi tare da ɗauke kanshi daga kallonta ya ƙarasa hawa upstairs ɗin da sauri ya wuce bedroom ɗin shi,   Sai bayan da ya 6ace ma ganinta sannan itama ta juyar da kanta tare da mayar da hankali wurin yin tafiyar,har cikin bedroom azmee takaita,ta taimaka mata wurin hayewa saman gadon,ta kwanta yayin da idonta ke kallon ceiling ba komai take tunawa ba,face yarda Sgr ya tarbo waist ɗinta a lokacin da tazo faɗuwa,da kuma lokacin da ya ɗaurota asaman kafaɗarshi,da kuma kallon nan daya juyo yana yi mata kafin ya tafi,  Zama azmee tayi daga gefen gadon tana kallonta tace"Me ya faru dake ne sehrish?meya haɗaki da sgr dana ga ya ɗaukko ki asaman kafadarshi"?   bata 6oye mata komai ba ta sanar da ita duk abunda ya faru a tsakaninta da sgr,  Jinjina kai Azmee tayi tare da cewa"u ave to be very careful rishi,tun farko saida na gargaɗeki akan shi,amma baki ji ba ko?   Muryarta tamkar zatayi kuka tace"Aunty azmee ina kiyayewa,wannan ma matsala aka samu har na manta da gyalena asaman gadonshi,banyi tsammanin zai dawo ba a wannan lokacin......'  Shiru Azmee ta ɗanyi kafin tace"Shikenan amma duk da haka ki ƙara kiyayewa nan gaba,karki ƙara yin gangancin maimaita kuskuren da kikayi yau,"   Sehrish tace"Insha Allah bazan ƙara ba,"   "Allah yasa,ni zan wuce,ki daure ki tashi kije kiyi sallah," Amsa mata tayi da"toh," sannan azmee ta miƙe tare da fucewa daga bedroom ɗin nata,ajiyar zuciya sehrish ta sauke,tunda ta kwanta ko kwakkwaran motsi wannan bata iya yi ba,jikinta duk yayi mata tsami,ta so ta tashi ta ɗan gasa jikin da ruwan zafi amma sam tagaza motsi,kamar an aza mata Bulo asaman jikinta haka ta dinga ji,yayi mata wani irin nauyi,a wannan yanayin bacci yayi awon gaba da ita.
  _💋Boss Bature💋_
A washe gari
Around 7:00am
A firgice Jahad ta farka daga dogon suman da tayi,sakamakon jin saukar ruwan sanyi da tayi asaman fuskarta,a gigice ta tashi zaune,lokaci guda ta fara ambaton sunan Hosana!hosana!  "Jahad ki buɗe idonki Ni ce fa" Jin muryar mutum a kusa da ita yasa ta ware idanunta tana kallonta,bakowa bace face Nurse Camilla,zuwanta kenan ta shigo cikin falon taci karo da Jahad a sume ƙasa,hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba,da sauri ta ɗauko ruwa mai sanyi ta yayyafa mata,  A hankali jahad ke kallonta da idanunta waɗanda suka rune saboda kukan da tasha,  Sanye take cikin jeans da t- shirt tare ta ɗaure sumar kanta da ribbom,     a ɗan ruɗe tace"Jahad me ya faru ne?na shigo na same ki a sume menene ya faru dake ne"?  Cikin shessheƙar kuka tace"Hossana tana cikin ɗaki,bansan tana a raye ba ko ta mutu,jiya da daddare wani ya faɗo mana a cikin bedroom ɗin mu har yayi ƙoƙarin yin raping ɗinta........'kasa ƙarasa maganar tayi saboda kukan daya kufce mata,hankali a matuƙar tashe camilla ta miƙe tare da nufar hanyar zuwa ɗakin nasu,  Miƙewa jahad tayi tabi bayanta cikin sauri,zuciyarta nata faman bugawa saboda fargabar a wane hali hossana ke ciki, karfa ace wannan mutumin ya ƙara dawowa don ya cutar da ita,  Yadda jahad ta bar hosana haka suka sameta,naɗe cikin bargon a sume bata motsi,   Hawa saman gadon camila tayi ta ƙarasa kusa da Hosana tare da kai hannu ta shafa wuyanta,kallon jahad tayi dake atsaye cike da fargaba tace"dauko mun ruwan da na bari a falo," amsa mata tayi da toh sannan ta fuce daga cikin bedroom ɗin,within minutes sai ga Jahad ta dawo hannunta ɗauke da bottle water ta miƙa ma Camilla,hannu tasa ta kar6a sannan ta buɗe murfin ta debo ruwan tare da watsa ma hossana a fuskarta,nan take hossana tafarka daga suman da tayi,a wani irin razane ta zabura zata yaye bargon jikinta tana cewa"karka ta6ani Abba banso banso!ka ƙyale ni in tafi,inba haka ba Ya omar zai kashe ka...."  Cikin sauri Jahad ta haura saman gadon tare da rurruƙeta tana gyara mata bargon jikinta gudun kar tsiraicinta ya fito,ganin tana ta faman fisge fisge tana hargowa yasa Camilla tayi mata magana cikin sanyin murya tace  "Hosana!ki kwantar da hankalin ki,babu kowa anan da zai cutar dake,Ni ce Sister Camilla tare da ƴar uwarki jahad a kusa dake,dan Allah ki shiga natsuwarki,"cikin rarrashi takeyi mata magana, Jahad tace"Hossana gani a kusa dake ki buɗe ido ki kalle ni,"  Jin muryar jahad yasa hossana ta buɗe idanunta tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya,fuskar nan tayi sumtun saboda kukan da tasha,idanunta duk sun ƙankance,   "kiyi haƙuri hossana,koma waye Allah bazai barshi ba,nayi ƙoƙarin na kwace ki daga hannunshi amma Allah bai nufa ba,inda na gode ma Allah da bai ƙarasa nufinshi akanki ba,nayi ƙoƙarin na kira ƴa Omar,amma layinshi yaƙi shiga,amma zuwa anjima zan ƙara jaraba kiran shi,nasan zai ɗaga,"  Cikin shessheƙar kuka tace"Jahad ki kira mun shi,a kiramun ya Omar yazo,inason naganshi,shi nakeson gani,"    Jiki a sanyaye Jahad tace "Kada ki damu zan kira maki shi,insha Allah,"
 gaba ɗaya lamarin ya girgiza Camilla,ta jima tana hasashen waye yayi ƙoƙarin cutar da yaran acikin gidan!duk irin tsaron dake gareshi,ba ita ba hatta jahad tashiga zargin waye yayi masu wannan zuwan da daddare don ya cutar da hossana,sun jima suna wannan tunanin, a ƙarshe dai bakowa suka fi zargi ba face ɗaya daga cikin security guards ɗin gidan,  Bayan sun gama jimamin nasu,Camilla ta tashi tare da fucewa daga bedroom din ta nufi kitchen don ta shirya masu breakfast,  yayin da ita kuma Jahad,ta taimaka ma hossana bayan ta sanya rigarta sannan ta kaita toilet ta taimaka mata wurin yin wanka da ruwa mai ɗumi yarda jikinta zai ɗan warware,sai da su kayi alwala sannan suka fito daga cikin toilet ɗin,
doguwar riga ta ɗaukko mata acikin wardrobe ta bata ta sanya sannan suka zura hijabansu atare,jahad ta shimfiɗa masu darduma suka hau sama tare da daidaita natsuwarsu suka kabbara sallah,har lokacin jikin hosana sai faman kerma yake yi,a tsananin tsorace take da abunda ya faru da ita adaren jiyan nan,bayan sun kammala sallar jahad tace mata taje ta kwanta tayi bacci,ita zata wuce kitchen wurin Camila,ta taimaka mata suyi aikin breakfast ɗin atare,  Bayan jahad ta fuce daga bedroom ɗin,hossana ta miƙe daga saman dardumar jikinta nata faman kerma ga rawar ɗari da take yi,saboda sanyin da take ji,lalla6awa tayi tare da hayewa saman gadon,takai hannu tare da janyo bargon ta ɗan kakka6e shi zata rufe Jikinta dashi,kwatsam taji sautin faɗuwar wani abu ƙasa,cikin sauri ta leƙa ƙasan gadon tana kallon abun nan daya fado daga saman gadon, Diamond ring ne ɗan ziriri dashi sai faman ƙyalli yake,gabanta taji ya faɗi rass!ganin zoben da tayi ya faɗo ƙasa,yunkurawa tayi tare da tashi daga zaune sannan takai hannu ƙasan gadon tare da ɗaukko zoban,ɗago shi tayi a daidai saitin idanunta tana ƙare mashi kallo, Zaro ido tayi hankalinta a matuƙar tashe ta furta"Ya Omar!!!!!!!!!" 😳
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
 Â
*💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Abban sojoji paid book ne,ga duk mai buÆ™atar karanta cigaban shi yayi mun magana kai tsaye ta number ta 08103884440 Whatsapp only banda phone calls, 300 ne only ðŸ¤
Zuba ma zoben ido tayi tana kallonshi hankalinta a matuƙar tashe,gabanta na faduwa,a hankali take jujjuya shi a hannunta,lokaci guda hawaye suka fara gangarowa daga idanunta cikin shessheƙar kuka take cewa"I can't believe it! Ya omar ɗina ne yayi ƙoƙarin raping dina? Shine yaso rabani da mutuncina?why ya Omar why!?innalillahi wa'inna ilaihirraji'un Allah kasa mafarki nake ba gaske ba.......'kukan da yaci ƙarfinta ne yasa ta gaza ƙarasa maganar,nan fa tashiga shararar kwalla,abun ba ƙaramin ciwo yayi mata ba,bata ta6a tunanin haka daga wurin shi ba,wannan zoben nashi ne,shi ya tabbatar mata da cewa Ya omar ɗinsu ne yayi yunƙurin yi mata wannan aika-aikan,amma meyasa!?
tsagaitawa tayi da kukan tashiga girgiza kanta tana cewa"A'a ya Omar ɗina bazai ta6a yi mun haka ba,na yarda dashi sosai,nasan cewa bada son ranshi yayi mun hakan ba,Ya Omar bazai ta6a cutar da hosanar shi ba,ina yi mashi kyakkyawan zato kuma bazan ta6a tona mashi asiri ba,bazan bari kowa yaga zoben shi ba ko jahad bazan nuna mawa ba,saboda nasan ba dole ta fahimce shi ba,kamar yarda ni na fahimce shi,"ƙarasa maganar tayi tare da ƙankame zoben asaman ƙirjinta ta ɗan runtse idanunta hawayen naci gaba da sauka asaman fuskarta, Dama ance so hana ganin laifi,hosana ta makance akan son ya Omar ɗinta,kuma ta yarda dashi 100%, tana cikin wannan yanayin taji motsin mutum cikin sauri takai hannu tare da janyo bargo ta ƙudundune acikin shi,6oye zoben tayi acikin aljihun rigar jikinta,sannan ta sanya tafin hannayenta tana goge hawayen fuskarta, Jahad ce ta shigo hannunta ɗauke da kakkauran tea mai zafi sai faman tiriri yake yi,ƙarasawa tayi tare da samun wuri daga gefen gadon kusa da hosana ta zauna, a hankali tace"ƴar uwata rabin raina ga tea na kawo maki, ki tashi kisha shi da zafi zafinshi karya huce nasan zaki ji dadin shi,'cikin lallami take yi mata magana saboda tasan a halin da take na fargaba tana buƙatar kalamai masu daɗi da zasu sanyata farin ciki, lamo hosana tayi batare da ta motsa ba abunda yasa tayi hakan saboda tanason ta daidaita natsuwarta don kar jahad ta gano wani abu, jin shiru yasa jahad,kai hannunta na dama ta ɗan bubbugi kafaɗarta tace"tashi mana hosana ko kinyi bacci ne"?ta tambaya tana kallonta naɗe cikin bargo, Har jahad ta yunƙura zata tashi,hosana ta soma motsi alamar zata farka,komawa jahad tayi ta zauna tana jiranta ta tashin,a hankali ta yaye bargon tare da tashi daga zaune tana mutsistsika idanunta alamar yanzu ta tashi daga guntun baccin daya ɗauke ta,wartsakewa tayi ta buɗe ido tana kallon Jahad,
Murmushi jahad ta sakar mata tare da cewa"babyn Omar ya jikin naki?nasan har yanxu kina fargaba akan abunda ya faru dake jiya,dan Allah hosana kada kisa damuwa kinji?insha Allah koma wanene asirinshi zai tonu,zamu faɗama ya Omar zai gano koma wane tsinan.........'a firgice Hosana ta toshe ma Jahad baki da tafin hannunta tana cewa"Jahad dan Allah kidaina maganar nan,kina tunamun abunda ya faru jiya,ni banason ma ana maganar nan,gabana faɗuwa yake yi,'ta ƙarasa maganar a sanyaye tare da zame hannunta daga bakin jahad, Ajiyar zuciya jahad ta sauke tare da cewa"Shikenan mubar maganar,yanzu dae ga tea ɗin kisha,kuma sister camilla tace na tambayeki in akwai abunda kike buƙata a girka maki kici," Hannu hosana tasa ta kar6i cup ɗin da jahad ta miƙo mata sannan tace"Bana buƙatar cin komai yanzu,ni dai akira mun ya Omar yazo inason ganin shi,' Murmushi jahad tayi tare da cewa"kada ki damu babyn Omar,nasan zaizo ne ina ta trying numbarshi amma taƙi shiga still switch off,amma nasan zuwa anjima zai kunna wayar ne," Jin haka yasa jikin hosana yin sanyi,don tasan dalilin dayasa Omar ya kashe wayarshi,bata ji daɗi ba saboda tasan zai sanya damuwa sosai aranshi,tausayinshi ne taji ya kama ta,babban abunda take fargaba shine kada ya hana kanshi zuwa wurinsu, tashi jahad tayi tare da fuce wa daga bedroom din ta koma kitchen,yayin da ya rage hosana ce kaɗai saman gadon tana kur6ar tea ɗin a hankali,duk jikinta yayi sanyi,
After some days
Abu kamar wasa yau almost 1 week kenan ba Omar ba alamar shi,hankalinsu ba ƙaramin tashi yayi ba,kwana huɗu ba Omar ko layin shi suka kira kullum a switch off suke samun shi,hakan ba ƙaramin tayar masu da hankali yayi ba,sun shiga damuwa sosai na rashin zuwan shi,musamman Hosana duk tabi ta takure kanta,ko abincin kirki bata iya ci,ko isasshen bacci bata samu,kullum cikin kuka take na rashin ganin ya Omar ɗinta,duk bayan ƴan mintina sai taje ta ɗauki telephone ta danna mashi kira,da zarar taji wayar akashe sai ta fashe da kuka,daƙyar jahad ke samu ta lallashe ta,akwai lokacin da jahad ta farka tsakar dare ta samu Hosana saman darduma tana yin sallar dare abunda bata ta6a ganin hosana tayi ba,kuma duk don saboda ya Omar ta tashi yin sallar daren,tana roƙon Allah yasa Ya omar yazo karya rabu dasu,batasan yaya rayuwa zata kasance mata ba,batare da ya Omar ɗinta ba,tana yin addu'ar tana matse kwalla,a wannan lokacin ba ƙaramin tausayi taba Jahad ba, A washe garin ranar jahad ta yanke shawarar zuwa tasamu Osman ta sanar dashi game da halin da suke ciki na damuwa da rashin ganin ya Omar ɗinsu,ko da Jahad taje ta samu Osman ta faɗa mashi,yayi mata alkwarin cewa zai bincika masu shi, Bayan tafiyar jahad,Osman ya nemi major a waya ya sanar mashi abunda ke faruwa,na halin da yaran suke ciki akan rashin ganin Marshal da basuyi ba na tsawon kwanaki ,jiki a sanyaye Major yace mashi yaci gaba da kwantar masu da hankali,insha Allah zaizo ne abubuwane sukayi mashi yawa. Hankalin Omar ba ƙaramin tashi yayi ba,lokacin da major ya sanar dashi halin da su jahad da hosana suke ciki,tsananin tausayinsu ne ya kamashi,musamman hosana da aka sanar dashi cewa ko isasshen bacci bata samu saboda damuwa akan shi,tamkar ya zubar masu da hawaye haka yaji,duk yarda yaso ya daure ya hana kanshi fargabar tunkararsu amma ya gaza yin hakan,ya nisanta kanshi dasu ne, saboda gudun karya ƙara jefa kanshi cikin matsala,shi kanshi daurewa kawai yake yi amma ba ƙaramin cutuwa yake yi ba,yana tsananin son ganinsu yanaso yaga wane hali suke ciki, amma ba yarda ya iya.
A 6angaren Sehrish kuwa ba ƙaramin jiki taji ba,a washe garin ranar da Sgr ya sanyata tsallen kwaɗi,ko school bata je ba,saboda jinyar jikinta da ta tsaya yi,ƙafafunta sunyi suntum,tun da ta lafe saman gadon ko motsi bata son yi,ba ƙaramin jiki taji ba sai da azmee ta taimaka wurin gasa mata ƙafafun da ruwan zafi,tayi mata tausa sannan taji sauƙin jikinta sosai har ta samu ta warware taci gaba da ƙiriniyarta kamar yarda ta saba.
Hayamm taji haushi sosai kamar ta binne kanta saboda tsabar baƙin ciki,tun washe garin ranar da azmee taje gyara part din Sgr,ta fito hannunta ɗauke da tray ɗin kayan abincin da baici ba,jiki na rawa hayaam ta ƙarasa tare da kar6ar tray ɗin tace tabar mata kayan takai kitchen, tana shiga kitchen dasu ta shiga buɗe kayan don taga idan sgr yaci abincin,sai dae abun takaici bai ta6a komai na abincin ba,yarda sehrish takai mashi shi haka aka dawo dasu bai ta6a komai ba,lemu kawai yasha,kuma ta manta bata zuba gashin acikin abun shan nashi ba,taji takaicin hakan kamar ta aza hannu abisa kanta tayi ihu saboda haushi,amma taci alwashin cewa saita shirya mata wani tuggun tunda ta tsallake wannan.
A 6angaren su Twins kuwa sai dae muce Alhamdulillah,Yara sun zama mazajan gaske,rayuwarsu ta gyaru sosai,yanzu basa wasa wurin yin ibadarsu suna neman tsarin ubangiji,don wani lokacin atare suke tashi suyi ƙiyamun laili da sauran nafilfili,sannan basa komawa bacci bayan sallar asuba,zama suke yi suyi ta karatun alkur'ani mai girma har gari ya waye, Allah sarki rayuwa kenan ayayin da matsalar su jahan ta ƙare, shi kuma junaid wani mummunan al'amari ya soma faruwa dashi batare da sanin kowa ba,shi kaɗae yasan halin da yake ciki,kuma yaƙi sanar ma kowa saboda baison ya tashi hankalin Abbanshi da kuma na ƴan uwanshi,baka ta6a gane halin da yake ciki saboda babu abunda ya canza na daga ƙiriniyarshi, da kuma wannan kyakkyawan murmushin nashi,abun yana damunshi sosai, wannan ɗigon jinin dake fitowa ta ƙopar hancinshi, kullum ne saiya tashi tsakar dare batare da sanin Abbansu ba, ya shiga cikin toilet yana wanke hancinshi, abun sai ƙara gaba yake yi, ga yanayin da yake tsintar kanshi aciki,yanayi mara daɗi wata irin kasala da kuma yawan faɗuwar gaba,da kuma razanar da yake yawan yi,ko kiran sunan shi kayi da karfi sai ya firgita,ba kowa ya lura da hakan ba,tabbas rayuwar Junaid tana cikin hatsari sosai,a cikin jikinshi ciwon ke cin shi batare da sanin kowa ba, hmmmmmmm.
A 6angaren Commandern ƴan iska kuwa wato haroon komai ya gama hargitse masa,kamar wani zautacce haka ya koma wurin neman jakar kuɗin shi,sam ya rasa samun kwanciyar hankali gaba daya plan ɗin da ya shirya na barin nigeria yana shirin rugujewa saboda rashin kuɗin nan,a ƙarshe ya yanke shawarar turo ɗayan videon nan nasu jahan don ya sake yi masu barazana dashi,su ƙara mashi wasu kuɗin da zai samu yabar ƙasar tunkan asirinshi ya tonu,
Wannan kenan👌
Gaba daya an canzama gidan kamanni sai faman gyare-gyare akeyi mashi ta ko'ina,kwararrun ma'aikata aka ɗauko wurin tsara decoration ɗin da za'ayi ma gidan, yarda kasan za'ayi wani shagalin biki haka suka ƙawata gidan,duk wannan shirye shiryen da suke yi na tarbar manyan baƙinsu ne da zasu zo acikin kwanakin nan,a yau dae mutum biyu ne zasu fara zuwa,daga ciki akwai uncle Abusufyan da zaizo daga ƙasar turkey,sai kuma hajiya azeema da zata zo daga lagos, gaba ɗaya tunanin matasan gidan Abbansu yasa aƙawata gidanne kawai saboda zuwan su Ammin sa ne,abunda basu sani ba shi da wata manufa yasa a gyara gidan, Tofah,
Wuraren ƙarfe 7:00am dai dai sehrish ta kammala shirinta na zuwa school,tana tsaye agaban mirror sai faman feshe jikinta takeyi da turare,bayan ta kammala ta koma wurin gadonta tare da kai hannu ta ɗauki hijab ɗinta data ajiye anan saman gadon ta zura ajikinta, bata ɗauki school bag ɗinta ba saboda tana so tafara zuwa kitchen wurin su Aunty azmee ta kar6a ma babban yaya breakfast ɗinshi takai mashi, fitowa tayi daga cikin bedroom ɗin tana tafiya tana ƴan kalle kalle kamar zatayi tuntu6e,decoration ɗin da akayima gidan ba ƙaramin kyau yayi mata ba,don ba ƙaramin ɗaukar ido yake yi ba, Ƙarasawa kitchen ɗin tayi tare da tsayawa daga bakin kopar tayi masu sallama,Azmee ce kaɗae acikin kitchen ɗin,jin muryar sehrish yasa ta juyowa fuskarta ɗauke da murmushi tace"Ƴan makaranta har an kammala kimtsawa ne? murmushi sehrish tayi tare da cewa"ina kwana Aunty azmee,ya aiki"? Azmee tace"Alhamdulillah,shigo daga ciki mana in haɗa maki breakfast ɗinki ki ci kafin ki tafi,' "A'a Aunty azmee bana jin yunwa,idan naje school zanci acan,' har ta ɗanyi shuru, cike da son jin gulma ta kuma cewa"Aunty azmee wai wanene zaizo zo yau"? Murmushi azmee tayi tare da cewa"Masu kama dake ne zasu zo yau,' "Masu kama dani kuma Aunty azmee"?ta tambaya fuskarta ɗauke da mamaki, azmee tace"kwarai kuwa kuna kama da azeema kanwar Abbansu junaid dake lagos,amman kinfi kama sosai da Uncle ɗinsu, Abusufyan dake zaune a ƙasar turkey shima zaizo yau,' wani irin farin cikine taji ya lullu6eta,saboda ɗokin ganin wannan uncle ɗin nasu da take yawan jin suna ambatar sunanshi,a ƙagare take da ta sanya shi acikin idonta, "Aunty azmee dagaske muna kama dashi?ko wasa kike yi mun"? Azmee tace"dagaske nake mana,ban ta6a faɗa maki ba,amma maganar gaskiya kamanninki dashi har sun 6aci,kullum na kalli fuskarki sai ya faɗo mun araina,saboda komai na fuskarki irin nashi ne,tun daga kan idanuwanki,hancinki,da kuma bakinki duk irin nashi ne,ke hatta launin fatarki chocolate colour irin nashi ne,da ace Abusufyan ya ta6a yin aure,zan iya rantsewa cewa ke ƴarsa ce' tunda azmee ta soma magana sehrish ta saki baki tana sauraronta, "abun ya jima yana ɗaure mun kai,shiru kawai nayi,amma kamanceceniyarki da wasu daga cikin matasan gidan nan har taso tayi yawa," Cika da mamaki Sehrish tace"Aunty azmee wai dagaske"? murmushi azmee tayi kafin taci gaba da cewa"na ta6a yi maki wasa ne irin haka"? Girgiza kai sehrish tayi alamar a'a, Cigaba da magana azmee tayi"kina yanayi da Abbansu junaid sosai kuma kina kama da Auntynsu Azeema,hatta junaid akwai kamanceceniya atsakaninku abunda yasa baza a gane ba saboda hasken fatarshi,amma kina kama da shi,bayan shi kuma sai Marshal Omar,shima akwai kamanninshi atattare dake,da kuma kanal yousouf,na jima da lura da hakan," tunda sehrish taji wannan jawabin na azmee take ta faman sakin murmushi,daɗi kamar ya kashe ta saboda ance tana kama da uncle Abusufyan ɗinsu, "Aunty azmee naƙosa na ganshi,Allah yasa kafin nadawo daga school ya ƙaraso,da kaina zanje inyi mashi sannu da zuwa sannan in kai mashi abun sha," Dariya azmee tayi tana cewa"Allah yasa toh,amma kin manta baki ce insha Allah ba," cikin sauri sehrish tace"Insha Allah Aunty azmee," Suna cikin firar nan tasu,sai ga junaid ya faɗo cikin kitchen ɗin ko sallama babu a firgice suka ɗago suna kallonshi, daga shi sai gajeran wando fari ajikinshi,sai faman washe baki yake yi,kamar wanda akayima albishir da gidan Aljanna, "Junaid anya lafiyarka kuwa?kaine yau kake yawo da short ajikin ka?ko ka manta akwai sehrish dani acikin gidan"? Acewar Azmee, Murmushi ya saki tare da nuna sehrish da hannunshi yace"Wurinta nazo,inason magana dake reesh,in ba damuwa ki biyo ni muje bedroom ɗina,' Kallon azmee tayi don taji me zata ce, "kije mana,amma kada ki jima," Amsa mata tayi da toh sannan tabi bayan junaid suka fuce atare izuwa bedroom ɗinshi dake a upstairs, atare suka shiga cikin ɗakin nashi,har wurin gadonshi yakaita sannan ya tsaya tare da nuna mata shaddojin daya jera asaman gadon nashi yace"Pls reeshi ki za6amun ɗaya mai kyau,inaso yau nayi shigar mutunci don na burge uncle Abusufyan yasan cewa na girma yanzu,'ashagwa6e junaid ya ƙarasa maganar, Sehrish kuwa zuba ma tsadaddun shaddojin ido tayi tana kallonsu,kala biyar ne sun sha uban aiki ajikinsu,hannu tasa tana ɗaɗɗaga kayan tace"junaid ae ni nama rasa wadda zan za6a maka acikinsu,saboda kowacce kasa acikinsu kyau zatayi maka,bakasan cewa kaine keyi ma kayan kyau ba"? Tayi maganar tare da ɗan juyawa tana kallon junaid dake tsaye yana ta faman sakin murmushin jin daɗin yarda sehrish ke hura mashi kai,
ta jima tana ruwan ido kafin ta cankar mashi wata haɗaɗɗiyar shadda gezner Ash colour sai faman salƙi take yi, mika mashi tayi tare da cewa"Wannan tayimun sosai kuma ina da tabbacin cewa in har ka sanyata ajikinka,sai uncle abusufyan ya razana da ganin irin kyan da zakai,' Kar6ar shaddar yayi daga hannunta yace"thank u so much reesh,amma fa ba yanzu zan sanyata ba,sai zuwa anjima in zanzo ɗaukarki daga school zaki ga kalar wankan da zan ɗauka," murmushi tayi tare da kama hanyar fita daga cikin bedroom ɗin nashi tana cewa"Allah ya kaimu lafiya,yanzu dae zan jiraka,in ka kammala shirin ka fito mu tafi kar nayi late,' Amsa mata yayi da toh,bayan ta fita ya tattara shaddojin duka ya mayar acikin wardrobe ɗinshi, ya zaro wasu jeans da t-shirt ya shiga zura su ajikinshi
_💋Boss Bature💋_
Lokacin da sehrish ta koma kitchen ɗin bata samu Azmee ba,sae dae Hayaam ta samu acikin kitchen ɗin,tana atsaye ta ruƙe qugunta kamar mai jiran wani abu, Ganin sehrish yasata cewa"Sannu ko" firgit Sehrish tayi tare da kai idonta inda hayaam ta ke atsaye tana sakin wannan shu'umin murmushin nata, "Yawwa"ta amsa mata atakaice tare da wucewa wurin trayn da azmee ta ajiye mata saman table wanda ta shirya ma sgr breakfast ɗin shi aciki,hannu biyu tasa ta ɗauki tray ɗin sannan ta kama hanya tare da fucewa daga kitchen din,hakanan ta dinga jin kamar bata yarda da hayaam ba,anya ba wani abu takeyi acikin kitchen ɗin ba?in ba haka ba meyasa ta tsaya atsaye ruƙe da qugu,kamar mai jiran wani abu, haka tayi ta wasiwasi acikin zuciyarta har ta ƙarasa part ɗin sgr, Sallama ta fara yi mashi,jin shiru ba'a amsa mata ba,yasa tayi tunanin ko yana acikin bedroom ɗinshi ne, A hankali tasanya kafarta tare da shigewa cikin palourn komai agyare tsaf ta same shi,asaman table ta aza mashi tray din sannan ta tsaya tana jiran fitowarshi ko zai bukaci wani abu, tana cikin tsayuwar nan tajiyo muryarshi daga cikin bedroom ɗinshi yana tambayar wanene anan!" Cikin sauri tace"Ni ce,dama breakfast ne na kawo maka," kusan minti biyar da yin maganarta sannan taji yace"A shigo min da coffee shi kawai nake buƙata," murmushi ta ɗanyi tare da mika hannu ta ɗauki cup of coffee ɗin dake acikin kayan breakfast ɗin nashi,ta nufi bedroom ɗin hannunta ɗauke da cup ɗin, sai da ta tsaya abakin ƙopar shiga Sgr ya bata izini sannan tasa kai tashiga,wani irin daddaɗan kamshin turarensa ne ya bugi hancinta,nan take taji wani irin yanayi atattare da ita, lumshe donta tayi tare da buɗesu a hankali ta kallo inda sgr yake, a hakimce ya ɗan kishingiɗa daga gefen katafaren gadon nashi, Gaza janye idanunta tayi daga kallon kyakkyawar surar jikinshi,wankan daya ɗauka ba ƙaramin fisgarta yayi ba,white trouser ne na suits amma bai sanya coat ɗin sama ba,iya vest ɗin ciki ya bari tabi shape ɗin jikinshi,daga ƙasan vest ɗin ta ɗan tattare hakan ya bayyana farar fatar shafaffen cikinshi, ya harɗe kafafunshi wuri guda yayin da idanunshi ke a lumshe, tafiya take tana tunkarar inda yake idonta akanshi har ta ƙarasa tare da ajiye mashi cup ɗin asaman bedside table ɗinshi tace"Gm sir,ga coffee nan na kawo maka,ko akwai wani abu da kake buƙata"? Bai amsa mata ba,a hankali ya dan buɗe idanunshi sannan ya yunƙara tare da miƙewa daga zaune ya sauko da ƙafafunshi ƙasa, Zaki iya tafiya,ya ambaci hakan ayayin da yakai hannu tare da ɗaukar kofin coffeen yakai bakinshi yana kur6ar shi anatse, Juyawa sehrish tayi ta kama hanyar fita daga bedroom ɗin a hankali,ji take kamar karta tafi ta barshi,don bata gaji da kallon kyakkyawar fuskarshi ba,
Yana cikin shan coffeen nan wani abu ya sarƙe mashi adaidai saitin throat ɗinshi,a hanzarce ya ajiye cup ɗin tare da zura fingers ɗinshi guda biyu cikin bakin cikin sa'a ya ruƙo siririn abun, Lokacin daya fiddo da abun daga bakin nashi yayi arba da dogon gashi,ware idanunshi yayi, hankali a matukar tashe yana kallon gashin yace"in my coffee...! Jin wannan maganar tashi yasa sehrish saurin juyawa don taga menene,a lokacin har tasa ƙafa zata fita daga ɗakin, Gabanta ne taji yayi wani irin mugun buga ganin siririn gashin da Sgr ya ruƙo a hannunshi, Yunkurin amai yashiga yi,nan take ya miƙe da saurin gaske ya faɗa toilet,kai tsaye ya ƙarasa gaban basin yana kwarara aman,tamkar ƴan hanjin cikinshi zasu fito,kasancewar shi mutum mai tsaftar gaske ga ƙyanƙyami ya tsani ƙazanta a rayuwarshi duk mun ƙankanta,ranshi ba ƙaramin 6aci yayi ba,gashi a abun shansa kuma har ya shiga bakinsa!!,a wannan lokacin komai zai iya aikatawa he can't even control him self, cos he has a very bad temper,kuma ta motsa. Tap ya kunna,ruwa yashiga zubowa yana kora vomitting ɗin da yayi,sannan ya tarba tafin hannayenshi biyu tare da ɗebo ruwan ya watsa su a fuskarshi yana faman sakin huci, Sehrish dake atsaye abakin kopan bedroom ɗin nashi,jikinta sai faman kerma yake yi,gaba daya tabi ta rikice kan ta ya gama ɗaurewa,taya akai aka samu gashi acikin abun shan Sgr?ita dae tasan cewa ba gashin kanta bane,saboda ta sanya hijab ajikinta,hasalima ba ita bace ta shirya mashi kayan breakfast ɗin nashi ba,tunkan taga hukuncin da zaiyi mata har tafara matsar kwalla,don tasan bazai ƙyale ta ba,dole ya hukunta ta,
A fusace ya fito daga cikin toilet ɗin,sai faman huci yake yi,ɗagowa yayi da idanunshi yana kallon inda sehrish take atsaye jikinta sai kerma ya keyi,tunda taga zufa na gangarowa a gefen fuskarshi, ta ƙara tsorata sosai, tamkar wani zaki haka ya tunkaro ta,a tsananin tsorace sehrish ta shiga ja da baya tana girgiza kai cikin shessheƙar kuka take cewa"wlh bani da masaniya akan gashin nan,banawa bane bansan ya akai ya shiga cikin abun shanka ba,' wata irin tsawa da Sgr ya daka mata nan take sehrish ta firgita agigice take zazzare ido tana kallon fuskarshi, biting lips ɗinshi ya shiga yi,yama rasa wane irin punishment zaiyi mata, Nuna ta da dogon yatsan sa yayi tare da cewa"as from today!bana son na ƙara ganinki a part ɗina!' Cikin shessheƙar kuka sehrish tace"Am really sorry babban yaya........ba laifi na bane bada sani na gashin ya faɗa aciki ba..........'tun kafin ta ƙarasa maganar ya ɗaga hannunshi da nufin ya sharara mata mari,runtse ido sehrish tayi tana jiran jin saukar marin nashi a kuncinta, ji yayi bazai iya ba saboda tunda yake arayuwarshi bai ta6a gigin ta6a jikin wata ƴa mace ba da sunan bugu,tun suna yara Abbansu ya hane su da yin wannan,kullum yana tunasar dasu akan su dinga daraja ƴa mace, Dunkule hannunshi yayi tare da yarfar dashi gefe guda,sannan yace"Get out from my bedroom!since before I show u my true colour!, ya ƙarasa maganar tare da juyawa yabarta tsaye anan tana faman shessheƙar kuka, Ji tayi bazata iya jure hukuncin da Sgr yayi mata ba, na hanata aiki a ƙarkashin shi ba, gaba ɗaya jikinta ya gama yin sanyi, a wani irin yanayi ta zube asaman guiwowinta,cikin sanyin murya,muryarta na rawa tace"nasan na 6ata maka rai sosai,na cancanci kowane irin hukunci daga gare ka,amma ina neman alfarma a wurin ka........'dakatawa tayi da maganar tana kallon bayan shi daya juya mata, ganin ya tsaya da yin tafiyar yasa ta gane cewa ita yake sauraro, anatse taci gaba da magana"ka yanke mun kowane irin hukuncin daya dace da laifin dana aikata,amma kada ka hanani yin aiki a ƙarkashinka,wannan horon yayi mun tsauri sosai,bazan iya jurewa ba,tun da nake maka aiki banta6a yin irin wannan gangancin ba,ina kiyaye wa sosai wurin ganin na tsaftace duk wani abu da zan kawo maka kaci ko ka sha,ba zanso wani abu da zai cutar dakai ba,wannan ma bansan ya akai hakan ta faru ba,don Allah kayi haƙuri ka yafe mun............'ƙarasa maganar tayi cikin shashsheka yayin da hawaye ke cigaba da zuba a idanunta, shiru Sgr ya ɗanyi na wani lokaci batare da ya motsa ba,hakan yasa ta fidda rai da cewar zai yafe mata, Hannu tasa tana sharar hawayenta tana kallon bayanshi,cigaba da tafiya sgr yayi kai tsaye ya tunkari wurin dressing mirror ɗinshi,hannu yasa tare da janyo drawer chest din dake ajikinshi,sabon scissors ya ɗauko cikin ledarshi, ya fiddo dashi yana kallonshi, lokacin daya juyo hannunshi ɗauke da almakashin nan,hankali atashe sehrish ta zaro ido tare da miƙewa tsaye daga kneel down ɗin da tayi tana ja da baya tana girgiza mashi kai,alamar karyayi mata haka, Gadan gadan Sgr ya tunkare ta,hannunshi ɗauke da almakashin nan sai faman salƙi yake yi,hannu sehrish ta aza asaman kanta tana cewa"Nashiga uku!innalillahi wa'inna ilaihirraji'un..........dan Allah kada ka datse mun gashin kaina ......'tana magana tana ja da baya yayin da shi kuma yake tunkararta,abu kamar wasa haka suka shiga zagaye ɗakin yana binta tana ja da baya,a ƙarshe daya fusata a zafafe ya damƙo hijabin dake jikinta tare da tun6uke ta daga jikinta yayi wurgi da ita gefe guda,yarda ya fusge hijabin daga jikinta gaba ɗaya ta tafi zata faɗi kasa,yakai hannu tare da janyo ta ta faɗo saman wide chest ɗinshi,kuka take kamar ranta zai fita saboda ba ƙaramin so takeyi ma gashin kan nan nata ba,ta kwallafa rai akanshi shiyasa kullum take ƙokari wurin gyara shi,har tasamu tatara shi da yawa bayan yanke shin da akai da zata fara aiki gidan,gashi yau akan kuskuren da ba ita ta aikata ba,za'ayi mata aski tana ji tana gani ba yarda zata yi, tunda sehrish ta faɗa jikinshi gaba ɗaya ya rasa duk wani kuzari na jikinshi,ƙamshin turaren jikinta ba ƙaramin kashe mashi jiki yayi ba,abunda bai ta6a yi ba arayuwarshi,a hankali yakai hannunshi tare da Cire ribbom ɗin da ta ɗaure gashin kanta dashi,ya warwaro shi duka tare da yin wurgi dashi gefe guda ya fadi kasa saman hijab ɗinta, Nan take lallausar suman kan nata mai laushin gaske ya tarwatse abayanta yayi mata tamkar hijabi, Ai ina baku labari tunda boss man ɗin nan ya zura hannunshi acikin sumar kanta nan fa yashiga murza gashin acikin hannunshi,laushin gashin kan nata ne yake fisgarshi har yayi hakan batare da saninshi ba, A hankali ya russinar da kanshi tare da kai tsinin hancinshi saman sumar kanta yana shaƙar daddaɗan kamshin dake fitowa daga cikin sumar kan nata,wani irin bugu zuciyarshi tashiga yi da sauri sauri take harbawa, ƙankame shi sosai sehrish tayi ta hanyar zagayo da hannayenta abayan waist ɗinshi ta ruƙo shi sosai kamar wani zai kwace mata shi,ba ƙaramin yanayi ta jefa Sgr ba ta kara sanya mashi kasala ajikinshi,kamar yarda itama ta shiga yanayin,tunda ta lafe mashi ajikinshi tayi lamo,wata irin natsuwa ta ji da bata ta6a ji ba atattare da ita,shessheƙar kukan nan da takeyi gaba daya ta neme ta ta rasa,tsit tayi tana sauraron heart beat ɗinshi, Suna cikin wannan yanayin na shauƙi sai ga Abbansu ya faɗo cikin part ɗin nasa yana neman shi,ganin baya acikin falon yasa ya wuce izuwa bedroom ɗin shi,tunkan ya ƙarasa ya hange su manne da juna kamar tip da tyre, adaidai ƙopar shiga bedroom din nashi,abban nasu ya tsaya cike da mamaki yana kallon wannan abun al'ajabin,ko motsi basa yi,bakomai yafi ɗaure mashi kai ba,face yarda sgr yake cakuɗa sumar kan yarinyar acikin hannunshi sai faman murzar gashin kan nata yake,ga kuma hancinshi daya cusa asaman kan nata yana shaƙar kamshin da sumar kan nata ke badawa mai daɗin gaske, Ita kuma ta ƙankame mashi qugunshi da hannunta,ta kwantar da kanta asaman chest ɗinshi, baki asake Abbansu ke kallon wannan tashin hankali,jinjina kai ya shiga yi cikin ranshi yana cewa"Oh ni hussein!tun yaushe wannan al'amarin ya soma faruwa acikin gidan nan batare da sani na ba!Hmmmm yanzu haka zare mata ido yakeyi yana tsoratar da ita don ya samu abunda yake so,nasan maganinka Rafayet,"ya faɗi hakan tare da kama hanya yabar part ɗin nashi fuskarshi ɗauke da murmushi,don shi wannan abun farin ciki ne awurinshi,ji yake kamar ya zuba ruwa ƙasa yasha don tsabar farin cikin ganin rafayet tare da mace,baida burin daya wuce wannan arayuwarshi,shi dae yaga Sgr yafara kula mace da sunan soyayya,yau dae gashi Allah ya nuna mashi, Janye hancinshi yayi daga cikin sumar kan nata,sannan ya tattaro gashin nata tare da sanya almakashin ya datse mata shi,sosai ya yanke gashin,yabar mata guntu wanda ko kafaɗarta bai sauko ba,' hankali a matuƙar tashe sehrish ta raba jikinta da nashi, da sauri takai idonta akan hannunshi dake ruƙe da dogon gashin daya yanke mata,kamar a mafarki take kallon gashin nata daya yanke mata, A hanzarce takai hannu tare da shafo kan nata don taji sauran daya rage mata, Fashewa tayi da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita,dakyar takai hannu tare da ɗaukar hijab ɗinta, sannan ta juya tare da watsawa aguje tana kuka ta fuce daga cikin ɗakin nashi, ajiyar zuciya ya sauke tare da takawa izuwa gaban dressing mirror ɗin nashi ya mayar da scissors ɗin aciki tare da gashin kan sehrish daya datse,duka ya tura shi aciki ya ajiye,sannan ya maida drawer chest ɗin ya rufe,
Komawa yayi tare da haye wa saman gadonshi ya kwanta,yanayin da bai ta6a ji ba atattare dashi ba yake ji,tsananin tausayinta ne ya kama shi,har ya dinga jin tamkar baiyi mata adalci ba daya datse mata gashin kanta,ya lura ba ƙaramin so takeyi ma gashin kan nata ba,lumshe idanunshi yayi a hankali yana tariyo abunda ya faru tsakaninta dashi,especially lokacin da ta watsa da gudu tana kuka,duk baiji daɗi ba saboda shi baiyi mata hakan da nufin ya 6ata mata rai ba.
    Â
  *💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
Saboda masu complain, nacewa nace zan tura da safe ban turo ba,Allah ne bai nufa zan tura da safen ba,
Ga half page nan,later zan tura sauran
komawa cikin bedroom ɗinta tayi tana ta faman sharar hawaye ranta na kuna,wuri ta samu ta zauna daga gefen gadonta tana ƙarashe kukan nata,babban takaicinta guntun gashin da Sgr ya bar mata da kyar in zaiyi parking da ribbom,koma yayin ba lalle ribbom din ya tsaya ba,ta jima tana azaune tana matsar kwallar bakin ciki,kafin daga bisani ta miƙe tare da nufar wurin dressing mirror ta tsaya tana kallon kanta acikin madubin,cikin shessheƙar kuka tace"Meyasa bai aske gashin duka ba yabarmun kwalkwali?me zanyi da guntun gashin nan daya barmun?ban son gashin!na tsani ganin shi,'ita kaɗae take ta faman sambatu rai atsananin 6ace,
Kwankwasa ƙopar ɗakin nata akai,a tsiwace tace"Wanene"!  Muryar junaid taji daga waje yana cewa"It's me junaid,tun ɗazu fa nake jiranki,ki fito mu tafi na sauke ki,'a ƙagare yake maganar don ya gaji da jiranta,
Ita gaba É—aya ma ta manta da batun zuwa makarantar,sai da junaid ya tunasar da ita, Â Â Â hannu tasa tana share hawayenta tace"junaid ka jira ni,acikin mota yanzun nan zan fito," Â Amsa mata yayi da"Okey," sannan ya juya tare da barin kopar dakin nata,
Sai da tafara shiga toilet ta wanko fuskarta sannan ta fito tare da É—aukar hijab É—inta dake ajiye gefen gadon ta zura ajikinta
Cikin sauri ta fito ɗauke da school bag ɗinta,ta fice waje wurin harabar ajiye motocinsu,hannu tasa tare da buɗe motar junaid ta shiga daga ciki ta zauna,  ɗan kallon fuskarta yayi tare da cewa"Reesh,na jima ina jiranki,bansan me ya tsayar dake ba,gashi ma har kinyi late,ina fata dae lafiya?" daƙyar ta ƙaƙaro murmushi tare da cewa"lafiya lou ba wani abu,mu tafi kawai ina ƙara makara,"   ajiyar zuciya ya sauke tare da jan motar suka bar gidan. Ita kuwa Hayaam dama tunda taga Sehrish ta nufi part din sgr da coffeen ta sulale ta shige dakinta don kar a gano abunda ta aikata.
*HOSSANA*
Zaune take saman gadonsu ta takure kanta sai faman shessheƙar kuka takeyi,ta sanya uniform ajikinta amma taƙi tashi ta zura hijabin,ta hana kanta duk wani jin daɗi,
Fitowa jahad tayi daga cikin toilet tana kallonta gwanin ban tausayi tace"Hossana,dan Allah kidaina wannan kukan,duk kinbi kin takure kanki,ni nasan cewa Æ´a omar ba hakanan ya daina zuwa wurin mu. Ba,Abubuwane suka yi mashi yawa shi ya sanya bai samu halin zuwa ba,'
muryarta na rawa tace"jahad ba zaki gane bane,bazan ta6a samun kwanciyar hankali ba in har bansa ya omar a idona ba,Allah in har baizo ba yau,zanci shinkafar 6era ne na mutu kowa ya rasa,'  dariya jahad ta fashe da ita,hakan yasa hosana ɗaure fuskarta tana jifarta da harara tace"jahad dariya kike mun ko?  tsagaitawa tayi da dariyar tana girgiza kai tace"hosana dole nayi dariya,shinkafar 6era fa kika ce?  ɗaure fuska tayi tana murguɗa mata baki,  Murmushi kawai jahad tayi tare da komawa wurin closet ɗinsu,ta buɗe tare da ciro uniform ɗinta ta shiga zura su ajikinta,shaf shaf ta kammala shiryawa,ta ɗauko school bag ɗinta,sannan ta dawo wurin hosana tace"tashi mu tafi kada mu makara,"  Girgiza kai hosana tayi tace"Jahad ku tafi kawai,ni zan zauna a gida,saboda ko naje ba gane karatun zanyi ba,'  Zuƙunnawa jahad tayi agabanta tace"pls hosana ki daina sa damuwa aranki kinji?ni da kaina yau zan nemo maki ya Omar,'  jin abunda jahad tace yasa hosana sakin murmushi tace"dagaske Jahad"?  ɗaga mata kai tayi alamar eh tace"nayi maki alkwarin,duk inda yake indae yana acikin garin nan saina nemo maki shi,"  Wani irin farin ciki ne ya lullu6e hosana,jiki na rawa ta tashi ta ɗauko hijabinta bayan ta zura safarta da takalmanta suka fuce atare,
  A waje suka samu motar osman na jiransu,bayan sun shiga ya tashi motar ya fuce dasu daga cikin gidan,hosana sai murna take jahad tace zata nemo mata Omar,batasan cewa ita da wasa ta faɗa mata ba don ta sanyata farin ciki ne kawai,
Wuraren ƙarfe 12 na rana,jirginsu hajiya azeema yayi landing daga lagos,kanal yousouf ne tare da su irfan suka je tarbosu,a lokacin hayaam suna a kitchen tare da azmee suna shirya lunch ɗin gidan da kuma na tarbar baki,daga kasa ƙafarka acikin main palour ɗin zaka ji daddaɗan ƙamshin abincin da suke girkawa ya gauraye ko'ina,
Cike da son jin gulma hayaam tace"Aunty azmee,wai Uncle ɗin nan nasu da zaizo daga ƙasar turkey,yana da aure ne"?  Azmee tace"a'a bai ta6a aure ba,ina tunanin ma ko budurwa bai ta6a ajiyewa ba,"  jinjina kai hayaam tayi tare da cewa"tabɗijancen amma da alama zaiyi ji da kai,"  murmushi azmee tayi tare da cewa"yarda kike tunani ba haka yake ba,Abusufyan wayayyan mutun ne,ta wani 6angaren ma bai ɗan jin magana amma dai nasan yanzu ya kimtsu tunda girma ya kama shi,amma lokacin baya da yake zuwa mana nan, yarda kikasan junaid haka ɗabi'unshi suke,da yake shi rainon goggonsu ne,'   murmushi hayaam tayi tana ɗan ta6e baki tace"Amma aunty azmee,ita wannan yarinyar sehrish,yakamata ace aikinta ya qare acikin gidan nan,tunda gani nazo kuma zan jima anan ne,ni a ganina bai kamata tana yawo acikin gidan nan ba,ita kaɗae ƴar matashiyya da ita,ya kamata ace tana gaban iyayenta yanzu,'ta ƙarasa maganar tana faman yatsina fuska,ta zuba ma azmee ido tana jiran jin me zatace,
shiru azmee tayi saboda bata da amsar da zata bata, Cigaba da magana hayaam tayi"Yarinyar ta cika rawar kai sosai,yakamata ta tsaya a iya matsayinta na ƴar aiki mana,ni ina ganin akwai abunda take hari acikin gidan nan shiyasa ta liƙe har ta samu matsayi a wurin babban yaya,"
"Hayaam muyi sauri mu kammala aikin girkin nan,lokaci yana ƙure mana,"da gangan azmee tace mata haka,don ta dakatar da ita daga yi mata zancen Sehrish,don ita ta tsani gulma arayuwarta,  ta6e baki hayaam tayi,aranta kuma taji haushin yarda azmee ta katse mata hanzarinta batare da ta ƙarasa maganarta ba,daga bisani kuma ta saki shu'umin murmushin nan nata,tana tunanin ko ya Sehrish ta ƙare da sgr,don tasan cewa dole yaga gashin nan kuma zai hukuntata akan hakan,taso taje tayi masu la6e amma tsoro ya hanata gudun kar wani ya kamata asoma zarginta, Ƙasa ƙasa tayi da murya tare da cewa"Koda ace bai hukunta ta ba,nasan cewa zai fara tsanarta ne,kuma zai gane cewa ƙazama ce ita,zanci gaba da shirya mata makirci har nasamu na maye gurbinta a wurin sg......'bata ƙarasa maganar ba,saboda jin shigowar Hajiya Azeema tare dasu kanal yousouf da sauran da suka je ɗaukota,zuba ido hayaam tayi tana kallonta,ganin irin ruwan wankan gwala gwalan data ɗauka,  jikinta na sanye da material launin sararin samaniya,mai tsadar gaske sai faman ƙyalli yake yi,rigar takai mata har wurin guiwarta,sai zane data ɗaura,ta yafa gyale asaman kafaɗarta,yayin da ta kashe ɗaurin ɗan kwalin nan ture kaga tsiya,amma ita nata sunan shi ture kaga arziƙi,don akwai abun arziƙi,gaba daya earrings dinta da awarwaron hannunta da kuma sarƙar wuyanta duk gold ne,ta wanku iya wankuwa,Hajiya azeema kenan ɗaya daga cikin biloniyas din family nasu,idan aka cire shugaba kuma jagora wato Surgeon General Rafayet,
Sai faman sakin murmushi take yi,tsantsar farin cikine ya lullu6eta yau gata agidan ɗan uwanta hussein,anjima ba'a haɗu ba,harkar kasuwanci ta 6oye ta,saboda bata cika zama a nigeria ba,kunsan business woman bata nan bata can kullum cikin hawa jirgi take wurin zuwa harkar kasuwancinta,  Atare suka ƙarasa cikin main palour ɗin,Kanal yousouf na ruƙe da Trolley ɗin da tazo dashi,   Anatse take bin ko'ina na gidan da kallo komai ya canza mata,ba kowa take muradin gani ba,face Junaid don har mafarkin shi tayi,shiyasa ta ƙagara tazo don tagan shi,juyawa tayi tare da kallon irfan tace"wai ina yaya hussein ne?naga kamar ba kowa gidan ko"?  "Abban mu ya ɗan fita garden tare da babban yayan mu da kuma ya Omar,amma ina da tabbacin cewa nan bada jimawa ba zasu shigo ciki,"ya ƙarasa maganar tare da nuna mata wuri yace"Aunty ki zauna mana,bari nayi ma Aunty azmee magana ta haɗa maki farfesun nan nata,nasan baki manta ɗanɗanon shi ba,"  dariya tayi tare da dan bugun kafadarshi tace"wato kallon acici kakeyi mun ko?daga zuwana ko hutawa banyi ba zan fara neman farfesu,kamar wata mayya,ni duk bama wannan ba,nifa hankalina bazai kwanta ba in har bansa junaid acikin idona ba,'   Kanal yousouf yace"Aunty gaskiya nafara kishi da junaid,haba kowa junaid junaid,ko hutawa ba kiyi ba amma kin fara ambaton sunanshi kamar shi kaɗae ne ɗa acikin gidan nan,"cikin zolaya yayi maganar tashi, Kafin Azeema ta kuma cewa wani abu,sai ga azmee ta fito daga cikin kitchen fuskar nan ɗauke da murmushi tana cewa"wata sabon gani, hajiya azeema,Sai yau zamu sake sanyaki acikin idanunmu"?tayi maganar a yayin da take ƙarasawa wurinta suka rungume juna,dama suna ɗasawa da ita,mutuniyarta ce kodan saboda iya girkin azmee yasa take shiri da ita sosai,don ita bata wasa da abinci,akwai son cin mai daɗi,kullum tazo Abuja wurinsu burinta tasha farfesun azmee,  Raba jikinsu sukayi dana juna,Azmee taci gaba da cewa"Hajiya azeema kece kika koma haka? Dariya azeema tayi tace"kinji ki da wata magana,kamarya na koma?nasan halinki fa azmee yanzu kince na ƙara ƙiba,'  Azmee tace"kin tsargu kenan,tunda gashi nan kin rigani faɗin abunda zance,'  Ta ƙarasa maganar tare da ruƙo hannunta tace"nasan kin kwaso gajiya sosai,shiyasa na gyara maki shinfiɗa inda zakije ki yada gajiyar da kika kwaso,sannan akwai special suya da kuma wannan farfesun da kika fiso na shirya maki shi,da zarar kin kammala hutawa zan shiryo maki shi,kici ki ƙoshi,nasan mutuniyar tawa bata wasa da cikinta,akwai bama ciki haƙƙinsa,"   Sai faman murmushi hajiya azeema ke saki,da alama taji daɗin karramawar da azmee tayi mata sosai,atare suka wuce ciki izuwa bedroom din da zata sauka,dama already azmee ta gyara mata ɗakin sai ƙamshi yake,   bayan sun shiga bedroom din,Sai da suka ƙara gaisawa sosai,kafin daga bisani Azmee tabar cikin ɗakin ta koma kitchen,   Ajiyar zuciya hajiya azeema ta sauke tare da cire mayafin cikinta ta ajiye shi saman gadon,sannan ta wuce cikin toilet,  Bayan shigarta kanal yousouf ya shigo cikin bedroom din hannunshi ruƙe da trolley dinta,jingine mata shi yayi ajikin wardrobe,sannan ya juya ya fuce,   fitowa azeema tayi daga cikin toilet din har lokacin fuskarta ɗauke da murmushi a fili tace"oh ni,koya junaid ya koma yanzu?nasan cewa ya ƙara girma sosai,gaskiya nayi missing shagwa6ar shi,nasan cewa da zarar yaji cewa na ƙaraso,zaizo ya ishe da rigima yana cewa Ina tsarabar shi,'ta ƙarasa maganar tare da hayewa saman gadon ta ɗan kishingiɗa donta runtsa,
Bata jima da kwanciya ba,Abbansu ya shigo cikin gidan tare da sgr da marshal atare suka ɗunguma zuwa masaukin nata,a hankali abba ya tura ƙopar ɗakin suka shiga da sallama,  Jin muryar ɗan uwanta,yasa ta yunkura tare da miƙewa daga zaune tana kallonsu fuskarta ɗauke da murmushi,   Ƙarasawa ciki su kayi,sgr da omar suka samu wuri saman doguwar sofa din dake dakin suka zauna suna fuskantarta,yayin da Abbansu kuma ya samu wuri gefen gadon kusa da ita ya zauna fuskar nan awashe sai faman farin ciki yake yi na ganin ƴar uwarsa daya jima basu haɗu ba,   gaisawa suka shiga yi da junansu,don ba ƙaramin kewar juna sukayi ba,  Abba yace"ina fata dae da shirin zama kika zo mana,dan wannan karan bazan bari ki koma ba,nagaji da kewarku da nake ta faman yi,'   "Yaya hussein,nasan ban kyauta ba,na rashin zuwana wurinku,abubuwane sunyi mun yawa shiyasanya na jima banzo ba,amma Insha Allah wannan karan har sai kun gaji dani,zan zauna ne har sai an ɗaura auren junaid,'  Fashewa sukayi da dariya gaba dayansu,banda Sgr wanda tun shigowarsu,ya jingina bayanshi ajikin sofa din tare da lumshe idanunshi,sarai azeema ta lura dashi dama sai da ranta ya bata cewar bazai tanka mata ba,   Omar yace"ae ni fushi nake da Auntyn tawa,haba aunty azeema yau kusan wata nawa kenan?yaushe rabon da mu sanyaki a idanunmu,baku son zuwa ganin ƴa'ƴanku,kuma babu damar mutum yace zaizo ganinku saboda kullum baku a ƙasar,'ya ƙarasa maganar tare da ɗaure fuskarshi,   dariya azeema tayi tana cewa"kwantar da hankalinka mutumina,ae wannan zuwan daka ga nayi,bazan koma ba har sai naga an shafa fatihar auranku,kai da wannan namijin zakin,'  tayi maganar cikin zolaya tana kallon Rafayet,aikuwa ya ƙara ɗaure fuskarshi alamar baiso,  Murmushi Abbansu yayi tare da cewa"kada ki samu damuwa,ae kuna anan ma zamusha biki,Abusufyan kawai nake jira ya ƙaraso,don nafison ya shaida wannan ɗaurin auren,ayi komai tare dashi don shine waliyyi"  Jin wannan maganar ta Abban nasu yasa shi buɗe idanunshi tare da miƙewa daga saman sofa ɗin ya nufi hanyar fita,duk suka zuba mashi ido, Sai da yakai bakin kopar fita sannan ya ɗan juyo tare da kallon inda Hajiya azeema take zaune yace"Allah ya huta gajiya,"yana faɗin hakan yasa kai ya fuce daga ɗakin,  Girgiza kai Abbansu yayi tare da cewa"Rafayet sai addu'a abun nashi ƙara gaba yake yi,"murmushi kawai azeema tayi aranta tace"Jinin Alexandra kenan,in har rafayet baiyi mun haka ba,bazan tabbatar da cewa nononta ya sha ba, Ganin rafayet ya fice yasa Omar miƙewa tare da yi masu sallama ya fuce yabarsu donsu samu damar tatttaunawa atsakaninsu yasan sunyi kewar juna sosai,
Bayan fitar Omar,azeema ta kalli abban nasu tare da cewa"Yaya hossein,ya maganar zuwan Abusufyan din?dagaske ne yau ɗin shima zaizo?kasan fa ya jima yana samana ran cewa zaizo sai kuma yaƙi zuwa daga baya,abun na damuna sosai,"fuskarta ɗauke da damuwa tayi maganar,  "ya tabbatar mun da zuwan nashi,kuma ina da tabbacin cewa wannan karan dagaske yake mana ba wasa ba,inaso yazo saboda akwai abubuwa da dama da nake son muyi magana akai,na damu dashi sosai,na damu da halin da yake ciki," Jinjina kai tayi tace"amma abba,akwai wata alfarma da nake nema awurinka,"   "Wace alfarma kenan"?acewar abban nasu,  Cigaba da magana tayi"idan Abusufyan yazo nigeria wannan karon banso ku bari ya koma turkey,dan Allah ka ruƙe shi anan,ya zauna akusa dakai,banason yanayin nesa dakai,har yanzu akwai sauran yarinta atattare dashi,shi ne ƙarami acikinmu akwai buƙatar mu janyo shi ajikinmu,don muji menene ke damunshi,meyasa baya son zama ƙasar nan,ni nasan akwai dalilin da yasa abusufyan yake gudun zama anan,tabbas akwai damuwa atattare dashi,"   Abba yace"dama ni bazan barshi ya koma can ba,bazan ƙara yin gangancin barinshi yayi nesa dani ba,koda can daya bar ƙasar batare da sanin mu ya tafi ba,narasa gane mashi ni kaina,ba yarda banyi dashi ba akan yadawo nan gida amma yaƙi saurare na,wannan karan dae mun ci sa'a ya amince zaizo,kuma insha Allah idan yazo bazan barshi ya koma ba,zan ruƙe shi awurina,'  Ajiyar zuciya azeema ta sauke,hankalinta ba ƙaramin kwanciya yayi ba,dama ita burinta Abusufyan yadawo kusa da Yayansu hossein su zauna atare da ƴa'ƴanshi,tafi son taga sun haɗa kansu wuri ɗaya,ita kanta ba da son ranta take zaune a lagos ba,sabo ne kawai sai kuma harkokin kasuwancinta da suka fi yawa acan,   Sun jima suna fira tsakaninta da ɗan uwanta,kafin daga bisani yayi mata sallama tare da fucewa daga ɗakin,komawa azeema tayi tare da kwantawa saman gadon,nan take bacci yayi awon gaba da ita,
A 6angaren sehrish kuwa tunda taje school,fuskarta babu annuri ko kaɗan duk tabi ta takure kanta asaman seat ɗinta,ko magana batasan yi,juyowa Amrish tayi ta kalli fuskarta tare da cewa"wai meyake damunki ne Sehrish?duk kin bi kin canza,ki faɗamun mana in akwai damuwa,may be ina da shawarar da zan iya baki,"   shiru tayi na wani lokaci kafin tace"Zan faɗa maki,but pls kada ki sanarwa kowa,"  "Insha allah,i will keep ur secret bazan bari kowa yaji ba,"amrish tayi maganar tare da mayar da hankalinta kan sehrish,   matsowa sehrish tayi kusa da amrish tayi ƙasa ƙasa da muryarta sannan tace"Amrish,babban yayanmu ne ya datse mun gashin kaina,dana kwallafa rai akanshi,na jima ina gyara gashin kaina,sai da yayi tsayi sosai yayi kyau,shi kuma ya datse mun shi da almakashi,baki ga wanda yabar mun ba,ɗan guntu ko parking ma bayayi,in nasa ribbom ma zamewa yakeyi,baya ruƙe gashin,'   Hankali tashe Amrish tace"Are u serious!shi da kanshi yayan naku ya yanke maki gashi?baisan cewa gashi tsada yake yi ba,?amma garin yaya hakan ya faru?ta tambaya tana jiran amsarta,  shiru ta ɗanyi kafin tace"ni kaina bansani ba Amrish,da safe ne naje kai mashi coffee,yana cikin sha wani abu ya sarƙe mashi a throat ɗinshi,ashe gashi ne ya faɗa ciki,kuma ni banawa bane,nayi ƙoƙarin nayi mashi bayani akan hakan,amma bai saurareni ba,kawai yasa almakashi ya datse mun gashin,'ƙarasa maganar tayi muryarta tamkar zata fashe da kuka,  hannu amrish tasa tare da dafe goshinta tace"Ya salam,amma banji daɗi ba wlh,ni babban abunda nafi takaici shine,wazai aure ki a haka da guntun gashi,kinsan fa mazan yanzu sunfi son mace mai dogon gashi,"cike da zolaya amrish tayi maganar tana ƙumshe dariya abakinta,  Harara sehrish ta watsa mata tare da cewa"Oh abun ya zama na zolaya ko?ina faɗa maki damuwata maimakon ki tayani jimami shine kike mun dariya,'   "No,ba haka bane sehrish,nadamu nima sosai,rai na ya 6aci amma kada ki sa damuwa aranki,zan iya taimaka maki da hular gashi in kinaso,'   Cike da farin ciki sehrish tace"dagaske kike ko wasa"?  Amrish tace"am serious,ina dasu ajiye a gida zan ɗauko maki ɗaya daga cikinsu,amma bisa sharaɗin zaki kawo mun gashin kanki da babban yayanku ya yanke maki,inaso zanyi amfani dashi wurin haɗa wata hular gashin,ba ƙaramin kuɗi zamu samu ba,'   murmushi Sehrish ta saki tare da cewa"shikenan insha Allah,zan kawo maki gashin gobe in zanzo school,'   "Allah ya kaimu lafiya,"Amrish ta amsa mata,ci gaba da fira su kayi atsakaninsu har sae da malamarsu ta shigo sannan suka dakata da yin surutun nasu,
_💋Boss Bature💋_
Ana gab da za'a tashe su daga school,ciwon ciki yazo mata mai tsananin gaske,gaza jurewa tayi hakan yasa ta miƙe tare da zuwa wurin Aunty ɗinsu ta nemi izinin fita a wurinta,bayan ta amince mata ta fito daga class ɗinsu,sai faman sauri takeyi,hannunta ɗauke da school bag dinta,wani corridor ta nufa inda toilets din makarantar suke a jere,ɗaya daga cikin toilet din ta buɗe tare da shigewa ciki ta rufo shi,juyawa tayi tana kallon cikin toilet din komai na cikinshi fari ƙyal atsaftace,hannu tasa tare da zuge zip ɗin jakarta,ta ciro pad din da tazo da ita guda ɗaya,dama tun last week take jin alamun zuwan al'darta amma baizo ba,sai dae stomach pain da take ta fama dashi,wannan dalilin ne yasa take yawo da pad a jakarta just in case,
  ajikin towel hanger,ta rataya jakarta,sannan ta zame dogon wandon jikinta,pant ɗin ta curo tana dubawa taga ko ya fara zuba,babu ajikin pant ɗin,amma da taje wurin yin tsarki bayan tayi fitsari sai ga ɗigon jinin ya fito,cikin sauri ta sanya pad din ajikin pant dinta,sannan ta sanyashi ajikinta,ta ɗauko dogon wandon ta mayar ajikinta,sai da ta zura shi ajikinta,ta ɗauko jakarta tana ƙoƙarin fita daga cikin toilet din kenan,cikinta ya murɗa mata,wani irin raɗaɗi mara daɗin ji,nan take ta zukunna ƙasa hannunta dafe da cikinta,zufa ce ta shiga gangaro mata agefen fuskarta,daƙyar take fitar da numfashi,lokaci guda gaba daya ta galabaita ta fita hayyacinta,anan ta faɗi kwance saman tiles tana juyi ita kadae acikin toilet ɗin,babu wanda yasan abunda ke wakana.
*Junaid*
*SANARWA SANARWA*💃💃💃💃
*ME TAKEN NA AMARYA HUTAA$$*
*MUNA FARIN CIKIN SANAR DAKU CEWA MUNA BADA HAYAR KAYAN AMARYA(WEDDING GOWN), KAYAN BRIDAL SHOWER, KAYAN BIRTHDAY PARTY, KAYAN FITAR SUNA, SANNAN MUNA BADA HEAD AND SHOULDER, MUNA DA POSS, MUNA ALKYABBAR KAI AMARYA KO TARON WALIMAR SAUKA, MUNA DA KAYAN FULANI FARARE NA YARA DANA MANYA MUNA DA NA AMARYA BLUE BLACK, SANNAN MUNA GYARAN JIKIN AMARYA DA UWARGIDA CIKIN KWANA UKU CAKAL ZAKIGA KIN KOMA TAURARUWA MAI WALWALI. MUNAYIN TURARUKAN WUTA DA HUMRA DA KOLACCAR, KOWANNE KALA KIKE BUKATA AKWAI CIKIN FARASHI MAI SAUKI.*
*LOCATION KANO*
08062073990 Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
Ina kuke mata hamshakai wayanda suka amsa sunan su wajen mazajen su ina mata masu son qamshi shin ko kunsan tsafta bata tafiya seda qamshi ina masu son turare mai riqon gida tareda qamshin shi mai sanyaya zukata mardie collection tazo muku da dadadan turarukanta masu lasting riqon gida harma da jiki ku tuntube mu da nmb kamar haka 08136666994 inda zaku samu kaya kamar haka Wadrobe balls Madarar kulleccham Vaseline kulleccham Kajiji Halut Couscous Khumrah Da dai sauransu harda abin wanke toilet yayi tas komi dafe warshi wato BETHALEX METAL ku garzayo kar ayi baku
It's not just good ...it's finger linking good faster than fast food, better fine dining. Snack Awarah Farah Zobo Samosa Cup cake etc Contact me 09063302182or 09012179727.
*💋Boss Bature💋*
Join this link to follow my tiktok acct👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1
قصة ØØ¨ رومانسية بين Ø³ØØ±ÙŠØ´ ÙˆØ§Ù„Ø¬Ø±Ø§Ø Ø§Ù„Ø¹Ø§Ù… Ø±ÙØ§ÙŠØªðŸ’‹ðŸ’˜â¤ðŸ¤â¤ðŸ’•💖
*Na sadaukar da wannan zazzafan page din,ga dukkan masoyan littafin Abban sojoji,especially members na paid grp dina,Abban sojoji paid grp,Father of soldiers,Abban sojoji Vip grp,da kuma Junaid romeo Much luv Allah yabar zumunci anatare insha Allah (08103884440)*ðŸ˜ðŸ˜˜
*Bazan manta daku ba,waɗanda suka ƙarfafamun guiwa wurin rubuta littafin nan,har yau ina alfahari daku, Fadeela lamiɗo da kuma sadeeq abubakar CEO na Lafazi writer association,da kuma auntyna takaina,bazan fadi sunanta ba,sai na nemi ixninta saboda tsaro🤣😂😅 Da kuma sauran members dinda akayi fadi tashi dasu,suma duk zan fadi sunayensu nan gaba*
*Abban sojoji paid book ne,duk maison siye zaiyi mun magana kai tsaye ta layina,but pls banda kiran waya,only message ta whatsapp,bana shariya muddin mutun ya turamun saƙo zan duba ne,indae ina free,in mutun yayi payment zan tura mashi duka na baya da aka wuce shi har inda muke so*
â¤ðŸ¤â¤
*Junaid*
Tun bayan daya kai Sehrish school ya biya gidansu wani abokinshi,wanda tun suna secondry school suke tare,acan ya yini har bacci yayi awon gaba dashi asaman gadon mamarsu abokin nasu,saboda tsabar gatanci bama gadon abokin nashi ba,a ɗakin mamarsu yayi baccin,daga shiga su gaisa da ita,ya samu ta shiga cikin toilet,shi ne ya ɗan kishingida saman gadon ya shiga sharar bacci,wuraren ƙarfe daya ya farka ganin lokacin tashin su sehrish daga school ya kusa yi,nan yayi sallama da mutanen gidan,jiki na rawa ya shiga motarshi tare da barin gidan,  da gudu ya fisgi motar saboda ya ƙarasa gida da wuri,ba don komai ba sai don alkawarin da yayi ma sehrish na cewa in zaizo ɗaukarta daga school zai nuna mata wankan da zai ɗauka na shaddar shi,   yana ƙarasowa cikin gidan bayan yayi parking din motarshi,ya wuce cikin main palour ɗin,a lokacin duk sun fita yin sallar azhar da ake cikin kira,bedroom dinshi ya shige tare da rage kayan da ke jikinshi ya faɗa cikin toilet,shaf shaf yayi wanka cikin minti goma sha biyar,ya fito daga cikin toilet din,jikinshi sanye da bathrobe,    Gaban dressing mirror dinshi ya zauna,yadda kasan mace haka ya zauna yana gyara jikinshi,sai da yabi ko'ina na jikinshi ya shafe da mai,sannan ya shiga gyara sumar kanshi,bayan ya kammala ya miƙe tare da komawa wurin wardrobe,ya buɗe tare da ɗauko shaddar,a natse ya shiga zura kayan ajikinshi bayan yasa vest da short farare kal,rigar takai masa har guiwarshi,sai wandon,lokacin daya kammala sanya shaddar ajikinshi dawowa yayi tare da tsayawa gaban madubi yana kallon fuskarshi ta ciki ya Allah!shi kanshi sai da ya tsorata da irin kyan da yayi,kamar shiya zana kanshi don kyau,shaddar ba ƙaramin kyau tayi mashi ba,sae faman salƙi take ajikinshi kamar wani sabon ango,kyakkyawan murmushin nan nashi ya saki tare da cewa"junaid kenan yakamata ka zama namiji mana,ka cire duk wata fargaba yau ka tunkari sehrish gaba da gaba ka bayyana mata irin son da kake mata batare da jin shakkar komai ba,'   shiru ya danyi aranshi yana cewa"gaskiya ina jin fargaba fa,anya reesh zata amince da son da nake mata?in tace bata sona fa?tabbas zan iya rasa raina,amma zan jure yau dae na fahimtar da ita tsananin son da nike mata,'  Ƙarasa maganar yayi tare da ɗauko hula mahadin kayan wadda take tsadaddar gaske sai daukan ido take itama ash colour ya aza saman kanshi,hmmmm abun ba'a magana madarar kyau ba kaman da sumar kanshi ta dan fito daga baya.  Zura takalmanshi yayi masu kyau da tsadar gaske suma mahadin kayan,sannan ya koma gaban dressing mirror ɗin ya ɗauko turarenshi ya shiga feshe jikin shi dashi ko'ina saƙo da lungu,nan take ƙamshin ya gauraye ko'ina na ɗakin,  Key ɗin motar shi ya dauko sannan cikin sauri ya fito daga ɗakin nashi ya sauko downstairs,babu kowa a falon duk sun tafi salla,
A hankali yake driving din motarshi fuskar nan dauke da annuri,sae da yafara tsayawa masallaci yayi sallah,sannan ya miƙi hanyar makarantarsu sehrish,shiga ciki yayi tare da yin parking ɗin motar sannan ya fito ya tsaya tare da jingina bayanshi a jikin motar,zuba ido yayi yana jiran fitowar sehrish amma babu ita babu alamarta,ga students sai fitowa sukeyi,wasu na hawa bus wasu kuma ana zuwa ɗaukarsu,   Gajiya ya fara yi da tsayuwar, "Wai ina reesh ta shige ne,ta barni tsaye ina ta faman jiranta,'rai aɗan 6ace yayi maganar,   Juyawa yayi tare da kifa kanshi ajikin motar ya ɗan lumshe idanunshi,   adai dai lokacin Jahad ta fito hannunta ruƙe da school bag ɗinta,tana neman hossana duk atunaninta zata same tane a wurin da suke jiran osman yazo ɗaukarsu amma babu ita,da alama ma Osman ɗin bai ƙaraso ba,  guntun tsoki taja tare da juyawa zata koma ciki,karaf idonta suka sauka akan Junaid,cike da mamaki take kallonshi,tana ɗan leƙen fuskarshi daga inda take,
Bakomai ne ya faɗo mata aranta ba,face alƙawarin da tayi ma hosana nacewa zata nemo mata ya Omar,aranta tace"ya Omar yace ƙaninshi ne wannan,kodae naje na tambaye shi ina ya Omar yake,may be ya taimakamun wurin haɗa ni dashi,  ƙarasawa wurin motar junaid tayi ta ɗan tsaya daga bayanshi,tare da yi mashi gyaran murya don ya juyo,   jin shiru bai juyo ba yasa tayi mashi sallama"Assalamu Alaikum,"  Nan ma bai juyo ba,hannu tasa ta ɗan ta6a bayanshi a hankali,aikuwa a firgice ya juyo,ita kanta jahad sae da ta ɗan tsorata taja da baya ganin yarda ya juyo kamar ya tsorata,    Murmushi ta sakar mashi tare da cewa"am sorry,naga kamar ka razana,tun ɗazu nayi maka sallama baka ji ba,'   harara junaid ya watsa mata,har sae da tasha jinin jikinta,rai a6ace yace"yanzu abunda kikayi mun kin kyauta!kinsan tun yaushe nike atsaye nan ina jiranki!"   Gaba ɗaya jahad ta gama ruɗewa jin abunda Junaid ke cewa, Cikin sauri tace"dama...am..inaso ne na tambayeka game da yayan.......'  Kafin ta ƙarasa maganar tuni junaid ya gama hasala,ruƙo hannunta yayi tare da buɗe motar,yace mata wuce ki shiga,   Murya na rawa jahad tace"bangane me kake nufi ba?  A tsiwace yace"Ni ki wuce mu tafi,'  duk yarda jahad taso ta fahimtar da junaid cewar ba ita bace wadda yake nema ba,amma yaƙi fahimta,shi duk atunanin shi sehrish ce,  Tursasa mata yayi har sae da tashiga cikin motar,sannan ya shiga yaja motar da gudu ya fisgeta suka fuce daga cikin makarantar,
A natse yake driving lokacin daya hau saman shantalelen titin,zuba mashi ido jahad tayi tana kallonshi,ta wutsiyar idonshi yake kallonta,ganin yarda ta zuba mashi ido yasa shi ɗan juyowa tare da sakar mata wannan kyakkyawan murmushin nashi,  mamaki ne ya kama jahad,gaba ɗaya abun ya gama ɗaure mata kai,aranta tace kodae yana da ta6in hankali ne?in ba haka ba, nida bamu ta6a haɗuwa dashi ba amma kuma ya nuna ya sanni har ya tursasa mun na shiga motar shi,yanzu ni bansan ya zanyi na fahimtar dashi ba,kada hosana ta fito tayi ta nemana acikin school,   "Reesh banji kin yabi wankan nawa ba?ko banyi kyau bane,"yayi maganar a yayin da yake kokarin parking ɗin motar a gefen titi,sannan ya juyo yana kallonta,  zuru jahad tayi tana kallonshi,hakan ba ƙaramin 6ata mashi rae yai ba,cikin shagwa6a yace"Wai menene haka reesh,duk kin bi kin wani sauya mun,saboda ke fa na ɗau wankan nan don nazo na nuna maki,amma kin zuba min ido kina kallona kamar yau kika fara gani na,'  A tsorace take da shi,don tagama yarda cewa yana da ta6in hankali,cikin en ina tace"amm...ni fa...ba..' kasa ƙarasa maganar tayi gabanta na faɗuwa,ganin yarda junaid ya matso dab da ita,ya ƙureta gaba ɗaya ƙamshin turaren shi ya gama kashe mata jikinta,  murmushi ya ɗan sakar mata tare da cewa"kallon ya isa haka reesh,let's talk about serious issue,akwai abunda na jima inason sanar dake,amma inajin fargabar amsar da zan samu a wurinki,'ya ƙarasa maganar yana kallon cikin kwayar idanun jahad amatsayin sehrish,   a hankali jahad ke bin kyakkyawar fuskarshi da kallo,tun daga kan eye brows ɗinshi,dogon hancinshi da kuma red lips ɗinshi,komai nashi mai kyau ne kuma mai jan hankali,   Anatse yaci gaba da magana,"reesh,nasan cewa baki ɗauke ni cikakken namiji ba kamar saura,saboda na cika wasa da shiririta da kuma shagwa6a,kuma bani da aikin yi sae zama acikin gida kamar mace, nasan ba kowace mace bace zata so ta aure ni a haka" ya ɗan dakata da maganar yana kallonta,wannan karon babu alamar wasa a fuskarshi,
 natsuwa jahad tayi tana sauraran shi,   Hannayenshi yakai tare da ruƙo nata cikin nashi,nan take jahad taji gabanta ya faɗi,  ɗagowa yayi awani irin yanayi yaci gaba da magana"duk wannan abun da nake reesh zan daina in baki so,idan har kika amince mu kayi aure,xan zama kamar yarda kikeso,nidae burina ki amsa mun cewa kina sona,kuma zaki aure ni,ni ban ta6a son wata ƴa mace ba in bake ba,na shaƙu dake sosai kuma ina da tabbacin cewa in mukayi aure zaki bani kyakkyawar kulawa,pls reesh tell me will u marry me"?   Tamkar zai yi kuka haka yayi mganar yana jiran amsarta,  Shiru jahad ta ɗanyi tana yanke shawara da zuciyarta,tunda dae bai da cikakken hankali bari na jaraba biye mashi kona samu mu rabu lafiya Ƙarasa zancen zucin nata tayi tare da mayar da idanunta akan nashi tace"bana tunanin cewa akwai macen da zata samu namiji kamarka ta nuna bataso,kai na daban ne,kana da komai da mace zata buƙata a wurin namiji,kayi mun sosai kuma ka kwantamun araina,tayin soyayyar da kayimun na kar6a hannu bibbiyu,kuma na amince zan aure ka.....'   Tsantsar mamaki ne ya kama junaid bai ta6a tunanin cewa rishi zata amince da soyayyarshi ba,cikin sauƙi haka batare da ta wahalar dashi ba,ajiyar zuciya ya shiga saukewa wani irin farin cikine ya lullu6e shi,mara misaltuwa a hankali ya shiga furta"Alhamdulillalh Allah nagode maka daka nuna min wannan ranar,dama sae da raina ya bani cewa reeshi ɗina bazata gujeni ba...."  Fuskar jahad ɗauke da murmushi take kallonshi har lokacin hannunshi na ruƙe da nata,   farin cikin da tagani a fuskarshi yasa taji aranta dama dagaske ita yake so,da ta bashi kyakkyawar kulawa,amma da alama akwai wadda yake so,tunda taji ya ambaci sunan reesh wannan ne yasa jikinta yin sanyi,
"Allah yasa ba mafarki nake ba,in ma mafarki nake kada ki tashe ni,'yayi maganar yana dariya tare da zame hannun shi daga nata,ya tallabo fuskarta da tafin hannayenshi,yana ƙare mata kallo,hakanan ya dinga jin kamar ta canza mashi,ƙura mata ido yayi kamar mai son gano wani abu,  "Reesh kin canzamin sosae,sai nike ganin kamar bake ba,'   Shiru jahad tayi tana cigaba da kallonshi,sakin fuskarta yayi tare da zura hannunshi cikin hijab ɗin jikinta,ae kuwa a firgice jahad ta ƙanƙame jikinta dake ta faman kerma cike da tsoran abunda zaiyi mata,   Cikin lallausar suman kanta yakai hannunshi yana shafa gashin kanta yace"meyasa baki ɗaure gashin kanki ba?bai takura maki ahaka?   atsorace jahad tace"ni na cire shi,yana acikin school bag ɗina,"   Zame hannunshi yayi daga cikin hijab ɗin nata,  "Zan ɗaure maki shi,ki ɗauko ribbom ɗin naki,"  Kamar karta ɗauko mashi amma tunawa da cewar yana da ta6in hankali in ranshi ya 6aci zai iya kai mata bugu,hakan yasa ta janyo school bag ɗin tare da zuge zip ɗin,ta curo mashi ribbom din ta miƙa mashi sannan ta mayar da jakar abayanta,  kar6a yayi tare da zura shi a cikin hannunshi,sannan ya ƙara matsawa kusa da ita sosai,cire hijabin jikinta yayi sannan ya janyota asaman chest ɗinshi,gaba ɗaya jahad ta gama rikicewa,ba ƙaramin yanayi junaid ya jefa ta ba,  lamo tayi ajikinshi tana shaƙar daddaɗan ƙamshin turarenshi,  Xuba ma yalwataccen gashin nata ido yayi yana kallonshi,kafin daga bisa ni ya sanya hannunshi tare da tattaro shi wuri guda,ya ɗaure mata shi da ribbom ɗin,   muryarshi taji acikin kunnanta yana cewa"Reesh,ya akai naga launin gashin kanki ya canza?ba brown colour bane?yanzu kuma naga ya koma dark black,?kodai idona ne ke nuna min ba daedae ba'?shiru jahad tayi batace mashi komai ba,saboda bata da amsar da zata iya bashi,  jin tayi shiru yasa ya ƙyale maganar,hannu yasa tare da rabata da jikinshi,bin ta da kallo yayi ganin yarda take ta faman lumshe ido kamar mai jin bacci,  Cikin sanyin murya yace"Reesh,kina jin feelings ɗin da nake ji agame dake"?  buɗe ido jahad tayi sosai tana kallonshi da wata irin kasalalliyar murya tace"eh,'   jinjina kanshi yayi tare da cewa"nasani,dama nasan kema zakiji abunda nake ji,pls reesh just for today kawai,kiyimun kiss koda a gefen fuskata ne,inaso naji ya ake ji,'  Shiru jahad tayi tana tunanin ya zatayi da wannan ɗan tahalikin,gashi duk yabi ya kashe mata jikinta,ita tausayi ma yake bata saboda ta6in hankalin da yake fama dashi,tausayin shi ne taji ya kamata,mutun har mutun amma bai da cikakken hankali tunda inda yana da hankali ai ba yarda za'ai ya kasa gane ba itace wadda yake nufi ba,tunawa tayi da hosana dake fama da irin lalurarshi,amma nashi haukan yafi na hosana,don bata ta6a ganin wanda bata sani ba,ta liƙe mashi da sunan tasan shi,    bata ƙarasa zancen zucin nata ba,muryar shi ta kuma katseta da cewa"pls reesh,just for today,"   ajiyar zuciya jahad ta saki tare da kai bakinta zata manna mashi kiss acikin dimple ɗinshi,batayi wani aune ba taji bakinta acikin nashi tsulundum,sakamakon wata mota da ta bugi bayan motar shi,wannan girgizar da motar tashi tayi ne yasa bakinta komawa cikin nashi,gaba ɗaya junaid yabi ya rikice ya zauce ya haukace mata,sosai ya ƙankame ta ajikinshi,yana kissing ɗin bakinta ta hanyar zura tongue dinshi acikin bakin,ita kanta jahad a lokacin ta gaza control ɗin kanta,biye mashi tayi,
Sosai junaid ya shiga romancing ɗinta kamar zai zauce,duk yarda jahad taso ta kwace kanta a hannunshi amma yaƙi barinta,sai da yayi mai isarshi sannan ya zame jikinshi daga nata,cikin sauri jahad ta kifa kanta asaman laps dinta,tana faman sauke ajiyar zuciya,sam tagaza yarda cewa itace da kanta ta ba wani namiji damar kissing lips ɗinta abunda bata 6ata yi ba,to dama dae duk inda mace da namiji suka ke6e irin haka na ukkun su shaidan ne,Allah ya kyauta.
   jikinshi ne yayi sanyi,shi kanshi baisan cewa abun zai kaisu ga haka ba,daƙyar ya iya tashin motar da wata irin kasala ajikinshi yake driving din,ya hau saman titi sosae tare da wucewa dasu gida,   _💋Boss Bature💋_
tashin hankali!Lokacin da Hosana ta fito a nan ta samu osman yana jiransu tsaye a bakin motarshi,   ƙarasawa tayi wurinshi tana cewa"ya Osman Ina jahad ɗin?ina ta nemanta banganta ba,nayi tunanin ta rigani fitowa ne,"   "Wai kina nufin jahad bata acikin school ɗin naku"?ya tambaya hankali a tashe yana kallonta,. daga mashi kai tayi alamar eh tace"babu kowa acikin makarantar ya Osman,na duba ko'ina ban ganta ba,"  Gabansa ne ya faɗi rass,saboda kullum jahad ita ke riga hosana fitowa,yau kuma hosana ta rigata fitowa,tabbas akwai matsala,  cikin sauri yace"shiga ki zauna bari nashiga cikin classes din na duba ko zan same ta acan,Allah dae yasa ba wani mummunan abune ya faru da ita ba,'  Ya ƙarasa maganar tare da yin saurin shigewa cikin makarantar,buɗe motar hosana tayi tare da shigewa ciki ta zauna tana jiranshi,  lokacin da Osman ya shiga cikin classes din yana neman jahad,duk ajin daya duba babu kowa wayam duk sun tafi gida,ko'ina ya dinga bi na makarantar saƙo da lungu yana dubawa amma babu jahad babu alamarta,tun yana sa ran ganinta har ya fidda rae,yafi ƙarfin awa ɗaya da rabi acikin makarantar yana neman jahad amma bai ganta ba,
 Cikin sauri ya fito jiki na rawa ya koma cikin motar,ya zauna a mazaunin driver,  Ganin ya dawo shi kadae yasa hosana cewa"Ya osman ina jahad din?baka ganta ba"?   "Na duba ko'ina banganta ba,bansan ina jahad taje ba,bari na fara kaiki gida nasan kin gaji sosai,"   jan motar yayi tare da fucewa daga cikin gate ɗin makarantar,duk yabi ya ruɗe saboda fargabar kada ace wani abune ya faru da jahad,yana jiyo hosana tana shessheƙar kuka tana cewa"Nashiga uku,Allah yasa jahad bata 6ace ba,bansan ya zanyi ba in na rasata ba,kamar yarda na rasa sehrish,"    "Kada ki damu jahad tana cikin ƙoshin lafiya,zan nemo maki ita,in ma ban sameta ba,zan kira major na sanar dashi halin da ake ciki,nasan zaiyi ma marshal Magana,"ya ƙarasa maganar a lokacin da yake shiga kwanar gidan Abusufyan,
Yana shiga ciki ya sauke hosana,sannan ya fisgi motar da gudun gaske ya fuce daga gidan,
Abunda ya faru bayan fitar motar osman daga cikin school din,Sai ga sehrish hannunta ɗauke da school bag ɗinta,daƙyar take iya tafiya saboda ciwon da tasha,ta jima acikin toilet din tana juyi kafin Allah ya kawo mata sauƙi harta samu ta fito, ganin babu kowa acikin makarantar yasa taji gabanta ya fadi,nan tashiga fargabar Allah yasa junaid bai tafi ba,tasan dole ya gaji da jiranta, Lokacin da taƙarasa wurin gate din taga babu kowa sai security guard din dake tsaron makarantar,tamkar ta aza hannu akai ta fashe da ihu haka taji, Ganin yarinya tsaye cikin damuwa yasa mai gadin ya ƙaraso wurinta yana tambayar ko lafiya, muryarta tamkar za tayi kuka tace"Mai ɗaukata nake nema,kuma naga babu kowa acikin makarantar,bansan ya zanyi ba," mai gadin yace"meyasa baki fito kin tsaya anan waje ba?me kikeyi acikin makarantar ne"? cikin shessheƙar kuka tace"bani da lafiya ne,bacci ne ya ɗauke ni kuma babu wanda ya tashe ni,shiyasa bansamu na fito ba akan lokaci," "Kuma baki da waya a hannunki"?acewar mai gadin, ɗaga mashi kai tayi alamar eh, "Ko numbar wani baki ruƙe a cikin kanki ba," "Bani da numbar kowa,ban ruke akaina ba," Cike da takaici mai gadin yace"kaji matsalar,ni yanzu bansan ya zanyi dake ba,amma me zai hana ki ɗan fita daga wajen gate ɗin,wata'ƙil shi drivern naki ya dawo daukarki,nasan ma zai dawo ne,da zarar sunji shiru baki ƙarasa ba", Amsa mashi tayi da toh,sannan ta fice daga cikin makarantar ta tsaya a bakin gate din,tana ta ƴan waige waige ko zata hango motar junaid,
_💋Boss bature💋_
A hankali motar junaid ta ƙetare babban gate din gidan nasu,a lokacin jahad ta ɗago da kanta,ta cikin glass ɗin take hangen katafaren gidan,wani irin farin ciki ne ya lullu6eta,yau gata acikin gidansu ya Omar dinsu,koba komai zata hadu dashi harma ta sanar dashi halin da suke ciki na rashin ganin shi,addu'a tashiga yi acikin ranta Allah yasa Ya Omar na nan, tsayar da motar junaid yayi tare da buɗewa ya fito sannan ya zagaya ya buɗe ma Jahad motar,cikin sanyin murya yace"Reesh,am really sorry game da abunda ya faru a tsakanin mu,na fita hayyacina ne shiyasa,kinsan cewa ba halina bane.....kuma bazan ƙara ba insha Allah, Murmushi jahad ta sakar mashi ayayin da take fitowa daga cikin motar tace"just forget about it,komai ya wuce,na yarda dakai sosai nasan cewa bada son ranka hakan ta faru ba, ba ƙaramin daɗi junaid yaji ba,ya jima yana mamakin nasarar daya samu akan reeshi ɗinsa,farin ciki kamar ya zuba ruwa a ƙasa yasha, Bayan ya rufe motar ya ruƙo hannunta suka shige cikin gidan atare,a ruɗe jahad ke kallon katafaren gidan,jinjina kai kawai takeyi acikin ranta tana cewa"wai dama a wannan daular ya Omar ke rayuwa!gidan yayi mun kyau ya haɗu sosai,Allah yasa yana ciki,inaso na cika ma hosana alƙawarinta na ganin na haɗata da ya Omar dinta, Babu kowa acikin main palour ɗin,sakin hannunta junaid yayi tare da cewa"bari na shiga ciki na huta,da anjima zan shigo muyi magana," amsa mashi tayi da toh,cikin sauri junaid ya wuce bedroom din Abbansu, tashin hankali,jahad fa batasan ina zata dosa ba,gata dae acikin gidansu Omar,batasan a ina zata ganshi ba, Tsayawa tayi ƙiƙam batare da ta motsa ba, Gyaran muryar da taji ne yasa ta yin saurin juyawa don taga wanene, Azmee ce ta fito sai faman sakar mata murmushi takeyi,jikinta sanye da jallabiya,ta ɗaure kanta da mayafi,ta fito fess abunta, Gaban jahad ne ya shiga faduwa aranta tashiga tunanin cewa kodae wannan ce mahaifiyarsu?Amma meyasa naga tana sakar mun murmushi kamar tasanni itama...? Bata ƙarasa zancen zucin nata ba,azmee ta ƙaraso tare da janyota jikinta ta rungumeta tana cewa"Sannu da dawowa kyakkyawata,ya school din? Tayi maganar tare da raba jikinta daga na Jahad, Zuru jahad tayi duk tabi ta dabarbarce ta rasa ganema wannan abun al'ajabin,tamkar a mafarki haka take ganin wannan ikon Allah, "Rishi lafiya naga kina bina da kallo?kodae bakya jin daɗi ne?nayi magana baki amsa mun ba" Cikin en ina jahad tace"am...um...lafiya lou,makaranta Alhamdulillah,' Azmee tace"ko ke fa,shigo daga ciki na hada maki lunch ki ci,ko kya dawo daedae don na lura yau ba ƙaramar yunwa kika kwaso ba," Tayi maganar tare da ruƙo hannun jahad taja ta suka nufi dakin sehrish,da kanta ta buɗe mata kopa tare da shigar da ita ciki tace"ki zauna ki huta,yanzu zan haɗo maki lunch,"tana faɗin hakan ta rufe mata dakin, Abun ya gama ɗaure mata kai,juyawa tayi tana ƙarema bedroom ɗin kallo ba ƙaramin kyau yayi mata ba,daga bisani kuma ta shiga damuwa akan wane hali hosana ke ciki,tasan cewa zasu nemeta sosai,kuma in basu ganta ba hankalinsu bazai ta6a kwanciya ba, komawa tayi daga gefen gadon sehrish ta ɗan zauna,ya zama dole in koma gida,kada hosana tayi ta kukan rashina akusa da ita,bansani ba ko zan samu ya omar acikin gidan nan ba,ni ba komai yafi ɗauremun kai ba face yarda suke nuna kamar sun sanni,bayan bamu ta6a haduwa da kowannansu ba,to kodae dukkansu suna da mental illness ne?ta jefa ma kanta tambaya,
Turo kopar azmee tayi tare da shigowa hannunta ɗauke da tray wanda ta shirya mata lunch,ƙarasawa tayi tare da ajiye mata tray din asaman bedside drawer dinta tace"Wannan farfesun da kike gani,hajiya azeema na shirya mashi,ƙanwar abbanku da nake gaya maki,tana nan ta iso,nasan bakisanta ba,amma kin ta6a ganinta lokacin da Sgr da Omar suka dawo daga U.S kin tuna"? Fuskarta ɗauke da murmushi takeyi mata maganar, Jin ta ambaci sunan Omar yasa jahad cewa"Ya Omar na nan"? Azmee tace"eh,yana acikin part dinshi,amma meyasa kika tambaye shi?maimakon ki tambayeni mutumin ki Sgr"? "Babu komai,kawai inason ganin shi ne,"ta bata amsa, Azmee tace"ki bari idan kin kammala shan farfesun sae kije ki same shi adakin shi,' gyaɗa kai jahad tayi tare da cewa toh,nagode sosai,bari na fara sha, Juyawa azmee tayi tare dayi mata sallama ta fuce daga dakin,a ranta tana tunanin ko wani abu ke damun rishin ne taga duk tayi sukuku.
Zama jahad tayi tare da dauko plate ɗin dake ɗauke da farfesun,sae uban ƙamshi ke tashi,duk da tana cikin tashin hankali hakan bai hanata shan farfesun nan ba,sae da taci ta ƙoshi, sannan ta miƙe tare da shiga toilet ta wanko hannayenta, Bayan ta fito komawa tayi saman gadon ta zauna cike da zullumin mai zai biyo baya,
_💋Boss Bature💋_
Marshal Omar na kwance saman gadonshi yayin da idanunshi suke kallon saman ceiling bakomai yake tunani ba face hosanar shi,kowane hali take ciki yanzu?taci abinci kuwa?tambayoyi iri iri ya shiga yi ma kanshi, yana cikin wannan tunanin wayarshi dake ajiye gefenshi ta shiga yin ringing,miƙa hannu yayi tare da daukar wayar,duba mai kiran nashi yayi ganin sunan Major ya bayyana akan screen din wayar yasa shi saurin ɗaga wayar tare da karata akan kunnanshi, Ko sallama major baiyi mashi ba saboda tsabar tashin hankalin da yake ci, "Y